Kenza eBookz

A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 8

A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 8

A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 8: A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 8. ****** ********* ****** Ranan kamu aka saka ni a lalle kamar…

3,138 words

****** ********* ****** Ranan kamu aka saka ni a lalle kamar yadda akewa ko wace budurwa kamu. Duk wanda ya ganni ko inna ta yasan bamu a cikin walwala ana dai sha, ani ne kawai na bukin ba cikin dadin rai ba. Gidan mama altine nake zaune da kawayena don a gidan mu babu fili ga magan ganun mama da basu da dadin ji. Ya kasance washe gari daurin aure nan mama ta dora a tsakar gida ga dakin Inna tab da yan uwan ta sai cewa mama take ita bata gane ba fa. Ace har yanzu ba, a fito da kayan amarya ba aje zuwa jere ko sai mutane sun watse ne za, a tafi jeren kamar marasa gaskiya. Wata daga cikin yan uwan Inna ta fito tana bata amsa da cewa in ma mutane sun watse ai ko wasuwasun mu zamu iya gyara dakin yar mu. Ballanta na rana muke jira yai sanyi mu tafi don bamu fada gidan mutane da rana tsaka ba kamar mun gaji da yar ta mu. Dole mama taja bakin ta tai shiru ta kyale su dai gani ai duk abin da akewa taratara din ake boyo yau rana ce da bata karya sai dai uwar diya tai kunya. Sai zuwa karfe biyar mutane suka fara shiga gidan mama Altine suna kwaso kayan da aka saya min na aure. Wata daga cikin kawayen mama da ta gaiyyata suzo saka ido ta shigo tana cewa mama. Ke laure wai kayan da naga ana fitowa dasu gidan mai kuli na waye ba dai kayan yar taki bace haka? Ni duk garin nan ban taba ganin yarinyar da akaiwa kaya haka ba ? Kinko ga kayan kamar ma na kamfani ne fa don a cikin ledan su ma suke, ga wasu irin manyan zannuwan gado da na fani kamar na makka dasu didin didin dasu. Gaban mama ya fadi tace ke haule wai da gaskiya kike ko ba, a baki ga komai nakai gida ba tace idan karya nake fita ki ganewa idon ki ai. Mama bata saya ba taja wani raggan zani dake shaye a igiya ta nufi kofan gida da saurin ta. Aiko tana lekawa tai tozali da kujerun da ake fitowa dasu tace kan uban nan ni za, aiwa munafunci ke nan. Watau malam yana da kudin yin wanan kayan haka wa yar shi. Shine ya barni da yara a zunbule a daki sun kai sun kawo ga girma kuma ba manema suka rasa ba. Da kyat kawayen ta suka samu ta natsu suka jata zuwa cikin gida dakin ta suna tausan ta akan idan tai haka taba da kan ta. Nan dai aka shiga shirin buki ba wanda ya tsaya kula mama da haukan ta da takeyi ta kasa boye hassadan ta a fili. Bayan sallah jumma, a aka daura aure duk dai ba wani shagali akayi ba tunda ba auren saurayi da budurwa bane, amma an ci ansha an koshi. Da yamma aka dauke ni sai gidan Alhaji garbati gida ne babban gida mai cike da iyali fiye da arbain a gidan. Sai da aka kaini dakina na dan zauna na yan mintina akace na taso akaini dakin uwayen gidan. Dakin uwargidan mama salla aka fara kaini dattijuwa ce sosai don ta manyanta sosai ba sai an fadi ba itace ta wanke shi ya wanke ta. Nan iyayyena suke fada mata cewa ga amanan yarsu nan sun kawo masu da fatan zata rike masu ni amana idan nayi ba daidai ba don Allah ta tsawata man. Tace kada suji komai ai da na kowa ne da fatan nima zan masu biyayya yadda ya dace karami yai wa babba. Suka ce insha Allahu in wanan ne baza, a samu matsalan komai ba a kaina. Nan dai suka mike suka bar dakin ina biye a bayan su sai dakin mai bi mata itama dai acan ba matsala sai cewan da tayi na daiyi hakkuri don su yara ne da su sa, a na dama wa yanda suka girmay ni. Mun bar dakin zuwa dakin wacce nake biwa ita ma din tana zaune da mutane da yaran ta bayan an gaisa aka fada mata zaman lafiya ake nema a gare mu. Sai cewa tayi haba zaman lafiya a tsakanin kishiya da kishiya ai sai dai zama na ki goga in goga tasan gidan da ta shigo ai har ta yar da ra kutso kai don kwadai ita da iyayyen ta. Ai babu wani zaman lafiya illa tazo ga tukunya nan lamba ashirin ta tuka mu tuka da ita don yau an zama daya. Daya daga cikin yan uwan mama tace to shi ke nan Allah ya bata ikin iya tukawa kamar yadda kowa keyi a gidan. Muka bar dakin muna jin ta tana yadda bakaken magana wai haka kawai an koso yarinya karama don jaraba an kawo masu a g raino a gida ace wai an basu amana. Dakina aka mayar dani aka zaunar dani a saman gadona da ya sha gyara nan aka shiga jero min nasiha na zaman lafiya har sai da na rasa na kamawa. Sukai min sallama suka fice gidan suka bar ni ni kadai a daki nai tsuru tsuru dani kamar manya. Ban san lokacin