Abban sojoji takun karshe complete - Chapter 68
Abban sojoji takun karshe complete Chapter 68: Abban sojoji takun karshe complete Chapter 68. A 6angaren Amrish kuwa,Har kusan one hour tana zaman jiran…
4,217 words
A 6angaren Amrish kuwa,Har kusan one hour tana zaman jiran Kanal Yousouf,tuni ta jima da kammala Cin abincin,ta mayar da plate ɗin kitchen,A saman doguwar sofa ta kwanta tana jiran zuwanshi,har bacci ya ɗauketa,wuraren ƙarfe ɗaya da rabi,Motar shi ta ƙaraso bakin gate ɗin gidan,Yana yin horn baba mai gadi ya buɗe mashi,A mutunce suka gaisa da junansu,saboda ya ganeshi sosai,kuma yousouf yayi mashi bayanin zuwanshi,Bayan ya buɗe mashi gate ɗin ya wuce da motar cikin gidan,parking ɗinta yayi,kafin Ya fito ya nufi cikin gidan,A ƙopar shiga falon Ya tsaya yana zabga sallama shiru ba'a amsa mashi ba,kusan sau biyar,A karshe ya yanke shawarar shiga ciki,Da sallama abakinshi ya shiga falon,Tunkafin ya ƙarasa ciki ya hango Amrish,kwance tana bacci,gaba daya mayafinta ya zame ƙasa,tsayawa yayi yana kallon kitson kalabar dake akanta,manya manya,tayi mata kyau,baisan ta yarda zai tashe ta,Tunawa da makullin motar hannunshi Yasa shi yin dabarar girgiza key din saitin kunnanta,Sautinne Ya farkar da amrish daga bacci,mutsu mutsu ta fara tana kokarin buɗe idanuwanta,duk bata Lura dashi ba,har ta miƙe tsaye ta Sauko da ƙafafuwanta ƙasa,Ta ɗaga hannayenta tana yin miƙa,Da sauri Yousouf Ya kawar da idanuwanshi,ganin yadda ƙirjinta ya fito sosai, Sai daga baya ta lura dashi,da sauri Ta ɗauko mayafinta,ta rufe kanta dashi, "Yaya yousouf,ka dawo," Batare daya kalleta ba yace"Am sorry,na barki kina ta jirana,wani uzirine ya ruƙe.ni" "Babu komai,"ta ambaci hakan tare da mikewa ta ruƙo trolley ɗin kayanta,Gaba yayi tabi bayanshi har suka isa motar,kowa ya shiga ya zauna kafin ya tashi motar,ya nufi hanyar gida dasu,yana driving suna fira da ita,
*Boss Bature*
*Amani*
Tana cikin gyara kitchen tajiyo muryar Jahan daga falo yana kwaɗa sallama,fuskarta ɗauke da murmushi ta tunkari falon,A zaune ta same su saman Sofa,su biyu sun ɗauki wankan suits,ba ƙaramin kyau su kayi ba,dama duk in jahan zai zo zance,Atare da Ayaan suke zuwa,kamar yadda suke twins komai atare suke yinshi,
"Yau kune a gidan namu,"tayi tambayar tare da samun wuri ta zauna tana fuskantarsu, Haɗa baki su kayi wurin gaisar da ita"Ina yini aunty,mun same ku lafiya"? "lafiyalou,Ya kuke?ya mutanan gidan naku?Ya jikin junaid da fawan"? Ayaan yace"Kowa yana cikin ƙoshin lafiya,marasa lafiya kuma jiki yayi kyau,". "Masha Allah abu yayi kyau,"acewar amani, "Bari nakawo maku abunsha"da sauri suka haɗa baki wurin cewa"a'a,bama bukatar komai," Dariya ta ɗanyi,ba ƙaramin burgeta suke yi ba,har magana ma wani lokacin in zasu yi atare suke yinta, Ta lura da jahan sai faman waige waige yakeyi, "Amal ko"?tayi tambayar fuskarta ɗauke da murmushi, Murmushin gefen fuska Jahan ya saki tare da cewa"eh,tana ina ne?naga banganta ba" "Bari nakira maka ita,"miƙewa tayi tare da juyawa ta nufi upstairs, "am so eager to see her,nayi kewarta sosai,"jahan ne yayi maganar yayin da yake zaro wayarshi daga cikin aljihunshi, Ayaan yace"In ka kwantar da hankalinka,Cikin ƴan kwanakin nan za'a shafa fatihar auranku,idan yaso saika mayar da ita madubi kayi ta kallonta," Harararshi jahan yayi "oh kana nufin zan aureta ne,kawai don na ajiyeta,na zuba mata ido ina kallonta?kaima ka sani wlh," Dariya ayaan yayi,kafin ya ƙara cewa wani abu,Amal ta sauko jikinta sanye da riga da skirt na material maroon colour,tasha uban makeup, Da sauri