Abban sojoji takun karshe complete - Chapter 33
Abban sojoji takun karshe complete Chapter 33: Abban sojoji takun karshe complete Chapter 33. Jikin abusufyan ba ƙaramin sanyi yayi ba,yaso ace akwai wata…
4,330 words
Jikin abusufyan ba ƙaramin sanyi yayi ba,yaso ace akwai wata hanyar da zai iya taimaka mata,don ta zauna a kanon,Amma ba halin yin hakan, yana cikin wannan zancen zucin wayar shi ta shiga ruri,da sauri yakai idonshi kan wayar dake hannunshi don yaga mai kiran nashi,Sunan Yaya Hossein ne ya bayyana akan screen din wayar, Da sauri ya answer kiran ya kara wayar a kunnanshi"Assalamu Alaikum,Yayana na kaina"_ On the other hand,Abba yace"wa'alaikum salam ƙanina na kaina,Ya kake fatan kun isa kanon lafiya," Fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Mun ƙaraso tun wuraren goma," Abba yace"Madallah,naji daɗi sosai,kai dawa kuka tafi ne"? Shiru ya ɗanyi yana tunanin halin da sehrish take ciki,ranshi ne ya bashi cewar Ya sanar ma Yayan nashi,May be ya iya dakatar da Sgr ɗin, Calmly ya soma magana"Ya hossein,Wlh an samu matsala,Da jahad na shirya tafiya,bansan ya akai ba,su ka yi musaya ita da sehrish,dama ta kwallafa rai akan son zuwa kano,To yanzu haka zancen da nakeyi maka,Muna tare da Sehrish ɗin,Kuma Sgr ya gane cewa da ita muka zo kano,ya bada umarnin ta koma yau yau ɗinnan,baiwar Allah tana cikin damuwa,yanzu haka tana can tana kuka,"yaƙarasa jawabin yana jiran jin amsar da abba zai bashi, "Kada ka damu,Ka lallasheta ta kwantar da hankalinta,Ni zanyi mashi magana,duk yadda mukayi dashi,in sha Allah i will inform you,"_ Ajiyar zuciya abusufyan ya sauke tare da cewa"Nagode sosai,Yayana nakaina Allah yabar zumunci atsakaninmu," "Ameen Ameen,ƙanina,"abba ya amsa mashi before suyi sallama, Har hankalinshi ya ɗan kwanta duk da yana zullumin amsar da abban zai bashi,don yasan halin Sgr wani lokacin idan ya burkice,mai tankwarashi sae Allah,
A lokacin da kiran abban ya shiga wayarshi,Yana zaune asaman sofa,ya aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya,Yana sanye cikin jeans da t~shirt,yayin da jahad ke zukunne agabanshi,Tayi kneel down fuskar nan tayi jaga jaga da ita,tasha kuka har ta gode wa Allah, Hannu yakai tare da ɗaukar wayar dake ajiye saman front table din gabanshi yayi picking call ɗin,tare da kara wayar a kunnanshi,Ya furta"assalamu alaikum," Acan 6angaren abba ya amsa mashi"Wa'alaikum salaam,My son ya kake ya gida,ya kuma aiki" "Alhamdulliah" Abba yace"Yawwa,Rafayet dama game da yarainyar nan ne,Sehrish,"tunda yaji ya ambaci sunanta,Ranshi ya bashi cewar sunkai ƙararsa ne, "Dan Allah rafayet,ka ƙyale yarinyar nan ta zauna,ba jimawa zasuyi acan ba,Yarinyar nan ta kwallafa rai akan son zuwa can shiyasa harta tsallake ta tafi ba tare da saninka ba,Amma kai shaida ne akan yarda takeyi maka biyayya sau da ƙafa,duk wani abu da zai 6ata maka rai,tana ƙoƙari don taga ta faranta maka rai,pls rafayet ta ci albarkacin wannan," shiru yayi batare da yace komai ba, Har sai da abban ya sake cewa"Rafayet naji kayi shiru," Ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa"its Okey daddy,na haƙura,"Yanayin yadda yayi maganar,bada son ranshi ba, Muryar abba ɗauke da farin ciki yace"Ko kaifa,Wlh har naji daɗi acikin raina,Allah yayi maka albarka " "Ameen"daƙyar ya iya furta hakan,Sallama su kayi ya janye wayar daga kunnanshi, mayar da idanuwanshi yayi kan jahad yace"U can go" Miƙewa tayi tana faman ɗangyasa ƙafarta,tabar falon nashi,ba ƙaramin jiki taji ba,Saukowa tayi downstairs tana cigaba da yin shessheƙar kukan, adai dai lokacin junaid ya faɗo cikin falon,Tsayawa yayi yana kallonta,ƙarasawa yayi da sauri wurinta yana faɗin"rishi lafiya meya faru"? ...