Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul - Chapter 44
Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul Chapter 44: Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul Chapter 44. ........A hankali ya wani kalar…
4,384 words
........A hankali ya wani kalar taɓe baki. Cikin halin ko'in kula da ganin yanda ta ke waige-waigen ya ƙarasa shigowa cike da izzar nan tasa da ƙasaita hankalinsa a kwance. Sai da yaje jikin desk ɗinta ta kashe-kashen daya kasance daga ita babu kowa sannan ya tsaya. Kaɗan ya ɗosana jikinsa a desk ɗin yay irin tsaiwar maza tare da harɗe ƙafarsa akan ɗayar daya dogara, gaba ɗaya ƙarfinsa naga desk ɗin. Idanunsa har yanzu akan Manaal da kamar tayi suman zaune ne ma oho mata😂. Babu wani ko ɗar balle tunanin wani ya shigo ya gansa ya kai hannu ya zare meat pie ɗin dake hannunta da take ci. Bakinsa ya kai ya gutsira, ya lumshe idanu yana mai taunawa a hankali... “Amma kasan hakan na nufin sakani a masifa ko? Dan ALLAH dan mi zaka zo nan a wannan lokacin da kowa ke can yana salla kai kana nan ɗaukar magana?”. Shiru kamar bai jita ba. Sai da ya mula dan kansa sannan ya buɗe lumsassun idanun nasa a kanta. Cikin halin ko'in kula ya cigaba da cin meat pie ɗinsa hankali kwance. Marairaice masa tai sosai idanunta na cika da ƙwalla, dan ta fahimci masifar bazata kaita ba. “Please dan ALLAH ka fita kada wani ya shigo ya ganka anan ka jamin surutu. Salla fa akeyi”. Da kaga yanda take maganar kasan bata da nitsuwa, dan sai leƙe-leƙe take kamar mai shirin yin satar naman miya a gidan soja. Baki ya sake taɓewa da janyo bowl ɗin da meat pie ɗin yake ya sake ɗaukar wani. “K miya hanaki zuwa sallar?”. “To ina ruwanka dan ALLAH da abinda ya hanani, ni dai dan ALLAH ka tafi kada ma'aikatanka su sakani a bakin duniya”. “Tunda babu ruwana da abinda ya hanaki zuwa salla. Kema ina ruwanki da ganina anan to. Naga dai company na ne, ina da damar shiga duk inda nake so a lokacin da nake so ko”. Yanzu kam sosai hawayen suka ciko mata idanu, ta tsatstsaresa da kallon da bama tasan tana yi masa ba. Cike da rauni ta ce, “Kadai fi son ka ganni a masifar ko Ajwaa....” ta kasa ƙarasawa saboda kallon daya watso mata. Baki ta sake tunzurawa sosai. Baki ya ɗan laɓe ya janye idanun ya sake kai hannu zai ɗauka meet pie ɗin da ya rage saura biyu kawai. Ai babu shiri ta kai hannu ta buge nasan cike da tsiwa ta ce, “Malam wai miye haka zaka cinye min abinci”. Bai kulata ba ya ɗauke bowl ɗin ma gaba ɗaya, sai da ya gutsira sannan ya kalleta cike da iskanci yana wani ƙanƙance su ƙasa-ƙasa ya furta, “Ko mai meat pie ɗin ta kama ba sai na.....” “Na shiga uku. Sai kayi mi?..” Maanal ta faɗa tana mai waro dukkan idanunta a kansa. Kaɗan ya rage ya kwashe da dariya. Amma dai ya dake ya basar. Sai ma dan neman magana ca yay, “Ni kibar min wannan kallon karna ƙware. Sannan miye wani kin shiga uku bana son fassara zance. Sai nayi ƙyautarki nake nufi”. Harara ta watsa masa ta koma kan kujerarta ta zauna. Dan ta fahimci idan ta biye masa ALLAH zama ta iya zubewa a wajen. Pretending ɗin danna keyboard ta