jahan ya sanya tafin hannunshi Ya rufe ma Ayaan fuska,wai don kada ya kalle mashi matarshi, Buge hannun Ayaan yayi yana fadin"Me yayi zafi?Bari na tashi na baku wuri,idan kun kammala Zancen ka kirani in dawo in ɗaukeka,"yana kai ƙarshen maganar ya miƙe tare da nufar ƙopar fita falon yana dariya, Ƙarasowa Amal tayi,Tana ƙokarin zama ya nuna mata laps ɗinshi wai tazo ta zauna asama,waro ido waje tayi tana girgiza mashi kai"a'a kunya nake ji idan aunty amani ta gani fa," Zare mata ido yayi"Ina wasa dake?zaki zo ki zauna ko sai ranki ya 6aci,"sam babu wasa a fuskarshi,dama haka take fama dashi,baida kunya ko kaɗan,ita kuma kunya gareta sosai,kuma sam bai iya soyayya ba,yafi ƙwarewa a harkar romance,ta ko'ina jahan yafi ƙarfinta,lalla6awa kawai take yi dashi don tana sonshi,
"Ni bazan zauna asaman cinyarka ba,Amma zan zauna a gefenka,in kuma hakan baiyi maka ba,ni zan koma ciki"idanuwanta cike tab da kwalla tayi maganar, Sassauta muryashi yayi"its ok,don't cry nima wasa nake maki,zoki zauna,"gefenshi ta zauna ya tsareta da idanuwanshi,sae faman gyara mayafinta take yi,saboda kallon ƙurullan da yake yi mata,. "Baki yi farin ciki da zuwana bane"cikin sanyin murya yayi mata maganar, "Yakamata ki saki jiki dani,nan bada jimawa ba,za'a ɗaura mana aure,ko baki sona ne"? Ƙasa kasa da murya tace"inasonka mana," "To meyasa ko kallona bakya yi"? Shiru tayi tana wasa da yatsun hannunta,matsawa yayi tamkar zai shige mata,ruƙo hannayenta yayi cikin nashi, "Amal,"ta amsa mashi da na'am, "Yakama ki koyi zama dani,tun yanzu in ba haka ba,zakisha wahalata,Kin cika kunya,ni kuma banason mace me kunya,its better ki cire kunyarki wurin nuna mun soyayya,kinji ko"? Ɗaga mashi kai tayi alamar eh, Shafa gefen fuskarta yayi"faɗamun idan munyi aure,a first night ɗinmu,me zaki yi mun,"shiru amal tayi tana tunanin amsar da zata bashi,hasalima bata gane me yake nufi ba, "Kinyi Shiru bakice komai ba"? Cike da jin kunyarshi tace"Ni bansan me kake nufi ba," Dai dai satin kunnanta yakai bakinsa tare da cewa"I mean...idan zamuyi sunnah," Still bata gane me yake nufi ba, "Ya jahan ni ban fahimce kaba," Takaicine ya isheshi,a ƙule yace"oh,kina nufin bakisan Komai ba?a haka zamuyi aure?that's impossible," Ganin yadda ya 6ata ranshi yasa tace"Am sorry,wlh bansan kan me kake magana ba," "Gaskiya idan har kinason mu zauna lafiya dake,to ki koyi yadda zaki farantamun kinji ni ko"? Ɗaga mashi kai tayi alamar eh, "Idan na tafi,kice ma Auntynki ta koya maki yadda zaki kwanta da mijinki,ina fata kinji ni"? Gaba ɗaya ta dabarbace,Amma tabbas bata gane me yake nufi ba, "Zan faɗa mata,"jinjina kanshi yayi yanzu naji magana......'ya jima a wurin Amal,kafin yayi masu sallama,ya kira ayaan ya ɗaukeshi suka koma gida, [3/19, 2:58 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*
Join this link to follow my tiktok acct👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*
*Father of soldiers*
*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*
Zazzafar haja daga Minjibir ventures,Ina masu buƙatar siyan kayan sallah Kada ku bari a baku Lafiya,Ga kaya na kece raini Na shiga tsara,Koda kudinka sai da rabonka,Kadan daga cikin abubuwan da muke siyarwa akwai Lace Veils Atamfa Shoes Bags
Address Hotoro ladanai kan titin ring road Chat 09126570345 Call 09136122503 saikun Zo💃💃💃💃
Remain few pages 😢
Bayan tafiyar Jahan,Amal ta sanarwa Amani abunda yace ta koya mata,tasha ruwan mamaki,amma ta wani 6angaren ba ƙaramin taimakonta yayi ba,tunda gashi Ya tuna mata abunda ta manta bata koyar da Amal din ba don tasan tana bukatar hakan,
