Kenza eBookz

Abdulmajid complete - Chapter 1

Abdulmajid complete - Chapter 1

Abdulmajid complete Chapter 1: Abdulmajid complete Chapter 1. [6/28, 11:15 PM] πŸ’„Meryerm AbdoolπŸ’„: πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬ πŸ–€β€¦

4,486 words

[6/28, 11:15 PM] πŸ’„Meryerm AbdoolπŸ’„: πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬ πŸ–€ ```ABDULMAJEED``` πŸ–€ πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬

✨ *Servant of majesty*✨

Na πŸ’„ _Meryerm Abdool_πŸ’„

Β© *Pure moment of life writers* P.M.LπŸ’ͺ🏽

```zanyi amfani da wannan damar nayiwa dukannin masoya da abokai da 'yan uwa musulmi murnan kammala Ramadan lafia, sannan nayi muku barka da sallah fatar Allah ya karb'i ibadunmu ameen```πŸ‘πŸ½

πŸ“ *Episode* 1⃣⏩5⃣

Ψ¨Ψ³Ω… Ψ§Ω„Ω„Ω‡ Ψ§Ω„Ψ±Ψ­Ω…Ω† Ψ§Ω„Ψ±Ψ­ΩŠΩ…

Dukkan yabo da godiya su tabbata ga Allah mad'aukakin sarki, mamallaki sarkin iya halitta, tsira da aminci su tabbata ga Annabi Muhammad(S.A.W) Tare da sahabbansa da iyalan gidansu da duk wad'anda sukabi tafarkinsa har zuwa ranar ceto

_Banyi niyyan rubuta wannan littafin don cin zarafi ko fuska ga wani ba, idan kuma yaci karo da halinka/ki saiki/ka gyara, a guji zargi._

*Ban yadda wani ko wata ya juyamin koda kalma d'aya ne sai tare da izinina*

Tukuici gareku ahalina ina alfahari daku a duk inda naje, Allah yabar kauna ya rayamu a musulunci damu da sauran musulmi baki daya. *ILYSM❣

*KADUNA STATE*

*kofar mashi*

Garden ne matsakaici mai cike da furanni masu fitar da daddad'an k'amshi da itatuwa ma'abota fruits, gurin yayi kore sharr sai wata sayyayar iska ke kadawa wacce kowane ma'aboci halitta zaiyi sha'awar ya shaka, gurin d'auke yake da resting chairs farare, ga wata k'orama a gefe tana gudana abin gwanin sha'awa da burgewa.

Na shagala da kallon gurin, inata baza idona abinka da bakauyiya, can gefe cikin daya daga cikin rest chair na hango wani matashi a kwance.

Daf dashi naje domin naji dad'in d'akko maku rahoto dakyau, idanuwansa a lumshe sanye da wani siririn farin glass da alama medical ne, amma hakan bai hanani gane cewa matashin ma'aboci golden eyes bane saboda yadda eyes balls nasa ya fito akan fatar idon, hancinsa ba dogo bane hasalima za'a kirasa da guntu in short, kalar fatarsa abin burgewace wato chocolate.

Kallon nai masa da sama har k'asa na fahimci baida tsayi sosai, baida jiki ko kad'an saidai yana da k'irar k'arfi, gashin kansa irin na hausawa ne amma kan yasha gyara yayi kyau ya kuwa kwanta ba laifi, yana da round face kamar mace wacce ke zageye da man pride, bakinsa mai matukar kyawu d'auke da soft red lip, ina cikin nazari banyi aune ba naga ya mik'e tare da sauko da k'afafunsa kan shoes nasa, mashaa Allah k'afarsa abin sha'awace kamar a rangada mata lalli.

Mik'ewa yayi tare da d'aukar phone masa da iPad nasa dake kan desk yayi, sanye yake da shirt orange da jean baki, idonsa na kalla saida k'irjina ya buga kwayar idon brown ce yayin da farin ya surka da pink, bansan time d'inda nace subhanallah ba, ban tab'a gani irin idonsa ba before.

Inacan duniyar mamaki sai ganin nayi yakai k'ofar fita daga garden d'in, hakan yasa na bisa a 150 saboda ci gaba da samo maku rahoto. Lolz

Wata 'yar k'aramar k'ofa naga yabi sai kawai na gammu '' cikin wani matsakaicin parlour wanda yaji kayan more rayuwa dai2 irin na masu rufin asiri, wata matace zaune wacce i k'iyasce zatayi shekara arba'in da d'ori, a fizge tana kama da matashin, husnul musleem rik'e a hannunta tana dubawa.

Sai wata yarinya dake kwance gefenta tana barci a kalla zatayi ten year, sai yaro a k'asa sai faman zane yake a littafi sa'an wacce ke bacci da alama ma twins saboda kamar da sukeyi.

