Abdulmajid complete - Chapter 10
Abdulmajid complete Chapter 10: Abdulmajid complete Chapter 10. "Ke d'iyata ta gari mai hak'uri, karki canza daga halinki na kwarai da nissanki kici gaba…
4,449 words
"Ke d'iyata ta gari mai hak'uri, karki canza daga halinki na kwarai da nissanki kici gaba dashi, gida zakina ba daji ba inda 'yan uwanki na, zakina don Allah Ramtuna kici gaba a yadda nissanki Allah ya arbarkace ku gaba d'aya" tuni idanunta suka kawo k'walla duk son da take na had'uwa da dangin ummin nata, gata kuma gaban su a yau amma kuma sai taji batason rabuwa da mahaifarta batasan rabuwa da Baffanta mai k'aunarta, shi kanshi Ard'o daurewa kawai yakeyi amma yasan zaiyi kewar Ramlatunsa...
Mami CE ta share mata hawayen da zuka zubo mata tare da bubbuga mata baya.
Suma Malam Garba da Alhaji nasiha sukayi musu da sanya musu Albarka, anan Ard'o yace zasu iya wucewa, Mami ce tace a kaisu inda iya Hari suyi mata godiya sannan tayi sallama da Ramlah, shikam Ard'o yama manta da wata Hari dan baiyi niyyan sakota a ciki, kai ya jinjina lallai karamcin dangin Asma'u yawane dashi duk da sunji kalar cutar war da Hari tayi ma Asma'u da Ramlah amma duk da haka godiya zasuyi mata..
"Aishatu kikai su inda innarku" Shatu da itama farinciki da ganin yau Ramlah ta had'u da dangin umminta, dama ta dad'e tama mata fatan Alkhairi a rayuwarta ga Alkhairin yazo kuwa, "to Baffa" sannan ta wuce gaba sukabi bayan ta...
*****************
Su Iya Hari da ke zaune zugum kamar masu zaman makoki, tunda sukaji karar mota suka leka, dawowa sukayi suna jiran shigowar Ard'o, saidai babu shi babu labarin shi, kamar an aiki bawa garinsu, tuni suka shaka wai ya wulak'antasu(ji hauka ita da akaba kud'i tayi abinci batayi ba) suna zaune sai zaginsa suke shida Ramlah ko salla sunk'i tashi suyi, yo dama sai anga dama akeyi, sallamar Shatu ce ta katse su.
Ganin Ramlah bayanta yasa Lanti mik'ewa da sauri da niyyan zuwa ta cafkota, ita kuma Iya Hari tana shirin bud'e baki ta fara cin mutunci, sai suka ga ta shigo, a firgice iya Hari ta mik'e tsaye tare da zaro k'ananun idonta, itama Lanti tsayawa tayi cak, kamar photo, murmushi Mami ta sakar musu tuni tsoro ya lullub'esu dan sun d'auka Asma'u ce.
Shatu ce taje ta d'auko tabarma ta shimfida mata, zama tayi sannan tace "ina wuni Iya mun sameku lafia" sai nan Iya Hari ta motsa tabbas kama sai yanzu da taji muryarta tafi ta Asma'u girma, jiki a sab'ule ta ansa itama Lanti haka ta jayo kafafu tazo ta Zauna.
"Nasan ba zaki ganeni ba, sunana Ameena ni yayar Asma'u ce kuma mahaifiyar Abdulmajeed mijin 'yata Ramlah" wani irin kwarjini tayi musu cikin rawar murya tace "Toto madallah" taja baki ta tsuke.
Shatu ce tayi musu cikakaken bayani sun girgiza ainun dajin wannan sabon Al'amari, amma maimakon suyi nadama sai b'acin ciki ne ya rufesu saidai ba damar su nuna dan suna tsoron matar danko shigarta abin dubawa ce.
"Iya dama naso ne da d'iyata tayi muku bankwana sannan kuma nayi godiya da rik'on da akayi mata, mungode Allah yayi Albarka".
