A gidana complete novel - Chapter 13
A gidana complete novel Chapter 13: A gidana complete novel Chapter 13. Sannan gidan nan yanzu zan sashi a kasuwa ruwanku ne ku zauna ruwanku ne ku fita,…
4,460 words
Sannan gidan nan yanzu zan sashi a kasuwa ruwanku ne ku zauna ruwanku ne ku fita, motar dana baka na barmaka dan dama kai na saiwa ku kashe kayanku a ciki ku fice min daga gidana, wannan shine uzuri na karshe da zan muku.
Goggo ce ta riko ta da sauri tace "Zainab ki taimaka kiyi hakuri wlh muma cutar mu tai tsinaniyar yarinyar nan."
Adam yana kuka yace "Honey kiyi hakuri dan Allah."
Cikin tsananin masifa ta juyo, kamar zata rufesu da duka tace "inyi hakuri? Duk wani abu da ya kamata ina maka shi inama, nice shanka, nice tufafinka, kula da mahaifiyarka, komai na rayuwa na dauke maka shi amma ka rasa abinda zaka saka min dashi sai wanan? A gidana? Ka kawota kacemin kanwarka? Na bata gurin zama, na dauketa kamar yadda na dauki kanwata, ashe karya kake min dakai da mahaifiyarka? Bazan taba yafemuku ba wallahi. Idan har kunasan zaman lafiyanku ku ficemin daga gida na fada muku."
Ta juya rai a bace ta bar gidan, tana fitowa ta kalli Khalid dake jingine da mota yana nazarin abubuwan dake faruwa, me Adam yama kanwarta haka? Wayarta yake ta kira anki dauka.
Bala ta kalla ta mai alama yazo, yana zuwa ta kalleshi tace "mutanen ciki zasu fita anjima, yanzu ka kira key walder ya canza min key din kofar nan yanzun nan, sannan kafin dare su barmin gidana, su baka takarda ka ajiyemin, in basu fita ba zuwa dare ka kirani a waya zan turo wadanda zasu fitar dasu.
Ta bude mota ta shiga, kallanta yai, hade rai tai ta shiga ta zauna.
Baice komai ba ya shiga ya zauna shima tace " mu bar gidan."
Yace "okay!"
Yana san tambayarta yarinyar amma baisan shiga abinda ba'a sashi a ciki ba.
Yana tada mota Adam da Goggo na fitowa da sauri, ya dan kalleta ta glass.
Muje!
Shiru yai yana kallan Ada da Goggo, kallanta ya sakeyi.
Please! Abinda ya fito daga bakinta kenan hawaye na gangarowa.
Jan motar yai suka bar gidan.
Tafiya kawai suke batace komai ba shima baice komai ba, ina zani?
Abinda kawai yake zuwa mata kenan, jitai Khalid yace "ina zamu?"
Kallan window tai tace "ina zani?"
Cikin sanyin jiki ya dan kalleta.
Kallansa tai tare da murmushi tace "hotel?"
Yace "Hotel?"
Tace " kaini ko ma inane, inda bazan sake ganinsu da abinda ya dangancesu ba."
Shiru yai baice komai ba, yana tunanin yanda zaiyi da ita.
Wayarta ta dauka ta kira director tace "zata dau hutun sati daya batajin dadi."
Mamaki ya kamashi yace "Zainab sosai ne rashin lafiyar? Kinsan muna bukatarki dayawa."
Ka taba ji na dau hutu? Ko hutuna ina dauka ne na shekara?"
Yace "kiyi hakuri, naji abin ne sama ta ka."
Zan dawo nextweek. Bata jira amsarsa ba ta kashe wayar.
Shiru tai.
Khalid yace "ina zamu?"
Kanta ta kwantar jikin kofa tana tunani, batasan kasancewa ita kadai a wannan lokacin tana ganin in ta zauna ita kadai lalai ciwon zuciya ne zai kasheta, to ina zata? Wa take dashi? Wayyo rayuwata? Allah nasan ni mai laifice ka dubeni.