ɗagowa tayi da idanuwanta waɗanda sukayi ja saboda kukan da tasha,Waro idonshi ya ɗanyi tare da ambaton sunanta"JAHAD" Cikin shesshekar kuka ta amsa mashi"Na,am" Hannu yasa ya tallabo fuskarta,"Dama bada ke aka tafi kano ba"? Jinjina mashi kai tayi alamar eh,sannan tace "Tare da sehrish aka tafi,amma dani muka shirya tafiya,Shine mukayi musaya ni da sehrish,yaya rafayet ya gano ni,Shine ya hukunta ni Hada tsallan kwaɗi ya sani," Hannuta ya ruko,tare da samun wuri saman sofa suka zauna, Ranshi aɗan 6ace yace"Allah dana son da haka bazan bari Babban yaya ya sanyaki yin tsallan kwaɗi ba,Meyasa zai sanya juliet ɗita,Aikin wahala,'? hannu yasa yana share mata hawayen dake sauka akan fuskarta,cikin lallashi yace"stop crying my juliet,Allah in baki daina zubar da hawayenki ba,Nima zan fara kukan,". Cike da zolaya,ya sanya hannunshi yana murza idanuwanshi,kamar zaiyi kukan, Da sauri ta ruƙo hannunshi tana faman sauke ajiyar zuciya tace"Nadaina". murmushi ya saki tare da cewa"Yaushe zamu fita yawo?Da anjima ko gobe"? Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Mu bari sai gobe,Yanzu har la'asar tayi,Nafiso mu fita da wuri,mu zaga garin nan," "Yadda kikeso haka za'ayi,"ya karasa maganar,tare da kai la66ansa zai sumbaci gefen fuskarta,Karaf idanuwanshi suka sauka akan na SGR dake ƙoƙarin saukowa downstairs,da sauri ya janye la66ansa,ya shiga ƴan kame kame, girgiza kai kawai sgr yayi don yaga abunda junaid ɗin ke ƙoƙarin yi,Fita yayi daga cikin falon batare daya tanka masu ba,
*Boss Bature*
*Sehrish*
hankalinta ba ƙaramin kwanciya yayi ba,jin cewa an barta ta zauna a kanon,taji daɗi sosai acikin ranta,duk da tana fargabar hukuncin da Sgr zai yanke mata idon suka koma gida,
Bayan sallar la'asar,Suka shirya tsaf domin zuwa hotoro,Unguwar da sukayi rayuwa a cikinta,Abusufyan ne ke driving ɗinsu,tana zaune a gefenshi tana latse latsen wayarta,Yayin da can ƙasan zuciyarta ke cike fal da fargabar zuwa anguwar,A hankali Motar ta shararowa da matsakaicin gudu,izuwa cikin unguwar bai direta a ko'ina ba sai a ƙofar gidansu,don bai manta da kwatancen gidan ba,duk da yaɗan so ya ruɗe saboda sabbin gine ginen dake a wurin,kasa fitowa sehrish tayi daga cikin motar,Saboda yanayin da tashiga,ta tsani yin toxali da unguwar,Saboda bata son duk wani abu da zai tuna mata rayuwarsu ta baya,
Fitowa abusufyan yayi daga cikin motar ya zagaya,ya bude mata ƙopar,"Daughter,mun ƙaraso fa,"jiki asanyaye ta fito daga cikin motar,yayin da idanuwanta ke cike tab da kwalla,A wani slow ta wurga kwayar idonta akan gidajensu,Ginin ya tsufa sosai,duk fentin ya ƙoƙe,ya gajarce,An garƙame gidan da ƙaton ƙwaɗo,duk yayi tsatsa,da alama anjima ba'ayi amfani da gidan ba,mayar da idanuwanta tayi akan gidansu maman sadeeq,A rufe yake gidan da makulli,Gidan ya tsufa shima Amma bai kai gidansu tsufa ba,saboda an canza mashi fenti,