Wani irin gunguru gum taji kanta yayi " kodai batasan irin rik'on tayi mata bane ita da Uwarta" ta fad'a a ranta, a fili kuma murmushi yak'e ta k'irk'iro Wanda Sam bai mata kyau ba dan bata saba yi ba.
"Aa babu komi d'iyagga, tau Laure a tahi aita Arme Allah ya Baku zama lahiya" Ameen" tace itama Lanti sanya Albarka tayi, nan Mami ta tashi ta debo kud'i cikin jakarta ta raba musu, sannan ta dunk'ule wasu masu yawa taba Shatu, nan kuwa su Lanti sai hararan Shatu ake, har waje suka rakasu koda suka fito harsu Baba sun fiffito sun tsaya a bakin mota suna jiran su, gaisawa sukayi dasu Iya Hari, sai wani d'ari d'ari sukeyi, ba Wanda ya nuna musu komai a fuska.
Hakan yasa suka d'auka basu sani ba suka d'an saki jiki, hadda yi musu gaisuwan rasuwar munafurci, shikam Abdool kallon su kawai yana jinjina kai lallai mutum ba kyau, nan k'awayen Ramlah suka iso rungume ta sukayi suna kuka itama kukan take, kud'i Mami ta raba musu suma suka wuce Delu ce kawai ta tsaya tana ta kuka, sun rungume juna ita da Ramlah dama itace k'awar ta ainihi sauran duk copy ne.
Ard'o ya rabasu tare da basu hak'uri, Cikin jikinsa ta shige tana Mara yan kuka, shi kansa ya sakata mota tare da rarrashinta "keko dai Ramlatun Baffa ai nace miki idan Mijin naki ya tashi tafiya zan biyoshi inga Mazaunin Ku, ko bakiso in taho na"?
Kai ta girgiza alaman tanaso "Yawwa share hawayen kije kinga ke kawai ake jira" da wayo ya samu tayi shiru Mami kam mamaki wannan soyayya kawai takeyi, Abdool kuwa kallon yadda take kukan take Cikin shagwaba shi dariya abin yake bashi shine zaija motar sai kawu Mansur gaba, ita da Baba da Mami ne baya, kwantar da ita Mami tayi kan cinyarta, tana rarrashinta sannan yaja suka wuce, dama su Alhaji tuni suka wuce.....
Wasai Ard'o kejin ransa yau ya sauk'e wani nauyi a kansa, saidai zaiyi kewar Ramlatunsa, godiya yayi Malam Garba sannan ya shiga gida.
"Tau Hari kega yadda Allah ka ikonai ko, Yau dai keda dangin Asma'u dakikai mata gori kullum akansu kuma ke tabbatar da suna sonta, inama tana raye taga wagga rana...."
Cikin harara ta katsesa "yo Malam mi a sabo nanga (meye sabo anan) dan Mayu sun d'auki d'iyarsu daga sun taimaka mana ma, kuma in kudd'i wane irina a bangani".
Murmushi yayi tare da cewa " baki tab'a ganewa Hari, Allah ya ganar dake" sannan ya wuce abinsu, nan kuwa suka zauna sai fad'a suke ita da Lanti kamar su ari baki (kuwwa baya ga yak'i) itakam Shatu zamewa tayi tai gida abinta tana nema musu shiriyar Allah dan ta fahimci sunyi nisa har yau basu san Annabi ya faku ba(rayuwa shirin Allah inji k'awata swerry)...
********************
A Argungu zabon zaman makoki akayi kowa yazo ganin Ramlah sai yayi hawaye, shikam Abdool ganin abin yayi yawa yasa ya zame ya dawowar sa yabo sai waya yayi ma Mami cewar ya koma, kwanansu biyu har birnin lafia sunje inda dangin Baba, sunyi farinciki da ganin Ramlah da akayi imma iya baki ne can musu, a kwanakin Mami ta Samar ma Ramlah passport sukabi flight sai Kd dan tabar su Husna inda Nanny su Saboda school, Inna kuwa ji tayi kamar a barmata Ramlah saidai ba dama hakan, saukinta ma yanzu matar kawu Mansur nanan tana debe Mata kewa, dan ya dawo yayi aure har da 'ya.
