A gidana complete novel - Chapter 10
A gidana complete novel Chapter 10: A gidana complete novel Chapter 10. Itakam dan aikinta ta duba sannan tai sallah da addu鈥檕i sannan ta kwanta.
4,479 words
Itakam dan aikinta ta duba sannan tai sallah da addu鈥檕i sannan ta kwanta.
************ Washegari
Khalid na zaune kusa da Abba sai dai da alama tunani yakeyi. Abba yace 鈥淜halid lafiya?鈥�
Yace 鈥淎bba akwai application din dana ciki na aiki sun turon naje exams sannan wacce nake tukawa mota ma tace na duba site dinsu zasu dauki ma鈥檃ikata.鈥�
Cikin jin dadi Abba yace 鈥渕asha Allah kai ina farinciki, insha Allah wannan karan inaji a jikina za鈥檃 dace da izinin Allah.鈥�
Khalid yadanyi murmushi, Abba yace 鈥渒ai amma matan nan Allah ya biya mata bukatunta ya bata miji ma gari.鈥�
Kallansa Khalid yai yasa dan dariya yace 鈥淪annu Abba, ka manta nacemaka matar abokina ce?鈥�
Abba yai dariya yace 鈥渁u namanta wlh, to Allah ya kawo 鈥榶a鈥檡a nagari.鈥�
Khalid yace 鈥淎meen, bari naje na amso abincin rana.鈥�
Nan ya mike ya fito.
Tsaya yai cak dan nesa kadan da wata mota datazo wucewa mace da miji na ciki.
Oh ba ita bace? Nan ya tuno, ranar daya dawo daga kai Zainab, wata budurwa da saurayi na cikin mota suka tsaidashi.
Saurayin ne ya fito yace 鈥渄an Allah kasan gidan Zainab?鈥�
Zainab? Saurayin ya kalli yarinyar yace 鈥淶ainab ko?鈥� Tace 鈥渆h da mijinta Adam, tana aiki a gidan tv.鈥�
Khalid ya nuna musu gidan dan yanzu kam ya fahimta sosai, sannan ya juya.
Shiru yai bayan tunowa dayai yace 鈥渋n kanwarsa ce meyasa tazo bata kirashi ba? Sannan yanayinsu barashi ne dasu ba yanzu kuma yaga yanayin kwalliyar ta da shigarta ba irinta sanda ya ganta ba鈥�
Da sauri ya girgiza kansa yace 鈥渒a sani ko saurayinta ta kawo? Sannan yanzu ma kila dan batada lafiya ne.鈥�
Murmushi yai yace 鈥渘izan fadawa Adam kanwarsa ne?鈥�
Da wannan ya wuce gida.
******** Zainab tunda ta tashi Adam baya gidan, waya ta dauka ya kirashi, yace mata yadan fita ne zaije gun Ziyad yazo gari.鈥�
Tace 鈥渁mma da wuri haka?鈥�
Yace 鈥渟orry honey naso jiran sai kin tashi kuma dai ganin baccin yake dawowa yasa na fito.鈥�
Dan dariya tai tace 鈥渮akuje gulma ko?鈥�
Dariya yai yace 鈥渁i haushinta ma Kwaro baya nan yau da sai na kawo Ziyad ya ganshi, kinganshi nan haryanzu bai yadda ba.鈥�
Zainab cikin dan rashin jin dadi tace 鈥淗oney!鈥�
鈥淪hikenan na daina.鈥� Kashe wayarta tai, sannan ta mike.
A falo taga Sadiya tana gyara falan, tace 鈥淪adiya!鈥� Gaisheta tai sannan tace 鈥淎unty kin fito?鈥�
Zainab tace 鈥渆h, ke da bakida lafiya me makon ki kwanta ki huta me kike anan kuma?鈥�
Murmushi tai tace 鈥渂akomai Aunty, Yaya fa?鈥�
鈥淵adan fita ne gun abokinsa.鈥�
Ayya.
Haka suka karasa gyaran gidan tare Zainab tai musu breakfast sannan ta dau nata ta shiga daki, dan tanada aikinyi.
Wayarta ce tai kara alamar shigowa text ta dauka.
鈥淏adau kin dau maganar dana fada miki wasa ba?鈥�
Ajiye wayar tai tare da sakin yin tsaki tacigaba da aikinta.
