A d u n i y a ta complt by huguma - Chapter 6
A d u n i y a ta complt by huguma Chapter 6: A d u n i y a ta complt by huguma Chapter 6. *_TURAREN WUTAR DA KUJERUNKI ZASU KAMA QAMSHI DARAM?_*
4,477 words
*_TURAREN WUTAR DA KUJERUNKI ZASU KAMA QAMSHI DARAM?_*
*_KI BANKADA LABULAYENKI KIJI SASSANYAN QAMSHI?_*
*QAMSHI IYA QAMSHI 24HR*
*HUMRA ME TSAYAWA A ZUCIYAR ME GIDA*
*NASAN ZAKI TAMBAYI KANKI A INA ZAN SAMU WANNAN?*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER*
*_tayi muku tanadin abubuwa da yawa irinsu_*
Khumra Turaren wuta Kulaccam Lablab Oil perfumes Original musk tahara Multipurpose spray
*karki kuskura kada kiyi ganganci ayi babu ke,kai tsaye tuntubeta ta wannan number*
08032119803
Ko ki lalubeta ta nan๐๐พ๐๐พ๐๐พ
*Instagram handle_incense by kabo daughter*
*Facebook_kabo daughter*
*Twitter_kabo daughter* *D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
*Arewabooks:Huguma* PAGE 16 ___________________________
*_CIKIN DUBU DABAN TAKE_*
*_TABBAS AKWAI TURARE AKWAI MUNA TURARE_*
*_NA GWADA NA GANI_*
*_YA SUBHANALLAHI_*
*_QAMSHI NA TASHIN KAN ME GIDA_*
*_QAMSHIN DAKE DAGAWA KISHIYA HANKALI_*
*_NATACCEN QAMSHI DAKE KAMA GURI DARAM_*
*_WANNE GANGANCI NE YA SAKAKI TSAIWA SANYA?_*
*_ME KIKE JIRA?_*
*WANNAN DIN GUARANTEE NE FA*
*TASTED AND TRUSTED 100% PERCENT*
*KI SIYA KI GODEMIN HAJIYA*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER*
*_DUNIYAR TURARE ME BADA ASALIN QAMSHI ME KAMA JIKI DA MUHALLI,NUTSATSEN QAMSHI ME SANYAYA ZUCIYA DA DADEWA A WAJE_*
*_IDAN KINA DA MATSALA KINA NEMAN TURARE ME KAMA WAJE,KINASON SAKEWA OGA SABON QAMSHIN DAKI DA PARLOR,KE KANKI KINASO KI SHIGA WAJE A DINGA TAMBAYAR WACE TA ISO NE?_*
*MAZA MAZA JEKI KI GWADA WANNAN_*
*INCENSE BY KABO DAUGHTER 08032119803*
*_zaki dariya za kuma ki godemin_*
*_gani ya kori ji_*
*hakanan sai an gwada akan san na qwarai* _________________________
Idanunshi a kanta sanda yake shigowa zuwa cikin ainihin falon da yake da banbamci da sauran faluka dake gidan. Itama shi take kalla,kaman yadda suma bambanta a kamanni da mahaifinta haka suka bambanta a halaye da kuma dabi'u.
"Kai....kai,ubanka.....cireshi daga bakinka......tashi!" Matar dake biye dashi a baya ta furta a zabure bayan shigowarta dakin,idanunta kuma suka fada akansa sanda yake cin Chip's din hankalinsa kwance. Debe idanunta tayi daga kansu ta maida kan yaron da ya tsorata sosai saboda yasan halinta,ba shiri ya miqe tsaye har farantin chips din dake saman cinyarsa ya fadi,tsirarun dankalin ciki da yayi saura ya tarwatse a wajen.
Gewayesu yayi da gudu gudu zai fice yana matsawa daga wajenta amma duk da haka bai tsira ba,bayan uwar harara da take narka masa sai data bishi da ranqwashi tana cewa
"Bansan inda ka dauko kwadayi ba don ubanka,saidai daga can bangaren uban naka,don mu nan ba makwadaita bane,masu kwadayin ma addu'ar shiriya muke musu.....ba zaka jazamin masifa ba......cin abincin da aka da kudin haram?,ina zamana lafiya?,to muddin zaka ci gaba da shigowa dakin nan kuwa sawuna a likkafa zan maidaka gidan naka uban" Tayi maganar tana daga tsaye tana kallon qofar da tuni ya riga ya fice daga ita.