A taƙaice cikin ƴan kwanakin nan,wata irin shaƙuwace a tsakanin Sgr da Sehrish,Soyayyarsu gwanin ban sha'awa,wani irin so suke yiwa junansu,a koda yaushe yana manne da ita idan har ba lokacin sallah bane tunda aikinshi na Nigeria Ya qare,jikinta yayi sauƙi sosai,tana samun kyakkyawar kulawa a wurinshi,komai atare suke yinshi,Cin abinci,bacci,da sauransu,Yanzu kowa na gidan hatta su Ammi sun gane cewa Sehrish da Sgr sun sasanta tsakaninsu,wannan yasa ammi bata ƙara neman Sehrish da su zauna akan maganar kar6ar takardarta ba,dama abunda suke fata kenan,
A 6angaren Omar da Hosana,abun sai son barka,hajiya azeema ta gyara mashi ita sosai,yanzu ta rage wannan soki burutsun nata,duk da akwai sauranta,Amma an samu cigaba,
Idan muka dawo 6angaren Romeo da Juliet,ko ban faɗa ba kunsani,Masoyane na gaske,duk da rashin jin Junaid haka Jahad ke son abunta,kamar yadda shima yake sonta,basu gajiya da bama furannin soyayyarsu ruwa,wata irin shaƙuwace a tsakaninsu,hakan yasa koda yaushe suke manne da juna,
A 6angaren Kanal Yusuf da Amrish kuwa,tuni ya bayyana mata soyayyarshi,kuma da Maganar aure ya fara zuwan mata,don baya buƙatar su 6ata lokaci wurin yin soyayya a waje tunda sun aminta da juna,abu ne kana so ana sonka,no need to waste time,hatta Abbansu yasan da maganarsu,
Saboda tafiyar Sgr da Omar U.s,Yasa aka shirya yin bikinsu a cikin ƙurarren Lokaci,gagarumin bikine aka shirya yinshi cikin sati guda,Wanda tuni an fara sanarwar ɗaurin Auransu wanda za'ayi ranar Juma'a,gaba ɗaya Social media ta ɗauka,gidajen talabijin dana radio,Ko'ina zancen auran Ƴa'ƴan Abban sojoji ake yi,Labarin ya karaɗe Duniya,wato bikine na zaratan samarin gidan wanda sukayi shura a duniyar nan tamu,daga cikin waɗanda za'a daura auransu,Akwai Omar da Hosana,Junaid da Jahad,Jahan da Amal,Yusuf da Amrish,Osman da Khadija,Adam da Nafeesat,Fawan da Yusra ɗiyar abokin Abbansu Tafeeda,dama sun jima atare tun lokacin da yake tashen rashin jinshi atare suke da ita,kafin Allah ya shiryi kowannansu,Ayaan da Yuhana ƴar wurin ƙawar Mommynsu Dr Harriet,wanda Mommynsu ta haɗa shi da ita,Don ayi auransu atare da Jahan,saboda ya nuna cewa in dai baza'a ɗaura Auransu da Ayaan ba sai dai shima a fasa nashi,wannan dalilinne yasa Mommynsu ta haɗa Ayaan da Yuhana kuma cikin sa'a,A rana ta farko da Ayaan ya haɗu da ita yaji ta kwanta mashi aranshi,ita ma kuma haka,sun amince da junansu batare da sunsha wahala ba,bayansu kuma sai Uban gayya,Babban ɗa a wurin Abban sojoji,General Ishaq tare da Amaryarshi Hajjaju,Sai daga baya Abbansu yaji labarin rabuwarshi da Laila,Yasha faɗa a wurinshi duk da yayi mashi bayanin dalilin rabuwar aurannasu,daƙyar ya samu Abba Ya haƙura da maganar, Abusufyan ma yana ɗaya daga cikin wanda zasu Angwance,Shida Uwar ya'yanshi Zainabu Abu,
Waɗanda aka sanyama biki kuma,Hafsat da Ya mu'allim,bayan dagar da suka sha dashi,da farko taƙi amincewa da auranshi saboda malamine,Amma daga baya ta amince da auran nashi,gaba ɗaya sauran matasan gidan,tun daga kan Captain Najeeb,Jabeer,khaleed,da Talal,kowannansu An sanya ranar auranshi,
Murna awurin Family dinsu ba'a magana,musamman Abbansu yafi kowa farin ciki,burinshi na qarshe da ya rage mashi a duniyar nan shine yaga auran ƴa'ƴanshi,kodan yaga ƴan jikokinshi
