Kenza eBookz

A d u n i y a ta complt by huguma - Chapter 8

A d u n i y a ta complt by huguma - Chapter 8

A d u n i y a ta complt by huguma Chapter 8: A d u n i y a ta complt by huguma Chapter 8. Sanda take sallamewa saita samu kanta da zama sosai a inda ta…

4,483 words

Sanda take sallamewa saita samu kanta da zama sosai a inda ta idar da sallar tana irga tasbihi da yatsun hannunta,yayin da kunnuwanta kadan kadan ke jiye mata tasbihin matar dake yinsa can qasa qasa,saidai lokaci lokaci yana qwacewa ya fito,har zuwa sannan bata waiwaya ko sau daya ta kalli fuskarta ba,amma daddadan turarenta bai fasa silalowa zuwa cikin hancinta ba.

Wayarta ta matsa haske ya bayyana ta duba lokaci. Tasan ko busari bai iso ba to dab yake da isowar,ta maida wayar ta ajiye tana kallon sararin cikin masallacin da babu kowa saisu uku. Daidai sanda zata dauke idanunta dai dai sannan taji matar dake gefan nata taja wani irin qaqqarfan salati numfashinta yana yayyankewa.

A tsorace ta waiwaya gefan damanta... Hannuwanta dukka biyun na tallafe da qirjinta,tana kuma daga kanta sama tare da qoqarin maimaita

"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" Saidai tana kakkamota ne da qyar saboda yadda numfashin yake son qwace mata.

Da hanzari ta miqe,hanzarin daya sanyata cilli da wayarta dake saman cinyarta. Jikinta dukka yana rawa a gaggauce ta matsa jikin matar

"Lafiya?,me yake faruwa?" Ta furta cikin matuqar tsoro da kuma rudanin ganin yadda take kaman shirin rasa numfashinta.

Bata iya amsa mata ba,wannan ya sanya sabreen zama sosai ta tallafeta da kyau zuwa jikinta tana sake maimaita tambayarta a rude

"Ina ganin kaman asthma attack ne" Mace guda dayan data rage a cikin masallacin ta furta bayan ta iso wajen itama tana dubanta

"Asthma?" Sabreen ta furta a gigice tana jin wani abu yana dukan zuciyarta. Shine ciwo guda daya da kullum taji sunansa sai zuciyarta ya tsinke,ciwo qwaya dayan da kullum takewa mummunan kallo,ciwo guda dayan da yayi silar wasu jigo na rayuwarta,har ila yau ciwo qwaya daya da yake wujijjiga rayuwarsu.

Da sauri ta finciko jakarta bayan da tunaninta ya dawo,ta zugeta da hannu daya daya hannun yana tallafe da ita,ta daga jakar ta zazzage duka tarkacen dake ciki,cikin matuqar sa'a ta hangi inhaler dihta.

A gaggauce ta dauka ta kara mata,hannuwan matar dukka rawa suke sanda ta dora nata hannun saman na sabreen kamar tana son tayata matsa inhaler din,kamar tanason nuna mata tsananin buqatarta da takeyi.

Cikin mintuna qalilan ta fara samuwa,saidai har yanxun bata daidaita yadda ya kamata ace ta daidaita din ba. Oily eyes dinta sun cika taf da qwalla

"Kamar asibiti tafi buqatar a kaita" Ta kasa haquri har sai da bakinta ya furta hakan

"Zaifi kyau dai gaskiya don da alama tana buqatar iska sosai".

Dai dai sannan wayarta data watsar ta dauki ringing. Matar ce ta matsa ta miqo mata,ta sanya hannu ta karba tana fadin

" Na gode" Tana duba me kiran.

Busari ne,ta latse wayar tana karawa a kunnenta

"Na qaraso,ina dab da bakin masallacin"

"Ka karba kayana wajen me gadi,gani nan fitowa asibiti zamu wuce" Bata tsaya sauraren abinda zai fada ba ta katse kiran.