Ta karasa tare da rufe idanunta.
Khalid yai shiru yana tunanin yanda zaiyi da ita.
Idanunta a rufe tace "muje Danbatta."
Bai san sanda yai dan burki kadan ba, ya kalleta tare da yin parking yace "danbatta? Bazaki iya zama a gidan mu ba."
Idanunta ta bude sannan ta kalleshi tace "cema nai gidan ku?"
To ina?
Tace "Gidanku."
Yace "mene?"
Da tana tunanin zuwa gun Dr ne dan tasan yayarsa sosai, ta taba zuwa gidanta a danbatta sau daya, sai dai jin kalaman Khalid yasa ta canza tunani.
Kallanta ya sakeyi yace "me zakiyi acan?"
In naje ni zanga mai zanyi.
"Bangane ba, a wani dalilin xaki bar gidanki ki tafi wani gidan?"
Gidana?
Ta tambaya tana kallansa, idanunta suka sake cicikowa, jin sunan kadai ma tada mata hankali yake.
Tace "ba sai ka wulakantani ba, ajiyeni anan ka tafi, zan je inda nake so da kaina."
Shiru yai yana tunanin wannan al'amari.
********
"Yau mun shiga uku, yanzu ya zamuyi?"
Wannan da wannan da..... Ta kalle Adam wanda yake rabe jikin kujera, tace "yanzu da uban me zamu tsira? Duk ka gama cinye dan gadan mahaifin naka agun tsinanen karatun da bansan me ka karanta ba, sannan yanzu gidan matar taka ma gashi ka mana sanadi."
Adam ya kalleta baice komai ba.
Haushi ya tuke ta yace " yanzu ya zamuyi?"
Adam ya kalleta yace "Goggo Zainab ta gama rabuwa dani kenan har abada, yanda ta tsani mahaifinta akan abinda yai, ni na san yanzu ko zata mutu baxata taba kara zama dani ba, na shiga uku na Goggo."
Goggo a kufule tace "mun shiga uku dai, kasan da aka uban wa ya saka."
Wayyo yau nikam me zan gani rayuwata ta juya min a lokaci daya.
Can tace "Ina tsinaniyar yarinyar nan taje? Wlh ko zan karar da zanin daurawa ta sai na nemota."
Ta karasa da matse kwalla, kanta ke wani irin ciwo.
********** Ayusher🏌🏻♀ [11/25, 2:26 PM] Ayusher Muhammed: 🍀A GIDANA🍀 .........................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
#OneLove❣
{31}
Kallansa tai sannan ta dauke idanta tace " akwai inda zani acan"
Bai tada motar ba sai dai yana nazari, kallansa tai tace "muje!"
Motar ya tada suka fara tafiya, hannunta rike da wayarta tana kallan sunan Dady, can ta danna kira.
Ringing uku aka dauka, sai dai me? Jitai muryar mace, Basma daga can take "Zainab?"
Da sauri Zainab ta kalli wayar wani abu ya tokareta, Basma tace "yahkuri na daga wayar, yanzu ya dawo break daga gun aiki ya shiga toilet ne."
Kashe watarta Zainab tai sannan ta rufe idanunta kamar mai bacci.
Har suka shiga danbatta bata bude idanta ba da alama daga tunane tunane bacci yayi gaba da ita, suna kan titin shiga danbatta ne yace "ina ne unguwar?"
Shiru yaji hakan yasa ya duba mirror din gabar motar, ganin tana bacci yasa yace "Hello!"
Zai sake magana yaga ta farka a zabure, tana Inalilahi wa Inalilahi Raji'un.
Idanunta ta bude a tsorace, tana maida numfashi, Khalid ya gangara gefen titi.
Kallansa tai ta tana jin haushin yanda yake gaminta yanayin da bata san kowa ya sameta a ciki.
Daurewa tai tace "muje." Yace "inane?"
Kallan garin tai sannan tace "I don't know."
Juyowa yai ya kalleta yace "You don't know?"
"Hmm yafi shekara biyar dana zo i can't remember."