Ba ƙaramin ƙoƙari Hajiya azeema tayi ba,tare da Mommy da Oummansu Sehrish,domin kuwa sune suka yi tattaki har zuwa Dubai wurin haɗa masu lefensu,jigunannun kaya haɗaɗɗun gaske,An kashe kuɗi kamar ba'asan wahalar nemansu ba,musamman a lefen Sehrish da Hosana da Jahad,shi Junaid ko sisi bai kashe ba,Komai da aka kashe ma Jahad Sgr ne ya ɗauki nauyin komai,hatta sadakin Junaid,Sgr ne ya biya shi gaba da baya auran gata za'ai mashi,Daga Hosana har Jahad sadakinsu da Gold aka biyashi irin na Sehrish,sauranne aka biya sadakinsu kowacce dubu ɗari uku uku,Amrish ta samu kyauta sosai a wurin Sgr da Abbansu,saboda sune suka biya kuɗin komai na kayan daki,da duk wani abu da zata buƙata,
Special Gift Sgr ya shirya ma Sehrish,Amma yace Sai sun koma California zai bata kyautarta ta musamman,Saboda ta bashi abu mafi daraja the most greatest gift,wanda kowani miji yake burin ya samu a wurin matarshi a rana ta farko daya kusanceta,tunkafin ma wannan kyautar acikin akwatinan lefenta hada na kayan adon mata,zallar Diamond ne acikinshi,
Ba ƙaramin gyaran jiki Amaren suke sha ba,masu gyaransu har daga kasashen ketare,koda yaushe cikin gyarasu akeyi,tun cikin satin da za'a ɗaura Auren,gaba daya amaren suka hallara a gidan,saboda programes da aka shirya,gidan yasha gyara sosai,An ƙawata shi,idan ka shiga cikinshi kamar ka bar Nigeria ne saboda tsabar haɗuwar da yayi,Naira tasha kashi,an ɗaukko masu aikin cikin gida,manya manya chefs waɗanda zasu gudanar da abincin bikin,da kuma Event planners wanda zasu tsara shagulgulan da za'ayi na bikin, Anyi shagulgulan biki na kece raini,An yi shiga ta alfarma,Anci ansha An godema Allah,kuma kowa ya nishaɗantu,
A ranar Juma'a,dubban Jama'a suka shaida ɗaurin Auran zaratan Samarin gidan Abban Sojoji A Abuja central Mosque,Masallacin ya cika maƙil da Mutane,ba masaka tsinke duk wani wanda ya amsa sunansa a Nigeria ya hallaci daurin auren,Bayan kammaluwar ɗaurin auran,A daren Ranar aka kawo duka amaren wanda acikin gidan Abba zasu zauna,don tuni an fara gine gine na wasu 6angarori da za'a ƙara,Amma kafin nan,kowaccensu zata tare a ɗakin Mijinta ne na wani lokaci,dama burin Abbane kowannansu in yayi Aure yafi son ya zauna a gidan tare da matarshi,saboda baison suyi nesa dashi,
Shirye shiryen tafiya U.s Ya kankama,tun ana saura kwana ukku ya rage jirginsu ya ɗaga,Sehrish ta lalla6a Sgr don ya kaita Gidan Yari taga Aunty azmee,Dayake yanzu farin cikinta yakeso,Baiyi mata musu ba,da kanshi yakaita prison,Lokacin da taga Azmee tasha kuka sosai kamar ranta zai fita,Azmee ta rame ta ƙanjame,idanuwanta daƙyar take buɗesu,Sun rungume juna sosai,koda Sehrish ta sanar da ita cewa zata sanya a sassauta hukuncin da aka yanke masu,sai cewa tayi ita batason fita daga gidan yarin saboda gudun ta ƙara faɗawa halaka,tafi son zama anan saboda tafi samun natsuwa wurin yin ibadarta da neman yafiya wurin Ubangiji,kuma ta nemi yafiyar Sehrish akan Laifin da tayi mata,tun daga kan juya mata da tunaninta da tayi,lokacin da ta manta dasu Hosana,tace ita tayi hakanne saboda halin da tashiga na yawan damuwa shiyasa ta mantar mata dasu,da kuma lalurar da ta ɗaura mata na yin gane gane,duk sai da ta nemi yafiyarta,ta kuma sanar da ita cewa itace take kiran Sgr a waya tana raira mashi kuka saboda Son da take yi mashi,Komai sai da Azmee ta sanarma Sehrish,A ƙarshe ta sanar da ita cewa Suyi ƙoƙari su nemo Haroon domin kuwa Haroon Jinin Salahuddeen ne,mahaifinshi Jabeer ɗane ga Aminullah,wanda ya kasance Ƙanin salahuddeen ne uwa ɗaya Uba ɗaya,Saboda ƙiyayyar da ke tsakanin duka 6angarorin guda biyu suka sanya dokar da zarar anga Jinin Salahuddeen A kashe shi,Suma kuma su Salahuddeen ɗin suka sanya dokar daga zarar anga Jinin Ubaid da Uba a kashe su,A sanadin tafiyar da Aminullah yayi tare da matarshi