Idanunta ta mayar saman fuskar matar. Wani abu taji ya taba zuciyarta,sai takejin kamar umminta ce ta dawo,sai takejin tamkar lokacin data rasa umminta. A duk sanda take mutum me dauke da irin ciwon tsananin tausayinsa yake kamata,duk da itama abar tausayin ce. Duk sanda taga babbar kaman haka yana fafutuka da wannan ciwon sai ta dinga tuna umminta.

Su biyun suka tallafeta don taji qwarin jikinta,suna takowa a hankali da ita har suka fito zuwa inda Kekenapep din yake

"Zan samu face mask a wajenka?" Ta tambayi busari.

"Eh hajiya" Ya amsa mata da sauri yana bude aljihun motar ya fidda shi sabo fil ya bata.

A kusa da ita ta zauna tana riqe da face mask din,saita sauke idanunta qasa tana jujjuyashi.

"Zan saka miki wannan saboda iskan mota,motan bana gida bane". Idanunta saman fuskar yarinyar,har zuciyarta tana jin qauna da jinjina taimakonta a kanta,ta lura tana d'anjin wani nauyi da kuma rashin sakewa. Qaramar yarinya haka me zuciyar taimako?,sai abun ya qayatar da ita.

Mintuna ashirin daidai suka qarasa private hospital din,wanda a nan file nata dana qannenta dukka yake. Tuntuntuni ta sallama asibitin gwamnati,yana daya daga cikin muhallan da suka samarwa rayuwarta gibi,yana daya daga cikin guraren da suka dasa qaton tarihi a rayuwarta,suka kuma ajiye mata wani tabo na har abada,shi ya sanya daga sanda ta samu dama ta nisanta kanta da dukkaninsu daga asibitin gwamnati.

Private hospital ne daya amsa sunanshi,babu nau'in wata kulawa da mara lafiya baya samunta,saidai kuma kudi ne zasu fita sosai daga aljihun majinyaci ko ahalinsa.

Private room suka bata,cikin mintuna goma sha biyar kacal suka bata dukkan taimakon daya dace,bata samu nutsuwa ba sai da suka shafe awa guda taga bacci sosai ya dauketa tana sauke numfashin a hankali ta cikin oxygen din da suka maqala mata saboda yadda taso galabaita sosai.

Zama tayi kawai gabanta bayan taja kujera,ta maqale hannunta a qirji bayan ta zube idanunta a kanta tana dawo da bayanan da likita yayi mata a kanta.

"Ta samu mummunan attack ne,tana samun kulawa sosai to amma kuma kaman yanayi ya nuna ba'a kiyaye wasu dokoki na masu ciwon,sannan kuskure ne ta dinga fita hakanan ba tare da inhaler ko wani a kusa da ita ba".

Idanunta ta qanqance sosai tana ci gaba da nazarin maganganunsa. Hakanan sai taji ranta yayi matuqar baci,indai har mace me irin wannan shekarun bata samu kulawa ba sai yaushe?,indai har ba za'a kula da dokokin da aka bata ba meye amfanin makusantanta?. Dukkan alamu sun nuna,tun daga suturar jikinta da komai nata ma cikin wadata da sukunin rayuwa take ainun,to meye zai hana su su bata kulawa su ahalin nata?.

Idan zata iya tunawa mutum daya ne ta gansu a tare a tsaye cikin store din,har tana bada umarnin a kira mata wani data kira a cici da kuma yawale. Yawonsu kenan yafi musu kasancewa da ita?,yanzu haka fa mahaifiyarsu ce amma sun gwammaci tafiya yawo akan su bata kulawa?.

Iska me zafi ta sake fesarwa ranta yana sake tunzura musamman bayan data duba agogon hannunta. Aqalla awa daya harda rabi da barowarsu store din amma har yanxun basu biyo address na asibitin data barwa wancan matar sun biyo bayan baiwar Allahn ba?. Sake juya wayarta tayi su huda suna fado mata a rai. Ta tabbatar zuwa yanzun sun dawo gida,suna can kuma zaune su daya a daki. Karon farko da taji kaman ya kamata ta siya waya ko qwaya daya ce ta ajiye cikin dakin saboda lalura irin haka,ko ba komai ba zata barsu cikin zulumi ba,zata kira taji lafiyarsu suma suji lafiyarta,duk kuwa da cewa komai runtsi a gida takeyin magrib.