A yau ne mutanen yabo suka shiryama Abdool walimar girmama sunyi k'ok'ari Sosai to ai Abdool d'inne na mutane kowa nashi, sun bashi kyaututukka sosai haka ya baro Yabo cike da kewar garin dan adan zamansa ya saba dasu, suma dai basu so tafiyar sa saidai ta Riga ta zama dole.
Saida ya biya ta Kilgori ya d'auki Ard'o sannan suka biya Sokoto suka sallami Alhaji Sada, tare da d'aukar Hakeem suka nisa hanya.........
🚗
Safe trip
💄Meryerm Abdool💄 [8/19, 10:15 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
📝 *Episode* 146--150
Ramlah data rud'e da ganin Argungu ta d'auka k'arshen kallo kenan, ashe kallo na gaba, balle ta taga jirgi ai gigicewa tayi, saida Mami ta rik'e ta a kafad'arta aiko ta k'ank'ameta, Aa ashe da sauran rigima da jirgi ya tashi, kuwwa tasa saida Mami ta rufe mata baki, tare da boye mata fuska a cinyarta, nan tayi baccin tsoro(tsoron k'arya ne Ramlatun Baffa aida bakiyi bacci ba).
Suna sauka driver yazo ya d'auke su, nan fa kallo ya samu ga Ramlah ido, baki, hanci duk abu d'aya sukeyi taga garin Gwamna ashe na Argungu wasa ne, lokacin da suka isa gida, nan ma wani sabon kallo ganin furanni ko'ina sai kalolin k'amshi suke fitar wa, ita dai Mami sai dariya take mata, ganin Abin bana k'are bana yasa Mami taja hannunta tana fad'in "Ramlah muje ki huta ai idan kallo zakiyi har ki gaji tunda kinzo kenan" kunya taji ta kamata tayi d'an Smiling.
Su Abj da Husna ne suka fito a guje suna fad'in "oyoyo Mami" dama ta kira Naninsu ta gaya mata dawowar ta, jin tsayuwar mota yasa suka fito, turus suka tsaya suna kallon Ramlah.
"Mami wannan wacece?" Cewar Husna.
Janyota zuwa jikinta tayi tare da fad'in "sannu sarkin surutu bako sannu da hanya sai tambaya ko? To Aunty Ramlah ce, itama kamar Aunty Nihal auntynku CE" Ajb zaiyi magana tace.
"Enough kids Ku bari mu huta mana, Mrs Ask" itakam Ramlah kallon take gwanin sha'awa, sun had'e cikin k'ananan kaya sunyi kyau 'yan birni dasu, rik'e mata hannu da Husna tayi tana murmushi "Aunty Ramlah muje" itama murmushi tayi mata, ciki suka shiga Ajb na rik'e da hannun Mami..
Da murna Inna Kande ta tarbesu, nan suka naje Parlour su Husna sai surutu suke ma Ramlah, abinci Inna kande ta gabatar musu bayan sunci sukayi hamdala, d'akin Nihal Mami ta bud'e ma Ramlah sannan ta nuna mata yadda zatayi amfani da komai, wanka tayi tare da d'auro alwala, gefen wardrobe d'inda Mami ta nuna mata na kayanta ta bud'e daga sama har kasa cike da suturu, wata atamfa ta d'auko a aje gefen gado, gaban mirror taje tayi Shafa, tare da fesa turare powder kawai ta shafa sai lip gloss, kayan ta saka, juyi tayi gaban mdubin tare da sakin murmushi har da rufe fuska da tafin hannunta "nita shin? Yau Ramlah nita a birni cikin daula, ba bugu ba b'aci sai lelena akai" ita kad'ai ke sambatu murmushi ta sake yi.