da dansu ƙarami wanda bai mallaki hankalinshi ba wato Jabeer,Akan hanyarsu ta dawowa gida,Ubaid ya sanya ƴan ta'adda suka farmakeshi,gaba ɗaya suka kashe shi tare da matarshi,Shi kuma Jabeer suka barshi yana ta gararanba a cikin garinsu,har Allah yasa wani malamin makarantar Allo ya ɗaukeshi,A wurin shi Malamin Jabeer ya taso,kunji yadda akai haroon ya kasance Jinin Salahuddeen,A wurin Saratu matar ya sayyadi Azmee ta samu labarin nan,Saboda ita kanta batasan wanene Jabeer ba,Ashe Danginsu sunsan komai game da Shi ita kaɗai aka 6oye mawa,sai daga baya take ji a wurinta,ta bata labarinne acikin ɗakin da aka kaisu dayake su biyune aka kulle acikinsa,kuma ta tabbatar mata da cewa Haroon ɗan Jabeer ne,domin kuwa Hamma Ghali baya haihuwa,shi kanshi ya san da hakan,Amma don baƙin zalunci ya 6oye mata komai akanshi,
Lokacin da Azmee ta kammala bata labarin nan,tasha kuka kamar kamar me,Ashe Haroon ɗan uwansu ne,abun ya ɗaure mata kai sosai,iya cuta dai sun cutar da rayuwarshi,sun kuma sanya ƙiyayyarshi acikin zuciyoyin ƴan uwanshi,bawan Allah,ko a wani hali haroon yake ciki ayanzu?
A nan Sehrish take sanar da ita game da aurarrakin da aka daura ciki harda na Amrish da Yaya Yusuf,ba karamin farinciki Azmee tayi ba ta kuma kara yin danasanin abunda ta aikata masu don Mutane ne su masu matukar hallaci,Bayan Sehrish tabar prison ɗin,Ta kwashe komai ta sanar da Sgr,Sam bai yarda da maganarta ba,har sai da ya tambayi Abbansu game da Labarin kawunshi Aminullah,Anan Abba ya kwashe komai ya sanar dashi har labarin mutuwar da su kayi shida matarshi,labarin yazo ɗaya da wanda Azmee taba Sehrish,kuma Abba ya sanar dashi cewa Bayan mutuwar Aminullah da matarshi,An tsinci gawawwakinsu Amma ba'a samu gawar ɗansu ba ƙarami da suka tafi dashi,wato Jabeer,tunda Sgr yaji hakan,nan take ya yarda cewa dagaske dai Haroon jininsu ne,Abun Ya ɗaure mashi kai,ya kuma ji tausayin yadda rayuwar Haroon ta kasance,bashi kaɗai ba,Kowa na gidan da yaji labarin Wanene Haroon,wasu har kwalla suka zubar mashi,Kuma yanzu ashirye suke dasu nemo shi,don su dawo dashi acikinsu,yaci gaba da rayuwarshi kamar kowa,
An sassauta hukuncin da aka yankewa Azmee da Saratu,An fito dasu daga ɗakin duhun sannan An rage masu shekarun da zasu yi a kurkukun,daga shekara 20 zuwa shekara 10 cuf,ba kowane yayi masu wannan ƙoƙarin ba fa ce Sehrish,ita ta nemi wannan alfarmar a wurin Sgr,Ya kuma amsa mata,
A 6angaren Aunty babba kuwa,Tuni an sallameta daga asibiti,ta koma gidansu kano,lokacin da ta samu labarin Auran General Ishaq da aminiyarta Hajjaju,Tasha kuka tayi danasanin rayuwarta fiye da tunanin me tunani,taji raɗaɗi da ƙunci acikin zuciyarta,Har abada bazata ta6a manta Asarar da tayi a rayuwarta ba,duk don saboda abun duniya,yanzu gashi ta tashi a tutar babu,da ita da zero basu da bambanci,
Daga cikin waɗanda zasu tafi U.s,Hada Junaid tare da Jahad,Ba don Abbansu Yaso ba,Saboda shaƙuwar da yayi dashi,Ya amince ne kawai saboda Sgr ya nemi daya bar mashi Junaid ya zauna a wurinshi tare da Jahad har ya kammala karatunshi acan,Kuma hada ƙarin Idan aka tafi da Sehrish da Hosana,Jahad bazata ji daɗi ba,tasaba da ƴan uwanta sosai,Abba baidamu ba saboda Allah ya hore mashi,idan yaso duk weekend zai iya hawa jirgi don yaje can ya ganshi,wannan abu ne mai sauƙi a wurinshi,tafiya dai ta kankama,Yau ta kasance rana ta ƙarshe da ta rage masu a Nigeria,Washe gari zasu tafi tunda Asuba,duk wani shirye shirye daya kamata suyi sun kammala shi,tafiyarce kawai ta rage masu,Gobe in Allah ya kaimu da Rai da Lafiya.
