Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul - Chapter 25
Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul Chapter 25: Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul Chapter 25. _Duk wanda bai fallowing ɗina ba…
3,917 words
_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_
🅿️➖4️⃣8️⃣
______________
........Akan ƙyawawan ƙafafunta da ƙumbunan ke a gyare fes-fes suna ƙyalli ya saukesu. Kafin ya tafi da kallonsa har saman baƙin wandon data saka irin mai manne jikin nan, yana gab da gwiwarta rigar asibitin ta bayyana, itace har zuwa sama fara da ɗigo-ɗigon jaa, tsabar neman magana da salon iskanci ya wani sauke a saman ƙirjinta ya kafe wajen da ido tare da ɗan datse lips ɗinsa. Da sauri ta koma saman gadon taja bargo ta lulluɓe jikinta gaba ɗaya tana furta, “ALLAH ya isa wlhy da mun kallon da musulunci ya haramta”. Murmushi yay mai fidda ɗan sauti sai dai sam haƙwaransa basu bayyana ba. Sai kuma ya taɓe bakinsa cikin halin ko in kula ya furta, “Daga baya kenan. Idan kin manta bari na tuna miki na san komai A to Z tun kan ki zama abin kallo. Ko kin manta wannan hannun ya miki wanka, ya wanke miki pupu, ya share miki majina, ya wanke miki pants, ya wanke miki blood na period. Ya.....” “That's enough malam. Kuma ka bar ɗakin nan tun kafin na maka ihu wlhy.” Murmushi ya sake yi yana taɓe baki da wani ɗan ɗage gira. Babu alamar zai ma motsa balle yayi abinda tace ɗin. Saima cikin tsareta da idanunsa da suka kaɗe ga jijiyoyin kansa duk sun sake fitowa. Muryarsa can ƙasa ya ce, “Ke baki gajiya da faɗa? Why are you being stubborn ne?”. Harara ta balla masa da faɗin, “Anyi faɗan da taurin kan, in baka son a maka ka fita rayuwata mana”. Sai da ya ɗan lumshe idanu ya buɗe akanta. Yanda yake mata wani shegen kallo tamkar idanunsa zasu narke a kanta ya saka tsigar jikinta tashi, kauda kanta tayi gefe da sauri, shi kuma ya ɗan ciza lips ɗinsa yana wani jan numfashi a hankali. “Nima ki fita tawa rayuwan mana. Kinbi duk kin hanani sukuni, kin hanani aure, kin sa duk nabi na tsani yaran mutane babu hujja”. Ai bama tasan sanda ta wara manyan idanunta a kansa ba tana harararsa, rasa abin cewa yasata faɗin, “ALLAH zai saka min sharrin nan da ka min”. Sai kuma ta sake sakkowa a gadon tare da fisgan hijjab ɗin sallarta ta saka. Ƙofa ta nufa fuuu dan gara dai ta bar masa ɗakin kawai sai yaci kansa yasha baƙin ruwa. Sai dai me ƙofar gam alamar saida ya rufe sannan. Ranta ne ya sake ɓaci, har takai hannu zata bubbuga sai kuma ta fasa saboda tunawa a asibiti suke kada ta shiga hakkin sauran majiyata. Dawowa tai inda yake cikin da tsantsar masifa da tsiwa ta balbalesa da masifa. Yanzu kam gaba ɗaya dauriyarsa ƙwacewa tai, dole ya kai hannu saman kansa dake wani irin sara masa da masifar ƙarfi ya dafe, dama tuni dauriya kawai yake yi, shi kaɗai yasan azabar da kan nan ke masa, dan shi dama a ciwonsa ciwon kai yafi yawa. Sam masifa ta rufema Maanal ido, sai cigaba da zazzaga masa take, “Please Besty my head ki daina min ihu”. “Anƙi a daina, tunda baka so ka fita mana, waya kawo ka nan ɗin?”