Kaddarar ramlah book 1 complete - Chapter 34
Kaddarar ramlah book 1 complete Chapter 34: Kaddarar ramlah book 1 complete Chapter 34. A hankali ya matsa gaba, ya ɗan shafi gefen nonona da hannunsa mai…
4,403 words
A hankali ya matsa gaba, ya ɗan shafi gefen nonona da hannunsa mai ɗumi. Wani irin shauƙi ne ya tsinkeni. Na rufe nonon da tafin hannuna, fuskata na kunce kamar zan fashe da kuka. Amma ba saboda zafi ba… saboda yadda nake jin jikina yana amsa wa, zuciyata na sauke numfashi mai sanyi.
Na ce da ƙasa da murya, “Bashari…”
Sai ya ce, “Shhh… Na gama. Ki huta yanzu.”
*****************
Nana hadiza
09030569336ƘADDARAR RAMLAH
SHAFI NA TAMANIN DA TAKWAS
Wannan littafin kuɗi ne, ba kyauta ba!
Biya Naira 700 kacal ki karanta cikin salama!
Domin biyan kuɗi:
Acc Name: Bilkisu Sani Kaura
Acc Number: 7040402435 (OPAY)
Tura shaidar biya zuwa WhatsApp:
09030569336 ko 07040402435
Masu son vip 👇Sai ku bibiyeni a
Arewabook @nanadiso10
https://www.arewabook,vs.com/book?id=6813670d91815df57bc25693
********
Cikin dare, gaba ɗaya na kasa bacci. Na dinga jin jikina kamar ana zuba min garwashi. Wani marayan kuka na fara yi na kasa tsaida kaina. Da ƙarfi na shiga kuka, cikin azaba da ɓacin rai.
“Wayyo Allah... kaina... kaina!”
“Basharii...!”
Na fadi da karfi kamar wacce aka wurgar da ita. Kafin in ankara, sai na ga Bashari ya shigo da gudu daga falo. Ya rikeni da tsananin damuwa.
“Ƴar kwalisa! Lafiya? Menene? Kaina kaina?”
Wannan ne kaɗai abin da na iya furtawa.
Abin mamaki, sai na ji Bashari ya fara kiran sunayen Allah da girmamawa. Wannan ne karon farko da na san cewa ya iya addu’a. Ya fara karanta ayoyin Alkur’ani cikin sanyi da tausayi, yana cewa
“Ƴar kwalisa, zaki warke insha Allah. Kinji?”
Ya ci gaba da raira mun ruƙya a hankali. Daga baya na fara jin azabar da ke ƙona min kai tana raguwa. Na lumshe ido a hankali, zuciyata ta fara samun nutsuwa. Ba da jimawa ba, sai bacci ya dauke ni a jikinsa yana rungumeni kamar wanda baya son ya sake ni.
Bani da masaniyar yadda dare ya wuce, sai da na farka da safe. Da kyar na samu na mike na tashi, na shiga bandaki nayi alwala sannan nayi sallar asuba.
Jikina a lokacin yana da zazzabi sosai, ga gajiya da rauni a sosai. Amma abun mamaki duk motsin da nayi, Bashari yana tare da ni. Ko dai ya rike ni, ko yana saka hannu yana dafa ni da tausayi. Hankalinsa ya tashi sosai. Ya sanya min hannu, ya karanta ruƙya a jikina, sannan ya ce
“Zan dinga yi miki ruƙya kullum ƴar kwalisa. Sai kin warke gaba ɗaya.”
Bayan ya gama, na koma na kwanta. Bacci ya kwashe ni har zuwa bayan la’asar. Na farka da jin wani irin nishadi da ƙarfi a jikina kamar ba ni ba. Ina tashi na ji komai ya lafa azaba, zazzabi, ciwon kai... duk sun bace kamar da sihiri. “Alhamdulillah...”
Na fada cikin jindadi da godiya.
Amma banga bashari ba sai hango flask din shayi da bread nayi agefe da Alama ya dafa yafita Na sha, sannan na tashi na haɗa ƙurfoti, na dora ruwan zafi, na yi wanka. Na canza kaya sannan nayi sallah. Cikin kwanciyar hankali, bacci ya sake dauke ni.