"Allah na gode maka" dadduma ta shimfida tayi sallah sannan ta fita parlour, da kallon sha'awa Mami ta bita itama da alama yanzu ta fito "iyye 'yar gidan Mami har kin fito, ba zakiyi bacci ki huta ba?"
Murmushi kawai tayi dan batasan tayi magana ayi mata dariya, zama tayi k'asa, tace "Mami ina wuni".
" lafia lau 'yata, ya gajia? "
"Uhm" ta kawai tace.
"Ki saki jikin ki kinji Ramlah nan ma gidane kamar inda Baffa, ni mamanki ce ga k'annin ki".
"Yawwa Mami kikace Aunty Ramlah itama Auntyn muce to ita take ne bamu ganta ba sai yanzu?"
"Oh Abduljabbar rigima, ba gata kun ganta yanzu, Bari dai ina Aunty Asma'u da nake nuna muku fotonta?"
A tare da Husna sukace "an ganta Mami?" Kai ta jinjina "eh kuma wannan 'yarta ce kunga kenan itama Auntyn Ku CE ko?"
"Eh Mami" suka fad'a tare.
Gata sosai Ramlah ta sameta gurin Mami gasu Husna suma suna nan nan da ita, gari aka zaga da ita Tasha kallo kamar idanu su cire, tun tana d'ari d'ari harta sake dasu, haka zatayi ta biyema su Husna, suyita wasansu da hira, maganar ta dad'i take musu suyita kwaikwayonta suka cewa ta koya musu, Mami dad'i takeyi a ranta ganin yadda ta saki jiki dasu, haka take tasata gaba suyi fira kamar k'awarta, dama haka take da 'ya'yanta tana jansu a jiki(sai mun ja yaranmu a jiki mun kusantosu damu muke gane damuwarsu harma mu samar musu mafita, yin watsi dasu ko d'aure musu fuska shike kaisu ga fad'awa a halaka, Allah ya shirya mu dasu baki d'aya).
*********************
4:00pm cikin Kd tayi musu Hakeem suka fara saukewa sannan suka k'araso gida, tarba sosai suka samu gurin Mami, dan tun safe suke kitchen ita yaran dama idai tana gida ita ke shiga da kanta kuma tare da yaranta saboda su koya, Ramlah da yake akwai kaifin baseera ga tambaya tuni ta fara gane makamar aiki irin na birnin, dama ta iya na k'auye tunda ita keyima Hari.
Baffa yaji dad'in yadda yaga Ramlatun sa ta saki jiki, tana mak'ale dashi sai firan birni take mishi dama Ramlah badai surutu ba.
Abdool kam tun da sukayi lunch yayi sallah ya kwanta so ko gaisawa sosai basuyi ba.
Baffa ne zaune da Mami suke fira, k'aramar jakarsa ya d'auko ya fito da takardu da ya mik'awa Mami "Ameena wanga takardu ne da suka shahi gadon Ramlah danaku na wajen Asma'u, sauran takardun haihuwar Ramlatu na, gasunan kuyi mata abinda ya dace dasu, ayi mata komai na d'aki irin naku na nan idan zasuyi, kuma don Allah kada Ramlatuna tazo garemu nan kusa, ni zan ringa zuwa da kaina ina ganinta".
Takardun ta duba kud'i ne masu d'an dama " to Baffa ban katse maka hanzari ba, amma ni ana tunanin tariyar Ramlah ba yanzu ba, karatu nakeso tayi".
Sannan taci gaba "idan akayi la'akari da k'arancin shekarunta, duka shekara 14 tayi karanta da Aure, to ana tunanin in siya mata shares da kud'in ta kamar yadda nayi ma su Nihal, ni zan d'auki nauyin karatun ta, sa'an Nihal ce to ina tunanin kaita school d'in su Nihal amma ya kake gani."
Murmushi yayi yasan karatu shine babban burin Ramlah duk kuwa da Hari ta tauye ta yasan hakan zai sakata farinciki, amma kuma ai Aure ya wuce komai "hakan nan na Ameena amma baki tunanin in ankai haka an tauye shi Abdulmajeed"?