**********
Wajen karfe 9 na dare suna gun dinner anata cashewa sai dai su manya sun zama 鈥榶an kallo, haushi duk ya ishe Goggo daga sun shiga gun rawa sai ace su fita, gaba daya haushi yabi ya isheta, waya ta dauka ta kira Adam.
Cikin masifa tace 鈥渒ai zoka maidani gida.鈥�
Adam dake hanyar gida shima yace 鈥淎h kungama bikin?鈥�
Tace 鈥渢unda na kiraka ai kaima kasan mun gama, tambayar kuma ta meye?鈥�
Adam yace 鈥済aninan zuwa.鈥�
Nan ya juya da kan mota, yana isa ya kirata ta fito ta shiga mota, hannunta rike da jakarta da take away guds hudu.
Kallanta yai bayan ta shiga yace 鈥淕oggo yada take away har hudu?鈥�
Tace 鈥渘awa daya naka na zainab da waccen kuliyar.鈥�
Dariya yasa yace 鈥淵anzu dama haka ake? Bamuje biki ba sai ki kinkimo mana abin biki?鈥�
Tace 鈥渋n bazakaci ba kace bakaci, sai ka fadamin magana? Gobe dai zata koma ko?鈥�
Kallanta yai yanayin fuskarsa ya canza yace 鈥渄ole ma.鈥�
Harararsa tai tace 鈥渕eye naga fuskarka ta canza? Sannan yau kaine kake cewa dole?鈥�
Adam yai shiru baice komai ba, saboda abinda ke damunshi yasa yabar gidan tun safe, dan sai daya jira ma su Ziyad din.
Suna isa gida ya wuce dakinsu.
Goggo ta takeaway din cikin dan jin haushi tace 鈥済ida kamar ba mutane? Itama waccen magen na tabbatar ba bacci take ba.鈥� Dakinta ta wuce cikin jin haushi.
***********
Duk yanda ya rufe idanunsa hangosu sanda suka shiga hidima yakeyi, da kyar bacci ya daukeshi.
Zainab kam sai data gama aikinta duka sannan ta kwanta.
Da sassafe ta tashi kamar yanda ta saba ta shirya Adam na bacci ta fita.
Tea kawai ta hada ta fito, tana fitowa falo Goggo na kuna socket tare da kallanta. Zainab ta gaisheta sannan tace 鈥渮an wuce.鈥�
Goggo tace 鈥渢o adawo lafiya.鈥� Fitowa tai Goggo ta tabe baki tace 鈥渁 kalla kya tambayeni ai ya biki?鈥�
Mota ta shiga bayan ta ajiye kayanta, suka tafi.
Sai da suka hau hanya yace 鈥測a mai jiki?鈥� 鈥淵a warke!鈥� Shiru suka danyi sannan tace 鈥淵a Baban naka?鈥� Da sauki sosai.
Shiru suka dan sakeyi kafin tace 鈥渒a duba?鈥� 鈥淎鈥檃 yanzu in na ajiyeki zani cafe.鈥� 鈥淥kay, in zaka wani gun ka dinga tafiya da motar, man motar yayi kasa?鈥� Dubawa yai sannan yace 鈥渆h, ba can ba dai.鈥�
Okay!
Daga nan ba wanda ya sake magana sai da suka isa, kallansa tai tace 鈥済a ledar Umman nan, kace nagode, yayi dadi sosai.鈥�
Baisan sanda murmushi ya bayyana a fuskarsa ba, dan bai taba zata zataci ba.鈥�
Dama yana murmushi? Kayanta ta kwasa tai gaba.
Tana shiga office dinta wani text ya sake shigowa 鈥渒in tambayi mijin naki ya musa?鈥�
Cikin kufula ta ajiye wayar.
Khalid na sauketa ya juya ya nufi cafe.
********
Sadiya ta gama shiryawa, ta fito.
Goggo na zaune tana kallo ta gaisheta, kallanta tai tace 鈥渒inga dama kin fito?鈥�
Sadiya tai kasa dakai tace 鈥測ahkuri Goggo shiryawa nake.鈥� Ina Adamun yake yazo ya kaiki ki samu ki gama ki kama gabanki.鈥�
Sadiya tace 鈥渒iyi hakuri Goggo nasan na takura miki.鈥�
Baki Goggo ta tabe tace 鈥渁kwai talaway danayo jiya in kinaso.鈥�
Talaway? Goggo ta murtuke fuska hakan yasa sadiya yin shiru.
