Kenza eBookz

Abdulmajid complete - Chapter 12

Abdulmajid complete - Chapter 12

Abdulmajid complete Chapter 12: Abdulmajid complete Chapter 12. Murmushi mai sauti yayi tare da mik'ewa itama mik'ar da ita yayi sannan ya ja hannunta zuwa…

4,474 words

Murmushi mai sauti yayi tare da mik'ewa itama mik'ar da ita yayi sannan ya ja hannunta zuwa toilet alwala ya umurceta tayi ba musu tayi shima anan yayi sannan suka fito darduma babba ta shimfid'a musu sannan ya jasu nafila, addu'a sosai yayi musu sannan yace.

"Zainab ayau kin zama sirrina nima na zama sirrinki, mun zama one, nasan kina k'aunata nima ina k'aunarki" d'agowa tayi ta kallesa.

Kanne mata ido yayi "yes I love u are u surprise?" Batace komai ba sai ido datake binsa "ina k'aunarki da gaske, so inaso mu gina aurenmu akan k'auna da hak'uri su kad'ai idan muka rik'e sun ishemu saboda suna nufin abubuwa da dama a cikin aure fatar kin gane?"

Girgiza kai tayi "na gane kuma inshaa Allah zan kiyaye".

"gud gal" ya fad'a tare da mik'ewa ya fita tare da dawowa da tire mai girma, kaza ce k'atuwa sai fresh milk da exotic ga cup da flates, gabanda ya diresu sannan ya janyota jikinsa ya fara bata a hankali tare dayi mata rad'a a kunne Wanda ni Meryerm Abdool bansan me yake gayamata ba.

Murmushi naga tanayi daganan ta fara bashi itama cikin kunya, a haka suka ciyar da juna, cikin ransa yana sak'awa "inama tare da Ramlatunsa ne, hmmm ko yaushe zai gansu haka da ita?" har cikin ransa yanason Zainab koba komai tanada hak'uri da kirki kuma yayi alk'awarin zama da ita tsakani da Allah tunda harta kasance mallakinsa.

A ranar dai an gwangwaje amarci tsami yakar Dr Majeed an angonce.

( _Sorry Ramlah team 😜_ )

*******************

*washe gari.....*

12:00pm su Ramlah ne, suke fitowa daga room d'insu wanda tashinsu kenan, tun da sukayi asuba suka koma saboda tsabar gajia duk da ba al'adarsu bane, ko yanzu ma yunwa ce ta kwakwulosu ko kayan bacci bata cire ba ta fito dan samun abin tab'awa tana fitowa Abdool na shigowa gidan da sallama idonta ya sauka a kansa sanye da yadi baki anyi mishi aiki da farin zare, sai sheki yake alaman ya angonce, kallo d'aya tayi masa ta kauda Kanta tare da ansa sallamarsa wayancewa tayi tare da gaidashi tana tambayan Aunty Zainab tun kafin ya ansa ta shige kitchen sai wayam ya gani, dai2 fitowar Nihal itama gaidashi tayi amsawa yayi "waiku sai yanzu kuka tashi kuke nufi" eh wlh Yaya duk gajia ce".

Tab'e baki yayi "gajia ko lalaci" tare da shigewa d'akin Mami, turo baki tayi "haba dai ai idan ba,a yaba ba bai kamata a tsine ba, kan kujera ta fad'a.

Minti kad'an Ramlah ta fito rik'e da plate d'in indomie " oh so much heart u Sisto thanks " harara ta dalla mata "no more thanks baby shige ki had'o mana tea kawai" mik'ewa tayi tare da cewa "done maa!" Smiling tayi "kyaji dashi tare da shigewa room d'insu.

