Kenza eBookz

Abadan complete hausa novel - Chapter 22

Abadan complete hausa novel - Chapter 22

Abadan complete hausa novel Chapter 22: Abadan complete hausa novel Chapter 22. gaza daurewa tayi a wannan karon ma sai data dago ta dubeshi cikin mamaki…

3,337 words

gaza daurewa tayi a wannan karon ma sai data dago ta dubeshi cikin mamaki shin abdallah yasan akwai masu farautarsa ua qyale ya zuba musu ido?,tamkar yaji abinda take zantawa cikin zuciyarta yace ''kada kiyi tsammanin abdallah wawa ne bansana ana farauar rayiwanshi cikin gidan ubanshi ba,i know kuma zuwa gobe zaki ga abinda zaya faru,naki kawai answer din question dina.....gaba ta gaba,are you ready madam?'' kai ta sake gyada masa kamar qadangaruwa ''ok,mami is unaware game da wadda na aura,nayi haka ne saboda ina son inyi suorising dinta,ta bani komai a rayuwa bansan me zan bata ba,na sani baya ga ni kece ta biyu cikin diyoyin da take so,bata san diyarta na dawo mata da ita ba,na tabbata zatayi matuqar farinciki da mamaki da ganinki...saidai kinsan me?,farincikinta da mamakinta zai dore ne matuqar taji cewa auren so da qauna ne tsakaninmu,kinsan abun duba?duk wani motion da act namu zai zama irin na masoya a gabanta daga wunin yau zuwa goben tafiyarki babu musu tsakaninmu,yi nayi bari na bari wannan shine abubuwan da zasu sana miki takardar rabuwa da ni thats all''

gaba daya ji tayi ya daurera da duka jijiyoyin jikinta,wadan nan tsauraran sharuda har ina?,har gwara ya samu bulala ya bugeta yadda yakeso kana ya sallameta yafi nata sauqi,ina zata sami tulin amsoshin tambayoyinsa wadanda bata tab tunanin ma a kansu ba?me yake nufi yace da ita?,ama ture ta wannan baki daya,ya zata iya tanqwara zuciyarta ta nuna alamu na soyayya ga mutumin da babu so ko qwauar zarra tasa cikin zuciyarta.....

''idan kuma baki iya tsallake wadan nan abubuwa.....fine....sai ki shimfida ta barma da daura damarar zama da abdallah kiga idan bazai saceki gaba dayanki ma ba zuciyarki ba cikin kwanaki talatin kacal,hakan kuwa kinga bazaya miki dadi ba tunda kince wai baki sonshi bayan tsayin daka da kikayi wajen kare mishi ranshi da lafiyarshi don kina da buqatar ra......'' ''naji....naji na amince''ta fada da sauri don katse soki burutsun da tace yana shirin yi mata ''good job,shikenan Allah ya bada sa'a''ya miqe daga inda yake,har yayi taku biyu ya kalleta still tana duqe ''kada ki manta da answer din tambayoyi na,don sune bqngare na farko na yarjejiniyar mu''

Sakaliyar la'asar ce data gama hada hadari wanda ya tilastawa garin lumshewa,sannu a hankali suke taku wanda idan ka gansu sai ka rantse shaqiqan masoya ne guda biyu hannayensu sarqafe cikin na juna,sanye suke da kaya kala daya saidai bambancin sunan yadikan,nata material ne na mata yayin da nashi ya kasance na maza,dukkansu sea green colour ne,abu daya zai saka duhu yadda fuskanshi ke qunshe da wani irin haske da annuri,yayin da nata fuskar ke duqunqune cunkushe da bacin rai duk da hakan bai hanata yin kyawu ba,maryam ne da abdalla kan hanyarsu ta zuwa gaida mami bayan ya tabbata da jama'ar gidan kowa ya koma inda ya fito