. “Ya ALLAH” ya faɗa da wata sassanyar murya yana kai ɗayan hannun ma ya tallafe kan gaba ɗaya. Dan da gaske ji yake kamar kwalwar ciki zata zazzago. A karo na farko gaban Maanal ya faɗi, dan yanda ya kira sunan ALLAH ɗin da tallafe kan sai kuma hankalinta ya tashi. A hankali ta fara haɗiye masifar tata tana kallonsa. Yayinda shi kuma ke cigaba da jujuya kansa a cikin hannayensa yana cigaba da kiran sunan ALLAH, sai kuma ya koma faɗin, “Please Besty my head, kaina Besty zai fashe ki riƙe min, dan ALLAH ki riƙe min”. Ai tsabar yanda jikin Maanal ke rawa batama san takai hannunta saman nashi ba, ta ture ta maye gurbinsa da nata tare da duƙawa a gabansa tana leƙen fuskarsa da faɗin, “Na shiga uku mike damunka? Miya samu kan naka? Ka tashi muje wajen likita na roƙeka”. Sai hawaye sharrr. Bai iya ya motsa ba, sai hannunta dake a saman kan nasa da sanyinsa ke wani ratsashi ya sake dannewa da nasa da ƙyau. Yayinda ita kuma zafin kan da yanda jijiyoyin ke harbawa ke ratsata. Matuƙar firgici ta shiga, dan tun tana hawaye har kukan nata ya fara fidda sauti. Da ƙyar ya ɗaga idanunsa da suka gama kaɗewa ya kalleta, cikin motsa lips ɗin da ƙyar tare da ɗan jujjuya kai ya ce, “Stop crying, bafa da yawa bane”. Kukan ta sake fashewa da shi da faɗin, “Hakanne bada yawa ba, kaga yanda idonka yay ja kanka yayi zafi? Nidai ka bari naje na kira maka Rafeeq...” tai maganar tana ƙoƙarin miƙewa da son cire hannunta dake a saman goshinsa. Da sauri ya riƙo ɗayan hannun nata yana jujjuya kai, sai kuma miya tuna ya saki hannun yana faɗin, “Am sorry”. Itama kamar wadda ya fargar sai tai saurin janye ɗayan dake a saman kansan, ta ɗan ja jikinta baya. Murmushi ya ɗan yi, sai kuma ya miƙe still dai hannunsa dafe da kan nasa ya ɗan raɓa ta gefenta ya zauna a gadon jiyyarta yana faɗin, “Help me naɗan kwanta anan ko zai sauka”. Batace komai ba ta matsa masa, kwanciyar yay rigingine ya lumshe idanunsa hannunsa dafe da kan nasa. Tun tana kallonsa daga tsayen harta kai zaune a kujerar daya tashi dan itama sai taji kawai tana wani irin jin jiri, yayinda baya data shuɗe ke son maimaita mata kanta a zuciyarta. Haka suke ita da shi, da wahala ɗaya ya kwanta ciwo ɗayan bai kwanta ba shima. In ko ba haka ba dukkan hidimar mai ciwo ɗayan ne zai yi. Zata iya cewa fara kaiwar AA ɗin lokacin balaga ne yasa Oum ta fara saka idanu akan al'amuransu, harma takan kasance tare da su batare data barsu keɓewa su biyu kawai ba. Sai dai duk da haka ƙaddara bata barsu ba. (Ƙaddarah!) Zuciyarta ta maimaita kalmar da amsa kuwwa. Rimtse idanunta tayi da masifar ƙarfi sai kuma Zuciyarta ta fara zafi, (Eh tabbas batace ƙaddara kawai ba, harda ganganci da son zuciya daga AA ɗin, eh son