*Ayi hakuri da wannan Yau sai ahankali,da babu kwara ba daɗi,Amma in sha Allah zanyi kokarin yin long pages na Ƙarshe,ina sa ran Sunday in Allah Ya yarda littafin abban Sojoji zaiyo maku bakwana,Lahadi kenan😢waɗanda ke buƙatar karanta Littafin daga farko zuwa na uku Suyi mun magana ta whatsapp 08103884440* [3/19, 2:58 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*
Join this link to follow my tiktok acct👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*
*Father of soldiers*
*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*
Zazzafar haja daga Minjibir ventures,Ina masu buƙatar siyan kayan sallah Kada ku bari a baku Lafiya,Ga kaya na kece raini Na shiga tsara,Koda kudinka sai da rabonka,Kadan daga cikin abubuwan da muke siyarwa akwai Lace Veils Atamfa Shoes Bags
Address Hotoro ladanai kan titin ring road Chat 09126570345 Call 09136122503 saikun Zo💃💃💃💃
Remain few pages 😢
*Har weekend zanyi posting,in sha Allah Ranar Lahadi Zan saki Last page Na Abban Sojoji,😢waɗanda ke buƙatar karanta Littafin daga farko zuwa na uku Suyi mun magana ta whatsapp 08103884440*
Godiya ta musamman ga waɗanda suka ƙarfafamun guiwa tun daga farkon Littafin nan har zuwa ƙarshen shi,Saƙon godiyata yana nan tafe 😍
gaba ɗaya saida abba ya tara ma'auratan A babban Falon gidan yayi masu nasiha sosai,Ammi ma tayi masu nasiha,abusufyan ma yayi masu,gwaggon katsina dasu Aunty azeema duk saida suka yi masu nasiha,Jikin kowannansu Yayi sanyi,su jahad sunsha kuka sosai,Saboda tafiyar da zasuyi subar Iyayensu da ƴan uwansu,hatta hosana da bata da cikakken hankali sai da tayi kuka,lokacin da ake yi masu nasihar,tun a daren ranar suka fara yin bankwana da ƴan uwansu,kafin asuba su tafi,
Wuraren ƙarfe 12 da dare,Oummansu ta tarasu a ɗakinsu,Bayan sun kammala sallar nafila,kowannansu Na sanye cikin Hijabi,Sunyi kyau kamar larabawa,saboda gyaran da suka sha,fatarsu har sheƙi take yi,hannayensu akwai zanen ƙunshin jan lalle da akayi masu na bikinsu,Sae ƙamshi ke tashi ajikinsu,Suna zaune saman darduma,
"Oumma yanzu shikenan tafiya zamuyi mu barki da daddy dasu abba"?Hosana ce tayi tambayar, Abu tace"ae tafiya ba mutuwa bace,Idan da rai da lafiya wata rana zaku zo mana,muma kuma zamu zo maku,"tuni idanuwanta sun cicciko tab da kwalla, Fuskar jahad ɗauke da damuwa tace"Ina zullumin tafiyar nan Oumma,jikina duk yayi sanyi,Zamu tafi wata uwa duniya,inda bamu son kowa ba,bamu da dangi acan,Bamu san ya zasu kar6emu ba," "Jahad,ki kwantar da hankalin ki,kidaina zullumi,kuma kidaina cewa baku san kowa ba,Idan har kuna tare da Omar da Rafayet to ku ƙaddara cewa tamkar duka family ɗinku suna atare daku,domin kuwa ina tabbacin cewa zasu baku kyakkyawar kulawa,fiye damu,Kada ku manta su ɗin jininku ne,Ƴan uwanku,Yayyanku kuma mazajenku,baku da wani makusanci daya wuce su aduniyar nan,bazasu ta6a bari rayuwarku ta wulaƙanta ba,ko yatsa wani yace zai ɗaga maku Bazasu ƙyaleshi ba,shiyasa ni bana shakku akansu,na yarda dasu sosai,Kuma ina matuƙar Alfahari dasu a matsayin Surukaina,Nasan zanyi kewarku sosai,Zan zubda kwalla akan rabuwa daku,Amma inna tuna cewa rabuwa ta zama dole,wata rana ma