Baisan sanda wata dariyr rainin hankali ba, haushi ya kamashi yace "then ki kira kaninta muji."
Wayarta ta dauka ta kirashi, daga can yace "Zee kece?"
Tace " Sabir Aunty na nan kuwa?"
Aunty Amina?
Eh Yace "mijinta ya koma Abuja da aiki ya akai?"
Okay shikenan, kafin ya sake magana ta kashe wayarta.
Khalid ta kalla tace "batanan."
Baki yadan bude yana kallanta kafin ya danyi wani abu daga cikin kirjinsa zuwa bakinsa, yace "yanzu ya za'ayi?"
Oho!
Fuskarsa ya hade yace "Then zan iya ajiyeki anan na tafi."
Kallansa tai da sauri sannan ta kalli waje tace "anan?"
Kai ya daga mata alamar eh sannan yace "kina tantama?"
Tace "shikenan, ka barni anan din."
Daurewa yai ya juyo ya kalleta duk fuskarta ta kumbura, idanunta sunyi jaa samansu sun kumbura yace "Am sorry na san ba hurumina bane sai dai yau ma zan sake ciga hurumin da ba nawa ba, wannan zabin kina gani shine ya dace?"
Dagowa tai daga jinginar datai tace "me kake nufi? Ba dai kana so kacemin na cigaba da zama da mijin da na kamashi da mace a cikin gidana ba?"
Gabansa ne ya fadi, abinda ya faru kenan? Yanayin fuskarsa ne ya canza dan ya tausaya mata, kauda kanta tai ganin kallan tausayin da yake mata tace "meye laifina? Kula dashi danai ko kuwa kula da mahaifiyarsa? Meye laifina dan na kula da mijina? A tunanina inayin daidai gwargwadon abinda zan iya bansan menene laifina ba........" Hawayen da taji suna neman zubo mata ne yasa ta kasa cigaba da maganar, Khalid ne ya kalleta duk da tausayinsa daya kamashi bai hana cemata "kina tunanin duk abinda ya faru baki da laifi kenan?"
Kallansa tai bayan ta dake tace "fadamin menene laifina?"
"Wani irin rashin kula da rayuwar da bataki ba da kikeyi da har za'ace bakisan kanwar mijinki ba? Wannan wace irin rashin kula da gidanki ne?"
Shiru tai tana tunani, tabbas duk matsalar daga nan ta fara, datasanta da duk.....
Dakewa tai tace "Naji wannan ne laifina bayan shi kuma fa?"
Shiru yai yana kallanta kafin yace "komai daya faru rabi naki ne, sannan bakya tunanin gidanku ya kamata kije?"
Fuska ta hade sosai tana kallansa kafin tace " tafi ka barni anan.
Bai kulata ba yaja motar suka cigaba da tafiya itama haushi baisa tace komai ba.
Wayarta ta daga ta kira Bala.
Bala na tsaye a na canza key din gidan wayarta ta shigo, ya gaisheta. Tace "sun tafi?" Yace "a'a."
Takardar fa?
Bai nan komai ba.
Shikenan tace ta kashe wayar.
A bakin kofar gidansu yai parking, sannan ya kalleta yace " ki kwana anan gobe na maidake gidanki."
Kin kulashi tai bata kalleshi ba, fita yai daga motar shima ba tare da yace komai ba ya dau jakar ta a booth ya shiga ciki.
Da wani kallo ta bishi tana mamakin hali irin nasa, ko kadan baya burgeta namiji sai tsinanen zafin rai? Ita sam ta tsani namiji mai gadara da neman isa.
Khalid ne ya shiga ciki.
Yana shiga tsakargida yaga Asiya a tsaye tana kiran su Amie su fito su wuce islamiya, kallanta yai tana ganinsa ta matso tana yaya an dawo?
Eh Asiya in zaki wace kiyima bakuwa magana a cikin mota kice ta shigo.
Bakuwa? Mota? Kallanta yai bai amsa ba ya wuce ciki.