A gurguje sukayi break tare da fresh up, yauma akon atampha sukayi brown and milk mai ratsin black anyi musu gown, koda suka fito parlour Mamace sai matar uncle Mansur da Abdool da kuma su Husna " Ahh Morning Mami" suka fad'a a tare "morning daughters, an samu tashi"

"Eh wlh Mami gashi har mun shirya, am Mami naga gidan saiku kaddai duk sun tafi"

"Naku wasa ba kunacan kuna bacci ba, kila ma sun wuce zamfara yanzu"

Zaro ido Ramlah tayi "nafaji kamar maganar Amal tana cewa sukam zasu wuce, duk a mafarki da d'auki zancen Ashe gaske"

"To lallai ai su sunji k'amshin gida"

"Allah ya kiyaye hanya zamuyi mata waya da wayan Yaya" cewar Nihal

"Oh Aunty Sarat barka da safiya ya gajia" um sai yanzu kuka ganta amma ai gwara ma ke matar uncle kin samu nikam ko oho" murmushi kawai tayi tare da ansawa da yake bamai son surutu bace.

"Lalala! Kai Yaya kaifa muka fara gaidawa duk gidannan".

" tab wannan gaisuwar anayi ana guduwa kitchen bana sonta"

"Uhmm to Morning Yaya Abdool ya Aunty Zee?"

"Kokefa lafia qlau, Zainab kuma tanacan tana jiranku"

"OK ai yanzu can zamuje"

"Yawwa naji Mami tace wai zakubi matar uncle Argungu kuyi hutu?"

Cikin murna sukace a tare "eh Yaya"

"Hmm kuna sane da one week ya rage a resuming school ba"

"Eh ai sati kawai zamuyi sai mu dawo mu koma kawai".

" to ba inda zaku" ya fad'a yana tsuke fuska "pls Yaya munyi missing Inna sosai" Ramlah ta fad'a, da muryan shagwab'a, ita ma Nihal begin nasa tayi.

Mami dake kallonsu tana murmushi bakinta ta sako "kaiko ka barsu suje mana, tunda driver zai kaisu kuma shizai koma ya d'akko su" duk da ta fahimci tafiyar Ramlah ce bayaso dan ko school yaso tayi day.

"Kunyi sa'a Mami ta saka baki"

"Yeeep! Mungode Mami" suka fad'a suna rungumeta, nansu Husna suka saka rikicin suma zasu, dak'ar Mami ta shawo Kansu akan zasuje da ita, kwashesu yayi har Matar Mansur ya kaisu gidansa.

Tun daga parlour suke zuba mata kira "Aunty Zee"

"Um nayi fushi Aunty Ramlah" dake haka take kiranta.

"Kema Nihal juya kawai banaso, matar uncle sannu da zuwa shigo mana, twins d'in Mami kuma banaso" ta fad'a tana musu hararan wasa.

"Sowie Aunty Zee pls wlh bacin gajia ce ya sacemu, pls apology" suka fad'a tare sukan su Husna sai dariya suke.

Juyamusu baya tayi, gaban ta suka shige tare dayin kneel down hadda kama kunnuwa, dariya ma suka bata aiko darawa tayi.

Suma dariyar gaba d'aya sannan suka k'arasa ciki, nan sukaci gaba da firansu kaman wasu k'awaye, tare sukayi girki rana da yake an kawo musu break da gidan Mami sanin suna can yasa bata aika musu na rana ba, sai 6:00pm Sukabar gidan cikin nishad'i dak'ar Zainab ta barsu suka tafi.

Koda Abdool ya dawo sun wuce dan tunda ya ajesu ya wuce gurin abokansa sai after magrib ya shigo, daya isko sun wuce sai jinini yake akan meyasa basu kirasa ya kaisu ba.

Abune ya tokare mata wuya dan tasan duk akan Ramlah ne yake fad'an da sauri ta nemi tsarin ubangiji akan wannan zazzafan kishin nata, bata Bari ya fahimci komai ba ta shiga rarrashinsa cikin salonta tuni ta shawo kan abinta.lol

********************

Washe gari su Ramlah suka Lula Argungu, cike da gargadi da dokokin oga Abdool.

Satin d'ayan da sukayi Argungu ba k'aramin enjoying sukayi ba, ga kakkaninsu sai nan nan suke dasu, sun zaga gari sosai sunga abubuwan tarihi birjik (dama duk Wanda yasan Argungu yasan garin tarihine musamman game da kamin kifi 😜 )

Har besse sunje da birnin lafia, sannan driver yazo ya kwashesu cike da kewarsu suka barsu suka Lula Kd.