duniyar zaku bari,ko ku tafi koni na rugaku tafiya,Sai inga wannan bakomai bane,duk mun nisan da zakuyi indai kuna acikin duniyar nan,zamuyi iyayin waya,harma Video Call,kuma zaku dinga zuwa mana,muma kuma zamu zo maku,shi Aure ba inda bai kai mutun......'hawayen da take 6oyewa ne suka soma gangarowa asaman fuskarta,da sauri ta sanya hannu ta sharesu, A hankali Sehrish ta ɗago da idanuwanta cike tab da kwalla tana kallon fuskar Oummansu, "Dole sai kunsa haƙuri A rayuwar auranku,kuma kuyi biyayya ga mazajanku matsawar bai sa6a ma Allah ba,duk abunda basa so ku kiyayeshi,duk wani abu da zai faranta masu rai kuyi kokari wurin ganin kunyishi,Sannan ku dage da yin addu'a banda wasa da ibada,duk wani jin daɗin duniyar nan ƙararre ne wata rana,kada ku shagala ku manta daku su waye,wata rayuwa kukayi abaya..,....."daƙyar abu takai ƙarshen maganarta,duk jikinsu yayi sanyi sosai,duk sun natsu suna sauraronta,gaba ɗaya idanuwansu cike tab da kwalla, Sosai abu tayi masu nasiha,Ta kuma ƙara tunasarsu dasu game da yin tsafta,gyaran jiki,sarrafa abinci,kusan raba dare su kayi abu na koya masu rayuwar zaman aure,A ƙarshe tace"Allah yayi maku Albarka,Allah Ya baku zaman Lafiya da mazajanku,Ina roƙon Allah yasa Wannan auren da kukayi ya zama silar Shigarku Aljanna,' Da ƙarfi suka amsa mata da ameen, "Allah Ya albarkace ku da samun zuri'a ɗayyiba,Allah Ya kare ku daga sharrin maƙiya da mahassada," "Ameen Ameen Oumma" Ganin yadda duk jikinsu yayi sanyi yasa ta soma ƙoƙarin faranta masu rai donsu sakin jikinsu, "Kunsan wani abu"?girgiza mata kai su kayi alamar a'a, "Lokacin dana taso rayuwata,danginmu duk sun watse,saboda talauci,kowa takanshi yake yi,babu wani haɗin kai,A wurin haihuwata Mahaifiyata Ta rasu,Mahaifina ya damƙani a hannun kishiyar Babata,Matar nan ta tsane ni,babban baƙin cikinta irin farin jinin da nake dashi,mutane har zuwa sukeyi suna roƙonta akan ta basu ni su raine ni,ganin irin baƙar wahalar da nakesha,Amma matar nan taƙiya,saboda gudun kada in samu rayuwar jin daɗi inyi arziƙi,ta tauyemun haƙƙina,Dama ance duk xakaran da Allah ya nufeshi da yin cara,Sai yayita,mutuwa ne kawai banyi a hannun matar nan Ba,nifa ban ta6a tunanin zan kawo wannan lokacin da raina ba, ban kuma ta6a tsammanin akwai wata rana wadda zata zo irin wannan ba,Hasalima bansan wanene abusufyan ba Shima baisanni ba,ina nijar shikuma yana a nigeria,Kaji wani iko na Allah,babu wanda yasan da wani,ban ta6a tunanin ma zanyi aure ba balle har in haifi ya'ya har ƴan uku,Sai gashi ƙaddara takai mahaifina aiki gidansu,Ni kuma silar mahaifina dayazo ya ɗaukeni sakamakon ganin irin wahalar da kishiyar babata take bani ya dawo dani nigeria,A gidansu Abusfyan,ƙaddara ta haɗani dashi,Har mukayi aure na haifeku,Yanzu gashi har kun girma kuma kunyi aure Wata rana kuma zaku haifi ya'ya,Lamarin ubangiji da girma yake,Allahu akhbar......."fuskarta ɗauke da murmushi takai ƙarshen maganar, Dariya hosana tayi"Oumma,Nima Allah yasa in haifi ƴan uku," Buge mata baki Jahad tayi"ko kunya babu,agaban oumma kike cewa zaki haihu,"dariya abu tayi,Sehrish kuwa murmushi tasaki, Ɗaure fuska Hosana tayi tana jifar Jahad da harara,tare da jan dogon tsoki," "Yakamata ku kwanta kuyi bacci,har kusan ƙarfe ɗaya da wani abu,gashi gobe tunda asuba zaku tafi," Amsa mata su kayi da toh oumma,
