Kenza eBookz

A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 95

A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 95

A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 95: A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 95. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU [16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi…

4,881 words

ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU [16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,

IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA NA,BARKI GA ALLAH,ALLAH SHI ZAI KARBA MIN HAKKINA A GARE KI ,,,,,

Saura yan kwanaki a fara azumin watan ramadan ko ina,kasa shen musulmai sai shirye shiryen taron wanan wata mai alfarma da albarka dake tafe a,wanan lokacin aketayi manya da yara da,tsofi duk farin ciki suke da wanan wata mai albarka . Zan iya cewa rashi dawowan sadauki a cikin lokacin da nake gani kamar har za a kama a azumi bai dawo ba garin a lokacin. Babu wani abin da na rasa,a gidan daga na ci da,sha da sauran abubuwa amma kuma sai na kasa gane may ke yawan haddasa min bacin rai haka na rasa ganewa. Gidan baba sai abin arziki yake samu daga diya da sarakain shi da,abokan arziki na gari. Ba kunya mama take habaici wa baba wai gashi dan na shi bai kawo ba amma fa wa yanda ba,a so sun kawo don sune ,ba,a so da alheri gashi Allah ya hore masu sin kawo mashi ya karba yana washe baki . Kai tun abin yana damuna har yakai yanzu na daina damuwa da rashin dawowan shi wanda wata biyu.ke nan rabon shi da gida. Sai yaya bashar mijin maryam abokin shi shine kawai ke dawainiya da mu tako wani fanni duk da,ban taba cewa muna bukatan wani abuba a gidan na rayuwa. Maryan yanzu cikin ta yakai wata biyar ke nan a jikin ta don har ya turo sosai mutum zai iya gane haka atare da ita duk cikin mu ita kadaice Allah yabawa haihuwa. Da kafa takan tako daga gidan ta zuwa gidan mu don motsa jikin ta idan zata koma tare muke fita har Iya mu taka mata mu rakata gidan ta don bamu da nisa sosai. Da dare muna cikin falo zaune ni da Iyan Rabi muna hira waja jen karfe tara na dare a lokacin . Sai jin sallama mukayi kamar daga sama muka ganshi har ya shigo tsakiyan falon a lokacin. Sadauki ne ya shigo muna gidan da sallaman shi ya murje yayi wani kyau yayi haske kamar wani dan kwara dashi. Cikin fara,an shi da walwala ya shigo muna a lokacin daga ni har Iya sai sannu da zuwa muke mashi a lokacin. Ganin da nayi fuskan shi a sake yake, yasani nima taron shi a cikin farin ciki kamar babu komai a tsakanin mu can baya. Zama yayi saman kujera tare da fadin wassh Allah Iya tace sannu na wurina da kokari andawo yaya hanya yaya aiki da sauran jaman can. Na,dawo daga,kai jakar kayan shi daki na nufo shi tare da dan dukawa na rugumoshi ban damu da wai iya tana gurin ba shima dai rungumoni yayi zuwa jikin shi. Iya dai kunya taji ta juya zuwa kitchen abinta tana murmushin yadda taga mun burge ta sosai a yanayin mu. Zauna da ni yayi saman cinyan shi yana sauke numfashi tare da kai hannun shi a saman wuyana a hankali yana dan shafawa cikin lumshe idanuwan shi. Daga inda Iyatake a tsaye take cewa uwar dakina nace ko sabon girki zamu dorawa yaron nawa ne ? Itace tadawo muna da hankalin mu muka tuna a inda muke zaune a lokacin. Da,sauri yace a,a kubar shi kawai zan sa,akawo abinda zanci yanzunan kafin nai wanka. Mikewa nayi daga cinyan shi nake cewa Iya zo zauna ki huta abinki ai dan naki bai faye danuwa da abinci ba idan bashi yaso ci ba kuma bama komai ne yake ci ba shi dole yanzun sallon abincin mu ya canza ai . Maimakon tazo ta zauna sai ta shiga dakin