Shirye-shiyen konawa school suka shiga.........

_ayi shiri lafia 'yan boarding kaddai a manta da kwaki da k'anzo_ 🤣😂

"Meryerm Abdool" [9/9, 3:14 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)

```Nafeesa Nuhu(Sadnaf) here is ur page for ur support, thanks much momyn Affan, Allah ya raya Affan& Ikram kan tafarkin musulunci ameen #Ana mugun tare#🤝```

*Manzon Allah S.A.W yace "idan kayi imani da Allah da ranar karshe to kasowa d'an uwanka abinda kake sowa kanka" ingantaccen hadisi ne. 👌🏻*

📝 *Episode* 176-180

Babban mall Abdool ya kaisu sukayi provision, tare da Zainab sukaje itace ke tayasu d'ibar kayan, siyayya sosai, gidan Mami suka wuce direct da ita akayi gyaran kayan tsaf, sannan ta shiga K'ara musu haske game da rayuwar boarding dayake itama ita tayi, sosai sukaji dad'in bayaninta dan sun k'aru dashi, nan ta wuni sai bayan isha suka Abdool yazo d'aukarta nan wata firar ta ballewa.

"Um kasan me ya Abdool? Nifa inaga journalist zan zama dan gaskiya akwai ni da tambaya" cewar Ramlah.

Murmushi yayi "kema kin gane da kanki kenan, aini har tsoro tambayan ki nake kada na kasa ansawa, musamman lokacin da nike d'an binni mai glass".

Dariya aka kwashe da ita har ita sannan tayi mishi hararan wasa tare da turo baki "badai zaka daina ba ko yaya?"

"Kyalesa Aunty Ramlah sai munyi maganinsa d'an binni mai glass kawai dashi, kinga rabuda shi ki koyamin filatanci kinji" Zainab ta fad'a tana k'unshe dariya.

"Kai Aunty Zee da wayo kema kin k'ara fad'a ba" Nihal ta fad'a itama dariyar ce take k'asa-k'asa.

"Ba ruwana daku gaba d'aya ai duk na harbo jirginku" mik'ewa tayi da niyyan shigewa d'akin Mami da yake ita bata parlon, da sauri Abdool ya rigo hannunta yana fad'in "haba Ramlah love Ramlatun baffa wasa muke fa."

Abu ne ya tsayama Zee a mak'ogoro dak'ar ta had'iye da addu'a tare da murmushin yake "Eh Aunty Ramlah wasa muke fa".

Kwace hannunta tayi ba tare data juyo ba " naki nayi d'in " dai2 da fitowar Mami tana dariya itama "kai kun fa dami dota da tsokana banaso fa" janta tayi zuwa seat tana Shafa mata kai, su kuma sai rike dariya suke ganin yadda ta kumburo baki wai ita a dole fushi tane, Abdool sai kallonta yake cikin K'auna shikam komai tayi burgeshi takeyi "Ahhhh ina sonki 'yar K'anwata" ya fad'a a ransa..

Zainab na ankare dashi tuni abin ya motsa (oh wannan kishin Zee anya kuwa, um barin yi shiru kada Zee team suji).

Agogo Mami ta kalla har tara ta gota "kai Ku tashi Ku tafi haka nan mungode" dariya Abdool yayi "Mami abin harda kora"? " eh dai Ku tafi dai, Ku kuma kuje Ku kwanta kunsan gobe sammako zakuyi tunda in schools days ne".

Zainab da ta matsu su tafi kada ta k'asa controlling Kanta har a fahimta inda Ramlah taje tana murmushi tare da jan kumatunta "haba Aunty Ramlah saki fuskar mana daga yaune fa" had'i dayi mata chakulkuli aiko batasan lokacin da ta saki dariya ba.

Nan sukayi musu sallama har mota su Ramlah suka rakasu, nan sukace sai sunzo gobe rakiya da yake sune zasu kaisu, saida safe sukayi kana suka koma ciki, su Husna suka kai d'aki wad'anda bacci yayi gaba dasu a parlour...