zuciya, koma tace zalunci......) Hawaye suka shiga solalo mata masu shegen zafi. Zaram ta miƙe daga gaban nashi ta nufi window jikinta na rawa. Yanda ta tura kujerar da ƙarfi harta faɗi ya sanya AA buɗe idanunsa da ƙyar. Kallo ya bita da shi, sai kuma yay saurin rumtsewa jin abinda take faɗa cikin kuka mai tsanani daga inda take.... “Dan ALLAH ka tafi, ka tafi nesa dani bana son ganinka. Ka barni naci gaba da rayuwata cikin salama. Namaka alkawarin zan bar aiki a companyn ka. Bana son tuna komai, bana so, ka daina kusantoni, ka barni, dan ALLAH ka barni na roƙe ka Ajwaad....” “Besty!” ya faɗa a can ƙasan maƙoshi daga bayanta batare data san sanda ya baro gadon yazo wajen ba. Kuka ta sake fashewa da shi tare da durƙushewa a wajen, “Ka daina kirana da wannan sunan, ka tafi kawai, ka tafi Ajwaad....” “Zan tafi, amma ki saurareni kona minti biyar ne”. “Bazan iya ba, baka da sauran space na lokacina, sam baka da shi.” sai kuma ta juyo tana daga durƙushen ta haɗe hannayenta waje guda alamar roƙo🙏. “Na roƙeka ka barni Ajwaad. Ka yi nesa dani, bana buƙatar jin komai daga gareka, bazan iya baka komai ƙanƙantar lokacina ba a yanzu”. Da ƙyar ya iya haɗiye abinda ya riƙe masa maƙoshi, ya lumshe idanunsa da sukai mugun kaɗewa mai ban tsoro daban tashin hankali ya sake buɗewa a kanta. Cikin wani irin murya mai matuƙar laushi da sanyi ya ce, “Kin fi son mu cigaba da kasancewa a wannan matsayar kenan? Mu cigaba da ɓatama waɗanda ke bibiyar rayuwarmu lokacinsu. Yes muna ɓata musu lokaci ne kema kin sani, dan in har bani ne MIJINKI ba, wani bai isa ya zama ba!!.” ya ƙare furucin ƙarshe a kausashe. Ɗago kai tai da sauri tana kallonsa da jajayen idanunta. Shima ɗin kallonta yake da wani mugun kallon tabbatarwa. Amma ta dake a kausashe ta ce, “Mi kake nufi Ajwaad?!”. Shima a kausashen ya ce, “Abinda kikaji na faɗa shi nake nufi. In dai ni Ajwaad Aliyu Darma ina numfashi a doron wannan ƙasar, wani banza wofi bazai taɓa aurenki ba Maanal. Dan haka tun kafin dare yay musu ki sanar da su suje su nema matan aurensu. Ki kuma sani ko mutuwa nayi kika auri wani in sha ALLAHU sai na hanaku zaman lafiya da fatalwata. Idan kuma kinji wasa bismillah, ga fili gamai doki”. Ya ƙare maganar yana miƙewa da kaɗa mata yatsarsa manuniya a saitin fuska tamkar zai tsokale mata idanu. Miƙewa tai itama a gabansa tana huci ga hawaye na zirara mata da gudun tsiya. Cike da tsiwa ta riƙe ƙugu da duka hannayenta biyu tana kallonsa babu ko gezau. “A tunaninka kana da wani ƙarfin yin duk abinda ka faɗa? Ka lalata min rayuwa sannan kai tunanin hanani auren wani? Shike nan mu zuba, nace mu zuba ni da kai dan ALLAH ɗan halak ka fasa, ka saka a ranka ni kuma Maanal Habib Umar Giro zanyi aure, kuma zan auri wanda kake da kusanci da shi wato Rafeeq. Ka fara shiri nan da wata biyu kacal, wata biyu....” ta ƙare maganar tana karkaɗa masa yatsarta itama da raɓashi zata