ta yana tambayana yaya muke yazaman mu da Rabin dan musa nace bata da wani matsala wallahi ita ai mutum ce mai dadin zama ga tsabta ga aiki bata gajiya wallahi. Sai ganin Iya mukayi da dan jakar bakon ta tafito daga daki tana fadin uwar dakina nikan zan tafi tunda maigidan yadawo yanzu. Da sauri dani dashi muke hada baki cewa haba dai ina kuma zaki kuma iya yace Rabi ina kike nufin zaki kuma ina anan zaki zauna gaba daya kina debe muna kewa kuma. Tace a,a haba nawa ina zan zauna a tsakanin ku na hanaku shakakatawa kuna sabbin ma,aurata da ku. Iya bafa inda zaki idan kika tafi dawa kike son na zauna a gidan nan idan ya fita shi ko baya garin ? Ba sai na dawo ba idan yai tafiya din amma zan zauna na hanaku hutawa a tsakanin ku ? Murmushi yayi tare da mikewa ya nufi inda take tare da karban ledan hannun ta yana cewa wai maji bata fada maki cewa zama zakiyi muna a gidan nan ba. Tace zama Alhaji yace ai babu inda zaki don kinzo kenan nan zamu zauna dake gashi kuma nayi sa,a uwar dakin naki naku yazo daya da ita yanzin . Murmushin jin dadi iyan Rabi tayi tace ai Alhamdullahi don kayi sa,an mace tagari da kowani namiji ke bukatan samu a rayuwan shi. Murmushi yayi ya shiga dakinta ya aje mata jakar kayan ta yafito bayan yabi dakin da kallo yaga komai akwai shi dakin na rayuwa yafito bai zauna ba don ya fahinci zaman shi zai takura mata sai ya wuce zuwa cikin dakin shi direct. Cewa iya nayi bari naje na hada mai ruwan wanka ya dan watsa yaji dadin jikin shi. Tace afiti lafiya hajiya nabi bayan shi zuwa dakin yana duke yana cire takalman cover shoes bakaken dake kafan shi da safa. Da sallama na shiga ya ansa min yana dagowa daga duken da yake yadda ya ansa min a cikin sakin fuska yasa na karasa gurin shi. Cikin kwarin gwiwa ya zuba min idanuwan shi na ce yaya hanya ya gajiya kuma? Kalau yabani amsa da hakan nakai gare shi tare da kokarin fara balle mai aninin rigan shi ta gaba. Cikin sanyin murya naji yana cewa kin huce ke nan da mijin naki Fatima ? Nace don girman Allah yaya ka daina wanan maganan adai gyara gaba please ? Wallahi yaya yadda kasan mama bata kaunan wanan abinda kake yi haka zalika nima bani kaunan ganin ka cikin wanan irin yanayin don kwata kwata ban iya controlling din kaina a hakan. Nakan jini ne kamar wata mara sa,a acikin mata don sai nake ganin kamar dunuya zata zageni a dinga nuna ni. Wata uwar harara ne ya balla min bashiri na kama bakina na kasa cigaba da maganata. Cikin maganan tausayi yace min don kina son na daina Fatima shine zaki dinga nisanta kanki dani ? Saboda kin mayar dani shasha haka kike zaton kowa yana dauka na a idon shi ko ? Na katse shi da cewa kasan halin mutane yanzu yaya bazasu iya fada maka gaskiya ba a gaban ka don abin hannun ka. Yana da kyau kai nazari akan zance na zaka gane manufata a gare ka ba don na rainaka bane ko wani abu a,a yaya gani nayi idan ban fada maka gaskiya ba a yanzu waye zai fada maka shi. Tsaki naji yaja yace kinga malama idan kin zo ne ki taimaka min kiyi abinda ya kawo ki . Idan kuma har yanzu raina manin wayyo ko hankali zakiyi ki fice min daga daki rainin hankalin naki yana son yai min yawa. Ke yarince dake zaki min wa,azin da mahaifana basuyi min ba ko may ? Naga baki son mu zauna lafiya a gidan nan dake don nafahinci kina son ki wuce matsayinki a gare ni. Raina ya baci nace amma yaya dama inaga dai ka yadda ka auri ni ne don ka dinga ci min mutunci ko ? Kiyi wa Allah idan kasan bada zuciya daya kake zaune dani ba baka sona ne ka sallamay ni na tafi gidan mu ka huta dani. Wani irin kallo yai min yace Fatima ke da bakin ki kike fadar na sallamay ki