Washe gari tun da sassafe su Zainab suka zo, anyi sa'a suma sun kintsa tsaf nan suka sallami Mami, suka wuce su Husna suka fara ajewa a school sannan suka Lula *F.G.C* su Ramlah hadda hawaye sai shagwab'a take zubuwa Abdool yana biye mata, Zainab dai d'aurewa kawai take amma kam abin tsikarta kawai yake.

Dak'ar ta barsu suka wuce, cike da missing nasu, dan zamansu sun saba sosai kamar kada su tafi sukeji musammam Abdool zai nisanta da mintin zuciyarsa.

( _Asha karatu lafia 'yan makaranta_ 🤣 )

********************

Abdool ne zaune cikin office yana rubuce-rubuce, turo k'ofa akayi da sallama ya shigo, ansa sallamar yayi ba tare daya d'ago ba "kaga mijin mata biyu fa, mijin Ramlatu angon Zainabu" Hakeem ya fad'a cike da tsokana.

Malalacin smiling yayi masa "kaji dashi dai imma da gatse ka fad'a haka abin yake dai, point of correct angon Ramlah zakace don itace uwargida kuma amaryar gaban goshi".

Dariya Hakeem ya kece da ita " ahaf ai kuwa saita gaban goshi shisa naga an rangad'a mata rival, kai yaron nan ko kunya bakaji k'arami dakai sai fitina har biyu gamu ko d'aya bamu ije ba".

"Kanka akeji kuma, nidai nasan menakeyi, hmm wani abun ma sai kaji an fara kirana Dady".

" Hhhhhhh, cool man muma fa muna hanya kuma ni matata da 2 zata fara".

"Ka tsaya wasa dai harna kai Ramlah gida itama ta aje nata, oh imma ka jinkirta ai sai na baka 'yata"

Harara ya banka mai "cuti amma kai baka sona wlh, saina zauna harka bani 'yar da ba'a haifa ba ma".

Dariya ya sheke da ita "naka wasa, kadaici gaba da ruwan ido kaga"hmmmm ba zaka gane ba amma I will give u much surprise, um ni kaga yaushe tafiyarka?"

"OK till u give it!, kaga ma file d'in wurina nakeso na hahhad'a nayi submitting nasu, ina ga dai zuwa upper week zan wuce" India aka turashi course na one year.

"OK but da Zainab zaka wuce ko?"

"Umm gaskiya saidai naje naga yanayin gurin in yaso daga baya saita biyo jirgi in naga akwai damar tazo saboda tsaro" ya k'ara sa fad'a yana dariya.

"Kaifa ka gama lalacewa fa yaron nan".

" lalalalah mutum da iyalinsa ana kira masa lalata" ya fad'a yana bud'e bakin tsokana.

"Kaji d'an tsari"

A cikin satin ya kammala komai, sallama yajema su Ramlah da yake time d'in suna school, aiko yaga kukan shagwab'a wai ita zata bishi can, tayi karatun a can shiko sai biyemata yake tabbas zaiyi missing nata sosai ya sani, Zainab ta tausaya musu dan tasan irin son da yake mata, baya iya boyesa ko kad'an ita kuma dole taso abinda yakeso tun balle Ramlah da takeji har ranta, saidai kasan zuciyarta sai zafi yake amma kuma tana Neman tsarin Allah da wannan kishin dan bata fatan cutar da Ramlah koda da fatar bakine, dak'ar suka rabu bayan ya cikasu da provision da pocket money.

Watan 2 a India ya turowa Zainab visa ta iskoshi, saboda tsaro inji shi, amma kuma kasan Ransa Ramlah yake missing sosai dan ko ganinta kad'ai ba k'aramin nutsuwa yake saukar masa ba.

Suna wasa time 2 time a wayar Mami in kuma suna school ta hanyar malamansu duk k'arshen wata yakan turo musu kud'i duk da Mami ta hanashi amma ganin yake ai nauyinta na kansa kuma dole ya sauke, zamansu a India zamane mai cike da nuna kulawa da tsantsan soyayya, kowa tattalin dan uwansa yake musamman Zainab har tausayi take bashi Sam bata gazawa da lalurarsa kullum cikin hidimarsa take.