wuce. Ai a wani irin fusace a kuma bazata taji an damƙo hijjab ɗinta an fisgota baya. Babu zato ta jita manne a jikin bango, duk da ko kaɗan jikinsa bai taɓa nata ba yanda yay mata rumfa da ingarman jikinsa saboda ya fita tsaho da cikar jiki nesa ba kusa ba, babu ta inda zata shaƙi iska ya masifar sake hargitsata. A kausashe a kuma faɗace, dan gaba ɗaya taswirar ƙyaƙyƙyawar fuskar sa ta canja. Ga jijiyoyin kansa sun sake fitowa, idanunsa sun masifar kaɗewa irin mai ban tsoro ɗin nan tamkar an watsa jini a cikinsu. Da kakkausar muryar da bata taɓa tunanin ya mallaka ba ya ce, “Idan kikace zaki zuba WASAN da ni kema kin san kece zaki sha wahala wlhy. Amma bismillah mu zuba ɗin, sai dai ki sani wani ɗan iska bai isa shiga GONAR dana jima da shiga ba har abada, yanda na fara mallaka ni zan cigaba da mallaka har ƙarshen numfashi.” Daga haka bai sake cewa komai ba ya juya ya fita a fusace kamar wani mafaraucin soji a daji. Yana gama maida ƙofar ya rufe tai wani irin zubewa a wajen ta fashe da kuka jikinta na rawa. Kuka take sosai, kuka irin mai zuwa da dukkan ƙarfinka dana zuciya. Kuka mai ban tausayi. Ita wannan mutumin kema alfahari da abinda yay mata a baya, ita yake ma iƙirari akan abinda ya aikata mata. Ita Maanal. Wlhy dolene ta tabbatar masa shi ba kowa bane, bai kuma isa komai ba, tabbas zata tabbatar masa, dole ne ma ta bbatar masa, ta hanyar auren RAFEEQ ne kuma kawai zata tabbatar masan. Ta jima a wajen tanayi, sai shigowar nurse ɗin dake kula da ita ne ya kawo ƙarshen yanayin. Hankali tashe tazo ta tadata a wajen, da taimakonta ta maidata gadon tana jera mata tambayoyi akan ko jikin nata ne. Kanta kawai ta iya girgiza mata. Sai kawai nurse ta shiga lallashinta, dan AA ne ya turota dama. Daɗaɗan kalamai ta dinga faɗama Maanal masu kwantar da zuciya, a hankali a hankali ta fara tsagaita kukan har tai shiru. Hawayenta ta share tas tare da sake yin lamo a gadon. Nurse ɗin ma tayi tunanin ko tayi barci ne sai ta lallaɓa ta fita dan akwai abinda zata ƙarasa sannan ta dawo. Kamar jira Nurse ɗin na fita RK na shigowa. Yayi sallama har fin sau uku da knocking amma shiru, sai ya ɗan kalla agogonsa da tunanin ko tayi barci. Ganin lokaci yaja sosai sai kawai ya yarda tayi barcin ne. Ƙofar ya ɗan tura ya leƙa, can ya hangota kwance a gado a lulluɓe, sai dai mi wani ƙamshin turare da ya san bai taɓa jinta da shi ba ne ya bugosa. Sai da gabansa ya faɗi, ai ba shiri ya shigo ɗakin da sauri. Tabbas ƙamshin turaren ne, turaren da in bai ƙarya ba a wajen AA kawai ya san shi. (AA!) Zuciyarsa ta sake maimaita masa sunan da amsa kuwwa. Sai kuma ya shiga waige-waige a ɗakin kamar zaiga AA ɗin a ciki. Duk abinda yake Maanal na jinsa, amma ta dake tai likimo kamar mai barci, dan bata son ya ganta a yanayin da take sam. Jin ya fice da sauri yasa ta lumshe idanunta da ƙarfi sauran hawayen dake a ciki suka wani zubo shaaa.....