Hawaye ne suka soma shararowa akan fuskarta,juyawa ta ɗanyi tare da kallon abusufyan dake tsaye,jikinshi duk yayi sanyi,Saboda tunawa da wasu abubuwa da suka faru a rayuwarshi, Mutanen dake kai komo acikin Layin nasu sai faman leƙensu sukeyi,musamman ƴan yaran anguwar, "Daddy,Kamar basu nan fa,naga gidan a rufe," Uncle yace"Bari na samu yaro na tambayeshi,Muji ko sun tashi ne," Yana ƙoƙarin rufe bakinshi,Yaji anyi mashi sallama ta bayanshi,Muryar wani dattijo ne,juyawa yayi tare da kallon mutumin,tsoho ne amma ba irin tukuf ɗinnan ba,jikinshi na sanye da koɗaɗɗen yadi,ƙafafunshi na sanye da wasu siɗaɗdun silifas duk sun fita hayyacinsu,kamar mahaukaci, Da sauri abusufyan ya miƙa mashi hannu donsu gaisa, Dattijon ya maƙe hannunshi tare da cewa"Haba Alhajin Allah,baka ga yadda hannuna yake ba duk datti a haka zaka gaisa dani," Murmushi abusufyan ya sakar mashi,"dan Allah kada ka hanani gaisawa dakai," Mika mashi hannun tsohon yayi suka gaisa,Sannan yace"bawan Allah,ban ta6a ganinka acikin unguwar nan ba,Kuma da alama kamar wani ku ke nema ko"? abusufyan yace"ƙwarai kuwa,wannan Ƴa tace,Munzo daga abuja ne,Muna neman..umm....."bai ƙarasa maganar ba,saboda ya manta da sunan mutumin, Sehrish ce ta ƙarasa mashi maganar"Malam nura muke nema,malamin makarantar islamiyya," Dattijon yace"Ae nan ne gidan shi,Sae dai kash,Sunyi tafiya zuwa kankia wurin jana'izar Wani kawunshi daya rasu," Jin haka yasa yanayin fuskar abusufyan ta ɗan canza,zuwa damuwa, "Amma,tun yaushe suka tafi"? Dattijon yace"tun makon daya gabata,Amma jiya munyi waya dashi ya sanar dani cewa Yau ko gobe zasu dawo," Ba ƙaramin daɗi suka ji ba,don har sai da abusufyan ya ɗanyi murmushi, Hannu yasa cikin aljihunshi ya zaro kuɗi sababbin ƴan dubu dubu kusan dubu goma sha biyar ya miƙa ma dattijon, Washe baki tsohon yayi tare da sanya hannu biyu ya kar6i kuɗin,tare da cewa"yalla6ai kamar ka sani wlh yau gidana da yunwa muka tashi,yara sai kuka sukeyi,Hakanan na gaji da zama cikin gidan, nace bari na fito na nemi na abinci,Ashe arziƙi ne ke kirana,Allah na gode maka,da ka haɗani da wannan bawan naka,Ya Allah kamar yadda ya farantamun rai,kaima ka faranta mashi nashi,ka biya mashi buƙatunshi na alkhairi,'yana addu'ar hada ƴar kwalla akan fuskarshi, Atare suka dinga haɗa baki suna Amsa mashi"ameen ameen, Abusufyan yace"baba taimakon da zakayi mana,idan sun dawo dan Allah ayi gaggawar sanar damu,Bari na baka lambar wayata, Ya ƙarasa maganar tare da zura hannunshi cikin aljihun wandonshi ya ɗauko wayarshi, Hannu dattijon yasa,a gaban aljihun rigarshi,Ya curo ƴar ƙaramar wayarshi tecno,taji jiki duk tafita hayyacinta,miƙa ma abusufyan wayar yayi"kar6inan yaro,sanya mun numbarka,kayi mun saving ɗinta da sunan Mai mutunci,Zanfi ganewa,Da zarar sun dawo in sha Allah,bi'iznil lahi,koda ƙarfe ɗayan dare ne zan kira in sanar dakai," Murmushi suka saki gaba ɗayansu,kar6ar wayar abusufyan yayi,madannan jikinta duk sun nutse ciki,daƙyar ya samu ya rubuta mashi numbar,yayi mashi saving da Mai mutunci,Sanna ya mayar mashi da wayar"Gashi baba,mun gode sosai,Sai naji ka,Allah yasa adace," Tsohon ya amsa mashi da ameen ameen,ae tunda ka farantamun raina,Kaima sai Allah ya faranta maka naka,har addu'a sai nayi maka idan nayi sallah, "Ina godiya sosai,"ya karasa maganar tare da ruƙo hannun sehrish suka shige cikin mota,key yayi ma motar,a hankali yayi reverse,tare da karya kwana,da gudun gaske ya fuce daga cikin unguwar, Nasarawa suka koma,a bakin gate din gidan ya sauke sehrish,Saboda zuwa masallaci,An fara kiran magrib,Miƙa mata key ɗin gidan yayi"kar6i nan,ki rufe gidan da kyau,Bazan dawo da wuri ba,Saboda inaso naje nayi mana siyayyar kayan abinci,dana amfani,"_ "Toh daddy adawo lafiya"tasa hannu ta kar6i key din,kafin ta juya ta nufi cikin gidan,tsayawa yayi acikin motar yana kallonta,har saida ta 6ace ma ganinshi,ya tabbatar da ta rufe ƙopar gidan,Sannan ya tashi motar ya fuce,