B'angaren su Ramlah sun maida hankali sosai akan karatu, duk abinda ya shige mata duhu zata tambaya hakan yasa ta zama zakaran gwajin dafi malamai da dalibai kowa sonta yake....

********************

Suna SS1 aka kawo wata new comer class d'in su, 'yan class sukayi ruu kowa son magana yakeyi da ita ganin ta mai kyau ga class, amma banda Ramlah da Nihal sai sha'anin gabansu sukeyi, tsab ta kalle class d'in da mutanen ciki ganin kowa na welcome nata amma banda su yasa hankali ya koma garesu, gaban seat d'insu taje tare k'are musu kallo tayi tare da sakin malalacin murmushi.

"Hi" ta fad'a Nihal tago tare da cewa "hello" Ramlah kam kallon d'aya tayi mata ta maida kanta gun text book d'inta, smiling ta k'arayi tare da mik'awa Nihal hannu.

"I'm Sadeeya M Bashir, buh u can call me Sadee M bash"

Itama hannu ta bata "I'm Aisha Yusuf Besse, Nihal by family name"

"Wow nice 2 meet u" sannan ta juya gurin Ramlah ta mik'a mata hannu tare da gayamata sunanta kamar yadda ta gayama Nihal tana murmushi.

Itama murmushi tayi mata "Ramlah Abdulrahim modibbo by name".

"wow i like ur style, may I have a seat here?"

Kallon Nihal Ramlah tayi sannan tace "why not" ta fad'a tare da nuna mata seat...

Tun daga ranar suka zama k'awaye irin sosai d'innan akayi sa'a kuma itama House d'insu aka ajeta room d'insu d'aya, nan suka koma su uku komai tare sukeyi.

Sadee irin marasa jin nannan irin bata yadda d'innan ba, classy girl ce ta sosai ga rawar kai kaman me, saidai fa itama akwai kai shiyasa zamansu yayi kyau, a class kuwa ji yake dasu suke d'aukar 1,2,3 position, zamansu da sadee sun k'ara wayewa idonsu ya bud'e sosai musamman Ramlah.

Sun koyi saka k'ananun kaya a gurin ta, haka tazo dasu trolley guda haka ta shiga basu tana koya masu yadda zasu saka, nan fa suka shiga nuna Kala ko'ina suka wuce 3stars kakeji, har Senior burgewa sukeyi.

Har Mami tasan Sadee haka iyayenta har sun kulla zumunci suma, su Abdool ma daga India suna shan labarinta.

Yanzu su Ramlah anyi mastering gurin swag haka idan suka dawo Hutu a gida ma sun daina saka atampha ko less English wears kawai, mini skirt, top, tight, pencil, body hug, bomber short iri-irensu dai.

Haka idan zasu koma Hutu zasu shiga boutique su sissiya tare da M bash suke zuwa dake itama anan Kd take, Mami dai ta zuba musu ido ganin iya gidane kawai basa fita dasu.

B'angaren su Abdool kuwa tunda suka tafi basu zo ba, dan ba damar d'agawa nan da can amma har cikin ransa yana missing gida yana missing Ramlah sosai, abun haushin ma an k'ara musu rabin shekara abun ya bata masa rai saidai ba yadda ya iya dole ya jure.

Su Ramlah an zama sun zama cikakun 'yan mata sosai musamman ita dama gata kamar kajin Agric, komai na cikar mace ya cika gareta, 8 shape d'in nan ya fito sosai, dukiyarsu ta Fulani ma sun cika barakallah, duk namiji lafiyayye ya kalleta sai yaji wani Abu a ransa........

_to friends ya kamata fa mu waiwayi Iya Hari, muji wace wainar suke toyawa 😜🤣_

💄Meryerm Abdool💄 [9/10, 4:14 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)