Daidai sanda tunaninta yakai nan taji an murda handle na qofar. Kyakkyawan matashin ne ya fara bayyana. Dogo me matsakaicin haske. Kai tsaye idan kace masa kyakkyawa bakayi kuskure ba,yana da cikakkiyar suma me santsi tun daga kansa zuwa habarsa.

Yana sanye da dakakkiyar shaddar getzner Neautaral color daketa yauqi da sheqi. Yanayin dinkin da aka yiwa shaddar yayi masifar dacewa da structure na jikinsa. Dinkin zamani dake nuna zallar gogewa da wadatar arziqi na wanda suturar ke kwance a jikinsa. Yadda shaddar ke walqiya hakanan hular kansa,wadda koda ba'a gaya maka kudinta ba zakasan cewa bada qaramin zare aka saqata ba. Qafafun sanye cikin takalmin Batozzi,hakanan cikin qasa da second biyar dakin ya gauraye da sassanyan qamshin turarensa.

"Hamma mun sameta,gata tana bacci" Ya furta da kwantacciyar muryarsa da alama kuma yana magana ne da wani a wayar dake manne a kunnensa,dukka hankalinsa da idanuwansa suna kan matar dake kwance cikin mazari yana d'okin isa gareta.

"Okay hamma......in sha Allah" Ya sake fadi da sauri sannan ya jefa wayar a aljihunsa yana isa inda take kwancen ba tare daya damu ya kashe wayar ba.

Rusunawa yayi sosai a gabanta yana riqe da hannunta da dukka hannayensa biyun. Yayi wani irin laushi,don idan ka kalli hannunsa da kyau kana iya ganin yadda suke danyin rawa.

Dauke dubanta tayi daga kansa haushinsa yana saukar mata,saita maida kallonta akan wanda suka shigo din tare. Shine dai wanda ta gansu cikin store din tare wanda ta bari ya biya kudin siyayyar da tayi.

"Kamar kece kika kawota ko?" Ya fadi saboda hada idanu da sukayi. Maganar tashi taja hankalinsa,yadan sassauta riqon da ya yiwa mara lafiyan ya kuma waiwayo da dukka nasa idanun yana dubansu,don shi sam sam bai ma lura da kowa ba a wajen.

Kamar yayi mata susa ne a inda yake mata qaiqayi,sai ta miqe a nutse tana saqala Jakarta a kafadarta,haushinsu yana sake turniqeta

"Eh nice bayan kun yasar da ita kun kama gabanku ba?,waishin kunsan muhimmancinta kuwa?,kunsan yadda ciwonta ke buqatar a dinga yawan kulawa da ita musamman ita da shekarunta suka fara yawa?.

Ji yayi maganganunta sunyi girma ainun,tasan wace ita din a wajensu har da zataga gazawa da kasawarsu?. Saidai bai datseta ba saboda yadda yaga hawaye suna cika idanunta

"Mutane da yawa basusan muhimmancin iyaye ba sai sanda suka rasasu......amma ku sani cewa......yadda suka baku kulawa a sanda bakusan muhimmancin rayuwa ba.....ba komai bane don kun basu kulawa a sanda sukasan muhimmancin nasu rayuwar......ba kowa a kusa da ita.....ba inhaler.....yanzu inda numfashinta ya katse fa?" Ta qarashe fada adan tsawace hawayen na fara gangarowa ta idonta qwaya daya,sai tayi hanzarin kauda kanta gefe ta dauke hawayen da yatsanta. Su kadai sukasan yanayin da suke shiga idan ciwon ya tasar musu shi yasa babu me fahimtar abun sai wanda ke cikin yanayin

"Kuji tsoron Allah ku kula da ita yadda ya dace,don yadda muke amana a hannun iyaye haka suma amana ne a hannunmu,kuma Allah zai tambayemu game da yadda muka kula da tsufansu" Tana kaiwa nan ta soma takawa tana ficewa daga dakin.