Asaman gado, oumma dasu jahad suka kwanta,Cikin lokaci ƙanƙani bacci yayi awon gaba dasu,banda Sehrish sai da tabari sunyi bacci tukunna ta fito daga ɗakin,Jikinta sanye da sleeping dress,Riga da wando Orange,ta yafa mayafi akanta,jikinta sai ƙamshi yake yi,yunwa ce ta fito da ita,tunda tasha ruwa bata ci komai ba,saboda zullimun tafiyar da zasuyi,dayake Yau da azumi ta tashi,bata nufi kitchen kaitsaye ba,Babban falon gidan ta shiga babu kowa,shiru kake ji,Kowa yana can manne da matarshi aɗaki,A hankali take bin ko'ina na gidan da kallo,Tabbas zatayi kewarshi sosai,Bazata ta6a mantawa da rana ta farko data fara zuwa gidan aiki a matsayin namiji,In ta tuna wasu abubuwan sai tayi murmushi,wasu kuma tayi dariya,Yayin da wani abun idan ta tunashi sai ta fashe da kuka
Tajima acikin Babban falon tana zagaye shi,kafin ta juya ta nufi kitchen don ta zuba abincin da zataci,Koda ta shiga kitchen ɗin,ta soma neman abinci,bata samu komai ba duk an cinye abincin gidan,Kamar ta ɗaura hannu akai tayi ihu saboda takaici,ko kaɗan bazata Iya jure yunwa ba,rabonta da abinci tunda asuba da tayi sahur,tunanin ɗaura girki ta soma yi,batare da 6ata Lokaci ba,ta haɗa chicken pepper soup,bayan ta kammala ta ɗebo dankalin turawa acikin store ta fere shi,
A hankali yake saukowa downstairs,Idanuwanshi da alamun bacci acikinsu,daga shi sai Short ajikinshi gajeran wando,Babu riga,daga gani atakure yake,Ya kasa bacci saboda rashinta a kusa dashi,Yayi jiran harya gaji batazo ba kamar yadda ta saba zuwa suna kwana a bedroom ɗinshi,Wannan dalilin ne yasa shi fitowa domin nemanta,yana ƙarasa saukowa babban falon kaitsaye ya miƙi hanya zai nufi corridor ɗin ɗakinsu,ba zato ba tsammani idanuwanshi suka hango mashi ita cikin kitchen ta juya baya agaban Gass Cooker,Abun ya ɗaure mashi kai,Kamar wata Aljanna,duk irin tsoranta amma sai gata a kitchen kusan ƙarfe 2 na dare tana girki,
Walking slowly ya nufi kitchen ɗin,A bakin entry ɗin ya tsaya,Yana binta da kallo,kasa kunne yayi yana sauraran waqar da take raira, "Nagode ma Allah dana cika buri,Na zama matar rafayet,Yanzu babu mai mun gorii,Sgr gashi gabana,umm umm matsayin miji mallaki na....." Murmushin gefen fuska ya saki har dimple ɗinshi ya lotsa,cikin sanɗa yake tafiya har ya isa bayanta,tunani ya shiga yi taya zai ruƙota batare data tsorata ba,don yasan halinta,yanzu ko magana yace zaiyi mata Zata iya firgita,gashi tana agaban gass cooker,kada asamu matsala, Motsi ya soma yi da lips ɗinsa yana ƙoƙarin yin magana,yaji tace"Ina nake jin ƙamshin turaren ya rafayet,kodai hancina ne.....'bata kai ƙarshen maganar ba,a hankali Sgr,ya zagayo da hannunshi ya ruƙe hannunta dake ruke da turner ɗin da take juya chips ɗin data ɗaura, Har ta wage baki zata fasa ƙara,Yayi saurin cewa"its me,"Ajiyar zuciya ta shiga saukewa,ba ƙaramin tsorata tayi ba,kwantar da kanshi yayi asaman kafadarta, "I ave been waiting for u,kin manta da mijinki ko" "Am Sorry ya rafayet,kana araina"