da wani kukan bakin ciki yazo min ba ga daki har daki amma ba ango a gurin ba gidan zaman lafiya a nan. Ina nan zaune a takure ni kadai a dakin naji sallama muryan mama naji uwargidan garbati na amsa mata sallaman ta a sanyaye. Tana dauke da wani zani kamar bargo na rufa da tocila a hannun ta na mike tsaye ina cewa sannu mama. Tace a, a Rahama ke kadai ce a dakin ashe to ga kayan kwanciyar angon ki na kawo maki idan kin kare girkin ki zakikaiwa wace zata karbi girki kayan ita ma a dakin ta. Bayani take min amma gabana sai faduwa yake min a lokacin na rasa fahintar komai da take fada min har ta fita tabar dakin ban fahince ta ba. Na kalli kayan data aje min a bakin gado tare da kura masu ido ina nazarin su. Na koma daga can kuryan dakin na zauna sama kujera tare da kara bin dakin wanda yake mallakina da kallo. Sai faman tunanen irin rayuwan da zanyi a gidan nakeyi ga maganan Sabuwa da ya tsorata ni da tace wai ni kishiya nake a gare ta. Baifi minti sha biyar ba da fitan mama din uwargidan shi sai na ji motsi alaman za, a shigo dakin nawa. Mamace again tare da maigidan nasu tana mashi jagora kallo daya zakai mai kasan baida cikkaken lafiya a tare da shi don yanayin tafiyan shi ma kawai ya nuna hakan. Da sallama ta shigo dakin yana biye a bayan ta ban iya amsa sallaman ba don girman su da nake gani. Tace Rahama ga anginki na kawo maki kin san dai yanayin da yake ciki da fatan zaki lalaba muna shi dai. Murmushi naji yayi ta juya ta fice daga dakin na mike daga inda nake na durkusa kasa nace a cikin sanyin murya ina wuni baba . Murmushi yayi yakai zaune a inda na tashi ya dan kalle ni yace yaya hidimar buki amarya ? Ban iya cewa komai ba sai sada kaina da nayi a kasa kawai babban rigar dake jikin shi naga yana kokarin cirewa tare da aje hular kan shi a gefe daya. Da alaman dama kayan sun ishe shi a jikin shi yake cewa dani sai kuma ga angon naki da matsala amarya. Sai lokacin na dan kalleshi naga duk ya ramay ya fada sosai ga yadda na san shi da farko. Dan tashi mana amarya ki miko min kayan can na saman gado na sauya ko ? Gurin da kayan suke na kalla tare mikewa zuwa daukowa na kawo mai na durkusa tare da bashi kayan. Ganin da nayi yana kokarin sauya kayan ne a gabana yasa nai saurin fita daga kofana na tsaya sai dana tabbatar da ya gama na shiga dakin. Yace yauwa zo ki zauna ko dauko ledan can ki dan samu kici wani abu daga ciki don nasan kina tare da yunwa. Nace a koshe nake baba sai da Inna ta tabani abinci naci kafin na baro gida dazun. Yayi shiru yana kallo na tare da nazarina sai kuma fuskan shi da na dan ga yanayin sa ya sauya a lokaci daya. Yace amma wanan din hakkin ki ne na yau da ya dace na baki ai na kawo maki. Nace a koshe nake shiyasa. Yace to ni miko min na danci kafin na kwanta ko ? Duk a takure nake a lokacin don yanayin yadda ya ke zaune cikin doguwar rigar jallabiya yasa nake kara jin nauyin shi sosai. To zo mana ki zauna nan amarya gaki tsaye kin kasa sukuni ko ? Gabana yai mumunan faduwa nace a raina wanan tsohon may yake nufi nazo na zauna zaman sa, a da sa, a dashi ko may ? Nayi maza na juya can daga gefe nakai zaune a kasa tare da dukar da kaina kasa ina wasa da yan yatsun hannuna cikin dan lankwasa su. Zuba min ido yayi a inda nake a zaune yana kallo na kafin ya bude baki yace Rahama yau gaki Allah ya kawo ki gidana cikin iyali na amatsayinki na mata tata. Yace don haka ina son ki kasance yarinya mai ladabi da biyayya ga wa yanda kika sama a gidan. Idan kinyi min haka kinyiwa kanki da nima adalcin rayuwa. Don bazan taba jin dadi ba a rayuwa idan har wani rashin mutunci ya fito daga gare ki a zaman ki na gidan nan. Idan kinyi haka kin min komai a rayuwana wanda hakan zai sakiji dadin zama dani bama ni kadai ba har ma kowa da zaki sama a gidan. Nace insha Allahu zaka samay ni kamar yadda kake tsanmani a rayuwana yace to Allah yai maki albarka ya tashi kata kata ya mike tare da nufar gadon da yasha shimfida yana cewa ki dai yi hakkuri da yanayi har na dan wani lokaci amarya. Daga haka naji yana bissimillah yabi lafiyayen gadon ya kwanta tare da mimikewa a sama yana sauke ajiyan zuciya. Can yake cewa idan kin gama zaki kwanta sai ki rufo muna kofan dakin daga ciki kinji. Nayi maza nace mashi tau ba, a dauki lokaci ba ina daga inda nake zaune naji ya fara nasari alaman barci ya dauke shi ke nan. A hankali na mike na nufi kofan na rufo kamae yadda ya umurce ni da nayi idan zan kwanta. Na koma kasa na kwanta ban dade ba sai barci dama jikina da gajiyan jigilar dana sha na jama, a atare dani.