Na farka da misalin ƙarfe biyar na yamma. Na juya da sauri domin ban ji motsin Bashari ba har yanzu bai dawo ba. Wayata kuwa ba kuɗi balle in kira shi, kuma na duba naga shima bai kirani ba. Hakan ya saka ni cikin wani irin damuwa.
Na yanke shawarar fita can gabanmu domin sayen kayan miya. Na dawo na dafa mana tuwo, sannan na sake gyara gidan gaba ɗaya. Da yamma, bayan sallar isha’i, sai bacci ya sake kwashe ni cikin nutsuwa.
Wajen ƙarfe goma na dare kenan, sai na ji ana kwankwasa ƙofa da ƙarfi. Cikin ɗan firgita, na miƙe na zura mayafi. Na buɗe ƙofar da sauri, sai kawai na ji hannu ya rungume ni da ƙarfi. “Ƴar kwalisa… yanzu tun safe na aiko Uwani baki buɗe mata ba? Jikinki ne ko wani abu? Haba Ramlah.”
Fuskar sa cike da damuwa, idanunsa sun nuna gajiya da ƙauna. Na kasa magana. Sai hawaye suka fara gangarowa daga idona. Na juya da sauri na koma ciki, zuciyata na rawa kamar garwashin wuta.
Ya shigo da ledoji hannunsa, ya rufe ƙofar, sannan ya bi ni ciki. Ya zauna gefena, yana kallona “Ƴar kwalisa, me nayi miki ne? Me yasa kika ƙi gaya min abinda ke damunki? Wallahi hankalina ya tashi.”
Cikin sanyin murya nace, “Bashari… I don’t know what to say. Na ji haushin yadda ka tafi ba tare da ka faɗa ba. Kuma kamar baka damu da lafiyata ba.”
“Ki yafe ni,” ya ce yana shafar gefen fuskata da hannunsa mai dumi. “Na fita ne domin neman likita, naga jikin naki har da asuba da zafi. Na siyo miki magani. Na ga ko ruwa sai da kyar kike sha.”
Na zube a jikinsa da kuka, sai na ji kamar duniya ta daina nauyi. Ya ɗora hannunsa a bayana yana bubbuga a hankali, yana faɗin
“Na san bani da daraja a idon mutane, amma wallahi har gaban Allah ina sonki Ramlah. Soyayya ce ke sa ni tsayuwa a kanki.”
Ya ɗaga fuskata da yatsunsa, ya sosa gira da ɗan murmushi mai laushi. Sai ya ce “Kinyi kyau sosai duk da kukan nan, amma zaki yi kyau fiye da haka idan kika murmusa min yanzu.”
Na ƙanƙame leɓe na da kunya, amma sai na saki ɗan murmushi mai rauni. Ya kai fuska kusa da tawa, ya sumbaci goshina a hankali, sannan ya ce “Ƴar kwalisa... Ki sani wallahi na canza. Ba zan kuma barin ki kina kuka ba. Ina son ki fiye da yadda nake son kaina.”
Na ji jikina ya saki. Na kwantar da kaina a kirjinsa, ina jin bugun zuciyarsa yana rawa.
“Idan na riga na gaji da duniya, sai kawai na tuna dake... sai zuciyata ta lafa,” ya ce cikin sanyin murya. “Bari na shigo da kayan.”
Ya fice, ya ɗauko su daga waje. Da ya dawo, sai ya cire kayansa cikin natsuwa, ya wuce bandaki. Bayan wasu mintuna ya fito da gajeran wando da vest kawai a jikinsa. Sai kamshi mai daɗi ya biyo bayansa turarensa na musamman.
Ya zauna yana buɗe ledar kayan abinci. Na ga fruit ne, yoghurt, kaji soyayya, da kuma kwalbar magani. Wani kaya guda ɗaya ya ware gefe, bai buɗe ba. Sai ya miƙe zuwa kicin ya yayyanka fruit ɗin cikin bowl da kyau, ya dawo ya ce “Ƴar kwalisa, sauko nan.”