sunfi minti talatin cikin bangarensa yana nuna mata salon kallo magana da ladabin da yakeso tayi masa gaban mamin wanda hakan shi ya kusan janyo rikici ya sake waiwaya ya dubeta suna gab da ahiga bangaren mamin kana ya dakatar da tafoyar tasu,tsatstsareta yayi da kallo,ta kauda kanta tana qoqarin sabule hannayenta dddaga cikin nashi ''malam bamuyi da kai zaka dinga min akallon mayi ba ko,idan kuwa kaci gaba daidai nake da na koma inda na foto na hada ya nawa ya nawa na koma inda nafi wayo'' ''kya sha tsinuwar Allah data mala'iku,runda ko banza miji nake agareki koda qarshen duniya zaki gudu,nike ma da magana dake,kinfara karya wasu dokokin tun yanzu,wanda hakan na nufin tangal tangal da muradinki ne,haka koka ga fuskar amarya na kasancewa washegarin ranar da aka kanta,look at ur self don Allah,jiya kin kwana kuka idanunki sun koma kamar kumburarren qullin qosai,an samu da qyar sun daidaita kafin yamma,sanna kina son ki sake wargaza mana shiri,to wlh u hv to make sure idan kika bari mami ta dago wani abu babu ke ba samun takardar sallama''

wani tafarfasa zuciyarya ke mata,ta debi a qalla mintina biyar kafin ta iya controlling kanta ta sauyawa fuskarta mood sabanin na dazu,cikin tafasar zuciyq ta miqa masa hannunta shkuwa yasa nashi hannu ya riqe suka ci gana da tafiyarsu daga nesa tamkar ka sacesu don kyai tsaro da marching da sukayi

A guje ta juya kamar zata ci da baka ta koma bangaren nasu tana zabgawa nene kira,saura kadan ta take zubaida dake kwance agashiyyan wanda cikin nene adnan da zahariyya an rasa wanda zai ce da ita yi haquri ba don komai ba sai don tsananin haushinta da sukeji kan wanda ta shiga halin sabo da shi da sauri nenen itama ra iskota don dana a tsaye take cikin safa da marwa ''yaya?,ya ake ciki?'' cike da tsananin tashin hankali kamar wadda aka gaya mata uwa da uba duka sun mutu tace ''wallahi nene yana nan bai mutu ba,tas na ganshi babu abinda ya tabashi wallahi,tare suke da yarinyar nan nene bata bar gidan nan ba,hannayensu riqe da juna,mun shiga uku nene kada dai ace ita ya aura?''maganar ba qaranin sa nenen tayi a tashin hankali ba,a aukwane ta juya kan kujerar data tashi zata dauki wayarta,garin rarumar wayar ta dauki remote,sai data fara dannawa ta lura ahine,wurgar da shi tayi ta suri wayar kai tsaye ta kira malam na hayi

Mgunyar dariya ya dinga kwarawa kafin yace ''sanda muka gudanar da aikin bata cikin gidan,don haka ki kwantar da hankalinki ki zuba ido kiga abinda zai faru,saidai babu lallai abunda zai farun ya zama abunda mukai nufi da shine,kasantuwar yarinyar na tare da shi''yana gama fada ya katse wayar,nene ta dubi wayar tana jadda maganar daya gaya mata,saidai ta samu relief jin cewa wani abu na iya faruwa da abdallan,nasu kenan yanzu zuba ido suga mai zai faru kenan?

cikin falon mamin babu kowa sai yan surutai da yake iya jiyowa cikin kitchen,hanyar saman mamin yai direct da ita,bai saki hannunta ba sai da suka dangana da bedroom din mamin yace zquna ina zuwa,cikin sassarfa ya sauko qasa ya dawo kitchen din

Tun daga falon ya soma qwala mata kira,ita da wasu mata ne su uku ta hudunsu baaba uwani da alama gyara kitchen din ake sakeyi da wanke abubuwan da suka babbaci ''omg,abdallah taushe zai girma ne jama'a''ta lumshe idonta tana fada jin irin kiran da yake mata ya qaraso kitchen din cikin hanzarinsa ya kama hannayenta ''suprise mami suprise''yake fada cike da murmushi yana dubanta,sai ta dan hade rqi ''suprise wanne iri?wai shin ma wanne abu ne ya fito da kai daga gidanka?,salon kaci gaba da takuramin ya sanya kaqi tarewa gidanka kace sai bayan sati biyu'' ''mami nidai kizo muje ols mami,nasan zan sanyaki fafincikin da kika jima baki irinsa ba'' ''abdallah barni in gama da aikin nan tukun kahe zan sameka ko wanne irin suprise ne sai in gani'' ya langwabe mata kamar qanqanin yaro ''mami bana ao ya huce fa don Allah kizo muje'' baaba uwani ce ta sanya baki dole ta ajjiye plates din hannunta ta bishi tana mita shikam yana qyalqyala dariyanshin nan dake fidda sigar kyawunshi