Bani na falka ba sai asuba ana kiraye kirayen sallah naji motsin shi haka yasa na falka tare da mikewa zaune zubur yace a kasa kika kwanta Amarya ? Ya dauki buta zuwa bandakin da akai min a kusa da dakina basai na shiga na taron gidan ba sai bayan ya fito ne na shiga nai tsarki na dauro alwala na shiga dakin. Bayan nayi sallah ban kwanta ba tunda na saba a gida bana kwanci sai aikin gida idan na tashi na gyara gadon daya kwanta tare da sharo dakin har zuwa kofana inda aka kewaye min shi nagyara ko ina tsab. Na fita zuwa tsakar gidan duk girman shi sai dana share shi kafin gari ya karasa waye, Na hada kayan wanke wanken da na gani birjit ko ina na gidan na fara wankewa . Sai lokacin matan gidan da yaran su ke fitowa daga barci duk wace ta ganni sai ta tsaya tana mamaki hakan . Ina gaishe su daya bayan daya suna shigewa dakunan su da yaran su. Ina gamawa na juya zuwa dakina na debi ruwa na shiga na watsa na saka wani lace mai laushi dashi cikin kayan da anty ta aiko min dashi. Duk da ban san kudin shi ba nasan mai tsadane kwarai ga dinkin yai matukar karban jikina kamar an auna ni kafin a dinka min shi. Can na fara jin hayaniyan matan gidan suna fitowa tsakar gida daya bayan daya haka yasa na gane cewa sun tashi ke nan na yafa gyale a kaina na fito na fara zuwa sashen mama tana kokarin fitowa daga dakin ta tana ganina tai murmushi take cewa a,a amarya baki huta ba gaki da gajiya kika fito kikai wanan aikin haka? Hutun may zatayi bayan dama an saba da komai tun a waje muryan sabuwa ce dake bayan mu hannun ta rike da wani karamin roba kore. Na durkusa na gaida mama da ina kwana mama tace lafiya kalau Rahama yaya dare yaya angon naki ? Sabuwa ta kara cewa dare kan ai kinga inda alaman shi ya nuna ba a wahala ba don ansan komai. Haba sabuwa wai may yake kawo wanan magana hakan ga wanan karamar yarinyar kuma ? Wanan ai ba sa, an yin ki bace may ta sani akan zancen ki dakikeyi yanzu sai muryan maigidan mukaji daga bayan mu lokacin ina durkushe a gaban mama yana cewa. Sabuwa ki kiyaye ni wallahi a gidan nan don zan iya saba maki akan yarinyar nan a gidan nan fiye da tsanmanin ki. Idan ba hauka ba irin naki yanzu wanan yarinyar zaki titsiye a gaban ki kina fada mata wanan magana haka ? Ina yatinyar take tashige daki ta kwana da kai ta fito kemaymay da ita har kake kiranta yarinya. Yarinya kan na bayan uwar ta ai wace bata san shigewa daki da namiji ta kwana ba kuma ta tashi lafiya tarmazazai haka ?. Ganin dayar matar tana cewa kai haba tunda wanan farar safiyan haka za, a tusa muna wani fitina a gida. Na mike daga gurin mama na nufe tare da durkusawa har kasa nace ina kwana mama ? Tace a,a amarya ni ba mamakin bace zaki iya kira na da yaya ko maman Aisha. Nai murmushi na kara gaishe ta ta amsa fuskan ta ba yabo ba fallasa cikin sa dacewa yaya daren Amarya ya angon naki koda yake gashi nagan shi ya samu lafiya ai a gaban mu. Inda sabuwan take na nufa itama na gaida ita a cikin ladabi sai cewa tayi ke tashi da kili bibin ki idan ban kwana ba zaki ganni ne nan ? Yace uhumm kaji ba ke abinda baki taba yiwa yan uwan ki an maki kuma kina jin haushi yanzu . Ni dai ina ganin sun rikice na juya zuwa dakina ban tsaya sauraren su ba. Sai zuwa can naji ya shigo dakin shima dai gaida shi nayi tare da mai yaya jikin yace jiki da sauki sosai. Zuwa can naji anyi sallama ya amsa wata budurwa ce daga cikin diyan shi dauke da kwanon