Su Amir na ganinsa suka gaisheshi suka fito da gudu suna sa takalmi.
Umma data idar da sallah ne a daki ta fito tace "Khalid? Kaine da ranan nan?"
Zama yai kusa da Abba yana cewa eh wlh.
Kallan Abba yai sannan ya kalli Umma dake kikarin zama, Abba yace "ya akai?"
Dan hannunsa yasa ya shafi keyarsa yace "matar danake ma aiki ne muka taho tare."
A tare sukace "ina?"
Khalid yace "ta samu matsala da mijinta ne shine na kawota nan kafin komai ya warware."
Fuskar Abba dauke da mamaki yace "iyayenta fa?"
Khalid yai dan shiru kafin yace "ba'a kusa suke ba, da alama kuma batada kowa a kusa."
Umma tai shiru kafin tace "kace ta shigo ne?"
Na fadawa Asiya, shiru sukai suna tunannin wannan abu.
Asiya data fito ne ganin mota a kofar gidansu yasa ta nufeta, Amir yace "Ya Asiya motar yaya ce?"
Bata kula su ba ta nufi motar.
Zainab dake ciki ta bude kofar tana kallanta, Asiya ta gaisheta cikin nutsuwa sannan su Amir ma suka gaisheta. Kanwar sa? Asiya ta daga kai tace "eh, ya Khalid yace ki shigo."
To, islamiya zaku?
Tace "eh Aunty."
Zainab tana tsaye tana kallansu gar suka wuce tai murmushi tace da alama age mate din su Nabila ce sai dai ta fisu nutsuwa, tunowa tai da fadan da sukeci haka kawai ta samu kanta da murmushi.
Kallan gidan tai bayan tazo jikin kofa ta tsaya, itadai ta kasa shiga ciki.
Abba ne ya kalli Khalid yace "ka shigo da ita bakowa ne zai iya shigowa gidan mutane kai tsaye ba."
Nan Khalid ya mike ya fito.
A waje ya ganta tana ganinshi ta hade rai, shima fuskarsa a hade take yace "ki shiga."
Wucewa gaba tai kai kace gidansu ne, tun daga tsakar gidan take mamakin gidan, gidane dan karami, soro inda dakin Khalid yake sai kofa ta ciki, kana shiga dan madaidaicin tsakargida ne wanda aka sumumteshi tsaf, daga gefe akwai rijiya, sannan bandaki a ta gaban rijiyar.
Daga can kusa da asalin cikin gidan kuma kitchen me a gun, gefen kitchen din kuma inda suke sa murhu ko gawayi.
Sai dai kidan a share yake tsaf, hatta gun wanke wanke an wanke gun tas, duk da ta raina gidan amma ta aminta da tsaftar gidan a haka suka shiga, Umma na tsaye a kan barandar tana ganinta ta fara lale lale da babbar bakuwa.
Zainab ta shigo cikin kunya.
Umma ta nemi data shiga cikin falan, Zainab ta shiga, Abba ne a zaune ta gani kafarsa daya babu yana jingine da bango duk da haka yana ganinta yace "barka da isowa."
Zainab ta zauna ta gaisheshi sannan ta gaida Umma, Khalid dake tsaye ya juya ya bar falan.
Tana ganin yabar falan kunya ta kara kamata, Abba ya kalleta bayan ya amsa gaisuwar yace "ashe abu kuma baiyi dadi ba?"
Kasa tai dakai batace komai ba, yace "bakomai ki zauna anan sai ki kira mahaifinki asan abin yi."
Gudum yin musu yasa kawai tace to.
Umma ce ta nuna mata dakin Asiya nan ta mike ta shiga, gaba daya itakam kunya ma takeyi, ya akai bata tafi hotel ba?
Umma ta shiga ajiye kawo mata abinci, kunya ta kara kama Zainab dole ta mike ta tayata ajiyewa.
Umma ta zauna kusa da ita tace "karki sa komai a ranki kiyi sallah kici abinci ki huta, Allah zai kawo mafita kinji."