Dauke dubanta tayi daga kanta,don gugar zana irin wannan tash ba kasafai ta fiya damunta ba. Idan d sabo ta jima da sabawa da ita din,ta kuma zame mata jinin jiki.
"Ni zan fara gaidaki ko kece zaki fara gaidani?" Muryarsa ta dawo da hankalinta daga duniyar tunanin data fara nausawa. Fararen idanunta ta aza a kansa,mutumin dake a mazaunin mahaifi a gareta.....wanda ya kamata a ce a yanxun basu da tamkarshi,koda baiyi ya mahaifin nasu ba.....amma ya zamana ya toshe wani babban kaso cikin gibi da rayuwarsu zata samu.
Qaramin bakinta ta motsa wanda sauri yakan kira da shegen bakin rashin d'a da rashin mutunci,da wannan muryartata da sautinta ke cike da sanyi da nutsuwa tace
"Ina kwana kawu?"
"Lafiya qalau na kwana,sai uban baqinciki da takaicinki dake shirin hallakarmin da rayuwa" Ya furta cikin hargagi tamkar dama yana jiran ta gaidashinne.
Har yantsu dogon yatsanta yana saman labbanta,yayin data kafe mutumin data kira a dazu da kawun nata da idanunta,tana dan motsa yatsan nata saman lebenta tana kuma nazarin fuskarsa furucinsa dama motsinsa.
Ko sau daya bata taba ganin mutunci kima da martabarsa ba......daidai da misqala zarratin bata taba daukarshi da wani babban matsayi ba......abu daya ta sani,komai lalacewar fura tafi kashin shanu......komai kashinsa da zabgewa gami da lalacewar martabarsa a idanunta sunanshi kawunta kuma qani ga mahaifinta.
Maida idanunta tayi ta lumshe kawai kaman yadda ta saba masa a yawancin lokuta......tasan me ya sanyashi wannan zuwan,wani boyayyen buqatarsa ne dake a qasan rai da bai samu biyanta ba. Ta tuna haduwarsu ta qarshe dashi a wancan satin daya wuce. Dama ta sani ba zai haqura ba.....shine zai fake da wasu abubuwa wanda shi kansa ba kubuta yayi daga su ba.....yazo ya samu wannan matar da qiyayyarsu ta jima da yin tsiro da jijiyoyi a cikin jikinta. Takai qarshen maganar sanda take bude idanunta saman fuskar bibo.
Haduwa idanunsu sukayi waje daya da nata,ta juya qwayar idanunta tana watsa mata wani kallo
"Ki dain kallona da wadannan tsayyayun idanun naki na rashin kunya masu kama da idanun mage.......kai ya kamata ka tsaya a kanta saboda tana jawowa bawan Allah zagi,wanda ya jima da mantawa ya zauna a duniyar.....amma ina kyautata zaton kullum ta Allah sai mala'iku sun tadashi zaune sun nuna masa qazantar da d'iyar cikinsa ke aikatawa. Ya rasu yabar yara sama da goma sha takwas amma ba wadda ke hana masa kwanciya lafiya a kabarinsa sai ke?,ai wallahi Allah wadai da haihuwar d'iyoyi irinki.....indai haka haihuwar take gwara mutum ya zauna a haka" Tana maganar tana jujjuya hannunta guda daya gami da yarfeshi,idanunta a kafe saman fuskarta,kaman yadda itama tunda ta fara maganar ko sau daya bata dauke dubanta daga kan bibo ba.
Maganganun nata sunkai mata iyaka,tana jin ta gama daukar iya abinda zata dauka a iya wunin yau,saboda haka a nutse ta sauke qafafunta qasa ta miqa hannunta ta dauki handbag dinta ta miqe tsaye tana gyara rolling din mayafinta
"Fita zanyi,kuma ina da buqatar na kulle mana dakin kafin na fitan,idan ba damuwa ko zamu koma tsakar gida mu qarasa maganar a can?"
"Kaji ko?......dama ai na sani,babu wani sauran wanda take gani da kima a duniya.......yau koda fadima zata dawo duniya bata isa ta juyata ba bare alhaji" Tayi saurin cafe zancan.