Ya miƙo min yoghurt ɗin tare da faɗin “Ki sha. na san yau ba ki iya cin abinci ba na lura ma kamar bakyason tuwo shiyasa nasiyo miki su cabbagesai kiyi shinkafarku ta birni har man salad nasiyo da kwai. Maza ki sakko Kuma ba zaki ce min baki da yunwa ba.”
Turarensa ya cike ɗakin, yana birkita min hankali. Na karɓa cikin jin daɗi, na sha yoghurt ɗin har na gama. Yana kallona yana murmushi, sai ya miƙo min farantin kaji.
“Karɓi wannan kazarma. Ki cinye yanzu. Ban son wannan ramar da kike yi. Ina son ki cikakke kamar da.”
Sai da ya tabbatar na ci sosai, sannan nima na zubo masa tuwon da nayi, ya zauna ya ci da jin daɗi . Yana ci yana kallona da murmushi, sannan yace: “Na sha maganina yanzu.”
Na gyada masa kai da murmushi na ce “To. Allah ya kara lafiya.”
Bayan mun gama cin abinci, ina zaune a gefe ina kallonsa yana gyara wurin da muka zauna. Idona yana lumshewa kadan-kadan, alamun bacci na zuwa, sai kawai na ga ya ɗago wata leda daga cikin kayan da ya shigo da su.
Ya buɗe ledar nan a hankali, sannan ya fara fidda abubuwa ɗaya bayan ɗaya
Atamfa guda biyar, kowacce na zamani ne, sabbin salo masu kyau da launuka masu ɗaukar ido,Lace ɗaya mai laushi da kyan gaske, Shadda tana sheƙi,Kayan kwalliya da mayafai masu kyau masu ɗaukar hankali.
Ya juya ya miƙo min kayan yana murmushi, sai yace da wata murya mai sanyi “Ga su nan ƴar kwalisa, kingansu kuwa? Wallahi kadan ne, amma tsada ne dasu gani nayi dana siyo miki kanana gwara na dakko manyan kadan. Matata mai tsada ce, dole ta saka kayan da suka dace da ita.”
Na ɗan ware ido ina kallon kayan. Ganin super da gizna cikin kayan ya sa zuciyata ta cika da farin ciki Cikin natsuwa da farinciki nace masa “Na gode sosai, Bashari. Allah ya saka da alheri, ya kara maka lafiya.”
Ya ɗan ɗaga gira yana dariya da nutsuwa, ya ce “Bakomai ƴar kwalisa. Gobe da asuba zan fita zuwa birni. Akwai aiki da nake ƙoƙarin kammalawa. Ki tayani da addu’a kawai.”
Na ce masa da fara’a “Allah ya taya ka riko, ya dawo da kai lafiya.”
A hankali na lumshe ido, bacci na kokarin ɗauka. Sai na ji muryarsa a hankali “Tashi mu kwanta.”
Na bi shi zuwa ɗakin. Mun kwanta ne, amma ba kamar yadda ya saba ba yau bai rungume ni ba. Na lumshe ido ina jin kamar wani abu ya canza. Sai na ja jikina a hankali, na matsa kusa da shi, na jingina a gefensa kamar jaririya.
Sai kawai ya juya, yana kallona da idonsa masu cike da kulawa, yace da murya mai nutsuwa “Menene ƴar kwalisa? Kina lafiya?”
Na lumshe ido nace masa “Bakomai... bacci kawai nake ji.”
Sai ya ɗan murmusa ya rungume ni a hankali. Muryarsa na fita kamar rada a kunne na “Ƴar kwalisa... kina son wani abu ne?”
Numfashinsa yana bugawa da dumi a fuskata, sannan sai naji jikina ya saki gaba ɗaya. Yadda ya rungume ni da dumi da taushi sai na ji kamar duniya gaba ɗaya ta narke a zuciyata. Bacci ya ɗaukeni cikin wannan kwanciyar hankali, a jikinsa inajin wani kalar dadi.
*****************
Nana hadiza
09030569336ƘADDARAR RAMLAH
SHAFI NA TAMANIN DA TARA
Wannan littafin kuɗi ne, ba kyauta ba!
Biya Naira 700 kacal ki karanta cikin salama!