```Allah mad'aukakin sarki tsarkakakke ne kuma baya karb'a sai Abu tsarkakakke👌🏻```

Muyi k'ok'ari mu tsarkake tsakaninmu dashi.👌🏻

*Namecy ur a d most grateful ever meet ur d best namecy, ur ur ur hmmm am speechless dear, may Allah bless be wit u always namecy _Maryam Y Zango_ here is ur page.💋💋💋*

📝 *Episode* 181--185

Iya Hari tun ranar da aka d'aura ma Ramlah Aure aka kuma ga 'yan uwanta tasan lallai Ramlah tayi mata nisa, kuma tayi mata fintinkau saidai tsinka, musamman ganin irin dukiyarda ke garesu, amma saboda bak'ar zuciya irin tata da sharrin shed'an(Allah yayi mana tsari da kaidinsa) suka had'u suka yi mata b'akar hud'uba na yadda zatayi ta maida Ramlah baya taya zata maida ita k'auye taci gaba da musguna mata.

Duk masifa da bala'in Hari da d'ibar albarka irin tata bata zuwa gurin boka ko malamin tsibbu saidai tayi addabeka ka gwammace inama baka Santa ba a rayuwa, amma a yanzu ta fara tunanin zuwa inda boka domin ya lalata auren Ramlah sannan ya saka mata bak'in jini a idon dangin mahaifiyar tata su korota inda take daga nan taci gaba da musguna mata bayan tasa an rufe bakin Ard'o, wannan kullum shine tunanin amma ina zata samu kudin zuwa shine matsalar dan kudi sam baya zama ga Hari saboda shegen kwalama da kwad'ayin tsiya, ga Ard'o yanzu zama k'ankamo injita, dama can halinsa ne (Inji fa).

Tunda aka wuce da Ramlah Ard'o bai k'ara maganarta a gidan ba, ko tanaso ta tambaya ba dama duk zuwanda yake Kaduna da zuwan da Abdool keyi gurinsa bai taba gayamata, saidai taga kayan tsaraba kawai ko tambaya tayi ina, cewa kawai yake ba damuwarta bace.

Ganin zaman kad'aici ya isheta ita kad'ai a gida yasa ta d'auko Hinde d'iyar Lanti dan tayata zama da taimaka mata, amma kuma sai hakan bata samu dan Hinde gantalliyar yarinya ce, b'atacciya kuma 'yar iska irin ta k'auye nan.lol

Inta kwanta bacci sai hantsi ya dubi ludayi take tashi, ko tsince bata kawar mata hasalima ko Inda ta kwanta bata gyarawa da kuma ta samu abin kari ta fita bata gidan biki bata na suna bata dakin saurayi bata matattarar 'yan iska ba ita zata dawo ba sai bayan isha, shima tana zuwa taci abinta sai dandali daga ta dawo sai bacci, aikin sisi bata mata kuma datayi mata kallon banza ko fad'a rashin kunya take mata inta zageta ta rama, inta doketa kota hanata abinci taje ta gayama uwarta, haka Lanti ke kwaso jiki wai akan me zata dokar mata 'ya kota hanata abinci ko tana nufin yadda tayi Laure ne zatayi ma 'yarta, wallah bata yadda ba dan ba jaka ta haifar mata ba, haka zata tasata gaba da masifa akan 'yarta kuma ba halin kwab'arta dan tarbiyarta ai(kaikayi koma kan mashekiya) wani sa'in Ard'o na jinsu bai cewa k'ala, saidai yayi murmushi kawai yasan farawane ma indai alhaki ne.

Haka Hinde ta zamewa Hari wani bala'i kadangaren bakin tulu a kar ka akai tulu a barka ka bata ruwa, gefe d'aya kuma Jauro ruwa a jallo yake Neman Hari, dan Ard'o ya masa kashedi da gidansa shiyasa bai sameta a can ba, amma yasa alwashin idonsa idonta ba'a mai kyau.