Wani irin juyowa tayi gareta ta zube mata manyan fararen idanunta
"Kaman bakiji me nace ba ko?,nace muje tsakar gida mu qarasa......bankai ga furta cewa banda lokacin sauraro ba" Ta mata maganar dalla dalla tana kallonta.
Sosai bibo ta kafeta da kallo,har yanzu babu abinda zai sauyata......wannan rashin shakkar da rashin tsoron suna nan rubuce baro baro cikin ayyukanta da dukka motsinta,dakiyarta da shariyarta da daukan abu me zafi ta wulwulashi ta sauya masa mizani idan taso.
"Idan ta fito kawu qofar kawai zakaja jam lock din zai shige,ka sameni a qofar gida muddin baka wuce minti biyar ba" Tayi furucin sanda take takawa zata fice a falon tana riqe da vail din abayarta daya zame tana qoqarin mayar da rolling dinta yadda yake.
"Tashi muje na sameta a waje din inji da wacce hujjar zata kare kanta kuma" Ya furta dukka jikinsa na nuna zumudi da qaguwar yaga ya bita.
Da kallo bibo ta bishi tana daga zaune a kujerar ba tare data motsa ba baqinciki yana kasheta. A yau tana jin kaman ta tashi ta rufe rufa'i da duka. Yau ya tabbata mara amfani kwata kwata a garesu gaba daya.
"Ko nayi gaba kya rufe musu dakin?" A zafafe ta miqe tana gyara daurin dankwalinta
"In zauna inyi me a nan?,Allah ya sawwaqe,ai ni tawa son zuciyar bai fara sauka har takan kayan haramun ba" Ya jita sarai,ya kuma san da biyu take maganar,saidai a yanzu baya jin yana da lokacinta,dukka tunaninsa yana ta'allaqe akan sabreen. Yasan halinta sarai,muddin ya haura mintunan data dibar masa,yayi imanin da gaske zai iya zuwa ya tarar ta wuce din abinta.
Tana rungume da hannayenta sanda take tsaye a qofar gidan nasu ta bashi baya. Fuskar nan dake shimfide da wani irin kwarjini yau din cakude take da ninkin rashin fara'a da walwala na tun asali da aka santa dashi. Har tsakiyar zuciyarta takejin wani abu yana tsikarinta duk da yadda iskar dake yawo sararin subhana ke kada doguwar riga da dan mayafin saman kanta tana watsa daddadan qamshin turaren dake tashi a jikinta. Turaren da ita kanta yake sanya mata nutsuwa da kwanciyar hankali,dadinsa ya sanya ta zabeshi a matsayin turarenta na dindindin,duk da batayi tunani matsayinta zaikai a nan kusa ta mallakeshi ba.
Ta kalli agogon hannunta,yaci mintuna hudu cikin minti biyar din data bashi,don haka ta fara takawa sannu a hankali tana matsawa daga gaban gidan nasu.
Tun batayi nisa ba ta jiyo taku da kuma muryar kawun nata,bata da buqatar kallon fuskarsa ko doguwar magana ta hadasu,buqata gareshi zata sallameshi.....kamar yadda tun tale tale.....kaman yadda tun can baya bashi da amfani a garesu a yanzun ma bata tunani akwai wani sauran amfani da yake dashi a rayuwarsu,don haka ta sabule jakarta,ta zuge ta zaro wani abu daga cikin kudin da yayi saura a ciki ta dunqule a hannunta tana jiran isowarsa
"Ke sabreena......sabreen" Ya hada da qwala mata kira tamkar ya bata bashin kudi tana kuma shirin gudar masa dashi. Ranta ya sake baci,ta tsani kwakwazo,a banza ma idanun 'yan unguwar da dukka kunnuwansu harma da hankulansu suna kanta,kowanne motsi ko taku nata a biye suke dashi,sauraro suke.....jira sukeyi na samuwar dukkan wata dama da zasu samu abun magana a kanta. Wannan ya sanya tadan saurara daga tafiyar da takeyi tana dakon isowarsa. Ko a sannan tana iya ganin idanun tsirarun mutanen unguwar da suka samu sararin fitowa da safen kamar ita yana karakaina a kanta.