Kallan Umma tai haka kawai tunanin Ummy ce a kusa da ita yazo mata, idanuntane suka ciciko a hankali hawaye ya zubo mata.
Umma ta kalli yanda duk idanunta ya kumbura, tausayinta ya kamata tace "yahkuri kinji."
Zainab ta share hawayenta sai dai ta kasa cewa komai, kawai jitai ta nasan Umma ta rungumeta ta rasa me yasa take ganin kamar Ummy ce a gun.
Umma ganin yanda take kallanta yasa ta fahimceta, rungumeta tai tana cewa "bakomai kinji, insha Allahu Allah zai kawo miki mafita duk da bansan me ya faru ba amma nasan ke mace ce ta gari."
Kamar ta tabo Zainab kawai Zainab tasa kuka, wannan kukan jitake kamar a jikin Ummy take yinshi.
Khalid wanda ya fita siyo juice a shagon kusa dasu me ya dawo rike da leda, yana shigowa yani yanda Zainab ke kuka, kusa da Abba kawai ya ajiye ya fita zuciyarsa na tausaya mata.
Wayar Abba ya dauka ya fita Yana fita ya daga waya ya kara kiran Razy.
***** Ayusher🏌🏻♀ [11/25, 2:26 PM] Ayusher Muhammed: 🍀A GIDANA🍀 .........................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
#OneLove❣
{32}
**********
Goggo na zaune tana ta cusa abinci kana ganin kasan cin dole da cin yunwa take ma abinci, Adam na zaune a gefe cikin takaici yace "yanzu Goggo har kinsamu damar dafa indomie kina ci? Muda rayuwarmu take neman shiga garari?"
"Kana sane ko jiya tsinaniyar yarinyar nan bata banni naci abinci ba so kake na muti kafin ma samu ba Zainab hakuri."
Kallanta yai gaba daya duk ya canza, kana ganinsa kasan a birkice yake, yace "Goggo koza'a mutu Zainab bazata taba komawa dani ba, kema kinsani, yanzu akam takardarta wlh sai ta kaimu kotu."
Goggo ta tsame hannunta daga plate din ta kalleshi tace "duk ba kai kaja mana wannan masifar ba."
Da sauri yace "wai kin dane zancen ni naja mana ki nemo mana mafita ko kuwa? Abinda ya faru ya faru amma Sai kara tusawa kikeyi, dana sani ke kanki kinsan nayi, haryanzu bansan uban me ya shiga kaina ba."
Goggo ta kalleshi bayan tasha ruwa tace "nidai mafita daya ce yasin bazan koma kauyeba, kasani tunda kai aure matarka ta dakoni ko da wasa ban sake zuwa can ba, kanina inya ishen da zancen Sadiya nasan abin makaranta kana kallo Zainab ke taimakawa mu tura, mo hanyar ban komaba kuma wlh yanzu bazan koma ba."
Cikin masifa yace "nima cewa nai mu koma? Tambayarki nake yanda zamuyi."
Itama cikin masifa tace "kaina zaka huce? Uban wa yasa ka ja mana?"
Haushi ne ya kamasu duka kowa yai shiru.
Adam ta kalla sannan tace "wai kai da uban me kake da kudin da take baka duk wata?"
Haushi ne ya kamashi bai tanka mata ba.
Goggo ta sake cewa "ko kuma me kale gani idan ka bata takadar sai dai kace mata bazaka bata takardar saki ba harsai ta barma gidan nan."
Kallanta yai da sauri yace "mene?"
Goggo tace "kana gani dai korarmu za'ai nan da awa anjima kaga dai key ake canzawa, kuma wlh tunda ta furta ko za'a mutu sai ka bata takardarta, gwara muma mu cafki gidan, ai harga Allah kaima cutarka kuliyarcan tai."
Shiru yai yana kallanta kafin yace "kina tunanin Zainab zata yadda?"
Tace "karma ta yadda, in bata yadda ba kace mata kuje kuton ai ita idan gari ce aikin gidan tv take mutane dayawa sun santa bazata taba bari sirrinta ya fito duniya ba, kasan yanda take san aikin nan nata."