Adam ne ya fito, sanye da jalabiya.
Goggo ta kalleshi tace 鈥渒ayi maza kuci abinka ka kaita, tsinanen lattin nan da kukeyi shiyasa bata samu ta gama.鈥�
Adam yace to.
Haka suka gama suka fito. Tunda suka shiga mota ba wanda yai wa wani magana, can ta daure tace 鈥淵aya!鈥�
Kallanta yai baice komai ba. Tace 鈥渒ayi hakuri ranar na hanaka.......鈥漵ai kuma tai shiru, ranar a hayyacinki kike kenan?鈥�
Kallansa tai tace 鈥渆h.鈥�
Kunyar abinda yai ya kara kamashi, tacigaba 鈥渘asan jiya guduwa kai dan karna ganka, kayi hakuri in na takurama.鈥�
Kallanta yai yace 鈥渘ine zan baki hakuri.鈥�
A kofar skul dinsu ya ajiyeta ya juya ya tafi, yana tafiya ta kira saurayinta yazo ya dauketa.
Wata irin dariya tasa a cikin mota tace 鈥渒ai ka ganshi?鈥� Sannan tai tsaki tare da kashe video din datake kallo tace 鈥淜ai ina mamakin mema suka gani agun mutumin can.
Kallanta yai fuska a hade yace 鈥渘ifa gaskiya ko tabaki banasan yanayi.鈥�
Wata banzanr harara tamai tace 鈥渂ansan iskanci kaikuma, ka kama kanka, kasan akan wannan abin wallahi zaka kama gabanka.鈥�
Da sauri yace 鈥測ahkuri.鈥�
Bakin wani shago ta nunamai tace 鈥渟aman Fanta nasha gaba daya a bushe nakejin bakina.鈥�
Parking yai sannan ya fita.
Khalid daya sai biscuit da ruwan pure water yana kokarin biya mutumin ya matso dauke da fanta guda hudu. Khalid ne ya kalleshi tabbas shine yace 鈥淪alamu Alaikum.鈥�
Kallansa yai bayan ya mikamai hannu, yace 鈥渒a sani ne?鈥� Khalid yace 鈥渘a dai ganka rannan da wata ka tambayen wani gida.鈥�
Ni? Can sai yai dariya yace 鈥渉aka kuwa nida Razy ne, Allah sarki mungode fa.鈥�
Khalid ya jinjina kai sannan ya fito.
Yana fitowa ya ganta zaune a cikin mota, Razy? Mekenan?
Takowa yai jikin motar har inda take ya kwankwasa glass din motar.
Budewa tai cikin masifa tace 鈥淢alam.........鈥�
Kasa karasawa tai ganin Khalid.
Khalid ya sake kallanta yace 鈥淪adiya?鈥�
Gabanta ne yai wani irin faduwa hankali a tashe ta kalleshi..........
****** Ayusher馃弻馃徎鈥嶁檧 [11/9, 11:19 PM] Zuraiyah Zuzu 馃専: 馃崁A GIDANA馃崁 聽 聽聽 ......................
聽聽 *H虧a虧s虧k虧e虧 W虧r虧i虧t虧e虧r虧s虧 A虧s虧s虧o虧c虧i虧a虧t虧i虧o虧n虧*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*艐膮 A虉踏蕪蕣謫搔蓻蕗 蕧蕣搔蓶馃弻馃徎鈥嶁檧*
{24}
Gabanta ne ya shiga dukan uku uku, nutsuwarta ta tattaro ta kalleshi. Idanunsa haryanzu yana kanta yana jiran yaji me zatace. Nutsuwarta ta daidaita sannan ta kalleshi tace "Barka, au ina wuni?"
Khalid yace "Sadiya me kike anan?"
Murmushin yake tamai sannan tace "naje yin registration ne shine naji yunwa nazo nan."
Yanda yake kallanta ne tasan tabbas bai amince ba, idanunta ne suka ciciko tace "Dan uwanane shi bari yazo kaji."
Tana neman sake tambaya ya bude motar ba tare da ya kula da Khalid ba yace "Raziyyah sorry na koma siyo abu ne."
Kafa tasa ta haureshi kallanta yai zai sake magana ya hango mutum a jikin window.