koma yi, shi kuma ya cigaba da cin meat pie ɗin yana duba drawing papers na zanen da tayi dake yashe a desk ɗin. A haka ya kammala cinye mata tas babu ko tausayi balle ya rage mata, ya ɗauka ruwan da tasha ta rage ya shanye. Sannan ya maida gaba ɗaya hankalinsa ga papers ɗin. A bazata taji saukar furucin sa cikin kunneta. “Kiyi gaggawar dakatar da Rafeeq yin abinda kika saka shi, in ba hakaba zaki haɗa rigimar da ke kanki baki san ƙarshenta ba”. Kallonsa kawai ta ɗago tana yi dan kamar ba shine yay maganar ba. Dai-dai nan Ema... Da Zaharadeen suka shigo suna dariya. Cak suka tsaya tare da jan birki saboda cin karo da abinda basu yi tunanin gani ba. Boss da kansa a office ɗinsu. Tashin hankali. Cikin firgicewar bazatar ganinsa da sukai suka shiga gaisheshi. Sai lokacin ya ɗago ya zuba musu kaifafan idanunsa. Yayinda Maanal ke jin kamar ta fasa ihun da sai Abuja tayi girgiza gaba ɗayanta. Dai-dai nan suma wasu biyun suka sake kawo jiki, ai a sukwane suka taka birkin da yafi nasu Deeni. Shiko tuni ma ya ɗauke idonsa a kansu ya cigaba da dube-dubensa kamar bai san da kowa ba a wajen sai kansa. A haka har suka gama shigowa, babu kuma wanda zai shigo bai taka birkin firgici ba da ganin CEO ɗin. Shi kuma yaƙi kulasu sai jeruwa suke kamar ƴan layin tuwon dare a boarding school (lolx🤣😂). Maanal kam ai ta kasa kallon kowa, tai ƙasa da kai kamar maƙaryaci a gaban sarki. Sai ta gefen ido ake ƴar kallan kallo tsakaninta da su Yaqub. Fin mintuna biyar sai da ya mula dan kansa ya ajiye Drawing papers ɗin ya gyara tsaiwa sannan ya ɗago idanu ya sauke a kansu bayan ya zuba duka hannayensa a aljihun wandon suit ɗinsa. Babu alamar wasa a tare da shi ko sassauci ya ce, “Waye Abideen a cikinku?”. Cikin tashin hankali Abideen ya ce, “Nine sir”. Kallon sama zuwa ƙar AA ya masa. Sai kuma ya ja idanunsa ya maida a kan fuskar Abideen ɗin yana sauke masa wani zafafaffen kallo. Tsohon mintuna biyu kafin ya janye a matuƙar daƙile. Pen ya ɗauka a gaban Maanal da ƙaramar takarda ya fara rubutu, sai kuma can ƙasa ya furta, “Nawa suka biya ka?”. A tare su Zaharadeen har ma da Maanal suka maida kallonsu ga Abideen da duk ya rikice. Rantse-rantse ya fara. AA da ko nuna yana ma jinsa baiyi ba ya ajiye pen ɗin da short note ɗin da yay a gaban Maanal ya miƙe sosai, batare da ya sake kallon kowa ba yay hanyar fita yana faɗin, “Ka tattara komanka ka saman a office”. Daga haka ya ratsa ta tsakkiyar hanyar da suka dare suka bashi ya fice abinsa. Shi ko Abideen hankali tashe yake kirama kansa ya shiga uku ya lalace. Sai da AA yay nisa sannan su Yaqub suka sami damar baibayesa da tambaya. Maanal dai suman zaune tayi da mamakin mugun sabon halin da AA ya ɗauka yanzu. Koda yake tuni fa yana da mugun halinsa, kawai dai ƙuruciya yasa bata fahimta a wancan lokacin. To dan ALLAH in ba mugun hali ba taya zaka zo ka turke staff ɗinka a bainar nasi kana masa wannan kausasan tambayoyin na nuna isa da izza. Wai mi masu kuɗi suka ɗau kansu da rayuwarsu ne?...... “Sis.. Maanal dan ALLAH kizo muje ki bashi haƙuri, wlhy zan faɗa masa gaskiya....” furucin