Tasan Abdool na buk'atar Aure, dan tun yana 18year yake fama da ciwon Mara, Wanda ke nuni dashi mai k'arfin sha'awa ne, to amma ai ita Ramlah za'a cutar ita, abinda ba zataso ga Nihal ba, so duk d'aya da Ramlah gunta, mema ta sani da Aure as 14 kuma tashin k'auye tana buk'atar wayewar kai da ilimi "Baba bana tunanin akwai matsala amma zamuyi magana".
" to ai dan dai kuna nan binni ne amma ai warin Ramlatu ta isa zama d'akin miji".
Murmushi tayi "haka akeyi a k'auyuka shiyasa zakiga anata samun matsala da wasu yaran akan Auren wuri, aje haihuwa aita had'uwa da yoyon fitsari da wasu ciwuka k'arshe mijin yaji bazai iya ba yayi saki, a maida yarinya bazawara ga kuma ciwo ga yara da k'ananun shekaru" jinjina kai yai alaman gamsuwa d'anshi kanshi ansha kawo mishi irin wad'annan cases a can Kilgori, nan dai sukaci gaba da tattauna wa ya bata goyon baya 100%.
Washe gari ya koma kice da tsaraba, hadda nasu Hari, Mami ta kira Abdool sun tattauna game da karatun Ramlah, dama shima tunanin sa kenan, toshi me zaiyi da ita a hakan ko k'irjin kirki babu, ai bayama tunanin tasan me Aure ke nufi, k'aunarta yakeyi amma badan wani Abu nata ba.
Sun yanke idan anyi Hutu tunda third term ake sai akaita JSS 3 tare da Nihal tunda tana saurin d'aukar Abu, kuma zai cigaba dayi mata lesson kafin shima ya fara aiki.
Zai fita yaci karo da ita ta shigo tsayawa tayi tare da cewa "ina wuni" hararar wasa yayi mata "um baxan ansa ba, bayan kin manta dani da karatun mu kin manta d'an binni mai glass".
Dariya ya bata a yanayin yadda yai maganar kaba baki tayi tare da cewa " Laa Ya Abdool baka barin sunan ga ko?" Tana turo baki.
Shima dariya yai "to ai ke kika sakamin INA"?
" um tona d'ebe maka".
"To 'yar k'anwata Ramlatun Baffa, ya maganan karatun mu?"
"Yawwa Yaya Abdool muci gaba".
" Allah kinaso in sakaki makaranta" gira ta d'aga mishi tana murmushi.
"Lalalala! Yarinyar nan........."
_kuyi hak'uri ban Zauna bana yau, kuma yau kiwar typing ya kamani_
💄Meryerm Abdool💄 [8/20, 11:17 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
```Abdulmajid fans, naga kuna k'aunar sakwatanci da yawa fa😜 to Ku kwantar da mind d'inku Ramlatun Baffa tace zata koya maku😝 love u guys bohot bohot👌🏻😘```
📝 *Episode* 151--155
"Lalalala! Yarinyar nan ni kike d'aga wa gira?" Tare da zare ido hadda kama baki, sunne kai tayi Rana dariya k'asa-k'asa.
"Yo ai e a nuhina" dariya yayi tare da lak'ace mata hanci "basakkwata kawai".
Turo baki gaba tayi " kaima ai" murmushi yayi yana feeling special "ai zaki koyamun" corridor yabi tare da fad'in "jirani ina zuwa".
Dawowa yayi da wata k'aramar leda mai kyau bata yayi " sako ne daga Zainab tace tayaki murnar Aure" cikin zumud'i tace "LA Aunty Zainab tana ina?" Harara yai mata "sai yanzu kika tunata, tana gidansu".
Rungume ledar tayi tana dariya " Yaya ka had'ani da ita ta waya inyi godiya" tau" yace tare da cewa "jeki nuna wa Maminki" da sauri tayi ciki tana murmushi, binta yayi da kallo tare da shafa sumar Kansa, yana murmushi, sannan ya wuce d'akin sa.