Zama matashin yayi kan 1seat bayan yayi sallama sannan YACE.

"Maamii sannu da gida."shima yaron yace " welcome ya Abdool. "

"Yawwa big boy me akeyine?"

"Homework ne."

"Ok a bada himma."

Itama Cikin kulawa bayan ta ansa sallamarsa tare da aje husnul musleem tace "yawwa Abdool dama ba fita kayi ba kenan?"

"Eh Maamii nad'an garden ne."

"A toh madalla, toya maganan horsemanship naka?"

"Eh Maamii inshaa Allah 2/3 week dai zasu kiramu."

"Sokoton dai koh" ta fad'a tare da kallonsa.

Shafa kansa yayi yace "itace Maamii."

"Nikam Abdool bansan meyasa ka nace sai Sokoto ba duk hospital d'inda ke Kaduna da zagaye ba wacce tai maka ne ko meye?"

Smiling yayi yace "ba haka bane Maamii inadai son naje gidane nayi wa garina hidima, kuma kinga zan k'ara sabo da 'yan uwana."

Nisawa tayi tasan abinda d'an nata ya gad'a gaskiya km hakan dazaiyi yayi dai2 saidai batason tayi nisa dashi ko kad'an.

Yaron da ke drawing jin yayan nasa na maganan tafiya yasa ya aje book d'in yaje kusa da yayansa yace "yace Ya Abdool da gaske tafia zakayi ka barmu?"

Shafa kansa yayi yace "Ajb ba dad'ewa zanyi ba, kuma zan ringa zuwa ina dubaku kaji my boy."

Girgiza kai yayi yace "nidai zan bika Yaya" ya fad'a yana narkewa jikinsa.

"To karatunfa Ajb?"

"Nayi a can."

Murmushi yayi yace "Ajb rigima, ita Husna tayi nata homework d'in?"dan ya d'auke masa hankali.

"Aa headache takeyi."

Mik'ewa yayi tare da zuga gaban seat ya dafa goshinta yace "Subhanallah tasha magani kuwa?"

"Aa batasha ba tai bacci."

Cikin nuna damuwa ya mik'e zuwa d'akinsa dan d'akko mata magani, Maamii kuwa sai kallonsa take tana k'ara godewa daya had'a mata kan 'yayanta suke tausayawa juna da k'aunar juna, sosai Abdool ke nuna kulawarsa akan kannensa ga saukin kai, yakan wasa dasu sosai sannan ya tsawatar musu idan sukayi ba dai2 ba( _shine gaskiyar rayuwa_).

^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^

*SOKOTO STATE* *Garin kilgori dake*

"Laure! Laure!! Laure!!!" Firgigit ta juyo tare da baro tagar ajin tazo gun mai kiranta tace "Delu ahe kece ina zakina halan?"

"Kekam Laure bakijin maganar Iya Hari, hi yassa kullum taka bugunki kaman ganga tase bataso kiyi boko, missa kika dagewa sai keyi, wane dadi agga boko?"

Dafa kafad'ar Delu tayi tace "Delu bansan missa Allah ya jarabceni dason boko ba, kullum inaji cikin raina zanyi boko kuma nayi alfahari dahi, amma bansan sai yauhe ba, duk ni gitto ta makaranta ji nikai kamar an damremin kafwa inji hena tsaya naji kara2" ta K'arashe maganar tare da zubar da hawaye.

Cikin tausayawa k'awar tata ta share mata hawaye tare da rungumota jikinta tace "kiyi hank'uri Laure da nuhar Allah zakiyi boko wata rana, yanzu ki d'auko turenki mu wuce gida tun kafin ki husata Iyaa Hari ta jibgeki tunda ba mutunci gareta ba."

Haka taje bakin tagar daga k'asa ta d'akko tiren gyad'arta, suka bar makarntar mai d'auke da 'yan ajijuwa da basu wuce biyar ba, suka doshi cikin gari.......

_Tirkashi to ma'abota karanta novel d'in Meryerm ko biyoni a sannu kuji da wanne salon nazo wannan karon_ love u friendsπŸ’ž

πŸ’„Meryerm AbdoolπŸ’„ [6/30, 6:44 PM] πŸ’„Meryerm AbdoolπŸ’„: πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬ πŸ–€ ```ABDULMAJEED``` πŸ–€ πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na πŸ’„ _Meryerm Abdool_ πŸ’„

Β© *Pure moment of life writers* P.M.LπŸ’ͺ🏽

```Jinjinar ban girma gareku zak'ak'uran marubuta, da girman kujerarku manyan mata masu duniya, gareku members of pure moment of life writers, ❀ more Greece 2 ur shinning elbowπŸ’ͺ🏽```

πŸ“ *Episode* 6βƒ£β©πŸ”Ÿ

Da d'an jayawa kafin a isa cikin garin tafe suke k'awar tata naci gaba da bata shawara da k'arfafa mata gwiwa.