Gaba daya mamakinta ya cikashi,yadda take haqiqancewa ba tare da tasan komai a kansu ba. Mahaifiyarsa itace rauninsa har abada.....wani abu guda daya me matuqar tsada da muhimmancin da ba madadinta. Har ta fice ya kasa tsaidata kaman yadda yaso har sai data bacewa ganinsu.

"Bita ka tsaidata......a qalla ko godiya ya kamata muyi mata,sannan kuma muji yadda za'a maida mata kudaden data kashe tunda na samu an biya bill na komai"

"Okay" Ya furta a girmame yana juyawa ya fice a dakin.

Kamar wayar dake aljihunsa yaji yana motsi,ya dafe wayar sai kuma ya sanya hannu ya fiddota da sauri. Mamaki ya kamashi,ya akayi bai kashe wayar ba. Hamman ne har yanzu akan layi,duka mintunan da sukayin wayar na a kunne,sai ya maida wayar kunnensa

"Waye yake mata fada saman kai?" Ya furta nutse

"Wanda ta kawota ne daga can store din"

"Don ta kawotan take ma mutane fada?" Ya furta adan harzuqe

"No hamma...." Ya fadi da sauri. Numfashi yaja yana ware idanunsa sosai

"Stop......banason a sake mata hayaniya a wajen nan....if not ran kowa zai baci"

"In sha Allah hamma"

"Idan ta farka ta dawo daidai give me a call"

"Done" Ya fada a taqaice kafin ya yanke masa waya,yana gama fadin kuwa yaji qit ya gintse wayar,saiya cireta daga kunnensa yana girgiza kai.

"Hamma.....hamma" Ya maimaita sau biyu.

Koda cewa tayi fada cikin yanke hukunci akan abinda bata sani ba.....bata da yaqini amma shi baiga laifinta ba,ya mata uzuri......hasalima ta burgeshi qwarai,dukkan alamu yana nuna tasan darajar dan adam ne,sai ya maida hankalinsa akanta yana duba shiga da fitar numfashinta.

*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*

*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*

*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*

*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*

*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*

*ZAFAFA BIYAR*

*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*

*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*

_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_

_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_

_K'ALBIM Mamuhghee_

_AJIYA A DUHU Billynabdul_

_DUNIYATA Huguma_

_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_

*hudu 2k*

*uku 1500*

*Biyu 1k*

*Daya 500*

_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_

*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*

*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA* *09033181070*

*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*

*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*

*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*

*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪

89825722 Nousaiba lawali maradi 1000cf

*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*

*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰 *D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

*Arewabooks@:Huguma* https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997

PAGE 22 __________________________ *_ALBISHIR A GAREKU!!_*

*_SHIN KUNSAN UMMUMAHNOOR LUXURIES TA TANADAR MUKU INGANTATTUN KAYAN ADO NA FITA KUNYA KUWA?_*

*_KAMAR SU_*

Atamfofi Laces Shadda Materials Takalma Jakunkuna Mayafai Trolley Sarka da dan kunne Oil perfumes

*_karki tsaya sanya har ayi babu ke,maza garzaya ta nan_*

Numbers 08034469681 08135142610

Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries

*_inganci da kwalliya shine muradinmu_* ____________________________

Batasan me yasa ba,batasan dalilin da ya sanyata takejin bacin rai sosai akan abun ba. Ta dinga fidda numfashi me dumi a hankali daga baki zuwa hancinta. Cikin nutsatsen takun nan nata take nufar inda tabar busari yana jiranta. Takun da yayi matuqar tafiya da hankali da tunaninsa baya ga zubin mamallakin takun.

"Wai har yanzu akwai irin mata masu wannan ajin?" Ya furta qasa qasa ba tare da yasan a waje yayi maganar ba,tana ta'allaqa dubansa a kanta,yana jin tana tafiya da gaba daya kuzari tunaninsa dama hankalinsa gaba daya.

Tamkar an zungureshi ko kuma anyi masa qaimi,sai ya saka hannu da wani irin hanzari yana bude murfin motar. Sam gaba daya ya manta da dalilin daya kawosu asibitin,ya kuma manta ma da waye yake tare,burinsa guda daya tal! A yanzu,ya samu isa gareta,yakuma samu daman yin magana da ita.