A 6angarensu Aunty babba kuwa,basu isa Enugu ba sai wuraren ƙarfe sha ɗaya na dare,Sunsha uwar tafiya,ba ƙaramin jiki suka ji ba,Acikin garin suka kama ɗaki a hotel,Tunda suka shiga ɗakin,kowaccensu ta baje saman gadon ɗakin,suka shiga sharar bacci kamar wasu matattu,Ga uwar yunwa na cinsu,sai da sukayi bacci mai isarsu,Kafin suka farka neman abunda zasu sama cikinsu,Oder sukayi aka kawo masu lafiyayyan abinci,kamar wasu kuraye haka suka tasarwa abincin suna Ci,Sai da suka ci suka ƙoshi,tukunna suka koma saman gadon,Suka dasa wani sabon baccin,ba tunanin yin sallah,a ƙagare suke washe gari yayi su wuce cikin dajin,
*Boss Bature*
❤🤍❤
Har Wuraren ƙarfe 12,Abusufyan bai dawo cikin gidan ba,gashi yabarta ita kaɗai,da farko bata damu ba,falo ta dawo ta zauna saman sofa,daya ke akwai nepa,hasken globe ya gauraye ko'ina,hannunta na ɗauke da littafin oummansu tana karantawa,Kalaman soyayya ne acikinshi,a cikin drawer ta samu littafin,Wani page ta buɗo acikin littafin Sunan oummansu ne akai dana Ya sayyadi,Aikuwa rai a6ace ta sanya hannu ta yage takardar tare da yin wurgi da ita,Mayar da hankalinta tayi sosai akan littafin tana karanta love messages ɗin dake aciki,da zarar taga wanda ke ɗauke da sunan ya sayyadi,jikinta har rawa yake yi wurin sanya hannu ta yage shi,
Tana cikin wannan karance karance,kwatsam!Aka ɗauke da wutar nepa,nan take duhu ya gauraye ko'ina,babu haske ko misƙala zarratin,gashi ta baro wayarta saman drawer cikin ɗakin,Sanin kanku ne sehrish muguwar matsoraciya ne,Tuni ido ya raina fata,Hankalinta yayi mugun tashi,jikinta ya shiga yin kerma,kamar gunki haka ta ƙame a zaune ta gaza motsawa,tana cikin wannan yanayin na tashin hankali,Tajiyo takun takalmin mutum,A matukar tsorace ta shiga ambaton sunan Daddynsu da ƙarfi"Daddy!daddy!dan Allah kana ina,nashiga uku,' Gabanta ne ya fadi lokacin da ta tuna cewa,daddynsu da Motarshi ya fita,da ace shine ya dawo cikin gidan to tabbas zata ji sautin ƙarar shigowar motarshi, Wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,jin motsin mutumin na tunkarota,a razane ta saki littafin dake a hannunta,ta miƙe daga saman sofa ɗin tashiga ja da baya,tana tafiya saɗaf saɗaf,hawaye duk sun wanke mata fuskarta,zuƙunnawa tayi ta soma yin rarrafe a hankali tana ƙoƙarin gano ƙopar ɗakin oummansu,cikin rashin sani takai hannunta saman wani gwangwanin maltina,aikuwa ya bada wani irin sauti rakwakwas,a gigice sehrish ta miƙe,gudu gudu sauri sauri,ita kanta batasan inda zata tunkara ba,Unfortunately tayi tuntu6e da wani abu,gaba ɗaya ta tafi zata faɗi ƙasa,ta saki wata irin razananniyar ƙara, Sai dai kafin takai ƙasa,Taji an damƙi qugunta,kwakkwaran ruƙo akayi mata,kafin aka janyota da ƙarfi,ta faɗa saman ƙirjin mutumin,koma waye wannan ba ƙaramin mutun bane,ƙarƙarfan gaske, Tashin hankali domin son sanin wanene wannan mutumin,Mu haɗu gobe inda rai da lafiya,In Allah yasa muna da rabon ganinta kenan
💫⭐💫⭐💫⭐💫⭐💫⭐💫⭐ *_INFECTION BABBAN CIYO NE_*
Ciyon da yake shiga tsakanin ma'aurata ya hana masu zaman lafiya. Da kwanciyar hankali a zamantakewarsu ta aure , ciyo ne da yake kassara martaban mace harma da mazan Kansu , ciyo ne mai hadarin gaske Wanda duk take dashi to ba ita ba jin dadin aure , saboda yana dauke ni'imar mace gaba daya yana hana mace jin sha'awar mijinta yana saka ciyon Mara mai tsanani idan yayi yawa , Wanda zuwa gaba yake hanawa mace daukar ciki. Ko kuma yawan 'barin ciki Sannan duk abunda mace zatayi domin gyaran kanta to bazai mata wani amfani ba saboda wannan ciyon wannan zaisa mace taga tana ta faman shan maganin mata amma baya mata aiki,