Kai ya jinjina cikin gamsuwa sannan yace "Goggo Allah banasan rabuwa da Honey."
Yai maganar kamar mai shirin kuka.
Tace "inka kara cemin Honey sai na wankeka da mari shasha shan banza, kai dai wlh banga amfanin ka ba, sam ni na rasa banzan hali da sokon tunaninka."
Adam yai shiru gaba daya hankalinsa ya kasa nutsuwa, wani bangare na zuciyarsa na kwadaitamai abinda Goggo tace.
Goggo ta kalleshi tace "tu ra mata sako a waya, ka fada mata in tanasan takardarta sai ta baka gidan nan."
Da sauri yace "yanzu?"
Tace "da sai yaushe?"
Nan ya dako waya yana kallanta.
••••••••••
Rasy dake kwance Bash na gefenta yana neman kai hannu cikin rigarta ne ta buge hannun sannan ta kalli wayarta dake kara, dagawa tai tace hello.
Khalid yace "Raziyya kinga dama kin daga?"
Nan ta fahimci waye tace "Drivern mota kiran wayar na menene? Na tabbatar banci bashinka ba."
Murmushi yai yace "kin bayyana kanki ko sai naje gidanku na fadawa iyayenki abinda kikeyi?"
Da sauri ta mike tsaye tace "gidan mu?"
Yace "eh kokin dauka bawanda zai san inda gidanku yake?"
Kumbura fuska tai cikin bacin rai, Khalid yace "mu hadu dake gobe a kano, zan kiraki inji inda kike, kada ki kuskura kik'i daga wayarki inba haka ba zan wuce Naibawa yar lemo na fadawa iyayenki abinda kikeyi, Ahhhhhh bansan ya zasuji ba insuka ji, bayan yayarki ta rasu, ina tsoron halin da zasu shiga."
Yana kaiwa nan ya kashe wayar.
Cikin takaici da bacin rai tabi wayar da kallo, a Zuciye ta cillar da wayar kan gado sannan tai wata kara mai karfi tace "Kyankyasan nan......." Bash ne yasa hannu zai riketa kafa ta sa ta haureshi a matse matsin kafarsa, wani irin kara yasa shima tare da durkushewa a gun.
*********
Umma zama tai a gabanta Zainab Taci abinci sannan ta fito daga dakin bayan taga ta zauna tana hutawa, Zainab tabi bayanta da kallo cikin wani yanayi.
Abba dake falo ne ya kalleta yace "Uwar 'ya an fito?"
Zama tai kusa dashi cikin tausayi tace "da alama batada wanda zata dogara dashi taji dadi."
Kallanta yai yace "kamar ya?"
Kai ta girgiza alamar rashin sani tace "haka kawai nakeji kamar ta dade cikin kewa tana neman wanda zai dubeta."
Shiru Abba yai cikin tausayinta shima.
Zainab ta kalli hoton Ummy a wayarta tai murmushi tare da kwantar da kanta akan dan karamin gadan Asiya, Ummy na!
Ta fada tana shafar hoton, sako ne ya shigo wayarta, kallan sakon tai cikin mamaki ta kara karantashi.
Gaba daya mamaki ne ya kamata, duk da tasan karshen zamanta da Adam yazo amma bata taba tunanin zai nemi bata takardarta bugu daya ba, sannan abinda ya kara bata mamaki wai ta bar mai gidanta?
Wata dariyar bakinciki ta saki tace "Ummy wace rayuwa nai duk tsawon shekaru na???? Me yasa nake gani kamar duk wahalar danasha bata biya min komai ba??"
Umma ce ta turo kofar dakin, Zainab ta kalleta tare da gyara zama, Umma ta ajiye mata ledar juice din tace " badai tunanin kike ba?"
Kallanta tai tana san fada mata abinda ke ranta amma gani take daga ganinta sainta zake???
Kai ta girgiza tace "a'a."