Sallamar tashi ta ratsa kunnenta a sanda take dab da isa wajen da Kekenapep din yake. Ta lumshe idanunta a nutse tana riqe masaqalin jakarta da kyau. Dama tasan hakan zata iya faruwa duba,zaiyi wahala a kallon farko da tayi masa ya iya tsallake halaye da kuma dabi'uj data hanga kai tsaye daga gareshi.

"Assalamu alaikum.....don Allah....." Ya katse maganar tashi da kan kanshi lokacin da yasha gabanta idanunsu suka gauraya waje daya.

Wani kwarjini na musamman,wani yanayi ya tsarga masa irin wanda bai taba jin irinsa ba. Nashi idanun ya janye a hankali yana qoqarin daidaita kansa tare da zallar mamaki yana kuma tambayar kansa

"Meye haka?,ita din wace?". Baisan iya adadin kalar matan daya gani ba tun da ya fara zama cikakken namiji zuwa yau. Baisan adadin matan da yayi mu'amala dasu ba daga jinsin yare daban daban,amma yau daya wata mace da baya tunanin ta rufa shekara ashirin da biyar a duniya na neman yi masa kwarjini?.

"Lafiya?" Ta jefa masa tambayar tana tsuke fuskarta tare da sake bada tazara tsakaninsu. Qoqarin daidaita nutsuwarsa yayi,sai ya sake mata murmushi hadi da gyara tsaiwarsa sosai a gabanta,yana jin ba wata mace da zata iya kaucewa tarkonsa muddin ya d'ana shi.

"Ba lafiya ba......maganar gaskiya kenan.......akwai gagarumin tashin hankali" A mamakance take duba fuskarsa tana yamutse tata tare da qoqarin sakeyi masa sabon karatun da baisan tana yi ba

"Amma fa a zuciyata" Ya qarashe maganar yana dafe qirjinsa.

Numfashi taja sosai har cikin huhunta sannan ta fesar tana kauda kanta gefe hadi da juya qwayoyin idanunta. Ba shine mutum na farko data taba gamuwa dashi me irin wannan salon ba,don haka tafiyar dashi bazai bata wahala ba.

Dukkan wani d'a namiji da zai ratso rayuwarta tayi imanin QADDARARSA ce a nan.......da kuma zallar tsautsayi. Mafi rinjaye daga cikinsu kuma SON RAI da SON ZUKATA.

Ba kasafai ta fiya bada kai ta farat daya ba,koda ta tsara amsarka,don tuni ta fahimci duk wani abu da akeson yayi daraja.....kar a bari samuwarsa ta zama ta sauqi. Don haka ta soma tattaki da zummar kubcewa daga gabansa.

A gaggauce ya sake tare mata gaba yana dubanta cikin marairaicewa

"Ranki ya dade.......na tabbatar girmanki yafi gaban a tsaidaki a hanya....to amma muddin na barki kika wuce din nayi imanin sa'ata ta rayuwa ce ta kubcemin gaba dayanta......ki tallafeni ki sammin minti uku kacal" Ya furta yana nuna yatsunsa guda ukun.

Juyowa ta sakeyi a karo na uku tana kallonsa. Ya fiya zaqin baki da yawa,maza irinsa suna da wani hali da dabia da tuni ta gama karatunsa. Tabbas akwai wani abu tattare dashi da wata qila take nema......tana hasashen yiwuwar samun wata qaruwa me girman gaske. Taga irinsa ba daya ba.....ba biyu ba....ba uku ba,har ba zata iya tantance adadi ba.

Duk da wannan hasashen amma bata yarda ta nuna masa komai ba. Sai ta sake kau da kanta tana yamutsa fuska

"Matsawarka daga hanyata kamar zaifi zame maka alkhairi akan ci gaba da tsaiwar......ina da tarin abubuwa a gabana....."