____________★
Da ƙyar ya iya fita a taxi ɗin ya nufi gate ɗin gidan nasu, dama satan fitar yayi. Daga fitowa sallar isha'i ya maƙale yaƙi komawa ciki. Sai da ya tabbatar Abah da yayunsa sun shige sannan ya fito a massallacin ya tari taxi ya nufi asibitin dan kawai ya ganta. Tun safen da RK yazo gidan da batun nata ciwon zuciyarsa ta kasa samun nutsuwa. Ji yake kamar ma nasa ciwon ya dawo sabo ne. Sai kuma gashi ya dawo a wannan bahagon halin yanzu. Da mamaki security daya buɗe masa ƙofa ke kallonsa. Sai dai shi ko kallon nasa baiyi ba ya wuce flat ɗinsa. A hankali ya maida ƙofar ya rufe yana sauke ajiyar zuciya ganin kowa bai gansa ba. Sai kuma ya dafe kansa dake matuƙar sara masa har yanzu tamkar zai cire. Yana shigowa falo na biyu yay wani irin turus ganin Mamy zaune. Zuba mata ido yay sai kuma ya ɗan wawwaiga kamar mai neman abu. Dan wani irin tsarga zuciyarsa kallon da take masa yake yi. Amma sai ya dake kamar yanda ya saba. Idanunsa ya maido kanta cikin sautin muryarsa mai fita ƙasa-ƙasa ya ce, “Mamy kina buƙatar wani abu n....” Hararar data wullo masa ta hanashi ƙarasawa. Sai ma duƙar da kansa da yay kawai. “Daga ina kake?”. Ta faɗa da kakkausar murya. Sam AA ya tsani ƙarya, baya sonta baya shiri da mai yinta. Gara idan bazai faɗi gaskiya akan abu ba ya gwammaci yin shiru kawai. Haushi ne ya turniƙe Mamy, cikin baƙin ciki da ƙunar zuciya ta wani daka masa tsawa. “Ajwaad bada kai nake ba ne?! Kasan dai bana son wannan banzan halin naka na iskanci ko? Nace daga ina ka fito??”. “Mamy Please my head” Ya faɗa yana kai hannu a saman kansa. Harara ta balla masa duk da zuciyarta ta motsa da yanda yayi ɗin. Amma sai a faɗace ta ce, “A'a your heart ba head ba. Ni zaka rainama wayo kama pretending ko. To wlhy bara kaji, idan ma wani abu kuke ƙullawa kai da ita to ka dawo cikin hankalinka, in ba hakaba wlhy kaine masha wuya. Dan har yanzu har gobe kai har ƙarshen rayuwa ina akan bakana. Yanda ƴan uwanka suka auri zaɓina kaima dole hakan zakayi. Dan haka ka sani na zaɓa maka yarinyar da sukazo tare da Abdulhakeem ɗazun a matsayin mata, a cikin satin nan za'aje nema maka aurenta. Kuma wata biyu kacal za'a saka...” Ai da wani irin bala'in sauri ya kalli Mamyn, ta watsa masa harara cike da tabbatarwa........✍️
✨ZAFAFAN DAI ✨
1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull)
Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000
0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070
Kati MTN:- 09032345899
Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_💞AJIYA A DUHU....💞_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
*_My TikTok account 👇_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram👇🏻_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_Arewabooks_*
Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30
*_WhatsApp channel_*
https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R
_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_
🅿️➖4️⃣9️⃣
______________
..........“Haka na faɗa kuma haka za'ai. Sannan wacece Maanal ɗin da wannan yaron Rafeeq ke magana ɗazun?”. Wani irin sake bugawa zuciyarsa da ƙirjinsa da kansa sukai a lokaci guda. Ya tsatstsareta da kaifafan idanunsa da suka gama jirkicewa gaba ɗaya kamar zai haɗiyeta da su. (Maanal! Waya gaya mata zancen Maanal? Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un.....) “Sai ka gama tunanin zaka faɗa min wacece ita?!”. Ta sake faɗa a tsawace kamar zata falle fuskarsa da mari.. Da sauri ya kai duka hannayensa biyu ya dafe kansa. Sai kuma yay saurin zubewa a kujerar dake kusa da shi jin jiri na neman zubar da shi a wajen. Ɗan tsai tai tana kallonsa, kamar zata matsa garesa sai kuma, fuuu ta nufi hanyar kitchen tana faɗin, “Idan ka gama pretending ɗin iskancin kazo ka saman ka faɗa min wacece ita. In ba hakaba ni zan bincika, kuma ka bari har ya kaimu ga hakan wlhy sai ranka yay mummunan ɓaci a gidan nan. Zuwa safiya kuma idan ita uwar taka da uban naka suka tambayeka game da Nuratu da Huznah dan ALLAH kace baka so kaga yanda zan maka. Dan ko ka yarda ko baka yarda ba sai ka auresu dole su duka kuma a rana ɗaya”. Daga haka tai ficewarta ta kitchen ɗin dan dama tanan ta biyo....