Kallanta yai sannan ya kara cuso kansa dan ganin waye.
Khalid na tsaye yana kallansa, Raziyyah hankalinta ne ya kara tashi ta kalli Khalid zatai magana ya juya ya bar gun. Kallan Jameel tai cikin takaici ta kwadamai jakar hannunta tai cikin takaici ta bar mota. Raziyyah lemon fa?
Ko bi takanshi batai ba ta nufi motar Zainab hankalinta a tashe.
Ya tada mota yana neman tafiya kawai ta bude gefen driver ta shiga.
Kallanta Khalid yai cikin mamaki fuskarsa a murtuke yace "Get Out!" Kallansa tai tace "zan fita amma sai na fadi abinda ke raina."
Khalid bai kalleta ba sai dai yayi shiru. Hawayenta ta goge tace "Bada wata manufar mukai karya ba na shiga wani haline na neman taimako."
Ganin bashida niyyar kulata tace "shine Ya Adam ya taimakeni, na tabbatar baka tunanin ni nakai kaina gidan a matsayin kanwarsa ko?"
Dan Allah kayi hakuri Wlh bada wata manufa nazo ba.
Shiru tadanyi a ranta tana cewa wannan dan banzan ko uban me ya kawoshi? Gashi da alama bashida yadda.
Khalid ne ya kalleta yace "am in hurry can you get out?"
Wani takaici ne ya kamata, ta share kwallarta sannan ta kalleshi fuskarta ta canza daga alamar tausayin datai tace "badai Zainab kake neman fadawa ba ko?"
Kallanta yai sannan yai murmushi yace "Oh this is your true self?"
Tace "koma menene banaji kanada hurumi a ciki, mijinta ne ya kawoni dan haka duk abinda ya faru tsakaninmu ne banaji mai tuka mota ya isa yai wani abin, kowa ya............"
Yanda ya juyo ya buga mata wani kallo ne yasa tai shiru, kasa karasawa tai gani tai ya bude inda yake zaune yazo kofar datake ya bude ya mata alamar da ta fita.
Mikewa tai cikin kufula ta bar gun.
Khalid yaja yabar gun ransa a bace.
Me Adam yake tunani? Me ya faru harya yaudari matarsa ta aure akan ta?
Raziyya kam ranta ne yi dubu gun bacu, cikin kufula tace "wlh baka isa hanani yin abinda na taso domin shi ba, tarwatsa rayuwar Adam dashi kadai na taso har nakai wannan lokacin.
Jameel ta kalla wanda ya fito yana kallanta. Karasowa tai cikin jin haushi ta mai wani mugun kallo tace "kunyi magana ne a shagon?"
Yace "Razy shiya tambayeni ni bankawo komai a raina ba wlh."
Kallansa tai tace "bana key din karamin gidan dakai."
Karamin gida? Cikin mamaki ya tambaya, wani banzan kallo tamai yasa hannu ya ciro yace "me zakiyi?"
Amsa tai tace "ka aikon da takardun gidan, na dau kasona."
Kasanki? Cikin mamaki.
Tace "mungama daga yau ni dakai." Ta juya zata fita, da sauri ya riko hannunta yace "Razy me kike shirin yi? Kinfi kowa sanin bazan iya rayuwa bake ba, sannan sirrinki fa duk na sani."
Juyowa tai ta kalleshi, tace "danka san sirrina sai akai me? Ni wanda na sani naka fa? Na fadama karna sake ganin ko missed call dinka." Tana kaiwa nan ta fita daga motar.
Da gudu y fito yace "in na kawo mana wata mafitar fa? Ni inaga ba lalai sai ta hanyar Adam zaki tarwatsa farincikinsa ba, me zai hana mubi tagun matarsa?"
Kallansa tai tace "koma menene ba ruwanka a ciki."
Adaidaitar datazo wucewa ta shige tai gaba tana maimaita kalaman Jameel, ta hanyar Zainab? Da sauri ta girgiza kai tace mutanen dake karkashinta uban me zasu tsinana.
***************
Haka ya cike application din aikin amma gaba daya hankalinsa na kan abinda ke faruwa, taya Adam zai dauko mace ya kawota?
A haka ya dawo Tv station din.