"Bansan ko me ke jiranki ba......amma na tabbatar koda baikai wannan tsaiwar tamu alkhairi ba bazai wuceta ba" Ya fadi a zaqe da fatan samun nasara

"Na roqeki kada ki watsan qasa a idanu,ki wofantar da wannan kyakkyawar damar a garemu gaba daya" Ya fadi yana marairaicewa tare da miqa mata wayar hannunsa yana kasheta da idanu gami da karyar da wuya da raunanar da idanun nasa.

A nutse ta sauke kallonta akan wayar ta kalla. Tsaleliyar iPhone 16 wadda kana dubanta zakasan bata wani jima da baro dumin kwalin da aka qerata ba. A yangance ta dauke kanta daga kai ta sake maidawa gefanta bayan.

Wani numfashi ya fusga da qyar bayan ya gama sauraren jerin lambar wayarta data karanto masa. Sautin muryar nata yana masa wani irin amsa kuwwa a kunnensa. Karon farko daya yadda cewa muryoyin wasu matan kadai suna iya haddasa fitina a zukata da gangar jikkunan maza. Sai yakejin yana sake zurfi ason ya kasance a tare da ita

"Sai nakega kaman girma da martabarki ya dara kihau napep.....da zai yiwu da kin sadaukarmin da wannan tsadajjen lokacin na saukeki a gida....." Yana ajewa tana daga masa hannunta,sannan ta fara takawa tana wucewa cikin abun hawan da busari ke jiranta.

Har ya bawa napep din wuta suka fice daga harabar asibitin yana tsaye a gurin. Sai daya tabbatar sun qwacewa ganinsa sannan ya buga qafarshi yana yarfar da hannunsa,wani shu'umin murmushi yana kubce masa. Ba shakka ita din ME ZAFI ce,ta kuma cancanci dukkan wannan dagawar da kuma jan ajin. Yana da makamai a hannunsa masu tarin yawan da zai iya yaqar zuciyarta yakuma yi nasara ba shakka ko kokwanto. Makami guda daya da dukkan namijin daya mallakeshi yake iya sanya kaza ta kwanta ta yanka masa kanta ta gasa ta kuma kawo kanta da kanta har inda yake don biyan buqatar ranshi.

Iya wassafa samuwar nasara kadai a gareshi ya sanya murmushi ya subuce masa. Ya sake buga qafa yana wassafa irin yadda zai tsikari rayuwarsa da tsinke yadda ya kamata

"Dole na qarawa kaina kusanci da dukkan qofofin da zasu budemin manya manyan qofofin taskokin da zan miki hidima dasu don mallakar muradina" Ya furta a sarari yana qanqance idanu,muradinsa yana sake ninkuwa,burikansa suna sake fadada.

Daidai qofar gidan nasu busari ya ajiiyeta bayan ya fiddo mata dukan kayan daga cikin motar. Cikin farfajiyar gidan ya ajiiyeta mata kayan sannan ya juya yana komawa ciki.

Tsaye tayi a farfajiyar gidan da iskar la'asar ke kai kawo. Ba wadatar yara sam,wanda koda ace akwai wadatar nasu tasan cewa ba kowa ne a cikinsu ke aikuwa ba. Kayan sun mata nauyin da ba zata iya dauka ba,tana tsaka da wanna tunanin ta hangi fitowarfitowar nadra,haneefa na biye da ita.

*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*

*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*

*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*

*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*

*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*

*ZAFAFA BIYAR*

*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*

*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*

_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_

_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_

_K'ALBIM Mamuhghee_

_AJIYA A DUHU Billynabdul_

_DUNIYATA Huguma_

_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_

*hudu 2k*

*uku 1500*

*Biyu 1k*

*Daya 500*

_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_

*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*

*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA* *09033181070*

*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*

*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*

*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*

*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪

89825722 Nousaiba lawali maradi 1000cf

*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*

*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰 *D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

*Arewabooks@:Huguma* https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997

PAGE 23 ___________________________ *_ALBISHIR A GAREKU!!_*

*_SHIN KUNSAN UMMUMAHNOOR LUXURIES TA TANADAR MUKU INGANTATTUN KAYAN ADO NA FITA KUNYA KUWA?_*

*_KAMAR SU_*

Atamfofi Laces Shadda Materials Takalma Jakunkuna Mayafai Trolley Sarka da dan kunne Oil perfumes