*KADAN DAGA ALAMOMINSHI* Bushewar gaba K'aikayin gaba Fitar kuraje agaban mace Fitar farin ruwa mai kamar madara ko mai kamar majina Ko fitar ruwa mabanbanta kala Rashin sha'awa Rashin jin dadin kwanciyar aure Yana haifar da budewar gaba, Ciyon Mara da sauransu ,
wannan yasa mukazo maku da sahihijn maganin sanyi wato infection yana wanke duk wani dattin Mara yana maganin sanyi sosai tareda saukowa mace niima maganin 3in1 ne na sha da sabulun tsarki da Wanda zaki dafa kina tsarki dashi , akwai kuma maganin sanyi na maza daban Wanda yanada kyau duk wacce ta siyama kanta to ta siyawa mijinta don kar ayi badi babu rai don ko kinji sauki in shi mijin yanada zai iya shafamaki .......* 07069711327 mmn Yusuf mai kayan mata sokoto🥰🥰
[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*
Join this link to follow my tiktok acct👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*
*Father of soldiers*
*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*
Am really sorry,🙏
Tayi matuƙar tsorata dashi,kasa ɗagowa tayi daga jikinshi,jikinta sae kerma yake yi,lokaci guda daddaɗan ƙamshin turarenshi ya daki hancinta,nan take ta ruɗe tana ƙoƙarin gano a ina tasan ƙamshin nan,duk duniya mutun ɗaya ne ta sani mai irin wannan ƙamshin turaren mai matuƙar ratsa zuciya,Ruɗewa tayi tana so ta canko wanene,kuma tana kokwanton anya hakan zai iya kasancewa gaskiya?zame hannayenta tayi daga saman waist ɗinshi da ta ruƙe,ta matsar dasu har izuwa mid back ɗinshi,Gabanta ne ya faɗi rass jin ta shafo doguwar sumar kanshi,muryarta na kerma ta furta sunanshi"BABBAN YAYA..!"tana ambaton hakan,Wutar ɗakin ta dawo nan take haske ya gauraye ko'ina tamkar da Rana,zuba mashi ido tayi tana kallon kyakkyawar fuskanshi wadda ke sanye cikin face mask black colour,Launin rigar jikinshi ya lumshe idanuwanshi,slowly ya ɗan waresu akan fuskarta,Ae tana ganin blue eyeballs ɗin nan nashi,Ta ƙara tabbatar da hasashenta,abun yayi mugun ɗaure mata kai,kallonta yake yi from head to toe,fuskarta duk tayi zufa saboda tsabar firgicin da ta shiga,ga hawaye jaga jaga a fuskar,duk don saboda an ɗauke da wutar nepa ta ganta acikin duhu,
Sai faman sauke ajiyar zuciya take yi,hankalinta har ya kwanta da ta tabbatar cewa shine,Tayi tunanin wani mugunne yazo don ya cutar da ita,tayi farin cikin ganinshi sosai kamar tayi ihu,Amma ta wani 6angaren tsoran hukuncin da zai yanke mata take yi,duk a tunaninta yazo ne don ya hukuntata,tunda ya bata Command taƙi bi, Ganin irin kallon da yake yi mata ne yasa tayi saurin sunnar da kanta ƙasa,tana wasa da yatsun hannunta, Hanky ya zaro daga cikin trouser pocket ɗinsa,Ya miƙa mata tare da cewa"Take it,"hannu tasa ta kar6a,ta shiga goge fuskarta sosai, "In kawo maka ruwa kasha"?cikin sanyin murya ta ambaci hakan, Girgiza mata kai yayi alamar a'a,kafin ya wuce cikin falon,Ya zura hannayenshi biyu acikin aljihun wandonshi, juyowa tayi tana kallonshi,A dai dai lokacin suka jiyo sallamar Abusufyan"Assalamu Alaikum", Amsa mashi su kayi da"Wa'alaikum salaam," Shigowa cikin falon yayi,hannunshi ruƙe da key ɗin Motarshi, Koda yayi arba da Sgr,cike da mamaki yace"Rafayet!Ashe dagaske ne,Abban ku ya sanar dani cewa,zai yi wa Omar magana ko shi ko kai wani yabiyo bayanmu don yaso yana nan muzo dashi,Banyi tsammanin cewa kaine zaka zo ba,Yanzu kawai ina karyo kwana da motata naga sojoji zagaye da gidan nayi ta mamaki