Umma tace "ko nazo mu zauna tare? Dama na fita ne na dauka kina san hutawa."
Zainab tai murmushi tace "zan kwanta ki huta kema."
Nan Umma ta juya tana murmushi.
****
Tana fita Dady ya kirata a waya, kallan wayar tai kafin ta daga.
Daga can yace "Zainab ashe kin kira?"
Murmushi tai tace "eh na kira dazu."
Yahkuri bangani ba sai yanzu dana dau waya zanyi waya ma ga kiranki.
Shiru tai kenan Basma batace mai komai ba ko me?
Tace "dama kira nai mu gaisa ta daga tace kana toilet."
Oh Basma ta daga? Ai bansani ba saboda ina fitowa na taho kila shiyasa bata samu damar fadamin ba."
Zainab tace "bakomai."
Ina aiki ne in na tashi ma kira, kafin ta kara magana ya kashe wayar da alama aiki yake sosai, sai dai ba karamin sanyi jikin ta yak ba ta kwanta kawai ta rufe idanunta.
😪
*********** Ayusher🏌🏻♀ [11/29, 11:59 AM] Ayusher Muhammed: 🍀A GIDANA🍀 .........................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
#OneLove❣
_Faty Muktar Allah ubangiji ya jikan Baba ya kai haske kabarinsa, yasa mutuwa ta zama hutu a gareshi Ameen suma Ameen_
{34}
Knocking din motar ya fara cikin tashin hankali, Zainab tana zaune ta zubawa takardar ido, bata taba tunanin wannan lamarin ba, lalai Adam, kallansa tai yanata jijiga kofar motar, zuge glass din tai ta kalleshi, da sauri yace "Honey ki taimaka ki ban takardar dan Allah ki yafemin na tuba wlh, Honey ki taimaki rayuwata dan Allah."
Kallansa kawai takeyi, Honey dan Allah ki yafemin, wlh wlh bansan meya shiga kaina ba.
Daurewa tai tace "ka biyoni inda ka ajiye motarka ka dauka"
Da sauri yace "Honey ki bari mu tafi tare, dan Allah ki tsaya ki........."
Jan motar datai ne tai gaba ya sashi zubewa a kasa wani zazzafan hawaye ne ya zubomai.
Zainab tana zuwa kofar gidan ta ajiye motar a inda ya ajiye, tunanin wanda zataba key dinshi tai sannan tai hanyar ciki, tai sa'a sai ga Amir nan.
Yana ganinta ya karaso da gudu yana cewa "Aunty Umma nata nemanki."
Kallansa tai sannan ta mikamai key tace "Amir ka tsaya a jikin motarnan zakaga wani yazo yana neman key ka bashi wannan."
Amsa yai sannan tai ciki, tana shiga taga Umma a tsaye tana zagaye, Umma! A hankali ta kirata tana kallanta, da sauri Umma ta taho, itama Zainab ta nufo ta, sai da suka matso kusa da juna sannan Umma tace "Alhamdulila dan na tsorata da akace bakya nan a waje ina tsoron kar wani abu ne ya faru kikai wani gun."
Tsayawa tai tana kallan Umma, ashe haka uwa ke da dadi? Murmushi ta mata sannan ta nuna mata takardar tace "ya sakeni Umma."
Da sauri Umma ta amsa, da yake ba boko tai ba sai dan wanda Khalid ya nuna mata a gida ta dai dan fahimta gane cikin kokonto da sauri ta kalleta tace "Har Uku?"
Murmushi Zainab ta sakeyi tace "Eh Umma."
Shiru Umma tai tana kallanta, kafin tace "ki shiga ciki ki sanar da mahaifinki."
Kai ta daga sannan tai ciki, Umma ta bita da kallan tausayi sosai dan har sai dataji idanunta sun dan ciko.
Gun Abba ta nufa ta sanar dashi yanda akai, hankalinsa shima ya tashi yace "wannan wani sakaram miji ta samu dahar zaiyi saki uku lokaci daya?"