*_kuyi manage da wannan pls_*

*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽

💖💖💖💖💖💖 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺 *ABADAN*🌺 💖💖💖💖💖💖 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 💖🌺💖🌺 💖🌺💖 🌺💖 💖

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺💖🌺💖🌺💖 🌺💖🌺💖 🌺💖🌺 💖🌺 💖 © *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *_home of expert and perfect writers_*

▶4⃣0⃣

*_An karbo daga Abu Hurairah Allah ya qara yarda da shi,Manzon Allah S A W yace''ana bude qofofin aljanna duk ranar litinin da alhamis,sai Allah ya gafartawa ko wanne bawa musulmi indai ya kasance baya shirka baya hada Allah da abokin tarayya,sai dai wani mutum wanda ya kasance akwai qulli ko gaba tsakaninshi da dan uwanshi musulmi,sai ace''ku qyale wadan nan har sai sun shirya,ku qyale wadannan har sai sun shirya_*

mami na gaba yana take mata baya,sai mita take masa na ya tasota tana cikin mutane,shidai baice uffan ba in banda murmushi da yakeyi,suka ahiga falo tana qoqarin zama yace ''a'ah mami mu qarasa daki'' ''kai abdallah.....abdallah trouble maker,muje dai inga suprise din nan da aka hanani sakat,amma ka tabbata indai bai kai ya kawo ba to zan ck tararka'' ''na amince,amma mami idan ya kai ya kawo din fa,me ni kuma za?a bani?'' ''sai abinda naga ya dace....'' ''zoben daddyn dake gunki kadai nike so'' hara rarshi tayi lokacin da take tura qofan bedroom din nata ''kayi kadan yaro,gwara ka fadi amount na kudi in baka da na baka wannan zoben,bakasan tarihinshi bane har yau.....''

maganar ta maqale mata saboda ido hudu da sukayi da maryam,jikinta a sanyaye hankalinta a tashe ta nufeta ta kama kafadunta bayan ta zauna kusa da ita ''maryam,lafiya?daga ina?,ya akayi ika baro gidanki a idin wannan lokacin?,ina fata ba matsala bace ta faru?,ina maigidan naki?'' ''gani...''taji ance,ta waiga da sauri don tabbatarwa,shaf ta mance ma tare da abdallan suka shigo sai da yayi magana harararshi tayi ''kaga malam bana aon wasa,fice min a daki zamuyi magana''

idonshi ya kanne guda daya h gami da daga girarshi ''wannu batu kam ai mu ya shafa mami,nima diyankin ne,nine kuma mijin diyar taki dai,tuwonki manki''yayi maganar yana zama kusa da mami hade da dora kanshi saman kafadarta suka sanyata a tsakiya

Ba don murmushin dolen da maryam ta qirqira ta dorawa allon fuskarta ba da babu shakka mami qaryata abdallah zata yi,duk da hakan sai da ta dubi maryam din ''bana son shashanci,maryamu gayan meke faruwa?'' da sauri ya karbi zancan ''ko zan miki wasa kan komai mami bazan miki kan wannan ba,idan maryam bani ta aura ba ina zan ganta ma a irin wannan lokacin naje na daukota''sai ya dawo gaban mamin yayi zaman dirshan harda lanqwashe qafafuwa,ganin haka yasa maryam itama zamowa tayi irkn zaman da yayi gabam mamin,saidai ita zuciyarta cike take da rauni,badon namijin qoqarin da take ba wajen danne zuciyar tata ba da tuni hawaye ya fallasa fa,cike da salo na iya sarrafa harshe cikin nutsatstsiyar muryarshi yace ''mami,zai iya yiwuwa kiga na miki qaton laifi,zai iya yiwuwa ma daga qarshe kice sai kin hukuntani kan maganar da zan gaya mikin yanzu,maryam bata da laifi ko daya don ni na nemi a boye abun,mun fara son juna har ta kaimu ga buqatar muyi aure,na boye miki ne mami saboda ina sane da dimbin so da qauna da kike wa tilon danki,farinciki bazaya bari idan na sanar miki ba ki kasa sanarwa da wasu mutanen ba musamman wadanda muke zqune gida daya da su wadanda bana buqatar kowa ya sani cewa maryam nake da muradin aura saboda tsaro,mami kinfi kowa sanin irin traps din da na shiga,an farauci dayuwata ba sau daua ba ba sau biyu ba kuma sau uku ba,wadansu trap din sun yi aiki wasu kuma Allah ya kareni basuyi tasiri ba,na tabbata da ansan maryam ce wadda zan aura ba abun mamaki bane wani mummunan abu ya faru da ita''

''mami...ga maryam nan ta sake dawo miki a karo na biyu,saidai wannan karon uasha banban da sauran lokutta,wannan karon ta dawo gareki da matsayi guda biyu,diyarki kuma aurukarki,nayi kwadayin ganin irin farincikin da zako shiga ta sanadiyyata ne mami shi yasa na sake dawowa da maryam cikin rayuwarmu,sanin maryam kikayi mami a fili amma a badini nafiki saninta kuma zuwa gobe zan warware miki ita don wace a sarari ki gani,ina fatan samu sassauci cikin hikunci boye miki wadda zan aura da nayi mami na''

ga mamakinsu saiga mamin itama ta sauko gabansu,hawaye ne bisa fuskarta wani na nin wani,a rude abdallah yasa hanninshi yana shate mata hawayen ''idan na bata miki mami kiyi haquri,hawayenki bala'i ne mami a gurina'' sai ta kasa cewa komai,jikinta ta janyosu gaba daya ta rungumesu ''barni abdallah na nayi kuka,kuka ne na tsantsar farin ciki ba baqinciki ba,tabbas addu'a bata faduwa qasa banza,na jima ina addu'ar Allah ya baka mace ta gari,lokacin da maryam ta shigo rayuwarmu na fuskanci dukkan halayenta na gari sai maji ina maka sha'awarta,domin hasken alkhairai da nake iya hangowa qunshe da ita,ganin hankulanku bai gamu guri guda ba yasa na fidda burin daga daina na dungumi yi muku addu'a gaba dayanku,kai har wayewar garin yau maryam ce a raina da ita na tashi har ka cimmani a kitchen tunanin maryam nake''

ta janye daga jikinsu bayan ta dauke qwallar idonta,kama hannun abdallah tayi da na maryam ta hade guri guda bayan ta dora nata a saman nasu ''na godewa Allah da irin wannan zabi da ya mana baki daya,naji dadi matuqa da kasancewarki maryam cikin zuri'ata,maryam,ga abdallah nan amana ce na baki ita har bayan raina,na baki amanar abdallah har abada,bani da kowa sai shi,ki zauna da abdallah cikin amana da aminci,abdallah kaima na baka amanar maryam,matuqar ka cuceta bayan zamowarka miji a gareta ban yafe maka ba,ku kula da junaku''abinda ta fada kenan tana jijjiga hannunsu

Duk yadda yaso ya daure sai da ya kasa,qaunar shi da maryam qarara yake ganowa cikin idanun mamin,baiso maryam din taga kasawarshi saboda haka ya kifa kanahi saman hannun mamin ya sumbata cikin dabara ya goge qwallar idonshi ''nikam na dauka mami,na dauka,Allah ya tayani riqo'' ''kefa maryamu na?''ta fada tana kalllob maryam wanda kanta ke duqe take cure guri guda,abune goma da shirin suka cunkushe a qwaqwalwarta,zuciyarta na gaya mata wayo kawai abdallah yayi mata,mai yasa bata bar gidan salin alin ba tare da mami ma tasan wadda abdallah ya aura ba bare ta mata wanna kandagrakin mai daddaure jijiyoyin jiki?,zata iya watsawa mami mai dimbin alkhairai da karamck qasa a ido koko zata yarda ta zauna da abdallan ta sarayar da dukkan wani haqqi da 'yancinta da ya take,ya aureta ta sigar 'yar burum burum,zata barshi yaci nasara a kanta ya sameta a bulus ya sameta ta sigar qarfa qarfa da banga banga?,wani sashen na zuciyarta ke mata qarfafa ata gwiwar alqawari ya daukar mata,kuma ta riga da ta cika masa gabar farko na yarjejeniyarsu,bata jin kuma zai karya alqawarin

daga qasa kuma hannunta yaketa yamutsa mata cikin wani irib salo da yake sa taigar jikinta tashi saboda nata hannun na kife ne cikin nashi tafin hannun,dob samun hanyqr tsira do son cire hannunta daga nashi tayi saurin cewa ''na karba mami,insha Allahu''cikin zuciyarta tana sauya qudirin ma'anar na karba in don kada Allah ya tuhumeta

Mami dake sauri ta koma gun mutane sai gata ta rashe a cikinsu,hira sabuwa ta barke duk da maryam na rakube gefe guda,ga zaton mami surukuta ce da kunya irin wadda tasan maryam din ko da can baya da ita bare yanzun,saidai ga maryam kuwa takura ce data sanyawa zuciyarta na nemo amsoshin tambayoyin abdallah,sai ta hada amsar sai taji duka sun wargaje,idan ta kamo nan ta qulla da can sai ya tsinke,ita kanta ta rasa dalilin da ya sanyata kasa barin gidan a lokacin da ta fahimci abunda ke faruwa,dik da tana ta bawa kanta amsar cewa girma da darajar mami ne saidai ita a karan kanta take jin amsar ba gamsashshiya bace bare ta doshi abdallah da ita

''ina zuqa,bari naje kitchen indauko wayat na kira mr stephien,dinner nakeso a shirya mib sabuwa daga nan zuwa takwas na dare a compound din gidan nan''mamin ta fada ikin zumudi da farinciki tana fita daga dakin

bayan fitarta shiru ne ya biyo baya,abdalla nata qate mata kallo ba tare data sani ba don kanta na duqe ne ''sai faman duqar da kai kike kamar wata mai gajeran wuya,amma dai ba haka mukayi da ke ba ko?,sauran qiris ki wargaza wannan matakin da kika kusa kammalashi,ki tashi ki dauko drink cikin fridge ki zuba kin,ki kuma zauna agaba na har sai maki tazo ta ganmu a haka dn mu sake wanke zuciyarta''

batasan lokacin da ta dago ba ta kalleshi da oily eyes dinta ba ta balla masa harara,idanu ya lumshe yana jin wani abu na tsirga masa,ko banza buqatarsa ta biya,burinshin dama ya kalli oily and brown ayes nata wanda tun jiya rabonshi da su ''ka isa ma?'' ''haka kika ce?'' ''eh''ta bashi amsa kanta tsaye tana kawar da kanta daa kanshi,gyada kansa yayi cike da mamakin tsiwarta ''za kuwa kiga kalar tawa isad,ki bar gani na kodaki gaban mami na baki muhimmanci,ina iya qin sakin naki naga wanda ya isa ya sani in sake ki''

bata san lokacin da kuka ya qwace mata ba ''tabbas abdallah ya gama raina mata hankali,a daki mutum a hanashi kuka haka ake,ita da ya kamata a lallaba ita ake raina ma wayo dauke kanshi yayi gefe guda tamkar bsi damu bs,saidai shi kadai yasan zugin fitar hawayenta da yakeji,hakan ya sashi gaggawar fadin ''Allah ya baki sa'a kici gaba sa kukan har mami tazo ta ruskeki a haka,idan tabi ba'asi kuma na warware mata zare da abawa kinga daga haka ta daina ganin girma da mutuncin mu baki daya,ni kuma naqi sakinki tunda igiyar na hannu na,qarshe kiyi biyu babu''

Jin hakan ya sanyata miqewa da hanzari kuma cikun nutsuwa ta durfafi fridge din,binta tayi da kallo a sace sakamakon yadda rigar tabi jikinta ta fidda surarta,ta ciro lemon ta dauki glass cup saman fridge,gabanshi tazo ta tsaya ta tsiyaya mishi ta miqa masa,qi karba yayi sai harara ma da ya gallamata ''kina tsammani idan mami ta shigo ta taddaki a haka kina bani abu ba zata zargi komai ba?kin min tsaye a ka kamar zamu shiga filin yaqi'' cikin qufula da hasala tace da shi wasu hawayen sabbi na bullowa ''ya isheni ya isheni fa,don me zaka dinga juya ni kamar wata waina,wannan wanne irin abu ne?''

sake dauke kanshi yayi ''har yanzu ke din a matsayin matata kike,ko babu yarjejiya tsakaninmu dole kiyimin dukka abinda nace tunda ban sakekin ba,ruwanki ne ki rusuna ki bani ruwanki ne ki bar leminki nima na riqe aure na'' ba maganar da taqi jinin ya fadeta kamar wannan,tilas ta rusuna ta miqa masa,sai da ya wani sha qamshi kafin ya karba,bayan zuciyarshi cike take fal da tausayi da qaunarta,daga shi sai Allah sukasan abinda yake ji cikin zuciyarsa

Ai kam a hakan mamin ta samesu ''a'ah me ya sameki maryam?''caraf ya karbe ''don nace ta miqon drink''girgiza kanta mami tayi tana miqar da ita tsaye ''a'sh banson sharri,bansan maryamu da qiwa ko ganda ba bare kan mijinta,halan bata da lafiya tafiyanne batasonyi ko?''ta fada tana kallon maryam,sam ita bata fahimci ma'anarta ba rashin sanin me zata ce yasanyata saurin gyada kai don shine kadai mafita ''ayya sannu,hau gado ki kwanta bari in lalubo miki magani,kai kuma banason takura ka qyaleta ta huta har ta warke,ko kuma na riqeta anan idan bakayi wasa tayi sati''

Wayyo Allah,ai duka sai a lokacin suka fahimci inda ta dosa,a tare suka hada ido ita da abdallah,wata iriyan kunyanshi da bata taba jin irinta ba ta saukar mata,da sauri taja idonta ta qulke gam,shi din na da sauri yaja qafafunshi ya fice a dakin don bazai iya hada ido da mamin ba tunda kallon da take masa kenan,ita kam ko a jikinta,cikin gurin da take ajiyar magungunanta ta duba ta fito da pain killer da paracetamol ta hado da ruwa ta kwowa maryam din ''tashi kisha kinjk marya,kada ki biyewa abdallah ya cutar da ke ba tare da kin warke ba,idan kinga ma da takura kimin magana zan maganinsh don nasan halinshi da rawar kai sarai,idan kinki jikin bai miki daidai ba ki sanar min sai a haqura da dinner din''ita dai kamar qasa ta tsage ta shige haka ta dinga ji,wannan abun kunya har ina,sai da taga ta sha ta kwanta taja mata bargo sannan ta fice a dakin

Tayi nisa sosai cikin saqe saqe da tunani taji dumin mutum a bayanta wanda sam bata san lokacin da ya shigo din ba,a zabure ta miqe zata sauka ya damqeta da hannu daya ''kiyi a hankali kada ki fama ciwon naki''ya fada cikin salon rainin wayo,kasa motsi tayo abdallah zai kasheta kam wallahi,sai kuma ya hade rai ''kikaci gaba da kuka zuwa anjima idanunku zasu kumbura,kinga idan anzo dinner sai ki tanadi amsar basu''ya miqe tsam daga gadon ya fice abinsa adakin bako waiwaye,ajiyar zuciya ta saki,sai da ya fita din sannan taji kamar ta bishi ta rufe da duka,gaba daya ma shi babu abunda ya shalleshi,babban isue da ya kamata ace yana cikin rashin nutsuwa amma ko a jikinshi.

🍂🍃🍂🍃🍂🍃

Readers Also Read

More by Ayshacool 1