cikin raina,Gaskiya ba ƙaramin daɗi naji ba," ya karasa maganar a yayin da yake ƙoƙarin rungumarshi,da alama Abusufyan ba ƙaramin daɗi yaji ba,Sai murmushi yake yi, "Na same ku lafiya,"? "Lafiya lou Alhmdllh,Naje masallaci ne,na biya naga wani Abokina daga can kuma na wuce wani store zanyi mana siyayyar kayan abinci,Inata fargabar nabar yarinya ita kaɗai acikin gida", Sgr yace"nayi mamakin ganinta ita kaɗai zaune acikin gidan,time ɗin dana shigo kuma bansan meya faru ba,duhu ko'ina,so sai daga bayane hasken ya dawo," Abusufyan yace"Ae ɗaukewa su kayi da wutar ne,yanzu nima ina kan hanyar dawowa naga sun dawo da ita," wurga idonshi yayi kan Sehrish dake tsaye hannunta ruƙe da hanky dinsa,ta kammala goge hawayen, "Daughter,zonan mana,"ya kirata da hannunshi,wurinsu tazo ta tsaya tana facing din Abusufyan, "Faɗamun meya faru?bayan na tafi"? murmushi ta ɗan yi,batare da tace komai ba, Mayar da idanuwanshi yayi kan Sgr yace"Amma dai ba nan zaka kwana ba ko"? "I will spend the night here," Abusufyan yace"ba ka ga yadda gidan yake ba ne?Ni nasan bazaka iya bacci acikinsa ba,Yakamata ka wuce hotel kawai,ina ganin zaifi maka daɗin zama," Girgiza mashi kai yayi"No,i wanna stay here," gyaɗa kai abusufyan yayi tare da kallon sehrish yace "Sehrish ki kaishi bedroom ɗin da kika gyara,ya zauna acan,Amma dai banso ba wlh,Don nasan cewa zaka takura sosai,Ga zafi ga sauro duk da na siyo maganin sauron,Amma bana tunanin zai iya dakatar da saurayen dake acikin gidan nan," Amsa mashi tayi da toh,Sannan ta juya tare da kallon Sgr tace"Mu shiga ciki," Gaba tayi yabi bayanta,daƙyar yake iya taka kasan palourn,saboda daudar dake a wurin duk da sun gyara shi, Shiga cikin bedroom ɗin su kayi atare,Wuri ya samu gefen gadon ya zauna yana ƙarewa ɗakin kallo, "Kana bukatar wani abu,in kawo maka," "No need"ya ambaci hakan a yayin da yake zaro wayarshi daga cikin aljihun wandonshi, "Sehrish!"Abusufyan ne ya kwala mata kira,da sauri ta juya ta fita daga ɗakin, Komawa tayi cikin palourn A tsaye ta same shi,Ga kayan da yayi masu siyayya hada gass cylinder saboda yin girki,Sojoji ne suka shigo dasu,A cikin buhu guda biyu,sae cylinder ɗin da suka ajiye nan, Ƙarasawa tayi wurinshi,"Gani Daddy," "Kunyi magana dashi ya fada maki ko yana buƙatar wani abu?" "a'a bai bukaci komai ba," Shiru Abusufyan ya dan yi,ganin damuwa akan fuskarshi yasa tace"Meya faru daddy," hannu yasa ya ɗan shafa sumar kanshi kafin yace"Daughter,bazai iya kwana acikin gidan nan ba,Ni nasan waye rafayet,Wlh nayi mamakin ganinshi banyi tsammanin cewa shi zaizo ba,Kalli fa gidan nan ki gani,babu wani shiri da mukayi,yanzu da zarar an ɗauke da wutar nepa,Shikenan zafi zai rufe mu,kuma ko kaɗan baison zafi,Gashi da ƙyankyami toilet idan bana bedroom ɗinshi ba,baya shiga na kowa,Kuma dole ya buƙaci yin wanka,Ni bansan ya zamu ƙare dashi ba," Murmushi Sehrish tayi,ita kanta ta jinjina ma ƙarfin hali irin na Sgr,yadda yake da ƙyanƙyamin nan,Amma a haka yace zai kwana acikin gidan,Koya zasu ƙare,? "Daddy,kada ka damu,tunda yaji ya gani,zai kwana anan ɗin ka ƙyaleshi kawai," Gyaɗa kai Abusufyan yayi tare da cewa"Shikenan kawai,Yanzu dai bari na shiga da kayan abincin nan kitchen," Yayi maganar tare da sa hannu ya dauki buhu ɗaya,hannu tasa itama ta kama ɗayan buhun,taja shi izuwa cikin kitchen,bayan sun kammala kwashe kayan sunkai kitchen, Ta dube shi tare da cewa"Zan iya dafa mana ko taliya ce? Abusufyan yace"Kina jin yunwa ne"? "A'a,bana ji,saboda kai dama zan dafa,naga bamu ci Dinner ba, "Ki barshi kawai,akwai kayan tea dana siyo da bread,idan kina jin yunwa ki haɗa ki sha,Yanzu dae bacci nake ji," Yayi maganar yana hamma, "A ina zamu kwana"tayi tambayar tana kallonshi, "Ki wuce inda mijinki yake mana,Ni zan kwana a palour ne,Ki dauko mun bargon da zan ɗan shimfiɗa in akwai" "Toh" ta amsa mashi tare da Kama hanya ta fuce daga cikin kitchen ɗin,Shima fitowa falon yayi ya tsaya a tsaye yana jiranta,