********
Adam kam yaci uban tafiya yana tafe kamar mara lafiya, dakyar ya iso ga uban yunwa dake damunshi, yana zuwa Amir ya bashi key ya tafi ball dinsa, shiru Adam yai yana kallan gidan data fito dazu, gaba daya ya rasa abinda xaiyi sai dai yasan duk abinda zaice yanzu a banza yake gwara yaje gun Goggo su samo shawara.
Jan motar yai ya fito, a hanya ya tsaya yasai biscuit da juice ya cucusa sannan ya karasa gida.
Bala na tsaye yana kallan Adam dake ta danna mai horn, Bala na kallansa bai ko binta kansa ba yana jin radio dinsa, haushi ne ya kama Adam ya fito a zuciye ya nufi Bala yace "kai Bala ka bude min gate ko sai na ci mutuncin ka?"
Bala cikin maganarsa ta hausar yan niger yace " Hajiya ta kira yanzu tace ku bar mata gida dan haka bazan bude ba."
Adam cikin kofula ya nufoshi, Bala ya kalleshi yace "ka tabbatar zaka iya dukana?"
Kallansa yai kamar zai karasa gunsa sai naga ya bude gate ya shiga, Bala yace "awa biyu na baku ku fito daga gidan nan, dan Hajiya tace inbaku fito ba na dau hukunci da kaina, sannan kunsan mu buzaye ba hakuri, nan da awa biyu yan sanda zasuzo inkunga dama karku fito."
Adam ya wuce ciki, haryaje zai shiga ya dawo da gudu ya zare key din motarsa dan dama ya saba wannan shirman balle in a gidane sau dayawa ma baya rufe motar.
Bala ya bishi da kallan takaici yana tuno abinda suka mai jiya, har fara yake su wuce awa biyun nan dan wlh sai ya rama wulakancinsa.
Adam ne ya shiga falo, Goggo na zaune ta soya dankali da kwai tana ci tana kallan tv, daga bakin kofa ya tsaya ya zuba mata ido, gefe ta hada tea dinta mai kauri.
Kallansa tai tace "Adam ka dawo?"
Kasa mata magana yai sai kallanta kawai da yake, kallansa tai tace "matsalarka kenan sai kai abu kazo kana nadama, kai dai dakai sa'a matarka nasan aikinta in ba haka ba uban wa zai bar ma gida?"
Haryanzu kallanta kawai yake tana cin abincinta tana magana, ganin yaki shigowa ne yasa tace "karka damu duk wanda yai saki da wanda aka saka sai yaji haka nadan wani lokaci amma komai zai warware a hankali, kazo kaci abinci naka na kitchen."
Ganin takaici yaki karewa ne yasa ya matso ya kashe tv din sannan ya kalleta rai a bace.
Kallansa tai tana kurbar tea tana harararsa kafin tace "uban wa yasa ka aikata? Da zaka nemi hucewa akaina?"
Huci ya fara yi yana kallanta, bata tankashi ba dan gani take duk saboda ya saki matarsa ne, abincinta ta cigaba daci, kawai jitai yasa kuka.
Kallansa tai tace "tashi kaje daki kayi abinka ni karka sani a gaba kamar ni na kashe ma aure."
Cikin masifa yace "bake kika kashemin ba amma kinada babban hannu a ciki."
Kallansa tai tace "a ina kenan?"
A zuciye yace "ta kwaci sakinta bata kuma bamu gidan ba, yanzu Bala yace mu fita nan da awa biyu."
Cup din tea din dake hannunta ta yar bata sani ba, tea din ya zube dan har kan cinyarta, ko zafin bataji ba dan ma ba tafashashe bane, Adam ne ya matso yana kuka yace "Goggo ya zamuyi?"
Kallansa kawai take kafin tace "Sakin ka bata kafin ta baka takardun gidan?"
Yace "cewa tai in na bata zata bani."
Baki kawai ta bude tana kallansa, yacigaba to na bata kuma ta koren dan da kafa ma na nufi gidan.
Nawa ka mata?
A hankali yace uku........