Cikin farinciki ta shiga nunawa Mami gift d'in ta "iyye kai madallah kinga ko 'yar cas da ita zatayi miki kyau, kin gode, taji jeki aje a kayanki" da yake Mami tasan da labarin Zainab d'in, gaban madubi ta tsaya tana gwadawa tayi kyau a wuyanta gwanin sha'awa, sai juyi take tana dariya ita kad'ai, dama Ramlah da kwalliya (Ramlatu hankali).
Da dare bayan sunyi dinner suna zaune parlour suna kallo tasa TV a gaba, duk wani attention d'inta ya tattara ya koma can, gani take kamar mutanen fitowa zasuyi saboda girman Tv gashi kuma ta zauna daf da ita, su husna kam rabi ne kallo rabi Assignment Mami kuwa nakan computer tana aiki, Abdool ya shigo har gaida Mami su Husna suka gaidashi, Ramlah kam batasan ma ya shigo ba.
Daf da ita yaje ya saka waiwaya mata hannun sa gaban idon ta "La Ya Abdool yaushe kazo?"
"Ina kuwa zaki sani duka imaninki na a watching, kinga ki dena zama kusa da TV haka kada ya bata miki ido".
Dariya Mami tayi " Ai Ramlah tawa ne da kallo" Tab'e baki yayi "aiko daga yau zata daina dan gobe zamu fara lesson ya zube mata text book da lesson book da sauran instrument a gaban ta.
" hada tadai rage amma ba maganar dainawa, kaima dai ka fad'a ne" Mami ta fad'a.
Itakam Ramlah ganin littafin birjik gabanta haka ta manta da maganan kallo sai tab'a littafan take tana murmushi, yadda takesan karatu aiki daina kallon zata iyayi....
**********************
Kullum da safe da marece suke lesson wata rana ma hadda su Husna akeyi idan basuje gurin lesson d'insu ba, islamiyya kuma da rana sukeyi anan ta unguwarsu mai had'e da tahfiz, uniform hijab har k'asa.
Garden suke shigewa suyi lesson d'in, idan aka gama ta koya masa sakwatanci, in yanayi taita dariya bai iya amma ya daga anan wai ya iya, musamman inya karemata bayan, sai yace "ke hwahinta" waita gane yake nufi aiko dariya takeyi harda rik'e ciki, shiko kallo yake bin ta dashi komai tayi burgeshi takeyi shidai yana k'aunar Ramlah, amma ai dole ya sota kodon k'aunar da Aunty Asma'u ta nuna masa.
Zuwa yanzu kam ta fahimci abubuwa da yawa, dama gata da saurin gane Abu, har turanci tana ji saidai bata iya mayar da kowanne, math ma haka take tsargesa tsab.
A General hospital ta Kaduna Abdool ya nemi aiki, dama Neman ma'aikata suke so nan take suka bashi upper, Hakeem ma anan ya nema shima dai sun dauk'eshi so ana tare har yanzu, kullum suka had'u zai ta tsokanar sa ina 'yar renonsa, banza yake yi masa wata kuma yake "kaji dashi aini naji dad'i tunda inada 'yar reno, kaifa ba wadda ta taya" dariya yakeyi "tab na daik'i rayawa aini matata Unique ce".
Tab'e baki yake "munji zamu gani".
Tuni aka kammala ginan asibitin an zuba komai na amfanin asibitin saidai yace saiya k'ara samu experience tukun zai bud'e ta.