kunu da kosai taje cewa baba ga abin karyawa inji mama akawo maku. Yace kice ana gaida ita da aiki ko inda nake bata kalla ba tafita daga dakin har takai kofa naji ya kirata yace suwaiba kun gaisa ne da sabuwar umman taki ? Tace baba ai ban gan ta bane tabashi amsa murmushi tayi tace ina kwana . Nace mun tashi lafiya yaya gida bata tsaya ba tabar dakin yace taso ki dibi kunun da kosan mai isar ki kisha. Nace sai zuwa anjima bani karyawa da safe haka ai yace to injin ku yan boko ne ?. Da naji alaman suna aiki na fito na samu ashe kowa ce ta fito tana aikin sana, anta da takeyi a gidan . Na kama wa mama dama kokon da takeyi za, a fita mata dashi nan da nan muka gama. Sai mai bi mata dake dafa shinkafa da wake itama na karbi wanke shinkafan na wanke mata tas na zuba tare da gyara wutan da icce ya jaye na hura wutan sai gashi ya kama. Ban koma daki ba sai dana kwashe mata shi a kwano na gyara yadda za, a fice dashi na koma daki na. Na samu maigidan ya shirya zai fita yace ina kika shige ne Amarya nace ina gurin da ake aiki ne. Yace to ni zan fita sai na dawo zan dan leka waje nagani ko akwai abinda zan iya yi a can na neman kudi. Kin san angon naki dan bida ne ba mai zaman gida bane ni. Na durkusa nace Allah yasa a dace Allah yaba da nasara a dawo lafiya baba. Yace kai ni fa wanan baban ba son jin shi nake a bakinki ba da dai za, a canza min suna ko Alhajina akirani dayafi min alheri. Nace to Alhaji Allah yaba da sa, a yasa a fita a nasara yace amin yar amarya ta yaushe rabon da naji anmin fatan alheri haka a rayuna. Nan yasa kai yafice ni gyara dakin na dan zauna sai barci ya kwashe ni afurin mai nauyi ban sani ba. Muryan yan gidan mu ne da suka shigo ganin kwanana ya tayar dani daga barci. Na mike zubur ina masu sannu da zuwa idanuwan su fes a kaina suna kallona ban san may suke son fahinta ba daga gare ni. Na gaidasu daya bayan daya tare da tambayan sauran mutanen gida. Da yake iya yan uwan inna ne sai kadan daga dangin babana sai cewa sukayi kowa lafiya sai maman ku ne dai da ta saka muna hauka wai sai baban ku ya fada mata inda ya samo kudin da yai maki hidima haka na fita kunya. Duk rantsuwan da yai mata ba yarda dashi ba wai idan bashi ya yi ba mijinkine yaba da kudin aka boye mata. Nace cikin murmushi tare da zama kan makarin kujera na kai mama ho yaushe zata bar wanan halin nata ne na hassada da bakin ciki. Ita da tace da tabar za, a kawo ni yanzu da taga sabanin haka shine kuma ta tayar da hankalinta. Rabu da mahaukaci wacce bata son azauna lafiya iji kauna babana ta fadi hakan. To yaya kuka kwashe da matan gidan naku yau da safe da fatan babu wani matsala dai ko daga gurin su. Nai dan murmushi nace babu komai mama batare da na fada masu abinda ya faruba da safe akaina a gidan. Sai dayan mama tawa tace ai ina ganin indan dai ta iya binsu zata samu sauki ga biyun mata wanan dai da take biwa ce matsala nake gani sai yaran su kuma don naga yaran a tsaye suke suma. Nan dai sukaci ga ba da yi min nasihohi na in zauna da zuciya daya dakowa na basu girman su tunda duk sun haifeni baki dayan su.

ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU [16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, ,

IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WASU MUN BARKI GA ALLAH YA BI MUNA HAKIN MU A KANKI YAR UWA DA FATAN ZAMU JI TSORON ALLAH MU RIKE AMANA DON AMANA GIRMA GARE SHI.

Readers Also Read