( _Sorry Iya Hari, farawa ne ma_ )..😏😂

******************

Komai aka masa rana tau za'a cimmata a yaune Dr Abdulmajid tare da Zainab suka diro Nigeria cike da nasarori ciki hadda tsulelen cikinsu d'an 8months, sunyi fresh abinsu musamman Dr Majeed idan ka kallesa saika k'ara kaman wani saurayi d'an 20 ya hade cikin suit ash, yasha cover ga glass as usual ya zauna daram, sumar sai sheki take, man pride nasa yasha gyara, Zainab kuwa cikin Arabian gown ja tayi rolling da gyalenta ga cikinta daya fito tutsu dashi, tad'anyi jiki irin na cikin nan.

Sale driver ne yazo d'aukar su, direct gidan Mami suka wuce wacce ta shirya musu better tana jiran isowarsu, tayi murna da ganin su musamman ganin Zainab da ciki cikin ranta fad'a tace "Ashe gwanda da akayi auren nan gashi har rabo ya samu zanga jikana" sai nan da nan take da Zainab ina zan saka ina zan d'auke, itakam sai sunne kai take alaman kunya, Abdool kam sai murmushi yake gaskiya no place like home.

Yanzu babban burinsa ganin Ramlah yasan ta k'ara girma yanzu, anyi sa'a kuwa end of week ne visiting, surprise yakeso ya musu....

Ranar visiting su Ramlah ne zaune kan bench su 3 sai fira suke sama-sama, lokaci zuwa lokaci zata kalli gate, duk da tarasa dalilin hakan, sai smiling take tana felling special.

Can ta hango su Husna d'auke da basket, zame jiki tayi sallat ba tare dasu Nihal sun sani ba sunyi nisa da hiran Uncle lukman wani Cooper da aka kawo musu dake bala'in son Ramlah, itakam Sam bata bashi fuska ba, dan tasan ba kyau ko a musulunci and then yanzu tasan ma'anar so kuma mutum d'aya takewa so shi kad'ai yayanta mijinta, shine fa Sadee ta d'age wai tasoshi ya had'u...

"Husna, Abj ina Mamin ne" ta fad'a tana isowa gunsu, ita Sam bata kula dasu Dr Majeed ba, inama zatayi tunanin ganinsu tunda tasan basa k'asar kuma ko jia sunyi waya.

Rungume hannayensa a k'irji yayi, tabbas girman d'an mutum ba wahala, ta canja gaba d'aya, badan yayi mata Sanin kwarai ba ai kila bazai ganeta ba.

"Aa ya ina magana kunmin shiru kodai Ku kad'ai ne?" Smiling Husna tayi tare da nuna mata inda su Abdool suke.

Idonta ne ya sauka kan na Abdool dake mata murmushi, cikin ihu ta daka tsalle "Lah Yaya what bunch of surprise" ta fad'a tare da fad'awa jikinsa, wani shock ne ya ziyarcesa tun daga yatsar kafa zuwa brain d'in sa.

Wani bak'on lamari wanda bai saba ji game da Ramlah shine ya ziyarcesa a yau, duk kuwa ba yau ne lokaci na farko da ta saba rungumesa ba, cikin wayau ya zameta daga jikinsa, Zainab na ankare da halin da ya shiga saurin d'auke kanta tayi zuciyarta sai harbawa take, ba abinda take ambato sai "innalillahi wa'inna ilairajiun" sannan ta samu nutsuwa, murmushi ta k'irk'iro "wato Aunty Ramlah Dr kawai kika gani".

" laa Aunty Zee ba haka bane ai kune kunyi min bazata Allah " ta fad'a tana isa gunta, rungume juna sukayi suna dariya.

"Um um" Abdool yace, inda yake suka kalla, tuni Zainab ta gane yaren wato ayi masa a hankali da baby, hararan wasa ta jefa masa, Ramlah tace "wani abun ne yaya?"