*_karki tsaya sanya har ayi babu ke,maza garzaya ta nan_*

Numbers 08034469681 08135142610

Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries

*_inganci da kwalliya shine muradinmu_* __________________________

Nadra,haneefa na biye da ita Dukansu suka watsar da abinda ke hannunsu sannan suka nufota. Fuskokin dauke da madaukakiyar fara'a wadda har tsakiyar zukatansu ta ratsa. Ita daya ce HASKE GIDANSU.....ita daya ce FARINCIKINSU hakanan ita kadai ce BAQINCIKINSU. Rashinta a kusa dasu yakan debe dukkan wata walwala da sakewa tasu,duk da tarin jamaar dake rayuwa a gidan amma duk sanda bata nan din suna jin gidan kamar babu kowa a ciki saisu.

Cikin jikinta ta rungumesu kaman yadda ta saba,sannan nadra din ta soma jan daya daga cikin ledojin. Duqawa haneefa tayi itama zata dauki guda daya nadra din ta tsaidata

"Bafa zaki iya dauka ba" Cak ta tsaya tana turo baki

"Anty wai da gaske bazan iya ba?" Murmushi ya qwace mata saboda hangen farincikin da tayi daga idanuwansu.

"Zaki iya auta" Ta furta tana bude ledar,jakankunan maggi da suka qarawa ledar nauyi ta ajjiye a gefe sannan ta daure mata ledar tana cewa

"Bismillah auta aiba raguwa bace" Hakan ya faranta mata rai,ta sukunya ta dauki ledar tana cewa

"Ita yaaya nadra kullun komai sai tace bazan iya ba,batasan na fita qarfi ba" Daga sabreen din har nadra data riga tayi gaba suka saki dariya.

Idonta a kansu har suka mata nisa sannan ta tsugunna a nutse ta kwashe maginta,ta fara takawa tana binsu zuwa Qofar da zata sadasu da babban tsakar gidan nasu. Zuciyarta a karye tana hangen haneefa daga nesa. Ta sake sakin boyayyen murmushi,akwai jarumta me yawa dangane da yarinyar,da alama zuciyarta dakakkiya ce kuma a tsaye take.

Dab da zata shiga din su kuma suna yunqurin fitowa su biyu. A hankali taja da baya tana basu hanya bayan ta sauke idanunta qasa,saidai duk da hakan da tayi bai sanya ta tsira daga garesu ba.

Qasan ranta akwai haushi takaici da kuma fushin rashin samun nasarar da batayi ba a safiyar dazu.

"Ke ya kamata mu bawa hanya ta wuce ai......gagara" Ta furta tana qanqance idanu idanun nata fes akan Fuskarta da kuma abinda ta riqo a hannayenta.

A hankali daada dake tsaye daga bayan bibo din ta gewayo ta gefanta tana cewa

"Muje mana bibo,yamma tana sakeyi"

"K'nnnn,gaskiya dai,fitar dare ai 'yan kwalta" Ta fada tana zakudawa tare da bin bayan daada bayan ta waiwayo ta ajewa sabreen wani kallo.

Da kallon itama ta bisu,sam ko kadan daada bata nuna ta santa ko tasan da zamanta......nata da sauqi don kome za'ayi a kansu baka taba jin ta tofa nata........batasan wanne matsayi zata aje daada ba a kanta cikin gidan,ta bibo kuwa fitacciya ce ainun,muddin magana ce a kansu,Ala cuta ala magani har abada bare ya fiye mata su,koda kuwa wanne irin nau'in alkhairi zasuyi mata ko zasu kowa cikin gidan.

Ajiyar zuciya ta saki tana ci gaba da kutsa kanta cikin gidan tana ta qoqarin kauda abinda takeji a yau yana taso mata qasan zuciyarta. Abune da take ganin bai kamata ta damu ba......ita din dai tasan kanta,ta yarda da kanta,sannan tasan wacece ita?,to me ya rage?,me take nema da shaidar mutumin yau?,mutanen dake rayuwar a DUNIYARta sam basu cancanci ta basu damuwarta ko tayi yunqurin gamsar dasu game da WACECE ITA?.