Irin wannan kallon nasu gareta ya zama tamkar jarrabi ko masifa cikin rayuwarsu. Akwai abubuwa da yawa tasan da akeson gaya mata amma babu wannan fuskar. Bataga dalilin zallar rashin adalci irin nasu da suke gwada mata ba suke kuma gwadawa rayuwarta ba. Sun sany hannu dukka da qafafunsu sun tankwabeta sun kuma tankwabe rayuwarta a sanda take da tsananin buqatarsu......a yanzu kuma data yankema kanta bata da buqarsu.....a sannan su kuma suke qoqarin dawo da ita su dankwafar da ita.....suka kuma fidda makamansu da harsunansu wajen illata mata gangar jiki da zuciya.
"Me na samu?" Ya iso gareta yana tambaya sanda motar da take da tabbacin waye a ciki ke dab da isowa inda take. Kowanne mutun da zatayi mu'amala dashi ko kuma tayi mu'amala dashi din......sau daya tak take masa wani karatu a taqaitaccen lokaci.......fahimtar waye kai?......meye qudurinka.......meye motsinka?.....mene manufarka......da sauran dukkan wani abu daya shafi rayuwarka yana zama RUBUTACCE cikin shafin qwaqwalwarta. Bata fiya manta abu ba,haka bata missing target saidai idan bata nufaci abu ba.
Ta baya ta miqa masa kudin sannan ta fara takawa zuwa ga motar da tuni ta iso inda suke harma ta samu wajen tsaiwa. *D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
PAGE 17
daga inda yake a zaune din yakejin kamar gilashin window din motar ya masa shamaki daga kallonta duk da yadda yake tarwai yake kuma iya baka daman gano komai dake ta wajen motar......duk da haka yana jin kamar ya rage ma idanunsa armashin kallonta,don haka ya kasa haqurin isowartata,ya sanya hannu ya sauke dukka gilashin nasa qasa.
sau daya tak ta taba ganinsa ido da ido,amma ta haddaceshi tsaf,tun daga abun hawansa har zuwa halayya da kamanninsa.......
Kakkaura kuma faffada da zaka iya kiransa me jiki saidai bai cancan ba. Maabocin iya ado sosai da murza hula ta zauna a kansa kamar shi yake saqa ma kansa ita. Yadda turarensa da shigarsa keda kyau da tsari haka ma kalaman bakinsa,saidai kash!.....daidai da wucewar daqiqa guda bata taba jin wani abu me kama da SO K'AUNA KO BEGE nashi ya tsartu a ranta ba.
Waishin mcikina meye SOYAYYA ne?. Ita kanta jerin kalmar SOYAYYA da yadda mutanen duniya suka daukaketa na daya daga cikin abinda ke sanyata dariya koda bata shiryawa hakan ba. SHIRME shine cikakkiyar ma'anar da take ganin yafi dacewa da a kirata ko kuma CUTA,idan akwai sunan da yafi haka lalacewa ma a nata ganin daidai ne a kirata da wannan sunan.
Yadda yake tsareta da kallo ya sanya qirjinta ya dinga suya duk kuwa da cewa ta saba da irin wannan shegen kallon. Kwarjininta na daya daga cikin abinda ya sanya take tsira daga guba da dafin MAZA duk kuwa da cewa ita da kanta take tsalle ta afka tsakiyar tarkon bisa tsananin lissafinta,ta kuma samu sa'a da nasarar zame kanta cikin SALO da kuma qwarewar iya wasa.
Da hanzarinsa ya fito ya zagaya don bude mata qofar motar,hakan ya bawa kawu dake lafe yana kallon komai qare masa kallo.
"Iya shaddar jikin yaronnan kawai ta isheni jari wallahi,wannan tsinanniyar yarina,yanzu meye aibun wannan da ba za'a aureshi ba?" Ya tambayi kansa da kansa yana naniqe da kudin hannunsa.
Idanunsa ya aza a kanta bayan ya bude mata motar,sai ya sakar mata murmushi,tadan lumshe ido tana qaqalo nata murmushin cikin dauriya da son maida masa. Gefe guda zuciyarta na cike fal da qarin wani mamakin akan D'A NAMIJI. ta tuna kalamansa akan matarsa dazun dazun nan,amma a yanzun gashi a gabanta ita kamar zai narke. Ta yaya zata yadda tayi aure a duniya?,ta yaya zata bari zuciyarta ta kamu da soyayyar wani namiji?,yaya za'ayi ta banzatar da lafiyar zuciyarta cikin soyayyar wani?,soyayyar halittar da babu tausayi ko jin qai a tare dasu?,halitta mafi son kai cikin halittun duniya gaba daya?,halitta me tsananin mugunta da son cutar da halittar mace 'yaruwarta?.