Lokacin tashinta nayi ta fito rike da kayanta, Ramatu na biye da ita tana bata hakuri tare da cewa "Dan Allah Aunty kiyi hakuri wlh wannan karan ba'a san raina bane, bansan yanda abin yake bane, dan Allah kiyi hakuri, Allah zan sake wani."
Ko kallanta Zainab batai ba, tunda ta fito yake kallansu, ko ba a gun yake ba kana gani Ramatu zakasan rokonta take, kai ya dauke cikin mamakin wannan hali. Harta shiga mota Ramatu na bata hakuri amma ko kalla batace mata ba.
Kallan Khalid tai jiki a sanyaye sannan ta share kwallar da ta zubo mata, Zainab ce tace "mu wuce."
Shiru yai ba kuma alamar tada mota a tattare dashi.
Kallansa ta sakeyi tace "muje nace."
Kallanta yai sannan yace "magana ake miki, inkin gama sai mu wuce."
Ranta a bace tace "in banida ra'ayi fa?"
Baice komai ba haka kuma bai tada motar ba, Ramatu ce ta zuro report din cikin motar ta window tace "Aunty plz ki duba wannan."
Ta juya tare da cewa Nagode.
Tana tafiya Zainab ta hade fuska tamau tace "Umarnina ba umarni bane ko me kake neman maidani."
Tafiya ya farayi sannan yace garin irin wannan hali gashi can mijinki na miki karya, ya dauka a zuciyarsa yai maganar sai jiyai tace "me kace?"
Kallanta yai ta mirror yace "Sorry."
Wani takaicine ya kara kamata, sorry? Cikin jin haushi tace "Zagi na kai hala?"
Baice komai ba dan baima san me zai ce ba, ranta a bace tace "Banajin zagi sannan bana shakkar abinda wani yake tunani akaina."
Tana kai nan ta dauke kai ta maida kanta jikin tablet dinta.
Khalid baice komai ba suka cigaba da tafiya
**********
Motar Adam ta bude ta shiga, zama tai jiki a sanyaye ta kalleshi.
Bai kalleta ba sai dai ya rasa meyasa yake san ya kalleta.
Atishawa tai tare da sa hannunta kan cinyarsa.
Kallanta yai sai dai yakasa zare hannun nata, cikin kulawa yace "bakyajin dadi ne?"
Kallansa tai idanunta ya ciciko tace "ina tunanin tafiya ne da wannan hade ran da kakemin."
Kallanta yai jikinsa yai sanyi, murmushi tai tare da cewa "bansan me yasameni ba, sai dai da alama na jawoma bakin ciki."
Da sauri yace "A'a Sadiya, nine zan baki hakuri."
Hawayenta ta share tace "kai zan ba hakuri yaya nama kiss bada saninka ba."
Shiru yai ya kasa cewa komai, sai dai gaba daya ganin tana hawaye hasa jikinsa yin sanyi.
Share hawayenta tai tace "can you hug me na karshe?"
Jiyai bazai iya musa mata ba a hankali ya dan matso, jawoshi tai ta rungume tare da sa kuka.
A hankali ya shiga shafa bayanta alamar lalashi, kallan wani a wajen motar tai wanda ke rike da waya da alama hoto yake dauka, Adam ne ya dagota yace "nagode Sadiya, sannan ki yafemin."
Ajiyar zuciya tai sannan ta kalleshi tace "banasan tafiya yaya ka bari na kara sati daya, ba abinda zanma kallan ka kawai nakesan na dinga yi."
Kallanta yai hankalinsa a tashe yace "a ina?"
Tace a gidan Aunty.
Gaba daya hankalinsa ne ya tashi karara yace "A gidana?"
Tace "Gidan Aunty."
Yanda take maganar ne yasashi kallanta cikin mamaki yanda take maganar ba kamar dazu ba.
Kallansa tai tace "am sorry Ya Adam amma bazan iya barinka da gidan ku ba, ko sati sai na kara a ciki."
Baki ya sake yana kallan ikon Allah, anya Sadiya ce?"
Yace "bangane ba."
Tace "kasan yaushe rabona da bacci? Kullum mafarkinka nakeyi, ta ina zan iya tafiya da wannan abin? Kabarni na zauna ko na sati daya ne kafin nan na saita kaina sai na tafi."
Shima gaskiya abinda ke damunsa kenan, ya kasa cireta a ransa, tsantsar sha'awa ce ke yawo dashi.