Ranar da akayi Hutu Nihal ta dawo, tana ganin Ramlah nanfa murna ta k'aru dama Mami tayi mata waya gurin malaninsu ta gayamata komai, nan da nan suka sarke kamar dama sun San juna parrot ta had'u da parrot dan kowacce ba baya ba, musamman Nihal ga barkwanci kamar Yusuf, nan ta shiga bata labarin makaranta,
Ramlah sai murmushi take tana imaging irin gata a school a class ana damawa da ita a hostel suna shagalinsu, oh ji take Kamar ace gobe za'a koma duk ta matsu ta ganta da uniform a school, kamar yadda take ganin yara da safe idan sunje kaisu Husna, kaga yara da uniform kala2 kowa tsaf dashi zaije makaranta shi yake burgeta ba kamar k'auyensu ba da sai can suke zuwa kuma sai rana ta fito muraratan wani ma sai yayi sati baije ba, kuma ba wani kwakwaran dalili.
Yanzu Abdool ya rage zama gida tun safe idan ya fita sai shida yake dawowa wani sa'in kuma inyai fitar marece sai 10 yake dawowa shiyasa basu cika had'uwa ba, lesson kuma ya dawo end of week.
Yanzu girkin gida sukeyi sun hutar da Inna kande da Mami, komai sun iya dama ita Nihal ta iya tun can, Ramlah ma yanzu anyi expert........
Hutu ne ya kusa k'are wa hakan yasa Mami taje school din tasu Nihal ta nema nata sukace a kawota ayi mata interview, sun yaba da kwazonta JSS 3 suka sakata kamar yadda Mami ta buk'ata aji d'aya da Nihal, uniform da house wears suka bata nan ma house d'aya aka ajesu, provision sosai Mami tayi musu, komai nasu a had'e, shima Abdool ya dad'a musu, Husna ganin tulin kayan da aka jibgo musu yasa tace itama a had'a da ita a kaisu tare, dariya sukai mata Mami kuwa tace "kwantar da hankalinki baby na 'yar k'anwata aike naki lokacin damasu zakiyi a komai ko school taki ta daban ce".
Dariya ta ringayi tare dayi musu gwalo, dariyar kawai sukayi dan sun San baho ne Mami ta maida ita, satin da aka koma Ramlah ta matsa a kaisu haka aka tattara aka kaisu bayan Mami ta sanbad'a musu kashe din kada su fad'i Ramlah matar Aure ce, musamman ma Nihal dan ta Santa da mugun surutu.
Ita Ramlah har ga Allah mantawa take da Auren sai sha'anin gabanta takeyi, tau 'yan boarding dai an isa ko wace wainar za'a toya a can oho!🤔
*********************
Yauma kamar kullum Mami ta fito zataje office, sai ganin motar Abdool tayi alaman bai fita ba, mamaki ya kamata dan a tunanin ta ya fita tun dazu dan dama bai cika tsayawa ya karya ba, ciki ta koma, can kan bed na hango shi yanata murk'ususu, cikin gid'imewa ta isa garesa " menene Abdool?"
Cikin muryan wahala yace "Mami cikina marata, Mami ciwo sukemin kamar su balle" tallabe kansa tayi ta d'ora akan cinyarta tana Shafa masa kan cikin tausaya wa tace "ka kuwa sha maganinka Abdool?"
Kaiya d'aga mata alaman eh, cike da tausayinsa tace "kuma har yanzu bai daina ba?" Nan ma da kai ya ansa mata.
Daga shi take son yi "Mami bazan iya tashi ba, d'an samo ruwan zafi ki dannamin gurin" cikin hanzari ta debo a flask tare da k'aramin towel sannu a hankali ta shiga Danna mishi, tun yana 'yar k'ara yana lumshe ido har ya rufesu ruf sai saukar numfashi Mami taji alaman ya samu bacci.
Gefe ta zauna tare da tallabe kumatunta ganin yadda d'anta keshan wahala, kuma tasan maganin abin amma ta zuba mishi ido, to amma meye mafita har ga Allah idan ta bashi Ramlah yanzu ta cutar da ita, dan tayi k'ank'anta a wannan sabgar, kuma hakan na nufin barin boarding kuma a shekarunta aka had'a mata karatu da Aure an cutar da ita, idan kuma aka cireta itama cutar wa ce "meye mafita" ta fad'a a fili.