Ba zata iya sadaukar masa da murmushinta na dogon lokaci ba,duk kuwa da cewa fake smile ne,don haka ta zame jiki ta shige cikin motar ya mayar ya kulle yana sauke ajiyar zuciya. Yana jin duk duniya ba wanda ya kaishi sa'a a yau din. Yana jin kamar duka ranar tashi ce.
A kujeran driver ya zauna yana qoqarin tayar da motar amma duka ido da hankalinsa yana kanta
"Ina muka nufa my life?"
"My life?" Ta sake jaddada maganar a ranta
"Ko ina ya baro matarsa ta sunna da har ita ya danqara mata wannan sunan?" Wannan ba baqon abu bane a wajenta,saidai har yanzun mamaki da lamarin maza bai gama sakinta ba.
"SAMHG store" Ta amsa masa a nutse tana gyara agogon hannunta daya goce
"An gama ranki ya dade" Ya fadi cikin zumudi yana tayar da motar.
Sun jima akan hanya yana tauna abinda zaice da ita,don a taqaitaccen saninsa da ita.....mutum ce me matuqar tsari,nutsuwa da aje komai a bisa gurbi da muhallinsa. Bayaso ya kwafsa kaman waccan karon,bayaso damarsa ta sake kubce masa,duk da cewa har kawo yanzun baisan me ya aikata daya rasa wancan damar a wancan karon ba.
Yaji babu dadi ainun saboda ya qwallafa rai sosai a kanta. Ta yiwa zuciyarsa wani mahaukaci kamu a ganin farko. Yayi tsammanin kudinsa da ajin mataki na rayuwa zai saya masa ita cikin qanqanin lokaci,sanin da ya yiwa 'yammata kenan a yanzun,ballantana ita dake da kyau da aji irin wannan.
Sanda yake wannan tunanin nata nazarin da karatunsa duka a kansa yake. Yadda yaketa rejecting kiran dake fama shigowa wayarsa a jejjere. Duk kiran da zai shigo sai ya katseshi. Tuni hankali da kuma jikinta ya bata wanda ke kira.
Idanunta tadan lumshe,koda yaushe su dinne dai,cikin wahala,qasqanci,tozarta da kuma wulaqanta zaune cikin gidajen aure. Ko meye kuma zai fito yaje yazo su din yake afkawa.
"Zan iya cewa wani abu?" Ya tambaya a ladabce yana murza steering motar cikin qwarewa
"Kafin sannan ya kamata ka daga wannan kiran ko?" Ta fada idonta akan fuskarsa.
Motsawa kadan yayi yana duban wayar ta qasa idanu,bai zaci ma ta lura da hakan ba. Haushi ya soma kamashi akan kiran da take masan babu qaqqautawa. Yasan zancan gizo baya wuce na qoqi,tunda bai jima da fita a gidan ba,yasan kuma abinda ya fito ya baro a gidan
"Tarin damuwa ce da matsaloli kawai take dauke dashi" Ya furta yana jan siririn tsaki.
Har tsakiyar ranta taji saukar maganar,ta lumshe ido kadan tana budesu. Yana nan din a haka,yana nan yadda ta karanta. Tayi qoqarin tureshi daga shiga layikanta,tayi qoqarin hanashi shiga cikin tarkonta don baya cikin irin mazan data zana bisa layi da gurbin rayuwarta,taso ta barshi ya samu me hukuntashi a gaba.....amma tunda har ya sake dawowa cikin rayuwartata cike da karsashi da zumudi,to tayi imani hukuntashi yana cikin qaddararta ne. Ba kuma zata qyaleshi ba,a wannan karon saita hukuntashin yadda ta saba hukunta maza irinsa. Maza irinsa basa tsira daga tarkonta......basa tsira daga kamunta,hakanan basa tsira daga hukuncinta.