Da sallama a bakinta ta sanya qafafunta cikin falon nasu,komai a tsaftace a kuma tsare,madaidaiciyar iska me dadi tana kai kawo tsakanin falon ta wutar sola dake maqale a dakin.

Sanda take zubewa saman kujera daidai lokacin haneefa ke isowa gabanta da school bag dinta da wani.littafinta a hannu

"Anty munyi C.A,a cikin talatin na samu ashirin da takwas......sannan an bamu assig....."

"Kai haneefa haba" Nadra ta fasa tana hade fuska. Murmushi ta saki,saita dagawa nadra hannu

"Qyaleta,zo.nan auta" Ta kirata sanda huda ke qarasowa ta aje mata ruwan pure water me sanyi guda biyu

"Ki aje komai sai zuwa anjima zan duba,duka yau tare zamuyi assignment din kinji?" Kai ta daga tana murna ta cilla da gudu ta koma bedroom dinsu da jakar.

Sai data bula ruwan sannan ta kalli huda

"Me yasa baku wuce islamiyya ba?" Gyara zamanta kadan tayi sannan tace

"Jiran dawowarki mukeyi" Rabi tasha ruwan ta ajjiye tana sake karantar wani yanayi na daban daga huda din

"Sai na dawo sannan zakuje Islamiyya huda?,yaushe aka fara wannan tsarin a dakin nan?" Tadan furta a zafafe tana dubanta. Qasa da kant huda din tayi,ba kasafai take ganin fushi ko fada dava Fuskarta ba,to amma duk sanda tayi din ya tabbata laifi sukayi mata babba.

"Kiyi haquri.na tsaya dora abinci ne" Sassautowa tayi kadan tana sauke boyayyen numfashi. Bata qaunar abinda zai zaunar dasu cikin gidan ko kadan ballantana idanuwa ko kunnuwansu suji ko suga abinda rayuka zasu baci. Hakanan koda wasa bata qaunar suyi wasa da makaranta. Tana jin ciwo idan ta tuna iya inda matakin karatunta ya tsaya a shekaru ashirin da daya hudu da take dashi a duniya,wanda a yanzun kimanin shekaru hudu kenan rabonta da wata bawa wai makaranta.

"Ku shirya ku wuce,duk da lokaci ya fita amma baiyi nisa ba ai" Ta fadi tana duba agogon hannunta sannan ta fara zareshi daga hannunta.

Tana zaune dukansu suka gama shiryawa cikin fari qal din uniform da baqar doguwar riga daga sama. Hankalinta bai dawo daidai ba sai data tabbatar sun fita a gidan.

Kai tsaye ta rage kayan jikinta ta zura sassauqar riga sannan ta wuce kitchen din dake falon tana duba girkin da huda ta fara yi.

Komai yayi daidai,dole ta sanya huda ta koyi girki tun batakai minzali ba. Tana fita ta bar mata nadra da haneefa,tun bata san ya zata kula dasu ba har ta koya. Ko a yanzun idan huda tayi girki,itama tayi sai na huda ya dara nata.

Sai data kammale komai sannan ta daura alwalar sallar la'asar,sanda ta idar idanuwanta sun fara nauyi,tana zaune daga saman abun sallar tana dan murxa idanunta. Ba baccin take buqatar yi ba a yanzu,tana son magana da jib ne. A yawancin lokuta a irin wannan lokacinne take samun tattauna maganganu ire iren wadannan,sam bata yarda tayi komai bisa idanunsu,bata taba bari ta rab'a lamarin rayuwarsu da nata rayuwar,komai tana tsaidashi ne iya muhallinsa.

Hakanan tana hamma ta miqe ta koma daki. Locker gefan gadonta ta jawo,ta fidda madaidaiciyar baqar jaka dake dauke da mini laptop dinta,sannan ta zaro wayarta dake cikin jaka ta sake dawowa cikin falon.

Readers Also Read