Hannu tasa akan cinyarsa tace "kaima nasan abinda ke damuna yana damunaka Yaya."
Shiru yai yana kallanta, tace "bamuyi zina ba yaya, junanmu kawai zamu ragewa sha'awa dan Allah ka barni na kara sati."
Samun kansa yai da cewa "ba zina bace?"
Da sauri tace "ai baka kusanceni ba"
Kallanta yai tare da dan fito da harshensa kadan.
Murmushi tai ganin komai na zuwa da sauki, gaba daya wasan ya daina birgeta, anya bazata canza sali ba kuwa? Tabi shawarar Jameel.
To amma Zainab ta ina?
Khalid ne ya fado mata arai, tai dan kwafa ganin irin wulakantata dayai.........
A haka suka isa gida ko kunya Hannunta nakan cinyarsa shi kuma ya kasa cirewa sai dan sanyi da yakeji.
Suna isa gida motarsu Khalid na shigowa.
Khalid yai parking ya zuba mata ido daga cikin mota ba tare da ya fito ba.
Itama kallansa tai sannan ta dauke kai, da sauri ta taho inda Zainab take ta bude mata tace "Aunty sannu da dawowa.
Kallanta tai tace "Sadiya an kammala?"
Cikin jin dadi tace "Eh Aunty na gode sosai."
Khalid yana jinta yanzu kam ya tabbatar yarinyar nan yar banza ce, tasan yasan komai amma ko kallansa batai ba?
Adam ne ya karaso inda Khalid yake, Zainab ta kalleshi tace "Honey!"
Cikin sanyin jiki yace "Honey sannu da dawowa."
Tare suka shiga itada Sadiya.
Khalid ya fito suka gaisa da Khalid, ya amshi account number dinshi, yace "kwaro zan shiga ciki gaba daya banajin daidai."
Khalid ne yace "Sadiya!"
Juyowa Adam yai da sauri yace me?
Khalid yace "a'a kawai ina mamakin girmanta ne, kasan a skul ka taba zuwa da hotonta kai da ita kana tsokanar Ziyd a class akan matar da zaka bashi ce."
Adam cikin tsoro da neman waskewa yace "Oh baka manta ba? Ni na manta anyi haka ma wlh."
Khalid ya kalleshi, Adam yace "ta kara girma da kyau ko?" Khalid gani yai ma bata lokaci ne sake mai magana kawai ya dau jakarsa da ledar da Zainab ta ajiye dan haushi ko duba cikinta baiba yai sallama da Adam yabar gun....
Suna shiga falo suka taradda Goggo a zaune tana waya da alama cikin fishi take magana.
Yoo dole ki kira ki lalemeni, sanda kuka sa aka hanamu shiga gun rawa fa? Sannan me kika cemin? Cemin kikai mune manya manya, amma meya faru?
Ganin su Zainab yasa tace "na kiraki."
Kallansu tai tace "kun dawo? Ya naganku tare?"
Ta fada tana hararar Sadiya ta gefe. Zainab ta gaisheta da gida kawai ta wuce ciki.
Kallan banza ta bita dashi tace "kullum a turbune ake dawowa."
Raziyya ta kalleta a ranta tace "ko kunya?"
(Nima nace kema ko kunya? Kina mace馃檮 kina abu kamar馃槖)
********** Ayusher馃弻馃徎鈥嶁檧[11/11, 9:55 PM] Ayusher Muhammed: 🍀A GIDANA🍀 ......................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
{25}
Duk yanda Khalid yaso yai bacci ya kasa, can ya tashi ya zauna yana nazarin wannan abu dake faruwa, shi kallo daya yana yarinyar nan ya fahimci ba yar arziki bace, ya akai gaba daya idansu ya rufe suka kasa gane wa? Me Adam yake tunani dahar zai kaita gidansa a matsayin kanwarsa? Indai akace kanwarsa kenan mahaifiyarsa da yaji tana gidan itama da ita aka hada baki kenan?
Haka yai ta saka da warwara haryai bacci, ya fito da safe Umma ta nufo asibitin. A waje suka tsaya suka gaisa tace "zaka wuce?" Yace "eh." Tace "Jiya nida naji kunya? Matarnan daga kai waina sai data sako min dubu biyu a cikin flask din? Ita haka akeyi? Muna godiya ana sake mana abin alkairi."