Lokacin da ta shiga bedroom ɗin,A kwance ta samu Sgr yana bacci ya ƙure fankar ɗakin har ƙarshe,iska ta ko'ina,hankalinta ba ƙaramin kwanciya yayi ba,wurin wardrobe ta wuce ta sanya hannu ta buɗeta,daga gida na kasa blanket din suke tare da bedsheet,hada mosquito net, Bargo ta dauko mashi,Sannan ta koma falon,har lokacin Abusufyan na atsaye,yana jiranta, Ƙoƙarin shimfiɗa mashi tayi,da sauri yasa hannu ya kar6i bargon tare da cewa"Yawwa My Own Daughter,nagode sosai," "Sae Allah yakaimu Daddy,"fuskarta asake tayi maganar, "Allah ya kaimu lafiya,take care of my son,don't allow even one mosquito to bite his skin,If not ranki zai 6aci,"cike da zolaya yayi maganar, Fashewa tayi da dariya,tare da juyawa tana faɗin"don't worry daddy,In sha Allah i will look after him,very well," Gyara kwanciyarshi yayi saman sofa ɗin,cikin lokaci ƙanƙani bacci yayi awon gaba dashi, Komawa cikin bedroom ɗin tayi,bedsheet ta dauko acikin wadrobe ta shimfiɗa a kasa,sannan ta matsa wurin gadon,ta ɗauko pillow guda ɗaya ta ajiye shi saman zanin gadon, Wurin switch taje,ta kashe light ɗin ɗakin,Nan take duhu ya gauraye ɗakin amma ba sosai ba,akwai hasken ƙwan dake a falo guda daya da aka bari akunne,ya ɗan haska ɗakin nasu, Moving tayi izuwa wurin gadon inda Sgr ke kwance yana bacci,addu'o'i ta shiga karantowa tana ɗan tattofa mashi,bayan ta kammala ta koma saman shimfiɗar da tayi,ta gyara kwanciyarta,sai da itama ta karanta addu'o'in tabi ta shafe jikinta kafin ta rufe idanuwanta,bacci 6arawo yayi awon gaba da ita,
Around 1:30 na dare,Ƴan nepa suka yi tsiyar tasu da suka saba,Tashin hankali,Ƴan sakanni da ɗauke wutar fanka ta tsaya cak,Wani irin zafi ya fara ziyarta ɗakin,Sai ga mutanen da gudun gaske sun fara kwararowa cikin ɗakin,Buuuuuuuuuu da wani irin kuka mai sautin gaske,tun yana juyi saman gadon yana kai hannu yana buge sauron dake ƙokarin attacking ɗinshi,har ya fara ƙokarin farkawa,Wata irin zuface ta soma tsastsafo mashi ajikinshi,Sharkaf ya jiƙe,tuni numfashinshi ya soma kokawar fitowa daga hancinshi,kamar an toshe shi,A firgice Sgr ya farka yana faman zazzare blue eyes ɗinshi,Hankalinshi yayi mugun tashi,arayuwarshi ya tsani sauro ko miskala zarratin baisan halittar nan,bai taso a inda ke akwai taba,Amma yasanta sarai a matsayinshi na Dr yasan irin cututtukan da take haifarwa,Gashi ya tsani duk wani abu da zai naƙasa lafiyar jikinshi,tuni jikinshi ya soma kerma,hannu yasa ya ɗebe rigarshi gaba daya,ya shiga kokawar korarsu daga kusa dashi bayan ya kunna fitilar wayarshi dakin yayi haske,ji kake fass fass!kaff kaff!!haka ya dinga bubbugesu,duk yabi ya ruɗe,