Domin biyan kuɗi:
Acc Name: Bilkisu Sani Kaura
Acc Number: 7040402435 (OPAY)
Tura shaidar biya zuwa WhatsApp:
09030569336 ko 07040402435
Masu son vip 👇Sai ku bibiyeni a
Arewabook @nanadiso10
https://www.arewabook,vs.com/book?id=6813670d91815df57bc25693
********
Washegari da asuba, na farka cikin natsuwa. A hankali na tashi, na nufi bandaki nayi alwala, sannan na dawo nayi sallah. Bayan na idar, sai na juya ina kallon Bashari yana zaune a kan daddumarsa cikin nutsuwa, yana lazumi. Fuskar sa cike da annuri da natsuwa kamar wanda ke cikin wata sabuwar rayuwa.
Na ce masa "Ina kwana… Bashari, wai kayi Islamiya ne?"
Ya juyo yana murmushi, sannan ya amsa cikin ladabi "Na dan yi kadan ƴar kwalisa, amma ban kai ga haddar Qur’ani ba. Duk da haka, ina da ilimin addini sosai. Wallahi, na saba da zuwa Islamiyya a baya, har na kai ga fahimtar darussa da yawa."
Ya ja numfashi, sannan ya sauke ajiyar zuciya mai nauyi. "Ƴar kwalisa, gaskiya ina jin tsananin bakin cikin dabi’u na da suka wuce. Har gobe, ba na jin daɗin yadda rayuwata ta taɓe. Na rasa iyayen gida da yawa saboda halayya na. Amma da taimakon Allah, nayi ƙoƙari na gyara komai.”
Ya ci gaba da bayani da murya mai raɗa
“Aliyu, na dawo da shi wajen iyayensa munje muka roƙi gafara, suka yafe masa. Haka sauran biyun ma, na basu jari, na saka su makaranta, sannan na nemi gafarar iyayensu. Yanzu, Alhamdulillah, suna tare da iyayensu cikin salama.”
Wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyata. Amma cikin wannan sanyi, akwai ɗan wani zafi da ya sosa min rai ganin cewa Bashari ya gyara dangantakarsu da iyayensu, amma ni… ba ni da kowa. Sai na lumshe ido na ɗan ɗago kai, ina kare masa kallo.
Ya cigaba da cewa “Kinsan inada gadon mahaifiyata gona guda huɗu ne. Na samu nasu rabon, na sayar da guda biyu, nayi jari da su. Na kama sana’a a birni tun kafin na zama haka, Wallahi ƴar kwalisa, ba kudin aikin daba nake amfani da su ba, sai dai nayi shaye shaye dasu. Amma cikin ikon Allah, ban taɓa amfani da su wajen kasuwanci ba. Inada baffa yayan mahaifiyata shine yake taimaka min, yana ba ni shawara kuma yana saka ni a hanya ta kwarai bangaren kasuwar yanzu ma haka shago daya nawa shine aciki tun da daɗewa.”
Na juya masa ido cike da tausayi da kuma yabo. Na ce da shi “Allah ya ƙara shiryar da kai, Bashari. Allah ya yafe maka. Ya kuma saka maka da lada akan kokarinka da wahalar da ka sha wajen gyara rayuwarka.”
Ya murmusa da jin daɗin kalaman da na furta. Nan na mike na ce “Bari na ɗan haɗa maka dumame.”
Na nufi kitchen cikin sauri, na haɗa masa dumamen tuwo da miyar . Bayan ya ci, muka zauna muka yi sallar safe tare. Sai na tsinci kaina ina jin wani irin farin ciki da kwanciyar hankali cikin zuciyata. Bayan sallar, ya kama hanya zuwa birni kamar yadda ya saba.Ya juya ya fita. Amma kafin ya buɗe ƙofa, sai ya sake waiwayowa ya ce “Kin manta da wani abu?”
Na girgiza kai cikin mamaki, sai yace “ kiss kafin in tafi... domin in tuna da ke a hanya.”
Ya dawo ya sumbace ni a goshi, sannan ya fice. Na tsaya a ƙofa ina kallonsa har ya ɓace cikin duhun safiya.
Tun daga lokacin da Bashari ya fita, zuciyata ta kasa samun kwanciyar hankali. Na zauna na miƙe, na koma na kwanta amma ina! Kamar zuciyata tana tambaya, tana yawo kamar tana neman abu da bata gani ba. Daga ƙarshe, na yanke shawarar cewa ba zan zauna haka ba. Na saka hijjab dina, na nufi gidan Uwani.
Da na shiga, muka gaisa da salam. Uwani ta ce “Matar Bashari kece?” Na dan yi murmushi nace “Eh, ni ce.” Ta dan yi dariya, tace“Ai jiya nazo har ƙofar gidanku ina ta bugawa amma baki buɗe ba.” Nace mata “Wallahi banji ba, ina can ina bacci sosai..” Ta kalleni da tausayawa tace“Yaya jiki yanzu?” Nace “Alhamdulillah, naji sauƙi sosai. Allah ya kara lafiya.” Sai kawai ta gyara zama tace“To Allah ya ƙara lafiya. Amma ai in gaya miki gaskiya, ana ta gulmarki fa.” Na dan ɗaga gira, nace “Gulma kuma? Uwani, wace irin gulma?”
Ta ce “Ana cewa ke kika hana Bashari dabbanci, ai yanzu wai Bashari ya daina dana Wai kamar ki kika chanza shi.” sai kawai na dan saki murmushi nace“To Uwani, Allah dai ya shiryesu. Aikin gulma ai ba ya hana hasken gaskiya.” Uwani ta ce“Gaskiya kam. Amma ya kamata ki dinga kula da abinda kike ji a gari.” Na ce mata “Haka ne. Amma Uwani, ba wannan bane dalilin zuwana.” Ta ɗago kai tace:
“To me ne?” Na ce “Ina son ki raka ni gidan su Bashari. Ina da magana da wasu can.”
Sai tayi dariya tace: “Ke ƴar nan, me zai haɗaki da waɗancan marasa mutuncin?”
Na dan danne dariya nace “Ba komai, kawai inason ki kaini.” Ta kalle ni, tayi shiru na ɗan lokaci, sannan tace “To shikenan. Bari na ɗauko mayafi.”
Bayan mun fita daga gidan Uwani, muka nufi hanyar gidan Baban Bashari cikin natsuwa. Rana tana dukanmu, iska tana kadawa a hankali. Uwani tana tafe da ni, tana dan tambayata “Ramlah, me kike so ki faɗa musu ne?” Na ce “Uwani, kawai dai naje na gaishe su ne da kuma dan magana da maigidan nasu.” Uwani ta gyara mayafinta tana cewa “Haka ne, amma fa ki daure zuciyarki. Mutanen can ba mutane bane.”
Da muka isa ƙofar gidan, sai muka shiga harabar gidan. Matarsa Baban Bashari ce ta fito da hannu a haɓa. Tana kallon mu da tsanani. Kafin mu kai gaisuwa sai ta fara magana cikin tsiwa “Ina zaku? Ina kuka dosa?”
Uwani ta ce “Sannu dai, mun zo ne dan gaisuwa da Baba.”
Sai matar nan ta harare mu, ta ce “To kuji tsoron Allah. Gaisuwa kuma? Kuje ku same shi can gindin bishiya yana shan iska. Kada ki ƙara zuwarmin gida kinji? Ku shigar mun gida kawai. Wayasani ko ke mayya ce.”
Cikin ƙyasa da rashin kunya ta juyar da kai ta koma ciki. Ni kuma da Uwani muka tsaya muna kallon juna. Uwani ta ce “Na fa gaya miki, Ramlah. Ki ga irin sharrin da mutane ke ɗauke da shi. Ba komai. Mu tafi can inda take cewa.”
Na ɗan lumshe ido, zuciyata cike da nauyi, sannan muka juya muka nufi gindin bishiyar da tace Baba yake. Cikin zuciyata kuwa, na ƙuduri niyyar cewa idan mutunci ya gagara a gaisuwa, to shiru ma gaisuwa ce.
Ko da muka iso bakin bishiyar, shi kuma yana zaune gindin bishiyar mangwaro yana shan rake, ya ware kafafu yana kallon wucewar mutane kamar wanda babu abin da ke damunsa.
Uwani ta juyo ta kalle ni, sai tace “Ramlah, sai kin dawo. Kada ya tozartani, ni kuma kinga tafiyata ba mutunci ne dashi ba.”
Nace mata da ladabi “Na gode Uwani. Allah ya saka da alheri.”
Na karasa na tsaya, sannan da sallama nace “Sannu Baba... ina kwana?”
Ya ɗago kai yana kallona daga sama har ƙasa.
Yace da wata irin murya mai tsauri “Lafiya kalau. Banganki ba.” Na samu guri a ƙasa kusa da shi na zauna a hankali, sannan nace “Eh... bazaka ganini ba, ni ce matar Bashari.”
Cikin mamaki da haushi, sai ya watsa min harara, ya ce “Ke? Ke fa kika ce ke matar Bashari ce? To banson wasa. Wani mahaukacin uba ne zai yarda da ɗansa ya aurawa ɗan iska irin sa? Ke da kallo ɗaya ma sai naji haushi! Yaushe Bashari ya zama mutum har zai samu matar arziki? Wallahi ke ba matar ɗana bace, ki tashi ki bar wurina kafin na maka ihu.”
Sai na lumshe ido, na dafe ƙirjina da hannu daya, sannan nace da nutsuwa da ƙasaitacciyar murya “Baba, ka saurare ni. Idan ka ce ka kore ni, zan tafi. Amma ka saurari kalmomi na kafin nan. Na fahimta cewa kana jin haushin Bashari. Na fahimta cewa kana kallon sa a matsayin wani abu mara amfani. Amma, Baba... ni ce matarsa. Kuma tun da nake da shi, ban ga illa daga hannunsa ba. Wallahi yana ƙoƙarin canzawa.”
Na ɗan ja numfashi, sannan na ci gaba “Baba... kai uba ne. Ka sani, Allah zai tambaye ka akan ɗanka. Idan kai ka yanke masa hukunci, wa zai gyara shi? Idan kai mahaifinsa ka ƙi yarda da shi, wa zai yarda da shi? Hadisin Annabi ya ce “Ku taimaki ɗan uwanku mai zalunci da wanda ake zalunta.” Aka ce masa, ya Rasulullah, ya taimake mai zalunta? Sai ya ce “Iya taimako shine ka hana shi zaluncin.”
Na ciro alƙur’ani da ke cikin jakarta, na nuna masa “Baba, cikin wannan Littafi ne Allah ya ce “Wa man ‘afaa wa aslaha fa ajruhu ‘alal laah” Wanda ya yafe kuma ya gyara, to ladansa yana wurin Allah.”
*****************
Nana hadiza
09030569336
09030569336ƘADDARAR RAMLAH
SHAFI NA CASA'IN
Wannan littafin kuɗi ne, ba kyauta ba!
Biya Naira 700 kacal ki karanta cikin salama!
Domin biyan kuɗi:
Acc Name: Bilkisu Sani Kaura
Acc Number: 7040402435 (OPAY)
Tura shaidar biya zuwa WhatsApp:
09030569336 ko 07040402435
Masu son vip 👇Sai ku bibiyeni a
Arewabook @nanadiso10
https://www.arewabook,vs.com/book?id=6813670d91815df57bc25693
********
Na gyara zama a hankali, na ɗan saki numfashi, sannan nace da sautin muryar da ta cika da ladabi “Baba... da yardar Allah na zo ne ba wai dan na ɓata maka rai ba. Na zo ne dan na bude maka zuciya ta. Dan Allah Baba, ka yafe min idan wani abu ya ɓata maka rai game da zuwana.”
Ya harare ni da idonsa, sai ya tura rake a baki yana taunawa, sannan yace “Ina jinki. Ki fadi abinda ya kawo ki.”
Na gyara zama sosai, nace “Baba... Ni ce Ramlah, matar Bashari. Ni mace ce, amma zuciyata cike take da raɗaɗi da tunani. Baba... meyasa zamu haifi yaro, amma mu barshi cikin duhu? Meyasa uba zai raina ɗansa, ya wulakanta shi, ya ɗauke shi kamar ba jini ɗaya suke da shi ba?”
Ya ɗan yatsina fuska, yana kallona da alamar bacin rai, amma ban damu ba. Na ci gaba “Baba, idan mutum bai taimaki dansa ba, wa kake zato zai taimakeshi? Alhali Allah yana cewa a cikin Alkur’ani ‘Yā ayyuhallazīna āmanū, qū anfusakum wa ahlīkum nāran...’
(Ya ku waɗanda suka yi imani, ku ceci kanku da iyalanku daga wuta.) Baba, mecece rayuwa idan ba ta da soyayya da kulawa daga iyaye? Bashari bai zabi haihuwar kansa ba. Amma ya taso cikin wulakanci da ƙyama daga gida. Ya girma cikin rashin kulawa. Daga ƙarshe sai rayuwa ta jefa shi cikin duhu, cikin mugunta, cikin shaye-shaye da daba. Amma Baba... yanzu ya canza.”
Na sauke ajiyar zuciya, hawaye na gangaro min daga ido, nace “Baba, wannan yaron da ka haifa wanda kake raina... shine yake bani ruwa na sha, yana dafamin abinci, yana duba jikina idan na kamu da zazzabi. Shine ya daukeni daga kasa ya gina ni. Amma shine kuma kake cewa dan iska ne. Baba, idan mutum yana da kuskure, sai a gyara shi ba a yashe shi ba.”
Na ɗan jima ina kallon fuskarsa. Na lura ya rage tsawonsa. Na ci gaba cikin karfin hali “Manzon Allah ﷺ yace:
‘Kowane ɗanku na da hakki akan ku, ku basu tarbiyya da adalci.’
Kai kake da hakki akansa Baba. Idan ka guje shi, wa zai karɓe shi?”
Na share hawayena da gefen mayafina, sannan nace “Baba... Dan Allah ka saka Bashari a ranka. Ya sauya. Yana ƙoƙari. Yana karanta Alkur’ani yanzu. Yana taimaka min da gaskiya da kulawa. Kuma wallahi Baba, a yanzu ni ce nake gani kamar ni na fi kowa sa’ar miji. Duk da yana da laifi a baya, amma yana ƙoƙarin canzawa. Idan ka cigaba da ƙin amincewa da shi, zai iya dawowa baya. Kuma idan hakan ta faru, sannu a hankali duniya zata yi masa kisan gilla. Amma idan kai da kanka ka rungume shi, wallahi zai ci gaba da gyara rayuwarsa.”
Na lumshe ido, na sauke ajiyar zuciya, sannan nace“Wannan ne ya kawo ni Baba. Na gode da ka saurare ni. Ni ban zo dan in ɓata maka rai ba. Na zo dan zuciyata ba zata iya jure rashin kulawar uba ga ɗansa ba.”
Ya tsaya shiru yana kallona, rakin da yake taunawa ya tsaya, sai yaja numfashi da ƙarfi, baice komai ba. Sai na miƙe a hankali, nace “Na gode Baba. Idan Allah ya yarda, in Allah ya kaimu, zan sake dawowa.”
Na juya na bar shi da tunani.
Da na juya zan bar wuri, sai kawai na ji muryarsa daga baya tana kiran sunana “Ke... dawo nan...!” Na tsaya cak, na juyo a hankali, zuciyata cike da tsoro da rashin tabbaci. Ya nuna min gefensa da hannu, yace “Zo ki zauna nan.”
Na ƙarasa cikin ladabi, na zauna a hankali kamar ɗiya mace a gaban ubanta.
Ya kalli idona kai-tsaye, yace da wata irin murya mai nauyi “Da gaske ke ce matar Bashari?”
Na ɗan sunkuyar da kai, sai na ce a hankali“Eh... Baba. Ni ce.”
Ya gyara zama, ya sauke ajiyar zuciya, sannan yace “Na ji duk kalamanki. Wallahi sun shige ni. Kuma kafin ma kisameni, wani abokina ya kirani jiya ya fadamin maganganu da suka sa ni tunani sosai. Yace min ‘Kai malam... baka tsoron Allah ne? Yaronka yana can yana fama da rayuwa, kai kana zaune ka juya masa baya. A'a malam... hakan ba daidai bane.’”
Sai ya kalli gefe kamar yana tuna abubuwan da suka faru a baya, sannan ya ce “Kina ganin ni ne na fara gujewa ɗana? Wallahi ba haka bane. Bashari ne ya fara guduna... sama da shekara ashirin ina ƙoƙarin jawo shi amma baya zuwa. Yana kallona kamar bashi da uba. Sai naga kamar shima ya zaɓi rayuwarsa ni kuma na zaɓi tawa.”
Ya lumshe ido na ƴan daƙiƙu, sannan ya ce “Kwarai kuwa, ina da sakaci. Ina da rashin kyautatawa. Na biye wa matata a rayuwa, nayi son zuciya. Na yi kuskure da yawa. Amma yanzu... yanzu na gane komai. Da na kalle ki kawai naga nutsuwarki, ladabinki, da yadda kika tsaya gaban mutum kamar ni kiyi wa’azi na tabbatar Allah ya karbi addu’ata.”
Ya kalle ni da ido cike da tausayi da gamsuwa “Na dade ina rokon Allah ya kawo wani abu ko wani mutum da zai zama sanadiyyar canjin ɗana. Kuma yanzu na yarda... ke ce wannan mutumin.”
Sai ya daga hannunsa sama, yana fadin “Saboda haka... daga yau, na yafe masa. Duniya da Lahira. Kuma ina rokon Allah ya yi masa albarka. Ya tsarkake shi daga kurakurensa, ya gyara masa gaba. Na yafe masa gaba ɗaya.” Na share hawaye da gefen mayafina, zuciyata cike da daɗi da farin ciki.
Ya ɗan lumshe ido, sannan yace “Yaya sunanki?” Na ce: “Sunana Ramlah.”
Sai ya ce “To Ramlah... Allah ya yi miki albarka. Allah ya bar ki a matsayin farin cikin ɗana. Allah ya tsare ku gaba ɗaya. Na gode sosai... kinji.” Na ce “Nagode Baba, Allah ya saka da alheri.” Na miƙe da ladabi, na masa sallama, zuciyata cike da farin ciki da sanyi. Sai na tafi gida ina jin kamar an sauke dutse daga zuciyata.
Bayan na dawo gida daga wajen Baba, na zauna ina jin numfashina kamar ana daddafe shi. Wayata da na bari a daki na ɗauka, sai na ga an kirani sau biyu. Da na duba, sai naga Maryam ce. Nayi mata flashing ta ɗauka nan take muka gaisa.
Cikin farin ciki tace “Ramlah, labari mai daɗi! An cire strike, makarantarmu zata koma aiki nan da week guda.”
Zuciyata sai da ta buga sau biyu. Cikin wata murya mai nauyi nace “To Maryam... Allah ya kaimu.”
Tace da zolaya “Hmm... Ramlah ko dai ciki ne dake?”
Nayi dariya cikin rauni nace “Ko ɗaya Maryam, ba ciki bane.”
Tace tana dariya “Wallahi kin ji daɗinki, Ramlah. Dama ni nayi auren nan. Wallahi kowane ma zan aura.”
Nace da kashedi cikin lallashi “Aa Maryam, kidaina cewa haka. Ki dage da addu’a, Allah zai ba ki nagari.”
Tace cikin gamsuwa “Hmm... Ramlah, bazaki gane ba. Yanzu mazan kadan ne suke son aure da gaske. Yawanci sai iskanci suke so. Amma ni, in Allah ya yarda, zan auri na gari.”
Nace “Allah ya baki wanda zai rike ki da gaskiya da tsoron Allah.” Tace“Amin. Naso nazo gidanki wallahi, amma bari sai na dawo city. Yanzu ina nan garinmu.”
Nace “To Allah ya kaimu lafiya.”
Na kashe wayar. Sai na zube a kujerar gefen gado, na zuba ido sama. “Ramlah, kina son karatu. Amma kin rasa mafita… kina da mijin aure, amma kuma burinki na ilimi bai mutu ba.” Nayi ajiyar zuciya. Sai na tashi na shiga kitchen na dauko jallop ɗin shinkafa da ragowar naman da Bashari ya siyo jiya. Na jera cikin karamin flask, na kira wani yaro nace yakaiwa habu na bashi.”