Khalid yace "dubu biyu?" Tace "eh wlh, dama nasan baka sani ba, ka mata godiya dan Allah, ina ma tsoron sake msta wani abin kar ta sake sako wani."
To Umma. Haka yace ya fito. Ya iso da wuri yana fatan ganin Adam dan jin wannan abin. Sai dai ba kowa a wajen, Bala ya kalla yace "yaushe Mai gidan yake fitowa?" Bala yai dariya yace " ai Alhaji sai azahar daka ganshi inhar ba da dalili ba." Khalid yai shiru tare da shiga ciki, Zainab tana gama shiryawa ta fito ta nufi kitchen, tea dinta ta hada yanda ta saba sannan ta fito falo.
Goggo na zaune tana kallo hannunta rike da cup din tea. Zainab ta gaisheta, Goggo ta amsa tace "Sadiya yau zata tafi." Cikin mamaki Zainab tace "yau kuma? Jiya Honey yace zata sake sati daya." A gidan ubanwa zata sake? Goggo tai subutan baki gun fadar haka, Zainab fuskarta dauke da mamaki tace "Goggo!" Murmushi Goggo tai cikin dan dabara tace "a'a gani nai wai ba amfani tanada harkar karatu tazo ta tare anan."
Zainab tace "inya tashi duk yanda kukai ya kirani a waya ina sauri ne."
Goggo ta dan tabe baki a ranta tace ai kullum cikin sauri kike indai kece.
Zainab ce ta fito dauke da kayanta, sannan ta shiga ta ajiye, ta zauna.
Ana fita daga gate din gidan text na shigowa wayarta "A haka in aka ganki sai a dauka kinada nazari amma yanzu na san bakidashi, na fada miki abu kinyi watsi dashi ko?"
Mekenan? Tai maganar a fili. Khalid ne yace " mutumin rannan ne?"
Ya fada hankalinsa adan tashe, a'a bansan waye wannan ba kuma. Ta fada tana kallansa, dan parking yai da motar sannan yace "zan iya gani?"
Shiru tai tana nazari, yace "in baki yadda na gani ba shikenan mu tafi kawai." Mikamai wayar tai batace komai ba. Tundaga text din farko zuwa na yau ya karanta, sannan yai shiru ya dau number ya mika mata. Kallansa tai tace "bansan waye wannan ba amma nasan komenene sharri yake shirin yi, nasan Adam nasan abinda zaiyi da wanda bazaiyi ba."
Khalid ne ya kalleta yana tuno waccen rainin wayan da aka mata. Kallansa tai tace "me? Baka yadda ba? Abokinka ne barshi dai da san jikinsa amma bashi da wata matsala."
Khalid ya juya ya tada mota yace "hakan ake fata."
Kalmar tadan tsaya mata sai dai bata sake tambaya ba, har suka isa.
Tana shiga yai shiru yana nazarin sakon nan da kuma yarinyar nan, tabbas ko za'ace yayi shishigi sai yasan me take a gidan nan. Number daya dauka ya kira, yayi mamaki dayaji number tana aiki, kenan Zainab bata ko gwada kiran number ba? harta kusa katsewa sannan aka daga.
Hello! Jin muryar mace ne yasa ya danne zuciyarsa tare da gwada sa'arsa yace "Razy?" Number tadan kalla, tana mamaki dan sim din a wayarta yake amma ba kowa yasan dashi ba tace "Yes? Waye?"
Khalid mamaki ya kamashi yace "me kike tunani kikeyi?" Sake kallan number tai sannan tace "waye?" Kashe wayar yai tare da yin shiru yana tunanin abinda ke faruwa, Raziyya tai shiru tana kallan wayar, wanene?
******** Goggo Zainab na fita ta nufi dakinsu Zainab. Budewa tai kai tsaye, Adam na kwance rungume da pillow yana sharar bacci. Dayan pillow din ta dauka ta makamai, a zabude ya farka, kallanta yai yace "Goggo lafiya? Mekike anan?"
"Me kake nufi da kuliyarcan?" Me nake nufi kamar ya? Kace bazata tafi yau ba? Uban me zata zauna tama? Adam ya kalleta yace "zata tafi amma wai ba yau ba." Cikin masifa tace "kai bansan iskanci, uban me zata zauna tama? Badai wani abin ya faru tsakaninku ba?"