kikoma gidan ku? Shiru nai mashi yace ok idan haka kike so sai kikoma ki fadawa wanda suka hada mu sai su raba mi tunda shi kike bukata ke ? Naga idan na biye mai daga dawowan shi zamu sake samun matsala kuma again. Sai nai amfani da shawaran yaya bashar da anty maryam na wuce shi zuwa bathroom na hada mai ruwan wanka tare da,aje mai duk wani abinda zai bukata na amfanin shi ciki. Yana shiga nafita daga dakin raina a bace da yan maganganun da mukayi da shi yanzu na koma dakina na zauna a bakin gadona ina tunane. Shima dai yana can yana wanka tunanen maganganun da mukayi dashi ne yasan ina da gaskiya na amma bai bukatan na shiga harkan shi har takai na takurawa zamantakewar mu dashi haka. Yafito ya shiya cikin rigar barcin shi falon ya dawo sai dai babu kowa a falon sai tv dake aiki shi kadai a lokacin. Kamar ya shiga dakina amma sai yadake kawai ya zauna tare da canza tashan zuwa na kwallon kafa. Jin motsin shi afalo danayi na sauke ajiyan zuciya maganganun su yaya Bashar da suka fada min na dole ne sai na kwanta mashi sosai zan iya,aiwatar da,shiri na akan shi yasa na sauke ajiyan zuciya tare da mikewa na fita. Rigan barci ke jikina alokacin sai faman kamshi ke tashi a jikina dan na gyara jikina bayan fitowa daga gurin shi nima. Murya na yaji a bazata daga bayan shi don baiyi tsanmanin zan kula shi bakuma har yadan shiga dan damu akan yaya akayi ya bari muka dan sake samun sabani bayan yaga na sauka daga fushin da nakeyi da farko dashi. Cewa nakeyi abincin da kace za,a kawo maka kaci fa kuma gashi baka bari mun dafa maka ba ? Ya dan dago kai inda nake yana cewa No ki barshi kawai banjin cin komai yanzun ma zai sha drinks da tea na sai na kwanta. Nace lokacin dana karaso inda yake a zaune yaya drinks kuma shi zai sa ka koshi yace is ok kawai. Zan zauna yace dauko min laptop dina na duba wani abu a daki please ? Juyawa nayi zuwa dakin nashi na dauko mai system din nashi maishegen kyau da tsada. Mika mashi nayi na juya zuwa kitchen tare da dora ruwan tea din nashi sai dai na faki idon shi na barbada garin maganin da,akabani in bashi yasha din a ciki. Najuyo mai tare da dauko drinks da cup har dan flaska din shayin nakawo mai. Yace inji lemon baida sanyi don kinsan mutum bai shan ruwan zafi dana sanyi a lokaci daya don gudun cancer. Nace baida sanyi sosai amma dai bari na zuba ma a cup sai ya huce kafi ka sha. Dakin Iya na wuce don jinta shiru danayi yau ba hira ke nan ta boye a dakin ta don ganin shi a gida da tayi. Na samay ta tayi barci sai rufo mata kofa tare da kashe mata wutan dakin dake a kunne lokacin. Na samu har ya bude system din shi ya fara aiki da zaiyi dashi a kan three seat yake zaune nima saman na zauna tare da kaiwa kwance ina kallon tv dake aiki. Can na dan ja tsaki tare da mika hannu na daga kwance na dauko remote zan canza chanel din naji yace baki son wasan ball ke nan dai ko ? Murmushi nayi tare da kai kaina saman cinyan shi nai filo dashi nace wallahi ni ban taba fahintar may ake ba a cikin shi don ban san komai ba akai. Dariya naji tayi yace kai amma shame on you matar dan kwallon duniya kuma bata san ball ba aiko kinji kunya wallahi. To yaya kunyan may tunda badani ake zuwa yin ball din ba can nan kuma ina diyan hausawa yaya zan san wani ball can a rayuna. Yace aiko ya zama dole ki sani don kada wata rana a tambaye ki mijinki dan lanba nawa ne ki kasa bada amsa naji kunya. Duk hiran da mukeyi hankalin shi na,wurin abinda yake acikin laptop din shi lokacin baidago kan shi ba. Muryan shi na kara ji again yana fadi amma ki saka a,ranki kulba dade kul ba jima akwai ranan da,zaji hade da yan