Cikin salo na dabarar da yake gani kaman ba zata gane ba ya latse wayar,ya kuma jefo mata maganar da tafi damunsa
"Hanan.......wannan karon bazan bari ki kufcemin ba"
"Nima bazan bari ka tafi ba" Ta furta,a bakinta bisa mizanin ma'ana qwaya daya tak da hankali zai iya fahimta,amma kuma an aje ajjiyayyar ma'anar da ake nufi da maganar can qasan zukata.
Wani irin dadin daya sabbaba masa lafiyayyen murmushi ya ziyarceshi. Bai taba kawowa ko kusa a ransa samun wannan gwaggwabar nasarar a kurkusa haka ba,amma kuma,sai wani sashe na zuciyarsa ke gaya masa
"Duk kyau ko matsayinta zata sauko......a yanzun fa mata ke neman mazan aure idanu rufe" Hudubar data shiga kunnensa kenan,kuma ya yarda da hakan dari bisa dari.
"Amma hanan banga alama ba......bansa inane mazaunin da kike rayuwa ba,gida unguwa da sauransu"
"Gaggawar me kakeyi?,kada ka samu damuwa" Ta amsa masa tana jin ya ginsheta gaba daya,tana jin ta damu qarshen zamansu yazo,ta qagu su isa SAMHG store ya ajeta ya bata sarari.
A hankali ya kutsa motar babbar harabar kantin saida dukkanin kayan buqatar rayuwa,wanda zaifi kyau ka kirashi da kasuwa a sauqaqe amma kuma a zamanance. Ba abinda basu hada ba na kayan buqatu,tun daga tufafi zuwa kayan masarufi. Wajen nada matuqar girman da idan ka kirashi da duniyar siye da siyarwa. Girmansa ya sanya yake da mashigu daban daban da kuma guraren fita mabanbanta.
Cikin tafkekiyar harabar wajen ya aje motarsa,ya kasheta cikin mutuwar jiki da kasala yana waiwayowa inda take zaune tana qoqarin rataya jakarta gami da daukar wayarta ta riqe wadda ke aje saman cinyarta.
"Idan ban damuwa zan dan tayaki tattaki zuwa ciki......don naga wajen kamar cike yake da maza da yawa......ni kuma ina kishin na barki ki fita ke daya a kallemin ke" Ya furta cikin kulawa da wani irin narkakken so dake ragargazar zuciyarsa.
Da wani sassanyan kallo ta jefeshi,qawataccen murmushin nan dake qawata fuskarta da kuma labbanta ta sakar masa. Ta rausayar da kanta gefe tana juya idanunta. So take ta sallameshi a iya haka,bata buqatar doguwar damuwa. A lokaci irin wannan da takai qarshen mission dinta,ko fita unguwa ba kasafai take damunta ba sai idan buqatar haka ta taso. To amma hakanan taji akwai buqatar ta fita din,akwai kuma buqatar ta fita tayi musu siyayya.
"Baka da damuwa akan duka wannan......wannan hanan din ba komai idanunta ke kalla ba ballantana su burgeta" Ta bashi amsa a nutse.
Murmushi ya saki yana qara narkewa a sonta,yana ji cewa zai iya yin komai don ya mallaketa,yana jin cewa muddin ya sake barinta ta subuce masa a wannan karon ya tafka babbar asarar da bazai iya maida madadinta ba,baya jin ma zai bari hakan ya faru dashi sam sam.....kai koda tuna hakan na iya faruwar bayason yayi.
"Na ga zahiri......na kuma tabbatar wannan halittar ta daban ce......gamu cikin neman sa'ar kasancewa da ita" Ya fada yana lumshe idanu. Kai ta kawar amma tana murmushin yaqe. Ya numfasa bayan ya gama qare mata kallo cikin shauqi ya dauki wayarsa dake aje tun sanda ya maidata silent ya bude.
Tarin miscall a qalla guda goma kyawawa daga gareta. Ya jawo maballin sama ya sharesu yana sakin tsaki can qasan ranshi tare da wucewa mobile app na banking da yake ajiyar kudadensa.
Sosai ta jingina da makarin motar idanunta a lumshe sosai,sai kayi tsammanin bacci ko kuma gajiya ne sukayi mata yawa,saidai a cikin biyun duka babu ko daya a ciki.