Ta dad'e tana sak'awa da warware wa kafin wani tunani yazo mata murmushi tayi ganin ta samo mafita.
Sai 2 ya farka, jikin ya saki gaba d'aya, ciwon ya rage sai kad'an ya rage, kusa dashi tazo dan tana d'akin dawowar su Abj ne ya fitar da ita ta sallamesu suka wuce lesson tayi sallah sannan ta dawo, office ma anata kiranta sai excuse ta basu.
"Abdool ka tashi? Sannu ya k'arfin jikin?"
Murmushi yayi yana k'arajin k'aunar mahaifiyarsa a ransa "da sauk'i Mami kina nan baki fita ba?"
"Bazan iya fita ba Abdool kana wannan halin" mik'ewa yayi tare da rungume ta "love u so much Mamina" itama peck tayi mishi a kumatu tare da Shafa sumarsa "bari inyi wanka Mami".
Fresh up yayi yai sallah, tea mai kauri ta kawo mishi tare da farfesun hanta, kad'an yaci sannan yasha tea tare da shan magani.
Zama yayi kusa da ita " Abdool" ta kirashi, d'ago wa yayi "na'am Mami"
"Ya labarin Zainab?"
Jim yayi danshi harga Allah ya manta da wata Zainab "tana nan Mami wani Abu ne"?
" batayi aure ba?"
"Eh gaskiya banji ba".
"In har bakada wata wacce kakeso bayan Ramlah, to kaje ka nemi Auren Zainab".
A firgice yace " Mami Neman Auren Zainab kikace fah?"
"Hakane Abdool kuwa kai kanka kasan dalili na nayin hakan, bazan iya baka Ramlah a yanzu ba, haka bazan iya ci gaba da ganin ka a wannan halin ba, kuma banyi dan rashin Adalci wa Ramlah ba, nasan ko ita taji zata fahimceni, dakai a matsayin ta ita kuma a matsayin ka, iya abinda zanyi kenan" jinjina kai yayi Cikin gamsuwa da zancenta.
Saidai ta ina zai fara tambayan da yayi ma Kansa kenan...
Sallamar Hakeem ce ta katsesa yayi ta kiran wayo yin sa shiru, ya biyo yaji lafia......
_wata sabuwa_ 😳
*wai ina labarin Zainab*
💄Meryerm Abdool💄 [8/21, 10:58 AM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
📝 *Episode* 156--160
Gaisawa sukayi da Mami tana tambayan iyayensa sannan ta wuce, kusa dashi ya zauna "wai ya haka ne yau ba'a ganka ba, ba'a kuma jika ba, menene inata kiran wayoyinka a kashe" yamutsa fuska yayi.
"Hmm ka Bari kawai ciwon ne ya zagayo, na yau is too pain, maganin ma kamar bansha ba, na jigata fa, sai yanzu nake tashi, ga Mami ko fita batayi ba yau".
Cikin tausayawa ya da kulawa yace " ayya sannu to ya jikin yanzu?"
"Not bad! da sauk'i" ya fad'a ya lumshe ido,
"Haka zakayi ta zama Abdool bayan kasan maganin matsalar ka? Fisabilillah?"
"Maganar da muke yi da Mami kenan, wai in nemi Auren Zainab".
Murmushin jin dad'i yayi " best way, kai gaskiya Mami tayi tunani mai kyau"
Girgiza kai yayi "ba zaku gane bane, nifa ba mata biyu a tsarina, ni Ramlah is OK for me".
Dafasa yayi " common my friend, sau nawa muke tsarama kanmu rayuwa, kuma ba shine tsarin Allah ba, kuma ita Ramlah koda baka ita akayi yanzu I believe ba abinda zaka iya mata cos kana sonta kuma tausayinta kakeji, as her age, so as an advice kayi amfani da wannan damar ka Samar ma kanka lafia, and then in ma son Zainab ne bakayi saika nemo wacce kakeso ba dole sai ita ba, mu'allin shahid d'in dai kayi aure".