Cikin bacci Sehrish ta dinga jin muryarshi yana faɗa da sauraye yana fadin"Don't come close to me!Am gonna shoot you"tashin hankali Sgr fa ya zauce da alama,duk sun rikitashi sun mayar dashi ƙaramin mahaukaci,Idan ya sanya riga bala'e biyu,ga zafi ga sauro,idan ya cire rigar kuma Sauraye zasu sha jini,bai da choice, A firgice ta farka,hankalinta a matukar tashe ta mike daga kwancen da take saman bedsheet ɗin,Wurin shi ta ƙarasa,yanayin da ta ganshi gaba ɗaya ya rikice ba ƙaramin tausayi ya bata ba,gaba daya yabi ya susuce ya hargitsa sumar kanshi, "Ya Rafayet,"ta ambaci sunan shi da wata irin kasalalliyar murya ta mai bacci,ƙoƙarin hawa saman gadon tayi don ta taimaka mashi ta kore mashi su,kafin su san abunyi,ae tana hawa saman gadon,ya ƙanƙameta ya rungumeta sosai,A faɗace yake ce mata ta kori saurayen su fita su bar ɗakin,ko ya harbesu da bindiga,tuni taji hawaye sun cicciko mata acikin idanuwanta,tsananin tausayinshi ne ya kamata,dama sai da Uncle yace bazai iya kwana a cikin gidan ba,Amma yace zai iya,wani iko na Allah,babu halittar da Sgr ke jin shakkarta irin sauro,Gashi Yau Allah ya haɗasu,ƙananun ƙwari sun firgita babban kwaro,Shaggu sun ga Farar fata,burinsu kawai su tsotsi jininshi,Dama abu tubarkalla masha Allah, gaba daya hannayenta na asaman bayanshi,ya cusa kanshi a kirjinta,numfashin shi da wani irin huci yake fita, Muryarta tamkar zatayi kuka tace"Ya rafayet,dan Allah ka natsu,zanje wurin daddy na kar6o mana maganin sauron,"tayi maganar tana ƙoƙarin janye jikinta daga nashi,ƙin barinta yayi,yaƙi yarda ta motsa daga jikinshi,gani yake kamar in tabar wurin Saurayen zasu shanye mashi jinin jikinshi ne, Ganin yaƙi sakinta yasa takai hannu ta ɗauki rigarshi da yayi wurgi da ita gefe saman bedmattress ɗin,Ruƙo rigar tayi a hannunta,ta shiga kore mashi saurayen dake akewaye dasu,
Duk wannan budurin da akeyi,Abusufyan na kwance saman doguwar kujerar,Shi kanshi zafi ya ishe shi ga saurayen a kewaye dashi,Amma hakan baisa ya farka ba,sae faman juyi yake yi, (Allah sarki,haka talaka ke fama,da zarar an ɗauke da wutar nepa lokacin zafi,Ya rasa inda zaisa kanshi,ga sauro ga zafi,yayin da masu kuɗi ke can suna shan sanyin A.c,a lokacin zafi,idan kuma na sanyi ne su kunna room heater,Talaka kuma Ya hura garwashin wuta😥)
Jikinshi sae kerma yake yi,Duk da ya ɗan ji sauƙin Zafin saboda fiffitar da take yi mashi tana kore mashi saurayen,ko gajiya bata yi baiwar Allah,Haka ta hana idonta bacci,ta zauna tana kula dashi,sai faman sauke ajiyar zuciya yake yi,har lokacin yana manne da ita, A hankali bacci yayi awon gaba dashi,kamar wani jinjiri,gyangyaɗi ta fara yi,tana fiffitar bacci na fisgarta,idanuwan nan sunyi jawur dasu,taƙi bari bacci ya ɗauketa,saboda gudun halin da Sgr zai shiga,idan ta daina yi mashi fifitar, Tafin hannunta ta sanya asaman fine face dinsa,ta shafa gefen fuskarshi har izuwa saman pink lips ɗinshi,kafin ta mayar da hannun saman dogon wuyanshi,fatar wurin tayi haske sosai mai matukar jan hankali,la66anta takai asaman cheek ɗinsa ta manna mashi kiss,ɗagowa tayi tare da aza tsinin hancinta cikin sumar kanshi,daddaɗan ƙamshin dake fitowa daga wurin ta dinga shaƙa,tana faman lumshe idanuwanta,da hannu ɗaya take yi mashi fiffitar,
Tana cikin wannan yanayin,ta galabaita sosai saboda baccin da take ji,Ƴan nepa suka dawo da wutar,a hankali fankar ta soma jujjuyawa,nan take iska ta karaɗe ko'ina na bedroom ɗin,wani irin farin ciki ne ya ratsa zuciyarta, "Allah na gode maka,da suka dawo da wutar nan,nayi farin ciki sosai," Lokaci guda Mosquitoes ɗin nan kowa ya kama gabanshi,saboda wutar mai ƙarfi ce,iska duk ta kaɗa shaggun, A hankali ta lalla6a ta janye Sgr daga jikinta,ya koma saman mattress ɗin,ta dauki wayanshi ta kashe fitilar ta daura ta saman bedside drawer,gefenshi ta kwanta,tare da jan bargo ta lullu6e jikinta,banda nashi saboda ta lura dashi baisan Zafi ko misƙala zarratin,
*Boss Bature*