"Um ba komai Ramlatun Yaya, ina su Nihal ne?" Ka gansu can, basu ma San nazo ba" nuna musu gun bench d'in tayi, can suka nufa a tare sai tambayan su take game da India (kunsan dai Ramlatun baffa da tambaya).

"Kinaji ko besty ni banga illar uncle Luku ba kawai ki amince masa" Sadee ta fad'a saidai me ba Ramlah da takema magana a gun.

Baza ido sukai suna nemanta can ta hangota tafe tare da wasu da bata sani ba sai su Husna "la haula Yaya Abdool ne da Aunty Zee yaushe suka dawo bamu sani ba" Nihal ta mik'e tana fad'a.

"Nihal wai wannan shine ya Abdool d'in?" "Eh wlh shine kinga matarsa Aunty Zainab"

"Kai Amma wlh ya had'u ba k'arya gashi Dr, wow gaskiya I love him"

Zaro ido Nihal tayi "me? Rufamin asiri kafa matarsa can" to meye ba sai naje ata biyu ba"

"To ai.." Shiru tayi.

"To ai me?"

"Uhmm share kawai Sadee" zata yi wata magana suka k'ara so hakan ya tilasta yin shiru.

Anan suka shimfid'a darduma, lunch sukayi as usual bayan an gaisa sun gabatar musu da Sadee, firan Yaushe rabo suka shigayi da Aunty Zainab ta yaushe rabo, jefi-jefi Abdool ke saka bakinsa, duk hankalinsa ya tattara ya tafi ga Ramlah sai kallon ta yake in style, mamakin girmata kawai yake, Zainab na ankare dashi, dama tasan za'a rina tun tana kwaila ya kalla balle kuma yanzu data cika fam, Sadee ma ta kula da kallon ta dai share ne kawai.....

**************

Sokoto sukaje suka kai musu tsarabansu, har gidan Alhaji Sada sunje, momyn zee tayi murnar ganin hankali kwance harda albarkar aure.

Sunje Kilgore inda Ard'o shima yayi murnar ganin su, daga nan suka wuce Argungu, nan fa Mama ta shiga tsokanar Zainab wai daga zuwa India sai dawowa da babbar tsaraba ita dai sai sunne kai take kunya, Abdool ne mai shige mata.

*2 weeks later...*

Wayarsa ce tayi k'ara my Zee ya bayyana a screen, da sauri ya d'aga "yadai Zee ko jikin ne?"

Cikin walahalalliyar murya ta ansa "Dr kazo gida banda lafia".

" u see saida da na gaya miki bazan fita ba labour kika saboda naga syn nata kikace lafia qlau kike, koma dai ba shine ganinan in d next 2mnt" saida ya gayama wani Dr abokinsa sannan ya d'aukota dan shi duk b'angarensa ne, bazai iya k'arbar haihuwarta ba, balle yanda yaga tayi wujiga-wujiga da ita, Mami ya kira tuni ta dira a asibitin.

Suna nan Zaune tun abin safe har har rana ana Abu d'aya, sai fitowa nurse keyi suna cewa ta kusa dai, yanaso yaje saidai zuciyarsa ta gama tsinkewa, ya tausaya mata sosai irin doguwar nak'udar nan ce, ganin tasha wahala tayi har k'arfinta ya k'are, yasa suka yanke hukuncin yi mata C/S.

"Dr ka yafemin bana tunanin tashi daga gadon nan, don Allah ka yafemin duka laifuka na" ta fad'a da muryan rad'a Wanda shi kad'ai yaji dan yakai kunnensa dai dai bakinta, cikin wahala take maganar, kama hannun Mami tayi amma ta kasa magana sai bakinta dake motsi.

Mami sarkin tausayi har da hawaye ganin yadda surukar tata ta koma "Aa Zainab bakiyimin komai ba, Allah ya fito dake lafia, Allah ya saukeki lafia" daganan aka shiga da ita Operation room.

One hour...

Jariri ne kato kaman ka lashe don kyau aka fito dashi, an shirya shi tsaf cikin Round up Red, cikin murmushi Mami ta amshi babyn tare da cewa "Mashaa Allah, barakallah".

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull