Abdulmajid complete - Chapter 4
Abdulmajid complete Chapter 4: Abdulmajid complete Chapter 4. 12:00pm suka isa, gidansu Abdool suka sauka, sun samu Maamii ta tarbesu da tsararran girkinta…
4,491 words
12:00pm suka isa, gidansu Abdool suka sauka, sun samu Maamii ta tarbesu da tsararran girkinta ko office bata fita ba saboda d'okin dawowar Son d'inta ita Kanta tasan tayi missing d'insa sosai, su Abj ma sai murna dawowar Yaya Abdool Suke, suna nanik'e dashi suna mishi surutu, saida sukayi dam, sukayi fresh up, sannan Hakeem yayi musu sallama, da motar Abdool ya wuce gida, idan yaje ya dawo da ita.....
Hutun one month sukayi sannan sukayi shirin komawa, a wata d'ayan ba k'aramin dad'i hutun yayi ma Abdool ba duk kuwa da tunanin Ramlah na mak'ale a zuciyarsa, sukanyi waya da Zainab time to time, sai yaji inama da Ramlah ne, sai yanzu yakejin haushin rashin barma Ardo waya da baiyi ba, Aida sun rik'a gaisawa da sahibarsa.
Saura kwana uku su koma suna zaune da Maamii suna hira dan a duniya bashida abokiyar hira da shawara kamar ita, har suka gangaro kan hirar Ramlah.
"Yawwa maganar yarinyar nan da muka fara".
"To ai banji daga gareka bane Son, tunda ka dawo bakace komai ba".
Shafa Kansa yayi " Eh wlh Maamii kamar yadda na gayamiki, yarinyar na cikin k'unci, ba K'aramin wahala takesha gun Kakarta ba, gashi shi kakan nata bamai magana bane, wani abin tausayin ma very young inaga iyakarta in tayi Nihal" ya k'ara she cikin pity face.
Itama tausayi kwance a fuskarta tace "toya kake ganin zamu iya taimaka mata ne?"
"Eh ni a tunani na in nemi kakanta ya bani ita na kawo ta nan gurin ki, sai a sakata makaranta in fact dai ta dawo hannun mu sai dai takai musu ziyara amma me kika gani".
"Eh to Zamanta anan d'in ba matsala a ciki amma kana ganin iyayenta zasu baka ita haka nan daga had'uwar asibiti?"
D'an jim yayi shima dan gaskiya maganar abar dubawa ce "hakane Maamii amma zan gwada na gani idan zai yuyu".
"Ina ne garinsu naji kace ba anan Yabon bane?"
"Eh nan kusa dasu ne wani k'auye Kilgori".
"Kilgori" ta maimaita haka taji kamar ta tab'a jin sunan garin saidai ta manta ina taji, sharewa tayi nan dai sukaci gaba da tattaunawa akan lamarin..
Tsaraba sosai yayi mata na suturu dogayen riguna da d'inkuna hijabai hadda takalma da kayan rubuta da kara2 hadda Zainab saida yayi ma tsaraba dasu Ardo su Alhaji, kai har mutanen Argungu anyi ma, Maamii ma ta bada nata.
Ranar da suka dawo bayan ya huta ya bawa su alhaji tsarabarsu, a ranar ya wuce Yabo, zainab ma a tsaitsaye yaje, danko ciki bai shiga ba, mutan Yabo sunyi farincikin dawowar dan ba k'aramin k'ok'ari yake a asibitin ba, mutum zaizo bako asi ya dubasa kuma ya siyamai magani, shiyasa sukejin dad'in sa, suma Suke kawo masa kaya irin nasu na k'auye, nono, kwai, har kaji da zabi.
Da sassafe yaje kilgori, Laure tafi kowa murnar dawowarsa, sai murmushi take, ganin tayi ya kara kyau da gayu, hadda cewa "iyye d'an binni d'an gayu dai" dariya ma ta bashi cikin ranshi yace "Ramlah kuruciya ho".
Sunyi murna da godiya da tsarabar da yayi musu, yaji dad'in yadda suka yaba, bayan ya tafi Iya Hari, kwace kayan tayi ta cirema Lanti da Shatu kala d'aya 2 hadda hijab, wai ai wannan salon munafurci ne menayi mata kaya kaman ya ganta a tsumma, wannan kayan kamar na Aure, imma sonta yake yayi k'arya dan bazata bashi ba( ni kuma nace tunda ke zaki bada ita ba).
Laure kam a ranta tace mi hikai da 'yar k'auye duk matan bunni.
Cikin kala ukun da suka rage ta d'auki d'aya ta kaima aminiyarta Delu, sai murna take da sanya Albarka.
"Nidai Laure anya d'an bunnin nan ba sonki yake ba?"
Murmushi k'arfin hali tayi tace "banda ke da abinki Delu mi yakai Dani, ai wutsiyar Rak'umi, tayima k'asa nisa".
" Hmmm abokiyata ai ba daganan take".
"Kega bar wagga zance, d'auko wata" murmushi kawai tayi sannan suka canja hira.
B'angaren Jauro kuwa ya lashi takobin sai yaga baya ga Abdool muddin yaci gaba da shige hanci...............
( _tofa gamu gani, wai ansa munafiki bikon aure_😏 )
💄 Meryerm Abdool💄 [7/23, 7:02 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽
📝 *Episode* 66--70
*life goes on....*
Zuwa yanzu Laure, ta fahimci abubuwa da dama game da karatun da sukeyi, both Islam and western, har rubuta ta iya, bak'ak'e da wasulla tana banbance su, har hadda izo biyu tayi a gunsa, a tak'aice ba k'aramar rawa Abdool ya taka a gun Ramlah ba, wani sa'in har Delu yake had'awa idan taje gurinsu, dan yanzu anan inuwar gidansu suke zama, da yake Laure ta gayama Ardo abinda Jauro yayi, shiyasa yace su rik'a zama nan, dan yasan kad'an a cikin aikin mahaukacin ya kwaso shegu irinsa suje suyi mashi illah.
Shikam Abdool baiso hakan ba, yaso su k'ara had'uwa da Jauro danya banbance masa aya da tsakuwa, a bangaren Jauro kuwa zuwanshi biyu bai samesu ba anan ba tare da rundunarsa kamar yadda Ardo ya tsammata, yana ganin basu nan yayi wani ihu irin na 'yan iska.
"Aradun Allah ya tsorata, saini Jauro mai sa maza su sheka da gudu, dan banza yana tsoron uwarshi ta haihi wani ba shiba" haka yayi ta cika baki 'yan korensa naci na k'ara fashe mishi kai.....
Yauma bayan sun gama kara2 zai wuce saiga Laure da leda waiya kaima Aunty Zainab, murmushi yayi tare da rik'e baki "ayya Ramlah luv baki d'oran aikin da yafi k'arfina ba yau kuwa?"
K'walalo ido waje tayi "Aboki mai glass kaima kana kyuya irin ta yara ashe?"
Dariya ta bashi yadda tayi maganar "Waya gayamiki kyuya ce, Zainab d'in ce batanan ai".
" to ina taje?"
"Tana Sokoto gidansu".
"Laa itama ba Yabo take ba kamar kaiya?"
"Um itama Bautar k'asa tazo anan kamar ni, kuma ta k'are nata tun tuni".
"Amma shina baka hwadamin ba, kuma in nicce INA gaisheta saika ke zataji" ta fad'a tana mishi kallon tuhuma.
"Oh my gosh! Mantawa nayi, amma fa ina gayamata gaisuwarki".
"A ina?"
"Ta waya mana, ko in kira maki itane?"
Washe baki tayi "eh inaso kirata".
Wayarsa ya Ciro ya danna mata Kira, ring 2 ta d'auka, bayan sun gaisa ya had'ata da Laure sannan yaje inda Ardo dake zaune yana kallon rigimarsu yana murmushi jin dad'i.
" Docta har zaka tahiya".
"Eh babba amma da magana nazo" gyara zama Ardo yayi dan yaji me yazo dashi "ince dai lahiya ko?"
"Eh lafiya lau dama akan maganar Ramlah ne nazo neman alfarma" nan dai Abdool ya kora mishi jawabinsa nason bashi ita ya tafi da ita idan ya tashi tafiya, dan duka 2week suka rage mishi.
Jim Ardo yayi yana nazari can yace "Bawai nak'i bana yaro, kuma ba ban amince maka naba, saidai hanzari ba gudu ba, kasan yanzu duniya mutum aka ciyyo ba dabba ba, kuma yana zama abin zagi gareni da ita Kanta Ramlah, kasan Abu ga k'aramin K'auye kowa da yadda zai hwassara zancen ga" tunda ya fara bayani Abdool ya k'asa kunne yana saurarensa, sai zufa ke keto mishi, yasan duk abinda ya fad'a gaskiya ne, to amma shi yanzu ya zaiyi da son Ramlah? Kar yaje yana can gida yana jiran ta girma yazo ya aureta yaji labarin an ba wani ita...Ardo ne ya katsesa "kayi shiru d'an ga da hwatar dai ba ranka ne ya b'aci ba".
Murmushin yak'e ya k'irk'iro "Aa Baba ko d'aya ai abinda ka fad'a gaskiya ne, amma kana ganin babu mafita?" danshi kanshi gabadaya ya k'ulle.
"Mahitar d'aya CE" bai San lokacin da yayi sanyayyen murmushi ba "Baba meye mafitar" cikin zakuwar son yaji.
"Aure! Idan har kana sonta ni zan baka Aurenta, saboda ka kwanta a raina" Ardo ya fad'i hakanne, saboda ya fahimci yana sonta.
Abdool kuwa k'irjinshi ne yayi mummunan fad'uwa, kamar saukar aradu yaji zancen, cikin rud'u ya kalli Ard'o duk da ba wacce yakeso kamarta, amma bai tab'a tunanin abin zai sama haka, shikam gani yake tayi k'ank'anta da Aure yanzu, bayan haka shi kanshi bai kawo yin Aurensa yanzu ba duk da yasan yana buk'atar auren.....baffa ne ya katsa masa tunani.
"Abdulmajeed kodai baka sonta na" karo na farko daya tab'a kiransa da sunansa.
"Aa Baba wlh ina sonta, Inadai ganin kamar tayi k'ank'anta da Aure ne" murmushi irin na manya Ardo yayi.
"Ina ai takai mataki, indai kana sonta kada kayi tunanin komi, katahi ka shawarci magabatanka, kace 'yan uwanka duk nan Suke ko?"
"Eh"
"To ka tahi kayi shawara dasu ba abin tashin hankali bana, sadaki kawai nika buk'ata ko nan da sati guda kazo a d'aura muku Aure".
"Inshaa Allah Baba, zanyi magana dasu zakaji yadda mukayi dasu" sannan yayi mishi Sallama.
Laure da batasan wace wainar ake toyawa ba, bayan sun gama waya da Zainab, ganin suna magana, yasa taja gefe kan dakali tana duba littafanta, wayarsa kadai ya ansa yayi mata sallama, ganin shi kamar baya cikin yanayin dad'i, yasa yaja jinin jikinta, ba surutu da salo yau, itama haka ta shige gida jiki a sabule....
Bayan gida kwantawa yayi kan kujera yana tunanin to ta inama zai fara? Daga k'arshe kawai yayi deciding d'in ya kira Maaminsa.
Bayan sun gaisa ya kora mata bayanin yadda sukayi da Ardo daga farko har k'arshe.
"Abdulmajeed" jin ta kira sunashi complete yasa k'irjinsa bugawa kaddai Maamii tace bata amince ba....katsesa tayi.
"Ka tabbatar kana sonta?"
"Eh Maamii" ya fad'a cikin sanyi.
"Hakan da wannan dattijon yayi shine dai2, kuma ya nuna yasan meyake yi, dan haka kaje ka samu kakanka kayi masa bayani, sannan ka Baba(cewa da babanta) nima inanan zuwa, kamar yadda ya fad'a cikin sati d'ayan za'ayi komai inshaa".
"Tau Maamii zanyi kamar yadda kikace.....................
💄Meryerm Abdool💄 [7/27, 10:17 AM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽
💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞 *TUKUICI GAREKU SANYIN IDANIYATA* 💕💕💕💕💕💕💕💕💕💕 Abdulmajeed Ramlah Rufaida Baffah Kausar Affan Hanan Abdallah Aminah Amerah Salma Salim Nuseey Twins Zee Amir Al'ameen Jidda Khadija Khairat Fatima Halifa Mufeeda Muzammil Fidoo Aysha Muhammad Ilham _Hmmm kunada yawa nd rest_ ❣may Allah bless be wit u always my kids😘
📝 *Episode* 71--75
Sauke numfashi yayi bayan sun k'are wayar da Mami, hankalinsa ya kwanta yanzu dan dama ita yakeji kada tak'i aminta, duk da yasan sauk'i irin nata, saidai yaga abin ne, a gaggauce yasan kuwa batason aikin gaggawa, shikam yayi mamakin saurin amintar ta.
"Yes! Any way I'm so much happy, zan auri love of my life" ya fad'a cikin farinciki, a ranar kwanan farinciki yayi, da sassafe ya d'auki excuse ya nufi Sokoto.
Alhaji Sada, yayi mamakin ganinsa saboda bai saba zuwa ba sai weekend, sanda ya kora masa bayanin abinda ke tafe dashi, yaji dad'i har cikin ransa, fuskarsa ta k'asa boyewa, kuma ya bashi goyon baya d'ari bisa d'ari, tare da tabbatar masa idan ya tashi komawa yazo ya d'aukesa suje tare a can k'auye.
Daga nan inda Hakeem ya wuce da yake ya gaya mishi zai shigo garin, saidai bai mishi bayanin komai ba.
Dariya sosai Hakeem yayi har saida Abdool ya nuna b'acin ransa sannan ya saurara.
"Aure fa kace dude! Kuma in a week, common kace u r joking, hw come wane irin aure kenan?"
Tab'e baki yayi "koma me zakace, I don't care, nidai nasan Aure zanyi kuma a satin nan, that all I know" ya fad'a tare da daga kafad'a.
"Tau naji Amma dai ba wancen yarinyar ba ko?"
"Ha'ah see u se trouble meye naka a ciki, ina nine me Aure ko, kai naka ido ne kawai, so put ur eyes and shout ur mouth".
Dafasa yayi saboda yaga da gaske ransa ya baci, " cool down! Nifa abin mamaki ne yake bani kawai, kuma naji kace yarinyar is too young" danshi bai tab'a ganinta ba.
"Hmm ai Kaine da abin haushi, na gayamaka dalilin auren nan, ba zuwa zamuyi mu zauna zaman Aure ba, ita Kanta nasan batasan ma me auren ke nufi, Hmmm kuma ai tayi k'ank'anta ba zata iya dani ba" ya fad'a ya shafo sajensa daya kwanta lup.
"Shegen kaya! Wlh bakaji Dr, kai killer ne in silent way, baki kawai na fika".
Smiling din gefen baki yayi "kaga ni ka tashi muje, time is going" tare suka fita gwanin Sha'awa, suka Lula zuwa Argungu.
A can d'imma ba'a samu matsala ba sunyi na'am da da abin da yazo dashi, Innah hadda tsokanarsa wai daga zuwa Har da yi mata kishiya, saboda yanzu ya daina yinta sai ta had'a shi da Ayatul kursiyyu yace ya fasa.
Dariya yayi yace kada ta damu zai bata eating noise, nan dai sukayi ta barkwancinsu sai marece suka koma Sokoto.
Washe gari sukaje Kilgori tare da Alhaji da Hakeem, Ardo ya tarbesu cikin karamci da mutuntawa kuma yaji dad'in ganin Alhajin hakan ya nuna yaron d'an gidan girma ne.
Amininsa Malam Garba kawai ya kira ya tabbatar da ya bawa Abdool, Ramlah ya dawo nan da sati d'aya a d'aura musu Aure, kuma baya buk'atar komai face sadaki.
Godiya sosai Alhaji yayi masa da wannan Karamcin da yayi musu, sannan yace yayi hak'uri amma zasuyi komai da akeyi a al'adance saboda itama a nuna mata 'yace kamar kowa, Ardo yaso su barshi kawai amma Alhaji ya nace shi zaiyi komai, dole ya Hak'ura amma da sharadin komai sai ranar Auren za'ayi, anan take suka bada kud'in nagani inaso dana gaisuwar iyaye, haka dai suka rabu cikin farinciki kowa na ganin karamcin d'an uwansa.
********************
"Ramlatuna!" D'agowa tayi ta kallesa k'irjinta na dukan Tara2 dan tunda Baffa ya kirata taji, gabanta na fad'uwa "na'am Baffa" ta ansa cikin siririyar murya.
"Ke yadda ina k'aunar ki?"
"Baffa ba Wanda yaka k'aunata duk duniya baya gareka".
Murmushin jindad'i yayi " yawwa Ramlatuna tunda harke yadda bani cuta miki, inason sanar dake inshaa Allahu, juma'a mai zuwa za'a d'aura miki Aure".
"Aure baffa!" Kalmar da ta fito bakinta kenan cikin firgici da zaro ido.
"Ko bakison Auren ne Ramlatuna?"
Girgiza tayi alaman aa dan ita bamasan maganan ta fito fili ba "Baffa nasan Bazaka cutar dani ba, Allah yasa hakan shine mafi Alkhairi".
" Ameen Ramlatuna, inshaa Allahu zakiyi hwarin ciki da wanga Aure, da yadda Allah k'arshe k'arshen wahalarki ya zaka, sannan kiyi shiru kakki hwadama kowa kinji?"
Kai ta daga masa "yawwa 'yar Albarka tashi ki tahi Allah yayi miki Albarka".
" Ameen " ta fad'a tare da fita jiki a darare ba k'wari...
B'angaren Mami ma sai shirin zuwa takeyi, tunda Abdool ya kira ya gayamata an tsaida magana sai shiri take sosai, amma sai ana gobe aure zata zo...
"Mutumina wai sai yaushe za'a buga I.V kaga fa lokaci sai k'urewa yakeyi".
"Kaidai ka cika neman rigima wlh, ai sai kaje kaita bugawa" ya fad'a tare da juya masa baya.
Dariyar ciki yayi, "Yawwa wai ka gayama Zainab kuwa?"
"Oh! Allah wlh shaf na manta, abubuwa sun sakani a gaba" ya fad'a bayan ya tashi daga kwancen.
"Wo sabon Ango duk rud'un bikin ne".
" kaji dashi, magulmaci" yana gama fad'a ya bar parlour gaba daya, da murmushi ya bisa "wannan yarinyar ta rikita min Aboki da yawa".
Bedroom ya shiga tare da zanyo wayansa ya kira Zainab, yasan zataji ba dad'i amma gara taji a bakinsa da taji wani gun.
Bayan sun gaisa nan yake gayamata maganar Auren nasa, dif taji ta daina ji, wani k'olulun bakin ciki ne ya tokare mata mak'oshi cikin rawar murya tace.
" Allah ya sanya Alkhairi "ta fad'a kawai tare da kashe wayar gaba d'aya, dama yasan za'ayi haka amma toya zaiyi, gara ya gayamata gaskiya taji Haushinsa a lokacin zuwa gaba tasan bai yaudareta ba daya rufe dan tayi farinciki zuwa gaba ta gane yaudaranta yayi(komai zakayi da mutum ka tsaya akan gaskiyarka, dan k'arya fure take bata 'ya'ya, gaskiya kuma dokin k'arfe Allah yasa mudace).
Kuka takesonyi amma yak'i zuwa, lallai ta tabbatar Dr Majeed baya sonta, har iya fad'a mata, zaiyi Aure, shikenan ta yayi mata nisa, nisan da bazata iya cimmasa ba, juyi kawai takeyi duk duniya tayi mata zafi, lallai rashin masoyi bala'i ne.
Tana haka ne ilham k'anwarta ta shigo wai tayi mata assignment, hantararta tayi tare da cewa tafice ta bada guri, kota takata anan, aiko a guje ta fita tana kuka dan bata tab'a mata irin haka ba.
Ganin tana kuka ne yasa Momyn su ta tambayeta meya faru, ta gayamata Zainab ta korota.
"Zainab kuma Ilham? Me kika mata" dan tasan yadda takeda sauki ga k'anninta.
"Banyi mata komai ba Momy, nadai ganeta kwance ranta a bace" mik'ewa kawai Momyn tayi zuwa d'akin Zainab.
Harta zauna daf da ita batasan tazo gurin ba, saida ta d'ora kanta kan cinyarta tana Shafa mata kai alaman rarrashi sannan tasan da zuwanta, fashewa tayi da kuka kamar ita take Jira "Momy na rasashi, shikenan na rasashi".
" Haba Zainab ki idan hankali ya gushe hankali ake sakawa ya nemosa, d'aure kiyimin bayani yadda zan fahimci abinda ke damunki" duk taji a jikinta bazai wuce Dr Majeed bane.
Saida ta gama kukanta, da sai yanzu yazo, uwar bata hanata ba sannan ta gayamata abinda ya faru.
Sosai ta tausayawa 'yar tata saboda tasan yadda takeson Abdool, sai dai bata nuna mata ba, saboda kada tasa ta k'ara karaya.
Cikin taushi da rarrashi ta shiga bata baki "kiyi hak'uri Zainab dama ita duniya haka take bafa komai da akeso ake samu ba a rayuwa, sannan duk abinda kikaga ya kub'ucewa mutum to dama ba'a k'addara zai samesa ba, kuma duk abinda ya samu mutum, dama ba'a k'addara zai kub'uce masa ba, dan haka ki kwantar da hankalinki idan da rabon Aure a tsakaninku sai kiga yazo har gida ya aureki, kedai ki dage da Addu'a da Neman zabin ubangiji".
Lafewa tayi jikin Momyn nata tana ajiyan Zuciya, sosai jawabin uwar tata ya ratsata tana k'ara godewa Allah daya azurtata da uwa ta gari mai maida ita kan seti idan ta juye(Allah ka k'ara ma iyayenmu baiwa da fasaha, ka k'ara muna k'aunar su da kyautata musu ameen, mungode da ni'imar iyaye na gari).
Saida ta tabbatar ta samu nutsuwa sannan ta fito ta barta.
Ana saura kwana biyu Aure Laure duk abin duniya ya mata yawa ita dai tasan bata murna da wannan aure haka kuma bata bak'in ciki dashi, ga rashin Aboki mai glass, tun ranar bai k'ara dawowa ba, dan ranar da sukaje bata nan.
Kilama Baffa cewa yayi kada ya k'ara dawowa saboda zaiyi mata Aure shiyasa ta ganshi wani iri a ranar, gashi za'ayi Aurenta ba tare dasun k'ara had'uwa ba, wata kila sai lahira ji kawai tayi tana hawaye, da sauri ta share kada wani ya ganta dan Iya Hari da Gwaggo Lanti, tsakar gidan, taci gaba sharan turken dabbobin da take yi.....
Iya Hari kuwa da basusan meke gudana ba sai nanayensu Suke ita 'yarta, Ardo ne ya shigo bayan sunyi mishi sannu da zuwa daga can zaune, k'arasawa yayi inda Suke hannu ya zura aljihu ya zaro kud'i ya bata.
Nan da nan ta Washe jajayen hak'oranta "Malam wanga kudd'i na minana?"
"Auren Ramlatuna, gobe idan Allah ya kaimu" ya fad'a mata kai tsaye.
Cikin zaro ido da masifa "Aure? Wa zata aura?"..................
_pls kuyi hak'uri da juna shiru da kukayi hakan ya farune akan rasuwar da akayi mana_ 😞
💄Meryerm Abdool💄 [7/29, 9:10 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽
( We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers)
❣❣❣❣❣❣❣❣❣❣ ```ina kuke masoyan Abdulmajeed, ga shafinku, ina matukar kaunarku a duk inda kuke Allah yabar kauna.``` ❣❣❣❣❣❣❣❣❣❣
*Yan uwa masu yimin ta'aziyya, da masu yimin sannu da jiki, nagode sosai da kulawarku, Allah ya barmu tare nagode bunch of love#❣#*
📝 *Episode* 76--80
"Gara ma kace ba'a ta kakai, dan bai tab'a yuyu ayima Laure Aure gobe, ni kuma a hwadamin yau, sai kace ban da had'i da ita, kuma ai Laure da mijinta" shidai Ardo ido kawai ya zuba mata.
"Nasan ko Jauro dani yaka magana bada kai ba, ni nibbashi Laure ba kaiba, to k'ak'a akai mata Aure gobe ace sai yau zan sani, ai wanga maganar banza ta" duk cikin d'aga murya da masifa take magana, ganin ta dasa aya, murmushi yayi.
"Hmm khadijatul kubra kenan" ya kira Iya Hari da anihin sunanta "kamar yadda na fad'a gobe da izinin Allah za'a d'aura wannan Auren ba hwashi, danni adda ikon aurar da Ramlatu, maganar kin tsayar mata da miji ko minana ma, ke kissani kuma ke yashahwa, bakida hurumin tsayarwa da Ramlatu miji, wadda baki k'auna, taya za'ayi ki zabar mata miji na gari? Kina tunanin bansan komi da kukeyi ba, ina sane nadai tsaya naga iyakar gudun ruwanku ne, daga ke har ita lantana nasan baku k'aunar Ramlatu saboda hauka irin taku, kullum tunaninku yaya zakuyi Ku ganta cikin k'unci shine tunaninku, toshi zakaran da Allah ya nufa da cara ko ana muzuru ko ana shawo to sai yayi" cikin kwanciyar hankali ya shiga zare musu magana kai ba kace cin mutunci yake musu ba.
Saida yayi musu tass sannan ya sarara musu, tsabar bak'inciki kamar zuciyar Iya Hari ta fito waye wannan shine ga duka ga tsinka jaka, magana ma kasa yi tayi, Lanti kuwa sai harara take aikawa Laure jira kawai take Ardo ya fita ta jibgeta, kamar ya sani yace.
"Ke Ramlatuna zonan" sannan ya fita aiko har tana had'awa da tuntube bisa da d'an gudunta, da harara su Iya suka rakasu "lallai Malam ni zaiyima cin mutunci akan wannan d'iya".
" Hmmm Inna bari ta dawo yau sai taci na jaki in yaso, gobe akaita gidan miji da kumburaren jiki, shegiya 'yar matsiyata" nan sukaci gaba da zaginta ita Ardo (ni kuma nace Allah ya Baku lafia, dan ciwonku saida Addu'a) lol.
"Ramlatuna naso ace na sadaki da dangin mahaifiyarki kahin in aurar dake, sai dai gashi Allah bai nuhwa ba, ina rokon Allah ya sadaki dasu ko nan gaba kema kiji dad'in dangin uwa Ramlatu" ya fad'a tausayinta cike da ransa, ba kad'an ba yake tausayawa Ramlah Sam batasan wani dad'i na uwa ko danginta ba.
"Ameen Baffa".
"Yawwa ungo wannan" biba bag ya mik'a mata.
"Kitahi gidan Gwaggonki Aisha, keda abukkanki kinji a can zaku kwana kuyi abin da kukeyi irin naku na Mata" sunne Kanta tayi alaman kunya.
Murmushi yayi, sannan ya wuce yanajin farinciki a ransa, gidansu Delu taje nan Delu ke mata mitan rashin fad'a mata da wuri, hak'uri tare da fad'amata dalilin rashin fad'ar, haka suka biyama sauran k'awayenta sai gidan Shatu, d'aki d'aya ta ware musu da yake tasan da zuwansu.
******************
Bayan fitar Momy sosai nutsuwa ta zoma Zainab tashi tayi ta d'auro alwala tayi nafila tare da karanta Qur'anil Kareem, tuni taji zuciyarta wasai saidai abinda ba'a rasa ba.
Gift ta bawa k'annenka suka kaima Abdool, yaji dad'in sosai duk dan hadda na Ramlah a ciki, agogo ne nashi mai kyau na azurfa, Ramlah kuwa sarka ce da abin hannu masu kyau k'irar silver, tare da card na marriage wishes, tukuici ya basu k'annin nata cikin da farinciki.
"Allah sarki Zee" ya fad'a cikin slow voice.
Hakeem kuwa cewa yayi "lallai wannan ko'a mata ita ta daban ce, son gaskiya take maka( bawai nuna zafin kishi ke nuna soyayya ba, so na nufin kyautata da mutuntawa a kowane hali take note girls) lol.
"Hakane" ya fad'a a tak'aice saboda sanin halin Hakeem da jan abu yanzu suyita rigima.
Lumshe ido yayi yau tsawon sati biyu rabonsa da Ramlah yana missing d'inta sosai.........
*Washe gari....*
Tun 12 angwaye suka shirya tsaf cikin farin wanka daga sama har k'asa sak, iri daya komai nasu, su isma'il ma su had'e cikin nasu kalar gayun, Alhaji da kawu Sani(da yake shi kad'ai ne a gidan yanzu) kawai Suke jira su fito dan sunfi son da suyi juma'at a can da an sauko juma'a a d'aura auren kawai.
Alhaji ne ya fito cikin shirinsa tsaf hadda su rawani, haka suka d'auki mota biyu, duk maza ba mace ko d'aya dan koda Alhaji ya gayama Hajia Inna cikin rashin Kulawa tace Allah ya kyauta shikenan maganar, sam baiji dad'i ba, ko kad'an, fatar ganewa kawai yayi mata.
Ganin saukar baki a garin yabawa wadanda basu san me ake ciki ba mamaki ciki hadda Jauro wanda baisan wainar da ake toyawa ba.
B'angaren su Laure kuwa gyara Shatu irin nasu na k'auye dai ba laifi, baffa ma yayi mata nashi k'ok'arin dan tunda satin ya kama yake bata tsumi mai kyau kuwa irin na fulani ko yanzun ma ya aiko hadda kaza, suna cikin d'aki tayi shiru dan k'irjinta ne ya tsananta bugamata ba k'akk'autawa, su kuma su Delu sai tsokanarta suke wai ta gayamusu sunan mijin, shiru tayi dan ba ansa.
Sai Murmushin yake da take yi musu, haka dai sukaci gaba da gadarsu cikin nishadi da raha.
Gidan Ardo, kuwa iya Hari ganin har wayewar gari ba Laure, ga Ardo yaki bada damar ta tambayesa dan shima bata samu ganinsa ba, haka ta zauna zuru cikin rashin jin dad'i, can ga Lanti da kwailarta, nan take tambayarta Laure dan sai mangariba tabar gidan da alwashin dawowa yau ta cika burinta na jibgarta, nan uwar ke gayamata har yanzu bata dawo ba hatta Malam bata saka a ido ba tun jiya.
"Hmm Inna akwai abinda Baffa yaka shiryawa to missa ya boyeta?"
"Nima abinda nika son Sani kenan, gashi bansan yaya nikai da shedanin d'anga ba Jauro, kesan baida mutunci(ato k'aik'ayi koma kan maishi).
"Kyaleshi Inna bai isa yayi komi ba, ai yasan inda yaka haukatai...." Jin k'arar motoci ne ya saka su lekawa.
Ardo ne shima cikin shigar girma tare da Malam Garba suka tarbesu an gyara d'akin gaban gidan tsaf an shimfida tabarmi, komai tsaf, cikin farinciki suka tarbesu, su Isma'il sunyi mamakin k'auyen wai Abdool yaga matar Aure tab! Amma ba laifi sunada karamci.
Abinci na alfarma aka kawo musu daga gidan Malam Garba aka dafa ga fura da abin sha, komai dai mashaa Allah, nan aka gaggaisa ana jiran isowarsu Baba da Abdool yaje d'aukowa kamin lokacin d'aurin auren yayi.
Baba da kawu Mansur ne suka ya d'auko, suna isowa yayi dai2 da fitowar Ardo daga cikin zauran ido hudu sukayi da Baba.
"Malam Umar!" Cewar Baba, cikin tsananin mamaki daya bayyana a fuskarsa.
"Malam Abubakar!" Ardo ya fad'a shima cikin zaro ido........
*to masu karatu munga alaman Sanayya amma a INA sukasan juna?*
*ya makata mu warwayi baya, dama hausawa sun ce waiwaye adon tafiya*
*muje zuwa wasa farin girki* ⛹🏾♀⛹🏾♀
💄 Meryerm Abdool ce😘 [7/30, 8:07 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate, we touch the heart❤ of the readers📝).
_falyakul khairan auli yasmut_ 🤐
👏🏽 *Allahumma yashfikah👏🏽 wishing d most quickest and fastest jet recovery dear Abdool💋*
📝 *Episode* 81--85
*ASALIN LABARI*