Goggo tai tambayar a tsorace, kallanta yai yace "me zai faru?" Yanda ya bada ansar ne ya kara tsoratata tace "kai bansan iskanci, tashi ka sallameta ta tafi, sam hankalina ya kasa kwanciya."
Adam yace 'naji dan Allah jeki." Fita tai ranta a bace sosai.
******
Juya motar yai ya nufi gidan, daga waje ya ya tsaya sannan ya daga waya ya kira Adam.
Adam dake kwance yana nazarin yanda zai sallameta ne sako ya shigo mai, Yaya dan Allah charge nake so kamin ina kitchen."
Mikewa yai ya fito, Goggo bata falan da alama wanka ta shiga, kitchen ya nufa ya tsaya a bakin kofa tana fere dankali, yace "ya akai wayar taki ba charge? Ko bakida charger ne?"
Hannu tasa bayan ta matso ta jawo rigarsa ya karaso cikin kitchen din, rungumeshi tai tare da sakin wata ajiyar zuciya tace "har hankalina ya kwanta, dazu gaba daya battery na yayi low."
Dagota yai yace "kar Goggo ta fito."
Kiss tamai a baki sannan tai murmushi, duk da gabansa dake faduwa. Sake mai kiss tai tana neman shiga canciki wayartai kara. Matsawa yai tareda daukan wayar, yana gyara sautin muryarsa. Khalid yace "Adam ina waje inba damuwa kazo zamuyi magana." Adam cikin mamaki yace "magana? Wacce?" Khalid yace "saika zo." Adam cikin mamaki yace "Khalid?" Kallansa tai jin sunan daya ambata, hankalinta a dan tashe tace "Khalid?" Yace "eh wai magana yakeso muyi."
Yawo ta hadiya sannan tace "kaje ka shirya bari na kai mai ruwa nace kana zuwa."
Kallan mamaki ya mata yace "ruwa?" Tace "eh wai karyaga ka dade."
To shikenan, ya fada sannan ya wuce daki. Fitowa tai ta dakko wayarta ta nufi waje.
Khalid dake zaune yana jiran Adam ya hangota ta fito.
Tana zuwa ta bude gaban motarsa ta shiga. Khalid bai kalleta ba ya dan duba agoggon wayarsa.
Kallansa tai tace "me zaka cewa yaya?" Bai tanka ta ba sannan bashima da alamar kulata, tace "wai dan Allah kai da kake driver meye naka na shiga hurumin dabe shafeka ba?"
Yanzu kam Khalid ya kalleta, wayarsa ya dauka yai dialing din numberta. Wayarta dake saman skirt dinta ne tai vibration. Khalid ya kashe sannan ya sake kiranta, kallansa tai hankalinta a tashe, yace "kome kike shirin yi ki dakata dashi, ki koma inda kika fito."
Kallansa tai tace "bazan dakata ba wlh harsai naga rayuwar Adam ta salwanta."
Kallanta yai kamar zai kulata sai kuma ya fasa, dauke kai yai wanda hakan ya sake bata mata rai, kallansa tai tace "Zainab ce ta saka ka bincika? Me kake tunani in na tura mata wannan video din?"
Ta fada bayan ta zaro wayarta ta dana video din, bata nuna mai wayar ba sai dai ga nishi nan na an fada kogi ita da namiji, sannan ta dakko pic din da suke rungume a mota ta nuna mai tace "ko na hada mata da wannan?"
Duk yanda Khalid yaso ya danne abin baisan sanda ya wanka mata mari ba, ransa a matukar bace ya kalleta, itama kallansa tai ranta a bace, zatai magana Adam ya bude kofa cikin mamaki yace "Khalid meta maka zaka mareta?"
Kallansa Khalid yai sannan ya kalleta wacce ta fashe da koka tare da rike hannun Adam, tace "ya zamuyi yaya? Ya san niba kanwarka bace shine ya maren."
Adam ya kalleshi yace "koma menene baikai harka mareta ba, akan wani dalili?"
Kallansa kawai Khalid yake kafin yace "nasan ko a skul kwakwalwarka bataja sosai amma banyi tunanin toshewar kwakwalwarka takai haka ba."
Adam ransa ya baci balle haushin an gwaba mai magana a gaban Sadiya, yace "mene?"