jarida zasuyi mako inter view akaona da kan ki don har sai ki fara shitleya basu amsa da zaki fada masu. Da sauri tare da dan dagowa daga kafan shi ina kall9n shi nace ni nidai din yaya. Yace cijin murmushi kekuwa Fatima din nan rana da lokaci sina tafe muddin muna araye zasu tambaye ki. Komaqa nayi na kwanta kamar yadda nake da farko tare da ajiyan zuciya nace ashe akwai aiki kuwa ke nan. Dariya sosai na bashi yadda yake dariyan yana ci gaba da,aikin ya ban sha,awa ban san lokacin da nakai hannuna ga fuskan shi ba na shafo a hankali. Wani irin irin ajiyan zuciya ne naji ya sauke tare da lumahe indanuwan sho gyaea kwanciya nayi akan jikin shi nace. Basai ka fada min abinda zan fada masu ba ko kuma nace ni ban san duk wani tambayan da sukai min ba ma. Ban san har ya rufe laptop din nashi ba sai ji nayi ya mike ya nufi gyrin tv ya kashe tare da kashe sauran na,urorin falon inda nake yazo ya dauke ni cak ya hada da computer din shi sai dakin shi. Saman kado ya dire mu ya jaye laptop din ta fado min saman jikina yana fadin barin fada maki abinda zaki fada masu tunda shine kawai kika sani a gamay dani. Bakina ya lalabo ya fara kai min kiss mun dade a haka can ona jin dadin abinda hannayen shi suke min sai kuma naji ya tsaya tare da zare bakin shi a cikin nawa a hankali Ya juya yana mayar da numfashi a hankali can yake cewa sorry fa kada kuma na sake maki fyede again . Ban san lokacin da dariya ya kamani ba nace yaushe kuma ai kasaba min yanzun ma gashi kayi min din again. Auto ashe bari ma na karasa tinda har nayi maki ma waida kada nai lefi nake gudu nace cikin dariya ai kaf8n kai min wallahi sai na rama nima don yau nice zan maka fyede da kaina. Kafin yasan may zanyi har na juya na haye mai ruwan cikin shi ko a hakali na cire mai rigar jikin shi bai hanani ba nan nashi ga nuna mai wani sallon da ni kaina ban ban san ina dashi ba. Sosai muka gwadawa wa junan mu how far we miss each other a lokacin, tsawon lokaci muka shayar da junan mu zuman ma,aurata ranan masha godiya ba adadi a gurin shi kamar ba yaya sadauki bane mai izzigilancin nan. Bayan komai ya lafa a tsakanin mu sai zancen shayin dana hada mai da magani yafado min a raina. Gabana ya fadi kada yazo baisha ba ai hasaran maganin gashi yaya bashar ya jadda min na tabarar da yasha ahi sosai fa. Ikon Allah sai naji yace ni wallahi har kin sani jin yunwa ma sosai wallahi nace ai ruwan shayinka na nan baka sha ba. Yace anya yadda nake ji din shayin nan kuwa zai dauke ni a yanzu gaba na ya kara faduwa kada yazo bai sha ba fa. Muryan shi ne yake fadin tsiyayo min insha kada kice zaki fita yin wani dahuwa da daren nan kuma. Don keta sai da na zuba mai da yawa kuma nai sa,a duk ya shanye cup din gaba daya. Sai da ya shanye yake cewa amma sai naji shayin ya dan canza test yau ko ya fara expire ne dai nace ko kuma don ya dade a bude yai sanyi yasa shi canza test ba yace indai a bude yake shi ya kawo hakan gaskiya. A haka muna dan hira naji yayi shiru barci ya kwashe shi lokacin ga gajiya ga aikin magani ke nan. Mikewa nayi nashiga bathroom nai wanka tare da dauro alwala nazo nai sallah raka,a hudu ina rokon Allah yasa mu dace ga maganin. Muna barci can shiyoyin asuba naji cikin barci yana wani irin nishi sosai abinda ya falkan dani ke nan a dan firgice cikin tsoro yadda naga ya dunkule guri daya ya dafe cikin shi. Cikin tsoro nake magana yayana may ya samay kane may ke damun ka kuma ? Cikin shi ya nuna min da hannu nace a dan razane subbahanallahi ciwon ciki kuma ko may ya gyada min kan shi da kyat . Nacw daure mu shiga bathroom kadan yi wanka ko zakaji dama sai na