Gari wanda za'a kirasa k'auye kuma garin fulani kai tsaye duba da yanayin gine-ginenda ke cikin garin, amma da alama manoma ne kuma makiyaya dan ko'ina ka duba shukace tun daga dajin garin har zuwa cikin garin, kama da gero, Masara, maiwa, albasa, tomatur, ata, tattasai kai har noman taba sunayi, ga kuma dabbobin na ciwo, a takaice dai da alama ba talauci a garin.

Dai-dai k'ofar wani gida Wanda zance duk garin ba irinsa naga sun tsaya, nan k'awarta tace "to Laure ni zan isa gida saike hito anjima Dandali" ta fad'a tare da tafiya.

"Tau Delu ki gaida Gwaggo" cewar Laure tare da sanya kanta a soron gidan, amma kuma fuskar taf tashin hankali k'irjinta sai bugawa yake dan batasan yau kuma wane kalan zagi zata samu ba.

Wata dattijuwace zaune tsakar gidan tana tunka tsawo, bakace mai tsamuraren jiki, ba laifi fuskarta irin ta fulanice saidai ta tamure itama, ga taba ta k'unsa a bakinta redio gefenta tana jin wakar *Barmani toge* cikin sanyin murya tayi sallama.

Dagowa tsohuwar tayi ba tare da ansa sallama ba tace "to gantalalliya sai yanzu kikk'are gantalin naki, keman Laure anyi tambad'add'iyar yarinya yanzu tun abun Hantsi sai yanzu kika dawo mini."

"Subhanallah, haba Hari wanga bacin k'are dangi da kikai ma diyanga marainiyar Allah dami yayyi kama? Hari wai mi diyanga tayyi miki da baki tab'a nuharta da alheri ba se sheri?" Wani farin dattijo ya fad'a yana aje buta fitowarsa kenan daga bayi.

"Haba Ardo wai missa kullum kurkiiyarga tayyi min laihi baka gani? Saima nawa kaka gani sannan ka bini da ganin laifi, koni kabar yimin irin haka ai sai kasa ta hwandare dama yaya lahiyar kura bale tayi hauka" ta fad'a cikin nuna bacin rai.

Girgiza kai kawai yayi tare da cewa "Allah ya kyauta" inda sabo ya saba da halin Hari Sam batason gaskiya.

"Ramlatuna shiga daga ciki ki aje turen saiki kawomana ruwan alwala garka kejina 'yar Albarka" ya fad'a tare da ficewa daga gidan cike da tausayinta.

Matse hawaye tayi tare da shigewa d'aki ta adon aje tiren, da harara ta rakata tare da banka tsaki tace.

"Munahuka dangin mayyu tai ki dawo ki iskoni saike hwadamin inda kittsaya."...........

_tofa meye sanadin wannan k'yayyar? Nida Ku mubi a sannu harmu gano bakin zaren_πŸ€”πŸ˜”

^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^

*KADUNA STATE*

*3 weeks later....*

Gabadaya sun fito waje domin raka Abdool zai wuce Sokoto saboda an kirasu, sanye yake da jean blue da shirt purple yana sanye da glass nasa as usual, left and right nasa yana rungume da Husna da Ajb, momynsu na bayansa, sai k'anwarsa Nihal data dawo Hutu week before tana rataye da lodge nasa.

Bakin motarsa suka tsaya ana k'ara bankwana, su Husna sun lafe jikinsa Sam basaso ya tafi saidai ba yadda zasuyi saboda tafiya ta zama dole...

"Abdool ka kula sosai ka tsare mutuncinka da kimarka, ka kula da ibadarka ka rike Addu'a sannan ka sada zumunci da 'yan uwanka kada ka nuna musu komai sai Alkhairi, Allah ya kiyaye hanya, ya Baku sa'a da nasara akan abinda kukajeyi."

Ba kad'an yaji dad'in addu'ar Maamii tasa ba, yace "inshaa Allah Maamii zan kiyaye, aci gaba dayi mana Addu'a, Addu'arki itace silar cigabarmu."

"Addu'a ba fashi Abdool Allah ya k'ara shiryaku baki d'aya."

"Ameen Maamii" ya fad'a sannan yace "my guy missing u" yace tare da rungumesu, suma rungumesa sukayi sukace "missing u too bro.

Dak'ar suka rabu yaja car d'insa cike da kewar familyn ya d'auki hanyar birnin Shehu..........

_wasa farin girki muje zuwa friends_ πŸŒπŸ½β›ΉπŸΎβ€β™€

πŸ’„ Meryerm Abdool πŸ’„ [7/2, 11:55 PM] πŸ’„Meryerm AbdoolπŸ’„: πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬ πŸ–€ ```ABDULMAJEED``` πŸ–€ πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na πŸ’„ _Meryerm Abdool_ πŸ’„

Β© *Pure moment of life writers* P.M.LπŸ’ͺ🏽

```Manzon Allah (S.A.W) yace:-``` *Yana daga cikin kyawawan dabi'un musunci mutum yabar abinda bai shafesa ba.*

( _Tirmizih da wadansu suka ruwaitoshi, daga hadisai arba'in_ )

πŸ“ *Episode* 1⃣1⃣⏩1⃣5⃣

Saida ya biya ta Unguwar Rimi ya d'auki friend d'insa Hakeem Wanda shima a Skk zaiyi horsemanship nashi saidai shi pharmacy ne, t'uki yayi cikin Jean vitae hankali suna tafe suna sauraren wak'ok'in larabawa na *Mishary Raseed Alfasy* dama Abdool ba rigima, tun Hakeem na mitar t'ukin har ya hak'ura dan ba yadda ya iya da mutumin nasa, gashi shi yace bazaiyi driving ba, dole ya bisa a yadda yakeso.

Basu suka isa ba sai after ishaa, direct family house nasu suka wuce, estate ne guda, mai d'auke da compartment 5 mafi girma daga ciki naga sun dosa, direct main parlour suka sauka.

Da sallama suka shiga, wani dattijone zaune kan kujera, ga wasu samari gefensa alaman magana suke dukkansu kusan tsaran Abdool ne, cikin farinciki suka juyo yare da ansa sallamar, tasowa sukayi suka rungume Abdool da Hakeem tare da fad'in.

"Ur highly welcome home bro" sannan sukayi musabaha, shima cikin murmushi, yace "fatar na sameku lafia?"

"Alhmdllh" suka fad'a tare da k'arasawa gurin dattijon gaba d'aya, fuskarka d'auke da murmushi ko ba'a tambaya ba kasan yana farinciki da zuwan jikan nasa.

Kan hannun kujerarsa Abdool ya zauna tare da rungumesa yace "tsoho mai ran k'arfe kaga jiya kaga yau."

"Zanga gobe da yardar Allah kuma, likkita bokan turai yau kaina a sakkwato?"

"Sharri kayan kwalba, sai yau ka saba ganina a sokoton?"

"Kai bature kada ka wayance yaushe rabonka da garin?"

Sudai samarin da Hakeem sai kallon drama suke suna dariya babu mai barin ta kwana cikinsu.

Saida suka gama rigimarsu sannan aka gaisa.

"Abdulmajeed ya Maman naku da kannenka duk kuna lahiya dai ko."

"Lafiya qlau Alhaji sunce a gaisheku sosai."

"Kai madallah, haka akason ji, kai sama'ila kuje dasu ciki sud'an huta, kasan halin likitoci basu son wahala" ya fad'a yana kallon Abdool.

Smiling yayi "haba tsoho nida nike sabon jini saidai kai daka kwana biyu jini yayi nisa."

"Ho dan nemanga tahi ka dawo ka taho mu gwada kaga aikin tsohon kashi"

Dariya yayi tare da bin bayan su Hakeem da suka fice suna dariya yace.

"Rufamin asiri dattijo A d'auri kashi ko a bata igiya" ya fad'a tare da ficewa.

Shima dattijon dariya yayi yana maijin dad'in ganin jikan nasa da aka kwana biyu ba'a had'u ba..............

^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^

Sumui-sumui ta shigo kamar munafuka taje bakin randa da niyyan d'aukar buta tayi alwala, taji muryar Iya Hari tace.

"Tau jikan mayyu, waje Musa ciki Fir'auna kinzo kina wani Abu kamat ta kwarai kewai ga musulma, ki gama gulmarki kizo ki sameni saike bani labarin ubanda kika d'auka a makarantar bokoko da ki k'wuk'wema zuwa dudda na hissheki ciki, ko wani salon karuwancin na a haka eye."

Itadai shiru bata motsa ba bare ta tanka, inda sabo ta sama da irin wad'annan cin fuskar da zagi daga Iya Hari, Sam bata ragamata ko k'adan akan laifin da ba ita ta aikatashi ba, amma kullum a Kanta take saukewa.

"Oho ina magana keyimini tsaye k'ik'am kamar icce niddasa ko, kedai anyi shegiyar yarinya mai bakin hali, maza ki aje butan nan ungu ki kaima Lanti saura ki wuce wurin gantalinki da kissaba."

Cikin sauri hadda hard'ewa ta amshi ledar tare da ficewa da sauri kamar mai jiran cas, da tsaki ta bita tare da cewa.

"Tai ki dawo ki iskoni kici na jaki, bak'ar iri."

Tafe take cikin nutsuwa idan ka ganta ba zakace 'yar kauye bace, saboda tafita daban dasu komai nata a natse kamar wata babbar mace duk kuwa da k'arancin shekarunta.

Daga sama taji ana kiranta, ko bata juyo ba tasan me kiran nata, tsayawa tayi ba tare data ansa ba kuma bata juyo ba.

Wani hargitsatsen matashi ne ya tsaya gabanta, kalar irin ta 'yan daban fulanin nan bakinsa bak'i k'irin irin na 'yan sha, ido jajir kamar gauta.

"Waike Laure minana abbusa kanki, walle keci azzikin ina sonki daba haka ba hmmm khattt...." Yayi kwafa.

Itakam kallo kawai ta bishi dashi ba tare da tace uffan ba.

"Ke halan icce kike ina magana sai kallona kikai ko nayi miki kyauna" ya fad'a yana wani k'wanbewa.

Sanin halinsa idan ba maganan tayi ba ba barinta zaiyi ta tafi ba yasa tace.

"Jauro daga ina haka?"

Wani dad'i yaji ya lullub'esa dan ba k'aramin so yakema Laure ba shiyasa yake daga mata k'afa lokuta da dama ita kadaice weak point nashi, ko Abu ya had'aku da kace don Laure tofa yanzu zai sarara maka, duk kuwa da tsagerancinsa dan duk garin kowa shakkunsa yake saboda dan Sara sukane kowanne lokaci yana tare da makami, ganin badan arziki bane yasa Iya Hari amincewa da soyayyarsu da Laure, saboda kawai ta musguna mata.

Ardo yaji duk abinda ake ciki amma bai nuna ya sani ba, ya barsu yaga iya gudun ruwansu, abinda kawai ya sani bazai taba Aurar da marainiyar Allah.

"Daga daji nike, kehwa INA zakina?"

"Hmm gidan Gwaggo Lanti" ta fad'a a takaice, tare da juyar da fuskarta ganin irin kallon da yake mata na k'urillah.

"To..toh mutai in rakaiki?"

Ganin no way 2 escape yasa ta yadda suna tafe yana mata hira, ita kam sai uh da uhum da to take binsa dashi.

Aiko har suka isa ba'a samu Wanda ya daga ido ya kallesu ba saboda sanin hali, haka yake gadinta kamar kwai, ba kuwa ubanda ya isa ya kalleta balle yace yana sonta duk kuwa da dimbin masoya da takeda shi, amma suna gudun rasa rai dan k'aramin aikinsa ne, kisa.

Saida yaga shigarta sannan ya juya zuwa sabgarsa..........

_Rikici ba gado ba_ 🀣😜

πŸ’„ Meryerm AbdoolπŸ’„ [7/4, 10:31 PM] πŸ’„Meryerm AbdoolπŸ’„: πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬ πŸ–€ ```ABDULMAJEED``` πŸ–€ πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na πŸ’„ _Meryerm Abdool_ πŸ’„

Β© *Pure moment of life writers* P.M.LπŸ’ͺ🏽

*DOLE NA JINJINA MUKU*

*MAMAN USSEY* *ABDOOL AAJ* *FATYY AZLAND* *UMMI A'ISHA*

_kud'in daban kuke, kamar yadda halinku na k'aramci ke nuna Ku, bazan gaji da fad'a ba wato da bazarku nake takawa πŸ’ƒπŸ» halin kirkinku yabiku har gadon bacci_ πŸ‘πŸ½

πŸ“ *Episode* 16--20

Saida sukayi fresh up suka d'an ci abinci da yake an shirya musu better, amma Abdool kad'an yaci dan idan da abinda ke bashi wahala to cin abinci ne.

Maamii ya kira ya fad'a mata sun sauka lafiya tare da gaisawa da k'anninsa wad'anda ya fara missing tun yau, cikin gida suka shiga suka gaida da kakarsa wato Haj, Saude wacce ta ansa su sama2 ko halinta ne haka oho!.

Daga nan suka shiga sauran gidajen suka gaisa da iyaye, yayyi, da kanni, daga nan suka koma inda tsoho mai ran k'arfe inji Abdool fa.

Hira suka sosai kaman ba wad'anda suka sha hanya ba har 12, Alhaji Sada yace suje su huta zuwa gobe kuma aci gaba.

"Wane gobe Alhaji nida zanyi sammako saidai na barku da Hakeem."

"Au abun 'yar hakane shine ka gudu *Yabo* dan kada ka zauna Sakkwato ?" Alhaji ya fad'a yana hararan Abdool.

Dariya yayi "Alhaji aiba laifina bane kuma ai anan Sokoto akwai consultant doctors da yawa k'auyukan sunfiku bukatar likita."

"Ho dan nema badai iya fad'a ba, Allah ya taimaka, k'ilama acan ka samo 'yar budurwa, koda yake naga alaman tsoron mata kakeyi, kila sai munyi maka gangami an d'aura maka a k'afa."

"Hhhhhhh kajika da shirmen tsufa, an gayama ni Kaine, aini matata ba'ama haifeta ba" shidai Hakeem sai dariya yake suna burgesa.

"Aa kak'i cewa mamarta ma ba'a haiheta ba, ja'iri zanso naga wacce zata aureka da shirmen nan naka, kaidai ba abinda ka bari na 'yan fari"

Dariya sukayi banda shi murmushi kawai yayi tare lumshe ido.................

_wannan kenan_

^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^

Zaune suke a Dandali, wasu na gad'arsu yayin wasu ke samartaka, wasu na siye da siyarwa, "Laure kina zuwa Yabo ran juma'a kai nono?"

"Kai Delu kema kesan dolena intahi inhar inason in tsira da mutuncina, Iya Hari, tun yau tayo tatsarta baki ganai ba mai yawa kuma nid'ai."

"Aa na d'auka ko mutuminki ya hana kinsan shi dole yabi dokarsa koya taka ta."

B'ata fuska tayi tace "wane mutumin nawa?"

"Jauro mana ko kinada wani bayan shina?"

"Ni wallah Delu kibar had'ani da wannan mugun abu" sai hawaye sharrrr..

Tasowa tayi da sauri tare da rungumeta "yi hankuri abukkiyata nifa da wasa nikai miki, amma ai bana fatan ki kasance matarsa koda maza sun k'are ko."

Sauke numfashi tayi tare da share hawaye "wallahi Delu na tsani Jauro bansan ya nikai dashi ba, amma ita Iya Hari ba Wanda takaso saishi, saukina Ardo har yanzu baice komi ba, ina tsoron kar shima ya yadda."

"Ina Ardo bai tab'a aura miki, Jauro kuma inshaa Allah saikin auri d'an arziki kamar kowa, me ake da J......" Kasa isuwa tayi saboda arba ta tayi dashi yana zuwa, da alama a buge yake sai layi yake ya tunkarosu ga muk'arrabansa bayansa suna take masa.

Jin k'awar tata tayi shiru ne yasa ta d'ago dan ganin meke wakana, arba tayi dashi ya kusa kawowa wurin da suke, d'aure fuska tayi tare da d'auke kai.

Cikin muryan 'yan sha yake magana "ya ke Laure baki ganeni ba halan kiyi fuskar shanu tare da d'auke kai" sannan ya kalli Delu da tasha jinin jikinta "ke munahuka tashi wuce gulmammiya."

Aiko da sauri ta d'auki tirenta ta cika bujenta.

"Haba Jauro wai meyasa kakaimin haka, kaga banson haka, hakad'ai ka korar min abokiyata."

Tunda ta fara magana kallonta kawai yakeyi cike da sha'awa Sam shi bai gane fad'a take ko hira take masa saboda tsananin so.

Wani daga cikin yaransa ne yace "ke oga kika dagama murya saboda ke rammai?"

Tsawa ya daga masa "kai Shago Laure ce fa, kakewa fwad'a?"

Ya fad'a yana zare ido kaman ya maresa, "tuba nike oga."

"Ka kiyaye gaba" koda ya duba har ta bar gurin, murmushi kawai yayi tare da k'arawa gaba.

_so kenan hana ganin laifi_

*Pls friend kuyi hak'uri dani ina fama da matsalan wayatane shiyasa bana typing da yawa.* love u all😘

πŸ’„Meryerm AbdoolπŸ’„ [7/7, 8:42 PM] πŸ’„Meryerm AbdoolπŸ’„: πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬ πŸ–€ ```ABDULMAJEED``` πŸ–€ πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na πŸ’„ _Meryerm Abdool_ πŸ’„

Β© *Pure moment of life writers* P.M.LπŸ’ͺ🏽

```Where r u? Here is ur page, Momyn sultan, Sakwara, Iya Amima, Sadnap, Sadnas, kanwata jannart, Rukie kax and d rest. ur d best among besties. πŸ’•```

*In dedicated 2 Abdool all over d world* πŸ’˜

πŸ“ *Episode* 21--25

Bayan sun dawo da sallar asubah a d'akin kakan nasa ya yada zango, ya iskoshi zaune kan kujera tasbaha a hannunsa yana ja, hannu ya bashi sukayi musabaha tare da yimai barka da asuba sannan ya zauna k'asa dai2 kafarsa yace.

"Ina kwana Alhaji?"

"Lafia lau Abdulmajeed ya gajia?"

"Gajia ta tafi, ya girma ya kuma hak'uri da jama'a?"

"Alhamdullilah, zuwa yaushe zaka tahi yabon?"

"Um zuwa goma nakeso na tafi, shima Hakeem tare zamu fita yaje yayi report a Uduth d'in?"

"Amma anan zai zauna ko?"

"Aa zasu bashi gida to inaga acan zai zauna"

"Ikon Allah tahiya zakuyi gabad'ai?"

"Aa ai Hakeem zai ringa zuwa yana gaida ku, ni kuma zan ringa zuwa end of week inshaa Allah."

"Tau ba damuwa, Allah ya taimaka ya baku nasara a aikinku" sannan ya k'ara da cewa.

"Kaci gaba da hak'uri Abdulmajeed, dama nasan kai mai hak'uri ne, kowane bawa da yadda Allah yake tsara mishi rayuwarsa, idan aka d'auke shi a jarrabawa akayi hak'uri sai kaga ya wuce sai labari, Allah yayi maku Albarka."

"Ameen Alhaji nagode, zan shiga daga ciki nad'an kintsa kafin lokacin yayi."

"Tau yaushe zakaje Argungu can inda kakanninka?"

"Shima idan nayi clearing abubuwa zanje."

"Tau ka shiga ciki kayi sallama da iyayenka da kakarka kaji ko?"

"Inshaa Allah" ya fad'a tare ficewa yana share hawayen da suka zubo masa Wanda ni kaina bansan dalilin zubarsu ba, (tofa kona meye? Mubi a sannu zamu fahimci na meye nan gaba).

Tsaf ya kimtsa shida aminin nasa bayan sunyi sallama da mutan gidan, uduth suka nufa saidai ya tabbatar anyi komai daya kamata ayi sannan ya wuce yabar Hakeem tare cousin nashi su Isma'il, saboda a dalilin sa ya cika garin yaso su samu asibiti d'aya saidai hakan bai samu ba.

Hakeem aminine na kwarai ga Abdool Wanda bayada kamarsa amintarsu ta samo asaline daga secondary har jami'a Wanda har takai ga iyayensu, kullum Hakeem yana lura da akwai wata b'oyayiyar damuwa tattare da Abdool yasha tambayarsa amma kullum amsar d'aya ce ba komai, ya dad'e da sanin halin Abdool na zurfin ciki Sam baya bari damuwa tayi tasiri akansa yana k'ok'arin boyeta, dole shima ya hak'ura yasan in lokacin ya Sani yayi to tabbas zai gayamasa.

Shima dai ya isa garin Yabo kuma ya samu karb'a mai kyau daga mutanen garin amma kam asibitin na buk'atar ma'aikata da kayan aiki, a dalilin haka yayi alkawarin taimaka musu iya k'arfinsa Dana aljihunsa.

_wannan kenan_

^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^

Tana tafe tana tunanin irin k'iyayyar da Iya Hari da Gwaggo Lanti ke nuna mata basu tab'a sonta ba, kullum cikin zaginta suke, k'arshe k'iyayya yakai su zab'a mata jauro a matsayin masoyi.......

"Ramlatuna" ko bata juyo ba tasan duk fad'in duniya bamai kiranta da wannan sunan sai shi kad'ai, juyowa tayi da murmushi akan fuskarka yana zaune bakin gidan yana duba littafi ashmawi Sam bata lura dashi ba ta tafi duniyar tunani.

Dawowa baya tayi tare da duk'awa tace "sannu Baffa, ban kula dakai ba."

Murmushi yai mata "daga ina kike da darenga?"

"Baffa daga Dandali tallen gujjiya."

"Bana hanaki zuwa Dandali da daddare ba?"

Duk'ar da kanta tayi ba tare da tace komai ba.

"Koda yake ba laihinki naba, kiyita hank'uri Ramlah da Hari inada tabbacin wata rana zata gane batai miki adalciba, kuma da yardar Allah inaji a raina sai ke zama abin alfahari a wanga karkara."

Wani k'unshi ya d'auko bayan shi ya mik'a mata "kici wanga nasan da wuya in keci abinci"

Ansa tayi zata shiga ciki tare da cewa "nagode sosai baffa" dakatar da ita yayi tare da nuna tabarma.

"Zauna nan kici" saboda sanin halin Hari idan ta gani ba barinta taci zatayi ba.

Ba musu ta zauna tare da kwance ledar nama ne agashe da zafinsa ci take hannu baka, kallonta Ardo yakeyi cike da tausayi yana mamakin hali irin na Hari, Sam batada zuciyar imani.

Cikin k'ank'anin lokaci ta cinye, ruwa ya bata tasha sannan yace ta shiga ciki, cike ta shiga zuciyarta wasai tana mai jin k'aunar Ardo har cikin ranta.

Shima d'auke kayansa yayi tare da shigewa ciki dama ita yake jira.

*Washe gari*

Kamar yadda ta saba tashinta da ruwan sanyi yauma hakane, dasu ta tasheta tare da binta da zagin k'are dangi kamar yadda ta saba.

Haka ta tashi tayi abinda ya zame mata dole sannan tayi shirin zuwa Yabo.

Zuwa karfe 9 sukaje titi don zuwa Yabo, sun kuwa yi sa'a sun samu mota, tunda suka fara tafia sai murmushi take kallonta Delu tayi "Laure missa meki na farinciki sai murmushi kikai ked'ai."

"Ni kaina bansani ba, nadaiji yau farinciki nikeyi Wanda bansan dalilin inaji a jikina wahalata ta kusa zuwa k'arshe."

"Tau Allah ya tabbatar."

"Ameen abukkiyata."

*A garin Yabo*

Abdool ne zaune kan mota bakin asibiti kasancewar yau ba aiki da yawa patients basuda yawa yaje yayi round shine ya fito waje yana shan iska, yau tunda ya tashi gabansa ke fad'uwa baisam me yasa ba, ya kira Maminsa yaji suna lafia, haka bangarensu Alhaji suma lafia.

Jin bugun zuciyarsa ya tsananta yasa ya rik'e gurin tare da yin Addu'a.

Jin ta sassauta yasa ya d'ago kansa karaf idanunsa suka sauka kan na NATA...........

Lokaci d'aya zuciyarsa ta buga kamar ta fito.....

_wacece wannan_ πŸ€”

*Friend kuyi hak'uri da jina shiru da kukayi hakan ya farune a dalilin rashin nepa da mukayi 2days* love u❀

πŸ’„Meryerm AbdoolπŸ’„ [7/10, 1:32 PM] πŸ’„Meryerm AbdoolπŸ’„: πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬ πŸ–€ ```ABDULMAJEED``` πŸ–€ πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬πŸ‡³πŸ‡¬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na πŸ’„ _Meryerm Abdool_ πŸ’„

Β© *Pure moment of life writers* P.M.LπŸ’ͺ🏽

*Annabi Muhammad (S.A.W) yana cewa:-*

_baya shiga aljannah wanda mak'wabcinsa bai amincewa ha'incinsa ba._

*'yar uwa koda kafiri kike mak'otaka ya zama dole ki sauke nauyin hakk'in mak'otaka daya rayata akanci, makota abune mai girma saboda fadar manzonmu.*

"Jibrilu ya kasance yana yimin wasiyya da mak'oci har saida na d'auke idan na mutu zai gajeni".

_Allah yasa mu gyara_ πŸ‘πŸ½

*Point of correction*

_Abdool service sukeyi ba internship ba, fatar kun gane frnds_.

πŸ“ *Episode* 26--30

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull