Kenza eBookz

Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul - Chapter 140

Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul - Chapter 140

Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul Chapter 140: Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul Chapter 140. .......Sageer na fitowa a wanka…

3,404 words

.......Sageer na fitowa a wanka shiri yayi ya barma Huznah gidan batare da ko kallonta yayi ba. Dan wlhy gaba ɗaya ransa a jagule yake, zuciyarsa a ƙuntace take. Yana buƙatar bama gidan iska ya samu ya huce idan ba haka ba komai zai iya faruwa, ji yake kamar ya mammari Huznah koma ya daketa, sai dai zuciyarsa na hanashi. Ace matarka ta aure da har rabo ya ratsa na haihuwa tana rayuwa da kai amma zuciyarta na akan wani can da baima san tana yi ba. Duk wani ƙoƙari yayi domin ganin ya karkato da hankalin Huznah a kansa sun taru sun rufawa juna asiri ashe a banza ne. To abanza mana tunda ta kasa ajiye abinda ya zama kabari a rayuwarta. Idan yace ma ya zargi AA Darma ko yaji zafinsa shi minene laifinsa tunda ko'a baya baice yana sonta ba, zuwa yanzu ma yana da tabbacin ya manta da wata Huznah a duniyarsa. Hakafa lokacin da akai kidnapping su AA ɗin nan tunda ya ɗakkota daga Kaduna suka dawo Kano ta saka kanta a wani hali, shi duk zatonsa abinda mahaifiyarta ta aikata mata ne akan yunƙurin zubar da ciki ya sakata shiga yanayin, ashe-ashe damuwarta akan AA ne. Abinda yasa ma har ya tuna haka a yanzu yanda ta dinga maimaita masa zancen da tambayarsa yaya ake ciki? An saki su Maanal? Suna cikin ƙoshin lafiya kuwa?. Duk da ya ɗan yi mamakin yanda ta damu da al'amarin Maanal ɗin tunda yasan ba sonta take ba sai yay tunanin ai yanzu Huznahr ta canja ne, ga yanda Ammie ta dinga kai-kawo akan nata al'amarin maybe shiyyasa itama yanzu ta damu da halin da Maanal ta shiga. Ashe-ashe nata tunanin ita daban ne. Kofa motar daya saya bata nuna farin ciki ba kamar yanda ta nuna damuwa akan kidnapping ɗin nan..... “Sageer wai kana lafiya kuwa?”. Abokinsa da tun ɗazun yake magana amma babu alamar ya jisa saboda yanda yay zurfi a tunani ya faɗa yana zungurarsa. Firgigit Sageer ya dawo hayyacinsa, sai kuma ya sauke kakkauran numfashi tare da furzar da shi ya juya yana kallon abokin nashi. Shi da shi amanar juna ne, basa ɓoyema junansu komai na rayuwarsu sai abinda shari'a ta hanesu da bayyanarwa wato sirrin aurensu. In ma zasu bama juna shawara ta wannan ɓangaren sai dai cikin hikima da iya lafazi bawai kai tsaye ba. Dan ko akan zamantakewar sa da Huznah ɗin ya taka rawar gani sosai a kai da shawarwari. Sageer ya sake furzar da huci sannan ya ce, “Toufeeq akwai matsala ne wlhy?”. “Matsala tami kuma?”. “A gidana”. “Gidanka kuma? Ai na zata mun wuce wannan matsayin komai ya wuce kuma itama Huznah ta kwantar da hankalinta yanzu tunda kayi wining game ɗin har ga Usman Fodio”. “Humm Toufeeq kenan, a zahiri ne nai wannan nasarar. Amma a zuciyar Huznah har yanzu bana ciki. Dan kuwa jiya da rana sanda nake cemaka zanje gida nakai mata naman nan karya lalace kawai na sameta cikin zurfin tunani.......” tsaff ya kwashe komai ya sanar masa. Mamaki sosai ya kama Toufeeq. “Kai amma Huznah bata ƙyauta ba, wannan ai rashin wayo ne kamar batai islamiyya ba dai. Koda yake wannan itace irin masifar dake yawo a gidajen aurenmu tsakanin mata a wannan zamanin. Ƙiri-ƙiri yarinya da igiyar auren wani a kanta harma da ƴaƴa tsakani sai kaga ta mutu a son wani dake waje. Imma tsohon saurayinta, in ma haɗuwar media bayan aure. Idan sun samu sakarkarun samarin mazan nasu sai kaga anata yaɗa fasadi ta hanyar waya da charting kai miji kana nan wasarere da baki kana ciyar da ƙatuwar banza kullum kana rana. Tun abun na tsayawa a wayar sai kaga sheɗan ya tunzurasu haɗuwa zina kuma ta shiga da aure. Shiyyasa wani lokacin wlhy bana ganin laifin mazan dake hana matansu yin harkar social media ɗin nan musamman masu rawar kai da son ƙarya. Dan wata acan take haɗuwa da lalatattun ƙawaye su sakata a group dake da maza sai mazan suna biyosu, idan wata bata kula ba wata fa daga nan ake haɗa alaƙa. Watama ba mazan bane da mata ƴan uwanta take lalacewar, innalillahi wa-inna ilaihiraji'un, mun ɗauki shaiɗanci abu mai sauƙi. Amma kam tabbas a yanzu wayoyinmu sune kawalanmu batare da mun fahimta ba. Amma Alhamdullah hakan ba yana nufin an taru an zama ɗaya bane. Dan wata mace wlhy ka ganta a media kamila, mumina ko ɗar baka ji idan ka ganta da waya koda tsakkiyar dare ne. Saboda abinda zai amfaneta kawai take yi sai nishaɗin yau da kullum. Wannan kam babban ƙalubale ne a gareka Sageer, dolene kuma ka tashi tsaye domin yin yaƙi da shi tun kafin al'amarin ya cigaba da nisa...” “Shiyyasa na sameka Toufeeq, dan a wannan gaɓar jinake kamar na haƙura na rabu da Huznah. Bazan iya rayuwa da macen da ba ni ne a zuciyarta ba. Gagangar jikinta kawai kenan na aura komi? Idan hakan ta kasance minene amfanin auren to? Gangar jiki wata rana tsufa zai risinar da ita ya tauyeta, itako zuciya da soyayya ta gaskiya har abada bata tsufa a zuciyar ma'aurata koda ɓacin rai ya danneta lokaci-lokaci sai ka samu tana motsawa.” “Hakane maganarka tana kan gaskiya. Amma bazan baka shawarar rabuwa da iyalinka ba. Kaima nasan kishi ne kawai ke cin zuciyarka. Dan haka kada kayi gaggawa. Amma kayi haƙuri ka ɗauki hakan matsayin ƙalubale da jarabawa. Sannan ka shirya fito mata ƙuru-ƙuru kawai tare da nasiha da lallashi da nusar da ita illar abinda take yi bayan ka nuna mata fushinka. Idan ta fahimta shike nan. Idan bata fahimta ba kaga sai muyi tunanin mataki na gaba ko”. Kai Sageer ya jinjina masa. Sai kuma zuwa can ya ce, “Shike nan na gode Toufeeq, zan gwada kuma na gani, in sha ALLAHU komi kenan zakaji”. “ALLAH ya kawo komai da sauƙi. Amma ka dage da addu'a dan ALLAH, komai yay tsanani maganin sa ALLAH”. Kai kawai Sageer ya jinjina masa.....

___________★

Anan Abuja kam Nibras da aka gama treating da magunguna iri-iri da aka amsa a wajen likitoci daban-daban a Nigeria da ƙetare ce ke shirin komawa gidan Darma. Duk da kuwa tunda Fawzan ya wuce basu taɓa waya ba. Maimakon ma ta damu ita hankalinta nakan AA, dan kuwa uwarta na nan na damuwa da tsalle-tsallen ganin ta samu lafiyar mahaifa ita tana nan tana shirya matakan takawa zuwa ga cimma AA. Dan a watan jiya ta cire tsoro ta fara tura masa saƙwannin soyayya ta WhatsApp da sabuwar number ɗinta. Sai dai tafi sati uku tana turawa kullum babu gajiyawa amma bai taɓa ko buɗe saƙon ba ma balle yasan tanayi. Sai ranar tana tura saƙon barka da juma'a taga an buɗe ko second biyu ba'ai ba. Kai tsaye ta fahimci a mistake ya taɓa irin saƙo ya shigo makan nan ka taɓa kawai. Tata jiran wani motsi ko zai duba amma bata sake jinsa ba, data cigaba da turawa kuma ba'a sake buɗewa ba. Ta tabbatar idan ta kira shi sai ya gane itace, dan haka ta koma turawa ta text message nan ma cike da roƙo da magiyar dan ALLAH ya saurareta. Amma har zuwa yau shiru kake ji. Ga wasu irin mahaukatan magungunan mata Mom ɗinta nata ɗura mata. Tun basa damunta har sun fara cizonta. Dan haka a karo na farko tace ita kawai a ƙarasa shirya mata komai ta koma tunda Yayanta yayi waya da Fawzan yace a satin nan suke saka ran dawowa matar Autansu kawai suke jira ta haihu. Wannan yasa shirye-shiryen komawar tata ya kammala tsaff dan so suke ana gobe zai dawo ta koma in sha ALLAHU. Kwance take yanzu ma a ɗaki ita kaɗai tunanin AA da sha'awar kasancewa da shi ta gama zagaye gurɓatacciyar zuciyarta, wayarta dake saman cikinta ta ɗauke ta shiga lalubo layin sa. Kawai sai zagayen cycle ɗin nan na dp ya nuna mata green alamar AA ya saka status. Mamaki ya kamata dan abinda bata taɓa gani yayi ba. Ko dp ɗinsa hoton agogone kawai a jiki, kuma tunda ta sanshi bataga ya taɓa canjawa ba. Da gudu ta danna, sai ko kai tsaye ya kaita status ɗin nashi, hoton jarirai guda biyu a cikin white showal da sky blue. Masha ALLAH yaran ƙyawawa masu matuƙar kamanni da juna, sai dai ƴan ƙananu da su dan basu da wani gurma. Gabanta ya faɗi wani ras. A take wata irin zufa ta shiga karyo mata, rawa jininta ya fara. Da gudu ta fito ta koma account ɗin Yaya Fawzan. Nan ma sai ga hoton jinjiraye ya rubuta Alhamdullah my boys sun iso. Tashin hankali, ai cike da rawar jiki ta dinga bin status na duk numbers ɗin ahalin Darma da take da number ɗin shi. Al'amarin kamar wani wutar jeji ko'ina ta shiga hotunan yaran ne ana musu addu'oi da su da mamansu. Ai bama tasan ta cillar da wayarta gefe ta fashe da kuka ba. Kuka sosai take yi jikinta har yana girgiza wa. Yanzu shike nan dai Maanal da gaske ta mata nisa tunda gashi har ta haihu da Ajwaad ɗinta. Haihuwar ma yara har biyu a lokaci ɗaya, ai ko wlhy bazata ƙyaleta ba, bazata barta ba, yanda tai mata wannan babban raunin a zuciya itama sai ta bar mata tabo a tata zuciyar. Dan duk abinda zatayi dan rabata da Ajwaad sai tayi.........✍️ 195

........Sai da ta gama haukarta da duƙe-duƙen alƙawarinta sannan ta tashi ta shiga bayi tai wanka, fitowa tai ta gyara jikinta tare da ƙarasa haɗa kayayyakinta sannan ta ɗauki wayarta, sai yanzu kuma wani tunani yake zuwa mata a rai, shin miyasa taga status ɗin AA? Hakan na nufin yayi saving number ɗinta kenan?. Sai kawai taji wani irin sanyi mai daɗi ya ratsa mata zuciya, murmushi ya kufce mata. Kaso ashirin cikin ɗari na nauyin da zuciyarta yay mata ya sauka. Haka ta shiga gunguro akwatina ta fito. Mom ɗinta na falo zaune sai Yayanta ɗaya da yazo gidan duk suka ɗago suna kallonta ita da akwatinan. “Ke lafiyarki kuwa? Ina zuwa da akwatina haka da yammar nan?”. “Mom gidana zan koma. Gara na koma yau Maanal ta haihu, Kinga kuwa daga yau zuwa koyaushe zasu iya dawowa ƙasar nan ko”. “To kuma shine dan rashin hankali babu bayani babu komai sai ki kama kinkimo akwatina zaki yafi? Ke wai yaushe zakiyi hankali ne dan ALLAH Nibras? Ke dai kullum kina girma amma gaki nan shashasha, sakara-sakara, gaula-gaula.” Baki ta cika da iska jin baƙaƙen maganar da Yayan nata ke jera mata. Idanunta cike da ƙwalla tace, “To amma Yaya Ma'aruff ya kake so nayi, kufa kuka matsa saina koma ɗin nan, naƙi kanata min faɗa kai da Yaya Asad, yanzu kuma na yarda zanyi abinda ya dace kana zagina. Suma can nazo ban koma ba ace ina baƙin cikin ta haihu har ƴan biyu”. “What! Yan biyu fa Nibras?”. Cewar Mom kafin Yayan nata yace wani abu. Idanun Nibras cike da hawaye ta ce, “Wlhy Mom ƴan biyu duk maza”. “Tab ɗi! Aiki ga mai ƙare ka. Lallai ita wannan da shirinta tazo...” “Shiri kuma kamar ya Mom, dan kawai ta haihu ƴan biyu shine kuma shiri? Ba ALLAH ne ya bata ba.” “Uhmm! Ku maza shashashai ne ba gane komai kuke ba. Ke ajiye akwatinan nan ki jirani zuwa anjima zan rakaki da kaina amma not now”. Sosai al'amarin ya girmi kan Ma'aruff. Sai yaji ma ya kasa yin magana ya miƙe kawai yay ma Mom ɗin tasu sallama dan ya fahimci yanzu hankalinta bama a kansa yake ba.. Yana wucewa Nibras ta dasa sabon kuka, ita manufar kukanta daban, abinda Mom ɗinta ke fassarawa daban. Haka ta zauna ta lalace a lallashinta da tsara mata abubuwa babu kunya yanda zata dage wai itama ta samo cikin, idan kuma ya gagara nanda watanni uku dashen da Doctor ya basu shawarar yi shi zasu koma ai mata. Haka ta ƙara ɗiɗɗirka mata maganin mata da abubuwa iri-iri ta tattara mata sauran kayanta anayin sallar magrib suka tafi gidan Darma....

__________★ SAUDIA

Ba'a basu damar ganin Maanal ba a lokacin, dan sunce sai an gama ƙara mata jinin da aka ɗiba jikin AA. Shima kansa AA ɗin basu barshi ya tashi ba sai bayan awa ɗaya ya samu natsuwa, haka suka dawo inda su Oum suke suka samesu cikin matsanancin farin ciki. Kafin ma su tambayi mike faruwa Oum ta fara basu labari, Ameerah ta nuna musu hotunan babys data ɗauka. A karo na farko kawai AA yaji jikinsa na tsuma koda wasan wasa basu taɓa kawoma ransu twin's ne a cikin Maanal ba. Dan basu ma taɓa yarda an duba musu mace ne ko namiji ba. Saboda duk abinda ALLAH ya basu suna farin ciki, hasalima sunfi ƙulafucin samun macen kodan basu da ita a gidan, dama Anum ce dan haka suka so yarinyar kamar ransu, yanzu kuma ta kufce ta barsu. A hankali AA ya zame yay sujidar shukur, kafin ya miƙe ya fita massallaci. Ai babu ɓata lokaci su Babban Yaya suka bishi, dan Abah ma yana can. Dukansu sai da sukai sallar godiya ga UBANGIJI tare da addu'oi, kasancewar azhar tayi suka gabatar sannan suka dawo. Zuwa lokacin an sake fito da yaran zuwa ɗakin da za'a maida mamansu dan dama sunje da su ne ana sake duba lafiyarsu da duk abinda ya dace. Babban Yaya ya fara amsarsu duka, ya rungumesu a ƙirjinsa yana mai jin ƙaunarsu tamkar Naufal. Yay musu addu'a sosai sannan Yaya Fawzan ya ɗauka. Shi kam ai sai da yaji hawaye na cika masa ido, yana masifar son yara a rayuwarsa kodan bai samu nashi da sauri bane. Amma haka yake ma su Naufal gata dama kamar kamar mi. Shima bayan ya gama rurrugumesu da musu addu'a mai gayya da aiki ya amsa. Shi kam da farko idanu ya zuba musu, zuciyarsa na wani irin rawa a cikin ƙirjinsa, shi Ajwaad Aliyu Abubakar Darma ne da ƴaƴa har biyu mallakinsa, ƴaƴan ma daga jikin Maanal Habib Giro Bestynsa. Yarinyar nan dai daya rayu da ita tun ƙuruciya, yay mata wanka yay mata wanki da abubuwa daban-daban, yarinyar da yake jinta tamkar jini da tsokar jikinsa, dan bai taɓa jin ƙaunar wata halitta bayan MANZON ALLAH da iyayyensa da ƴan uwansa irin Maanal ba. Da ace ana buɗe zuciya aga yanda asalin soyayya take da idan aka buɗe tashi sai masoya da kansu sun girgiza. A hankali hawayen da suka cika masa idanun suka ɗigo akan yaran, sai kawai ya rungumesu a cikin ƙirjinsa ya ɗauke hawayen batare daya bari kowa ya lura ba. Addu'oi sosai yay ma yaransa. Bai iya ya sake bama kowa ba sai da akazo aka amshesu dan ba'a son ana yawan daƙunasu. Daga nan ne fa suka fara kiran ƴan uwa nan Nigeria ana sanar musu tare da tura musu hotunan babys. Kafin wani dogon lokaci ahalin Darma ya ɗauki farin cikin ƙaruwa da suka samu. A kusa-kusa an haifa musu yara huɗu kenan. Ga ta RK, ga na Uncle Najeeb dan shima matarsa ta haihu namiji kusan wata uku kenan, tsakaninta da Nuwaira babu nisa. Ga kuma na AA har biyu. Saura Najma da Ameerah kuma da Maimoon, duk da dai na Maimoon basu da ƙarfi a kansa suna son kayansu..

A ɓangaren Ammie ma da yaran gidansu tunda Oum ta kirata ta sanar suka kaure da farin ciki. Ammie harda hawayenta. Itama batayi ƙasa a gwiwa ba tai kiran Nene a waya ta sanar mata. Suma su Shahidah Aunty Sakeena ta kirasu ta gumtsa musu. Sai kuma ga hotuna AA ya turama Ammie da kansa. Suma nan suka fara yawo a tsakaninsu. ALLAH sarki Yaya Yazeed sai da yaji hawaye na neman cika masa ido, lallai ya yarda wani baya haihuwar ɗan wani. Yau ga ƴaƴan Ajwaad da Maanal dai a duniya. Hajiya Yaya kam kunya taji ta mamayeta, sai hawaye kuma suka shiga biyo baya. Ta zuba ma Yazeed idanu cike da tausayi da rauni ta ce, “Ka yafe min Yazeed, nasan na cutar da kai, na rabaka da Maanal bayan nasan kana sonta. Duk da dai wani baya haihuwar ɗan wani, haka wani baya auran matar wani. Amma nima nayi abinda bai kamata uwa tayi ba kodan ƙyawawan hakayyarka na ɗa nagari. Duk cikin ƴaƴana babu mai min irin biyayyar da kake min da hidima. Amma son zuciyata da zugar sabuwa ya kaini ya baroni na ƙuntata yarinya saliha irin Maanal....” “Dan ALLAH Mamma ki daina cewa haka, duk abinda ya faru yana cikin ƙaddara tane ai, tun farko kuma dama Maanal ba matata bace ba. Harga ALLAH kuma na haƙura dan ta dace da Ajwaad, shine ya cancanci dama aurenta kodan soyayyar dake tsakaninsu mai ƙarfi tun ƙuruciya. Nima in sha ALLAHU ALLAH zai bani tawa”. Ammie da zuciyarta ta ƙara raunana da tausayinsu tace, “In sha ALLAHU Yazeed ALLAH bazai taɓa taɓar da kai ba. Kuma ALLAH da zaka yarda mizai hana ayi ƴar gida kai da Khadijahn Kano, yarinyar nan nada nutsuwa da hankali. Gata da iliminta na addini dan Kawunku Sani baya wasa da ilimin addinin yaransa. Amma fa idan har kaji ta maka dan babu mai sake tirsasaka auren wanda baka so kaji”. Murmushi Yazeed yayi yana wani sinnar da kai, ƙasa-ƙasa yace, “Ammie in dai tana sona mizai hana na amince”. Yanda yay ɗin sai ya bama Daddy da Ammie da Hajiya Yaya dariya dan duk suna a falon Daddy ɗinne. A karo na farko Daddy ya ce, “Wannan kuma aikinka ne Son, kai zaka sameta ka koya mata soyayyar ka. Mu namu addu'a ne da farin ciki, dan suma ƙannan nan naka na gaji da zamansu haka, zan basu gargaɗi na ƙarshe idan son samu ne zuwa ƙarshen shekarar nan kaga sai a haɗa duka na aurar daku nima na huta, sai nasan hidimar ƙannenku ne kawai ya rage min”. “Karka damu Daddy in sha ALLAHU zamuyi ƙoƙari, yaran nan kuma ka barni dasu kawai yanzu lokacin da zaka fara hutawa ne”. Sosai Daddy yaji daɗin bayanin Yazeed, hakama su Ammie da Hajiya Yaya....

★★

Kamar yanda doctors suka faɗa basu sami ganin Maanal ba sai dare, kusan 8 ta farka daga barcin da suka sakata sannan aka barsu shiga ɗakin da take ita da babys ɗin. Tunda suka shigo ta zuba musu idanunta da suka shanye suka ɗan kumburo. Suma kallonta suke kowanne fuska da murmushi, Oum ta zauna kusa da ita tana mai kamo hannunta cikin nata, Abah kuma ya zauna a kujerar kusa da gadon, sai AA ya zagaya can ɗayan gefen shi da su babban Yaya. Ameerah da Najma na zaune suma a bakin gadon ta gefen da mazansu suke.........✍️

196

........A hankali ta motsa lips ɗinta ta ce, “Oumna? Abanah!”. Cike da so da ƙauna suka amsa mata a tare, sai kuma ta kalla Ameerah da Najma suma ta kira sunansu. Amsa mata sukai suma cike da farin ciki. Ta sake juya kanta a hankali ta kalla Babban Yaya da Fawzan suma tace, “Yayana, Yaya F.” Suma da kulawa suka amsa mata fuskokinsu da murmushi har babban Yaya da kakan daɗe baka yana yi ba. AA ta tsare da kallo na sakanni, shima kallon nata yake ƙasa-ƙasa, yana jira a kira sunansa yaji tsitt. Sai kawai catai “Yaya F. Wanene wannan?”. Mi zasuyi inba dariya ba, musamman Yaya Fawzan. Ya ce, “Lilly baki ganesa ba ko?”. Kai ta jinjina alamar e. Aiko aka sake sanya dariya. Babban Yaya shima dai yau ya ɗana. Ya ce, “Lilly wani ɗan riƙo ne da aka kawo mana kin manta da shi, miskili, rigimamme ga dukan yaran mutane saboda Bestynsa. Ga kishi da duk wanda ya kula masa ita. Idan kaga yana dariya sai da besty, idan kaga yana surutu sai da Besty”. A hankali tana murmushi ta ce, “Lah Yaya na tunashi. Yaushe yazo?”. AA dake kallonta yana murmushi ya duƙo yana dungure mata kai kaɗan, cike da raɗa yanda ita kaɗai ta jisa duk da suna a kusa da su ya ce, “Randa na baki cikin my twins baby's nazo.” Sosai maganar ta bata kunya, tasa hannu ta ture masa fuska. Su dai su Abah murmushi suke cike da jin daɗi da farin ciki. Irin wannan yanayin yake fatan dinga ganin iyalansa a ciki akoda yaushe, yana son farin cikin iyalansa matuƙa. Dan haka yake jin daɗin ɗan zaman nan nasu na saudia kamar su kasance a haka dindindin. Amma ba komai, ko Nigeria suka koma ya shirya tsaff da sabon shirin gyara zamantakewar gidansa fiye da ta baya in sha ALLAHU...

_________★

Readers Also Read