______★
“Jaan! wai ina kuma zaka naga ka ɗauka key?”. “Zan ɗan duba Ajwaad ne, dan tun fita sallar isha'i yay wani wajen. Kin san Oum akan Ajwaad dai, na tabbatar tana can zaman jiransa hankalinta a tashe. Ballan tana baida lafiyar nan”. Baki Nibras ta ɗan taɓe, tare da ballama Fawzan da yay gaba abinsa harara. Wani irin takaicin Oum na keta mata zuciya. Harta koma ta kwanta sai kuma ta miƙe zaram, sakkowa tai a gadon ta saka slippers ɗinta tabi bayansa batare data neman hijjab ta suturta jikinta ba duk da kasancewar kayan barci ne kuwa, dan ma dai sunada girma basa nuna mata ko'ina na jikinta. Tuni Fawzan har ya shige sashen AA, dan haka itama ta afka kawai. Isowarta dai-dai Fawzan ɗin na jijjiga AA cikin matuƙar tashin hankali da kiran sunansa. Sosai zuciyar Nibras ta motsa, tai mutsuwar tsaye tana kallon yanda mijin nata ya tallafi abin sonta da duka alamu suka nuna baya cikin ƙoshin lafiya. (A tabbas masoyi, dan kuwa da dukkan zuciyarta take jin ƙaunar ƙanin mijin nata kuma ɗan ƙawar mamanta. Mahaifiyarta da Mamy aminan juna ne shekaru masu yawa. Bata san komai daya faru ba wata rana mamanta ta bata umarnin shiryawa akan zatayi baƙo. Sam bata jayayya da ita, dan duk abinda take so itama tana so. Dan haka babu musu ta shirya tarba ta musamman ga wannan baƙo, duk da bata saka a ranta zata iya aminta da shi matsayin miji ba. Dan tana da nata tsarin itama akan mijin aurenta. Sai dai me, tana ganin Fawzan a matsayin baƙon nata duk ta rikice, dan guy ɗin it is hot kuma handsome. Bata wani ɓata lokaci ba ta miƙa wuya, kamar wasa soyayya ta ƙullu duk da ta fahimci shi ba wai hundred percent ya bata ammana bane. To amma mamanta ba Maman yara bace, tuni ta shirya mata duk ta yanda zata mallaki Fawzan ɗin har akai gagarumin biki na nunama tsara. Dan kowa yasan family na Ambassador Aliyu Darma ba gidan wasan yara bane. Bayan tashen dukiya da suna da yay Ƴaƴansa ma gwarazan kansu ne a fanin nema. Sai dai me, bayan aure da baifi wata ɗaya ba AA ya dawo Nigeria sakamakon jiyya da yay a ƙasar waje na tsawon shekaru biyu. Tun fa da Nibras ta ɗaura idonta akan AA taji komai ya ƙwace mata. Dan hundred percent shine irin zaɓin data jima tana ma kanta. Bawai dan Fawzan bashi da qualities ɗin AA bane. Kawai dai akwai abubuwa da yawa da suka bambanta su duk da a fuska suna kama da juna. Tayi iya bakin ƙoƙarin ta na ganin ta danne kwaɗayinta amma abu sai ƙara girma yake a zuciyar tata. Dan takai har siffanta kanta take tare da shi a lokacin da take tare da mijinta. Tabi hanyoyi da yawa akan AA amma ko kallo bata ishashi ba, dan yana da tsari akan mu'amularsa da matan yayyan nasa.......) “Nibras! Nibras!”