fita na hada ma abinci ko yunwane don kaga jiya bakaci komai ba ka kwanta hakana sai ruwan shayi . Ban samu amsa ba sai murde murden da yakeyi a lokacin kawai na ciwon ciki na mike na shiga na hada mai ruwa na dawo ina yake kwance. A hankali na duka cikin kunnuwan shi ina rada mai ya tashi mu shiga bathroom din yai wanka hannun shi ya miko min da taimakona muka shiga har bandakin . Ranan dole yanayin da yake ciki na cire kunya na hada mai ruwa da kaina nai mashi wanka wankan tsarki ne kawai ya daure yayi da kan shi lokacin. Ba laifin wankan ya sa yaji dan sauki ana kiran sallah mukai sallah ya koma ya kwanta nafito zuwa sama mai abinda zaici inayi ina lekashi dakin shi. Ranan a daki nakai mai ya dan daure ya tsakura kadan yaci yace baijin dadin bakin shi ko kadan. Koda Iya tafito ta samu na hada abin karyawa ko sai gyaran gida kawai tayi nafito daga dakin a cikin shirina na samay ta tana aiki muka gaisa da ita. Tana tambayana kwanan dan ta nake fada mata wallahi Iyya yau dannnan naki ciwon ciki ne ya hana shi barci . Tace da sauri subbahanallahi ciwon ciki kuma da sauki dai ko nace da sauki don ya ci abinci yace idan ya tashi zai sha magani . Dakin na koma sai dai bai saman gado yana bayi ina na tsaye har zan juya sai naji yana kakar8n amai daga cikin bandakin . Da sauri na isa gurin amai yake shekawa wani irin bakin amai ba dadin gani. Wasa wasa amaiko yaki tsayawa sai faman sheka amai yakeyi hankalina yai matukar tashi sosai na fita na kira wayan yaya bashar na fada mai sadauki fa ba lafiya ciwon ciki da amai ya damay shi. Yace subbahanallahi gani nan zuwa yanzun nan muna gama waya dashi nake shawaran kiran mama na fada mata . Itama kiran ta nayi don kada taji daga baya taimin fada gata tana a cikin gari kuma. Tana ganin wayana tunda safe haka gaban ta ya fadi ta dauka take tambayana Fatima lafiya ko nake fada mata abindake faruwa tace subbahanallahi gamu tafe yanzu. Yaya bashar ne ya fara shigowa lokacin muna ban daki dashi har bedroom din yashigo nan yasamay shi yana wanan bakin aman nashi. Yace subbahanallahi man may ke faruwa ne kuma yadago kai da kyat jin muryan aminin shi idanuwan shi sun canza launi sosai. Yace wallahi ban sani ba man ciwon cikine sai kuma amai da ya biyo baya da kyat yake iya magana a lokacin . Shi ya kamashi ya kwanta bai dade da kwanciya ba sai ga baba mama da mummy sun iso suma. A falo suka fara zama nazo na gausa dasu suke tambayana nake fada masu abinda yakeyi ai sai aje asibiti baza a barshi a gida ba hakana bamu san may ke damun shi ba . Naji tsoro sosai a raina kada aje asibiti ace poison aka bashi fa yaci nawa ya samay ni garin neman kiba na samo rama kuma. Mun shiga inda yake kwance sai faman murdan ciki yakeyi sosai yana juyi mummy ta dan dubashi tare da bashi tace Alhaji aje asibiti kawai. Ina gefe daya a rakube hankalina a tashe yace No abari kila zai bari ai baba bai yarda ba suka sashi a gaba ya tashi aje asibiti dai. Inda nake tsaye idanuwana suna fitar da hawaye ya dan kalla yace cikin karfin hali Fatima dauko min kaya na saka. Jin haka suka fito daga dakin suka barmu a tare sai kuka nakeyi cikin karfin hali bayan ya gama sa wando ya jawoni jikin shi yana cewa. Ki daina kuka mana Fatima bakya son ki rasani ne ko ? Ban bashi amsa ba na saka mai rigan tie shirt tare da dan shafawa fuskan shi dan mai sai ajiyan zuciya yakeyi sosai. Bashar ne ya leko yake cewa yagama ne mu tafi nace mai eh a lokacin ina rugumay a jikin shi muka fito daga dakin da kyat yake tafiya. Har sun fita bashar ya dawo cikin gida kaman zai dauki abu yace min a hankali kin bashi maganin ne nace mai eh yace ok dama ance zaiyi amai ya wahala sosai kada ki damu komai basu ganewa ai. Shiru shiru suna,asibitin dashi muna gida da Iyya hankalin mi a tashe sosai a lokacin dashi. Mama ce ta bugo waya tana fada min in kwantar da hankalina likitoci suna kan shi suna bincike yanzu haka. A raina nace ina naga kwantar da hankali asirina zai tonu haka kuma daga taimako . Sai guraren sha biyu da wani abu bashar ta dawo gidan yake fada min an bashi gado asibitin sunce wai canji ruwa ne ko kuma yaci wani abu a can wanda suke gani kamar bai dace da cikin shi ba. Nan yake ce min mama tace yazo yaje dani yanzun don suna son zuwa gida suyi sallah su tinda yadan ji sauki . Mun isa mun samay shi kwance yana barci har ya fada sosai bashar yake tambaya baiyi aman ba ko sukace yayi har sau biyu bayan tafiyan ka ai. Ina tsaye kan ahi na kura mai ido ina kallon yadda ya koma a raina nake cewa wabda duk yai maka wanan asiri Allah ya saka maka. Muryan mummy ne take fadin bari muje gida mu dawo sai azo maku da abinci nace ai da a barshi Iyya tana can tana hadawa ai. Sun wuce aka barni da yaya bashar basu dade ba maryam suka iso da mahaifiyar yaya bashar din nan muka zauna atare dasu. Sai dai mama tana bugo waya akai akai tana tambayan ko ya tashi a lokacin ko yana aman har yanzu ? Nace bai kara yi ba yana dai barci ne tace Fatima kada ki yarda a cika dakinbda suruti kinji ku barshi ya huta please nace to mama. Nan kuwa muka fara ganin yan uwa da abikan arziki harda ma wanda bamu sani ba suna shigowa gaidashi. Mummy tagama shiryawa tace wa mama su fito su zo mama tace haba hajiya kubura kamar ban gode ma Allah ba ke nan ai. Gaki ga matar shi da yan uwa a kan shi may kuma zan koma yi adduan mu yake bukata kuma ya samu ko? Allah dai ya bashi lafiya sai kun dawo agaida su mummy taji dadin hakan sosai suka tafi tare da,Abdul. Yadda yan uwa suka nuna mai yasa na gane cewa sadauki dan gatane sosai don sai ga yaya Imiran da matar shi tare da abincin sukazo muna. Nan dai guri ya cika makil Nafisa da kawayen ta sun shigo su ma nan suke cewa yanzu Naffy ke fada muna mukace bamuga zama ba ai uwar dakin mu na cikin tashin hankali. Kowa yai mamaki jin abinda suka fadi may ye hadina dasu kuma sai cewa Raiha tayi muna zuwa muna cika cikin mu ana muna,taron arziki ai dole ne mu zo gurin ki. Wani likitane ta ke duba shi ko na kira P M O ne yazo da kan shi ya duba muna shine dai. Kowa yasan zasu uya don sunyi kamari wuce pmo ma balle director gaba daya. Yaya Ahmed suka shiigo da matar shi jamila a lokacin dressing din ta kawai ya isa mutum ya gane ko ita wacece. Sai yatsune yatsune takewa mutane tana kallon shi tace au ashe shine ban ma taba ganin shi bani. Sosai na mayar da hankalina gurin su Nafisa da kawayen ta muna hira maryam sai haushina suke ji da Amirah. Suko yadda na ke tare da,su yai masu dadi sosai a ran su don sai jana suke da hira ina dan murmushi. An cika duk yan gidan su ne gungun gungu a haraban gurin falkawa yayi da karfi yake kiran Fatima Fatima da sauri yaya bashar ya shiga dakin Abdul ne yakirani. Na mike da sauri gabana yana faduwa idanuwa aka sako min caa da kyat nake tafiya a lokacin. Jamila matar yaya Ahmed bata sanni ba sai ranan take fadi au matar tashi ke nan ashe ? Ina shiga ya falka Bashar yana tsaye a kan shi lokacin na karasa gurin shi ya miko min hannun shi yana cewa zauna kija min hannu na da kafa please. Mummy ma tashigo dakin don ganin ya falka a lokacin tana mashi sannu da jiki ya amsa mata da kyat da sauri ya dago yana son mikewa yace amai yake ji sosai da sauri na dauko roban da aka sayo don ya dinga yi a cikin shi. Amai