"A taimaka a karantomin account number na dan bada wani tukuici" Idanunta ta janye daga saman wayar nasa,saita tashi ta zauna sosai tana dan sakin murmushi
"No need" Ta amsa masa a yangance kaman yadda ta saba magana
"Please.......ba wani abu bane me yawa.....just tukucin bani damar ganinki da kikayi a yau ne" Bata sake ce masa komai ba,sai ta zura hannunta cikin jakarta,wani dan siririn card me ruwan zaibar gold ta ciro ta aje a gefansa. Ta dauke kai tana qoqarin bude murfin motar wanda ita kanta tasan ba zata budu ta sauqi ko dadin rai ba......ta kwana da sanin meta aiwatar mata.
Cikin qasa da minti daya taji ya furzar da iska daga bakinsa gami da cewa
"Done.....ina fata zakiyi appreciating"
"Why not?,godiya me kima......godiya nake qwarai......but motarka tana nema ta riqeni fa"
"Da zatayi hakan data taimakeni ai" Ya amsata yana sake lafewa jikin kujerar. Kyawawan sexy eyes dinta ta waro waje kadan,sai kuma ta daga hannunta tana duban agogo
"Akwai alqawari da nayi,bana so kuma na saba......idan ka sani na saba kuma......next time kafin na baka daman sake haduwa dani....." Katseta yayi yana dariya ta hanyar hada hannayensa biyu waje daya sannan ya saukesu ya juya yana buda side dinsa
"Lemme check meye ya riqemin amaryata haka".
Da lumsassun idanunta ta bishi da kallo har zuwa sanda yake zagayawa gaban motar zuwa daya side din da take zaune. Yayi dukan dabarunsa amma hakan baiba,don haka ya zagayo yana fadin
" Bansan me yake faruwa,lafiya lau qofar yake,bari nasa a duban.....am really sorry" Ya sake apologizing yana hade hannuwansa.
taka Kai kawai ta daga masa tana irgen lokutan cikar target dinta. Cikin saa kuwa ya juya ya fara takawa yana barin wajen,wanda hakan ya bata damar janye kallonta sannu a hankali daga kansa,ta kuma maida saman wayarsa dake ajiye a wajen tana bada haske,tabbacin yunqurin hanata komawa key yayi daidai kenan,saita katse kiran da takeyi daga tata wayar zuwa tasa don sanya wayar awake.
A nutse ta jawo wayar ta wuce zuwa ga maballin kira.
Tarin miscall dinne kuwa ta samu kamar yadda tayi zato,dukka kuma daga number dake ajiye cikin wayar da sunan MOM SUHAIL.
"SUHAIL" Ta ambata a fili,idan har bawai ta manta ba suhail din shine sunan first born dinsa kamar yadda T.j ya tabbatar mata.
Wani irin tausayin matar da batasan ko wacece ba ya fara ratsa ta. Tana shirin karkata akalar binciken nata zuwa wani sashe na daban saqon SMS ya shigo wayar.
MOM SUHAIL kamar yadda yake a rubuce ta bangaren kira. Bata tsaya dogon jinkiri ba ta bude,gajeran saqo ne kamar haka. *D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
PAGE 18
_Nayita kiranka baka dauka ba,kome meye mukayi da kai kafin ka baro gida ai ya kamata ka tsaya kaji dalilin kiran da nake maka babu qaqqautawa,bayan ka fito ciwon suhail ya tashi,a yanxu haka muna asibiti,amma babu ko sisi a hannuna,baka barmin komai ba,already kuma account dina yana buqatar naje banki na gyara bare nayi hidimata da kudina yadda na saba_.
Wani abu me tauri taji ya tsaye mata a wuya,ta zura hannu a jakarta ta ciro wayarta,tanason taga nawa ita ya kashe mata?,nawa ya saka mata alhali ko sisi matarsa bata amfana dashi ba?.
Naira dubu dari ta tarar. Wani matsiyacin tsaki ta saki,cikin dukkan arziqinsa ya rasa da meye zaiyi mata kyauta sai naira dubu dari?. Bata tsaya batawa kanta lokaci ba ta sauka ta koma mobile app dinsa da bai jima da fita a kai ba.
Daga password har username dinsa fes cikin kanta,tamkar hadaka ko gamayya sukayi dashi wajen creating dinsu a sanda zai bude manhajar. Cikin qasa da second goma komai ya bude,tarin miliyoyin kudaden dake kwance cikin account din nasa suka bayyanarwa idanunta,sai ta koms ta jingina da kujerar motar tana kallonsu,kamar ma bata tsoro ko shakkar dawowarsa.
Numfashi take fitarwa d'ai d'ai qirijinta na sake quntata. Tarin zallar rashin imanin maza yana sake tabbatar da kansa a zuciyarta.
"Yana da wannan kudin ya fita yabar matarsa babu ko sisi?,yana da irin wadannan kudaden yabar yaronsa cikin halin ciwo?,yana da wannan kudin ya gaza siya masa abun hawan da idan lalura irin wannan ta taso baya kusa zata kaisu zuwa ga asibiti cikin gaggawa?.
Tsanar MAZA tsanar SOYAYYA da kuma tsanar AURE suka sake linkuwa cikin ranta. Irin wannan shaidojin na gani da ido ta din saidai ta bada labarinsu. Shi din ma ba komai bane a cikin maza......bata kuma san namiji na nawa bane shi din da a yau xai shiga makarantarta.......a yau zata sanyashi ya koyi darasi kaman sauran,saidai nasa darasin yazo ne a gaggauce saboda gamawa da babinsa da tayi,da kuma dadewa da tayi da sanin shi din wayeshi?.
Beneficiaries dinsa ta duba,cikin sa'a tun batayi nisa ba taci karo da sunan da yayi daidai da sunan matar *ameena mu'azzam*.
Kai tsaye ta saka amount din da yayi mata ta kuma karkatasu zuwa ga account din.
Daidai lokacin data hangi tahowarsa,ta daga hannunta ta zare wania abu daga jikin qofar,sannan ta maida hankalinta kan wayar kamar ba me wayar ne yake dosota ba.
Hankali kwance ta koma ta goge alert massage din da kamfanin sadarwa suka aiko,ta kuma koma zuwa ga email a gaggauce ta goge nashi tayi minimize ta maida wayar mazauninta tana karanta sunan banking da yake amfani dashi,sannan ta zaro tata wayar tana duba ma'ajiyar lambobi dake cikin wayar.
Sunayen dake ajjiye cikin wayar ta fara bi,cak ta tsaya saman wani suna da yayi daidai da sunan banking nasa,ta danna malatsi na tura saqonni,ta kuma aika da saqon a gajarce
"Done" Ta jefa wayar a jaka daidai sanda ya iso bakin window din suna sake yunqurin buda motar.
Ja daya bakaniken ya yiwa murfin ya bude,sai ya waiwaya yana dubansa cikin mamaki,wanda shima cikin manakin ya iso
"Oga ina tunanin kaine baka jawo ta da kyau ba"
"Kai amma nayi mamakin faruwar hakan" Ya matsa yana kama hannun motar ya matsashi har sau uku. Mamaki yadan sake kamashi,amma kuma kiransa da tayi d nuryarta me laushi ya dauke hankalinsa daga nan.
"Okay na gode to" Ya fadiwa bakaniken yana cirar wani abu a aljihunsa adan gaggauce saboda kiran nata.
Bude mata qofar yayi,ta sako qafafunta ta fito tana gyara zaman abayar jikinta. Cikin nuna kulawa yake fadin
"Da alama motar bata gaji dake ba,kamar yadda me motar shima bai gaji da kallin wannan kyakkyawar surar ba......don Allah ayimin lamuni a bani exact gurin da zan sameki.......da gaske nake,banzo da wasa ba,ni din ba irin sauran samarin yanxu bane......da niyyar aure nazo" Ya qarasa maganar yana lanqwashe murya.
A nutse ta watsa masa idanunta da suke sake narkar dashi. Batajin daga rana irin ta yau ma zai sake samun damar tsaiwa da ita a muhalli daya irin yanzun. Wannan itace dama ta qarshe kuma lokaci na qarshe a wajensa tsakaninsa da ita.
"Ba damuwa......ka samu number dina ai.....komai zaizo da sauqi?"
"Are you sure?" Ya tambayeta yana kallonta cikin kokwanto. Saboda shi kansa yasan samunta din abune me wahala.....ta subuce masa wancan karon.....hakanan haka ya qaraci karakainarsa da nemanta amma ko me kama da ita babu ballantana ita karan kanta din. Kai kawai ta gyada masa sannan ta juya ta soma takawa tana barin wajen gami da cewa
"Godiya nake......fatan alkhairi"