. Kiran sunanta da Oum ke ƙwalawa ya maidota hanyyacinta. Sam bata san lokacin da Oum ɗin ta shigo sashen ba. Oum ɗin ce ta ƙara katse mata gajeren tunanin da faɗin, “Nibras ɗakko bowl a kitchen ki sawo ruwa a ciki. Kai kuma Fawzan ɗakko towel ƙarami a toilet ɗinsa”. Cikin rikicewa Fawzan ya amsa mata. Dan shi dama bai iya rikicewa ba. Har ya tafi Oum ta ƙwala masa kira. “Kaga dawo mu kamashi zuwa can sama ɗin zaifi”. “Oum kin san bazamu iya ɗaga shi ba. Auta bana wasa bane. Bari na kira Babban Yaya dai”. Oum bata musa masa ba, ya shiga kiran Babban yaya. Cikin ƴan mintuna kuwa sai gashi. Shima hankalin nasa a tashe yake. Da ƙyar suka kama AA ɗin su biyu suka miƙar zuwa upstairs. Dan gaba ɗaya jikinsa ya wani irin saki sai numfashi yake da ƙyar da kiran sunan ALLAH dana Oum yana faɗin Kansa kansa dai. Sai da suka shinfiɗesa a gadon sannan Fawzan ya nufi ɗakko towel ɗin, dai-dai da dawowar Nibras. Sai faman hawaye take, dan ji take kamar ta maido ciwon kanta ko zata ji sassauci. Babban Yaya ne ya amshi ruwan da towel ɗin yana faɗin, “Oum kuje falo bari nai masa. Dan jikin nasa ma ya ɗau zafi duka yana buƙatar ruwan sanyin”. Oum dake hawaye bata musa ba. Sai dai Nibras ba haka taso ba. Dan takaici har ɗan hararar babban yaya tayi ta gefen ido. Ganin yanda Oum ɗin ke hawaye Fawzan ya kama hannunta cike da lallashi, dole itama Nibras ɗin ta biyosu badan taso hakan ba. Sai dan tasan rijiya ba wajen wasa makaho bane ba. Shima babban yayan kamar AA yake baya ɗaukar raini.. Tsaf babban yaya ya gogema AA jiki yana tofa masa addu'a, a hankali jikin ya dinga hucewa shi kuma yana sauke ajiyar zuciya. Sai da ya koma sanyi ƙalau barci ya fara ɗaukarsa sannan ya barsa haka. Kaya marasa nauyi ya ɗakko a closet ɗinsa ya canja masa, dan ya zame waɗan can duka da boxer kawai ya barsa sanda yake goge masa jikin. Koda ya sanar ma su Oum suka shigo itama zama tai a ta ɗayan gefen tana tofa masa addu'a, hakama Fawzan na daga wajen ƙafafunsa yana tausa masa su da tofa masa addu'ar kamar yanda babban yaya da Oum keyi. (😀AA ɗan gata kenan). Tsahon lokaci suna a hakan kafin barci mai nauyi yay awon gaba da shi, wannan addu'ar da suke masa ce kawai mafita, dan in irin wannan ciwon kan ya bugesa sam maganin asibiti baya masa. Ba kuma dan ciwon bana asibitin bane, kawai dai ita addu'a dabance, maganin kowacce irin masifa ce.. Yanda yake sauke numfashi kaɗan-kaɗan ya sakasu dinga sauke ajiyar zuciya suma. Yayinda Nibras dake ta hawaye ta kasa haƙuri sai da ta tambayi Oum cikin dauriya, dan ji take kamar ta shaƙeta kota tureta daga zaman datai kan AA a saman cinyarta. Kishin matar take ji, tsananin kishinta mai zafi. Bama ita ba, duk wanda zai raɓar mata AA bata ƙaunarsa sam musamman mace. Kai hatta Mamyn ma haushinta take ji, dan ta jima da fahimtar daga Mamy har Oum ɗin dukkan soyayyarsu akan AA tafi ƙarfi. Dan kowa nayi ne bakin rai bakin fama duk da Mamy na ɓoye kurwanta wa kowa sai su da suka sani ita da Saheeba da ƙalilan ɗin mutane......
_____________★