yayi sosai bakikirin dashi nan hankalin duk wanda ke gurin ya tashi sosai sai kawai ya rufe idon shi ya zama colarbs jiki ya sake mai da sauri na karasa ina kiran sunan shi bashar yace na fita dakin . Don kuka yaci karfina a lokacin ganin na fito ina kuka yasa mutanen da sauri suka karaso jikin maryam na fada ina kuka tace may yafaru nace baya numfashi maryam da sauri mazan gidan su suka shiga gurin shi dakin Ina nan naga bashar yafito da sauri ya nufi gurin likita duk wanda ke gurin hankalin shi a tashe yake sosai naji dadin su Nafisa da kawayen ta don sun nuna damuwan su sai akaina. Likita yazo da sauri suka shiga dakin yana fadin suma yayi bayan ya duba shi ai hankalin kowa a tashe can sai ga baba da su umma sun zo. Ikon Allah sai Nafisa ke fadin to baidai mutu ba balle aji dadi ba,azo ba sai yanzun da akaji ance baya da rai yana nan daram. Taba wasu haushi musaman yan uwanta amma babu yadda suka iya da halinya dole aka saka mata ido uwayen dai sunji kunya sosai. Yana falkowa yake fadin Fatima jamin hannuna da kafa please, sai da yaba kowa tausayi a dakin na koma dole dakin duk da ga iyayyen shi amma ina dan matsa mai hannayen shi da kafa a hankali. Har dare muna tare da mummy don cewa tayi anan zata kwana amma sai yaya bashar yace duk mu tafi gida dashi da sagir da Abdul zasu kwana gurin shi. Hakana na kwana a cikin zullumi tun da safe washegari ina asibitin gurin shi. Ance mutum mai yawan bautar Allah yakan zama wani lokaci kamar waliyi ne saboda yawan ibadan shi. Hakane ya faru da mama don tai sallah nafila tadan zauna tana tasbihi kafin a kira sallah asuba tayi sallah. Nan tai mafalki ana ce mata kada ki damu taimakon shi Fatima tayi amma zai mike. Ta falka firgigi da ita tana cewa subbahanallahi Fatima kuma haka yasa zuciyar ta zargin akwai wani abu a kasa amma koma may ye zata binciki Fatima din taji. Sun shigo gaida shi da safe ne ta kirani gefe muka gaisai da ita can ta dafani tace ki kwantar da hankalinki insha Allahu zai samu lafiya kinji. Can naji ta dafani sosai tace Fatima may kuka ba saudauki ya shane haka mai karfi don nagani a mafalki na yau. Ras, ras gabana ya fadi uku uku lokaci daya nadaugo kai na da sauri na kalleta tace ba boyo tsakani na dake fada min nace cikin kuka mama yaya bai bar sha ba har yanzu. Shine yaya bashar ganin muna yawan samun matsala ya koma gurin mutumin nan shida maryam suka anso wani wanda zai amaye abinda yasha gaba daya a jikin shi. Ina fadin haka na dago kaina kalle ta murmushi naga tayi ta dafani tace Allah yai maku albarka Fatima kun karasa aikin dani ce ya dace nayi shi tun farko. Kuma duk halin da kuke ciki na sani maryam ba ban sani bane amma tunda kikayi yadda nake so dake rufin asiri a tsakanin ku yasa na ja bakina nai shiru dashi. Tace ban son jin zancen nan a bakin kowa daga Allah sai ku da kukayi don koshi kada ki yarda ya fahince ki don zai dauka wanan wahalan da yakeyi kashe shi kuke son yi ba taimakon shi ba . Don haka ki rike wanan sirin a ranki ki boye sirin mijin ki danaki a kowa kinji Allah yai maku albarka nagode Fatima abinda nai hasashe ke nan tun farko akan ki. Tare da mama muka dawo dakin yana zaune ya ramay ya fada sosai kamar bashine yadawo bulbul dashi ba. Ya samu sauki don aman ya tsaya sunce har cikin dare sai da yayi aman sosai bakikirin dashi. Yanzu sai barcine ya ke damun shi da ya dan falka sai ya koma yaci gaba da barcin shi. A sibiti muka fara azumin wanan shekaran da wata ya kama na azumi amma ya samu sauki sosai. Azumi uku mukayi a asibitin aka sallamashi ya dawo gida nan naci gaba da jinyan shi da kaina.

Readers Also Read