Abideen da ke binsu da wannan furucin su duka a birkice ya dawo da ita a hanyyacinta. Yayin da su Zaharadeen ke ƙoƙarin kamashi dan ya nutsu asan mafita. Amma ina duk ya ruɗe. Sai da ƙyar suka danna shi ya zauna a kujera. Ema ya bashi ruwa yasha. “Ni dai shawarar dazan baka Abideen ka tashi kaje kasan dai boss baya son jira. Kuma tabbas tunda ya shigo office ɗin nan da kansa case ɗin nan naka babba ne. Amma ka rufama kanka a siri ka gaya masa gaskiya a tambaya ɗaya nasan zaka iya samun sassauci tunda ya tsani ƙarya ko kwalo-kwalo akan laifi kaima ka sani”. Musa ne da wannan magana cikin damuwa. Dukansu sun gamsu da shawarar Musa ɗin. Dan haka duk suma suka shiga cema Abideen ɗin ya tashi yaje. Da ƙyar ya iya miƙewa ya fita. Duk suka bisa da kallo. Sai da ya fice gaba ɗaya Zaharadeen ya kalla Maanal cikin sauke ajiyar zuciya da ƙwarewa a gulma. “Sis... Manaal wai tun ɗazun boss yana nan ne dama? Sannan yayi wata magana ne?”. Karan farko Maanal ta watsa masa harara. Cike da tsiwa ta ce, “Miyyasa baka tambayesa ba sanda yake nan? Ko sai ni marainiyar wayonka”. Mutsut Zaharadeen ya haɗiye gulmarsa. Dan wani irin kwarjini ma yaga Maanal ɗin ta ƙara masa. Ga shi ta wani tsare sa da mayun idanunta masu haske. Harara ta rakashi da shi, sai kuma taja siririn tsaki ta maida kanta ga aikinta. Akan rubutun da yay ta sauke su. _“Ki saman ki bani amsata nan da awa ɗaya a office, in ba hakaba wlhy zan dawo da kaina na ɗaukeki na kaiki. Kar kiga ba canja topic yanzu tausayi kika bani”_. Muƙut ta haɗiye yawun daya maƙale mata a maƙoshi. Ita kam ga shiga uku da mutumin nan. Kafin ta samar ma kanta mafita Yaqub ya zauna dan su cigaba da aikinsu. Dole ta haɗiye komai da bashi hankalinta dan aikin mai muhimmanci ne. Sai dai kaso sittin na hankalinta ya tafi ga al'amarin AA ne da ƙarfin halinsa.....
_________★
Tunda taga awa ɗayan daya bata ya kusa cika hankalinta ya ƙara tashi, dan ta tabbatar AA baya faɗar magana bai cikata ba, tun ma kan yakai haka. Ta kasa samun nutsuwa, ta kasa tsaida zuciyarta waje guda. Ga Abideen har yanzu bai dawo ba tunda ya fita. Office ɗin nasu yanzu kam yay tsitt kowa damuwa shimfiɗe a fuskarsa. Sai dai fa kowa ya maida hankali akan aiki tuƙuru. Ganin fa saura mintuna biyar rashin nutsuwarta ya ƙaru. Kamar ance ta ɗago ta kalla ƙofa sai idonta akan AA ya wani kafe office ɗin nasu da kaifafan idanunsa. Ai bama tasan ta miƙe ba har Yaqub na ɗagowa shima ya kalleta. Key ɗin motar nan da wasu documents ta ɗauka tana faɗin, “Sorry Yaqub ina zuwa. Na manta CTO yace na kai masa documents ɗin nan tun ɗazun.” bata jira amsarsa ba ya fito. Dai-dai AA na gittawa da baƙonsa da alama ya nuna rakkiya ya masa, tsabar wulaƙanci yi yay kamar bai ganta ba, sai da ta ɗan kallesa taga ya mata wani salo da yatsu biyu ta baya yana saki wani ɗan iskan murmushi. Jitai wani ƙululu ya tokare mata maƙoshi. Amma babu yanda ta iya dole ta nufi elevator. Tana isowa AS ya bata umarnin ta shiga kawai. Harararsa tayi sannan ta wuce fuuuu ciki, tako bugo ƙofar har sai da AS ya ɗan zabura, dan harga ALLAH tsoro yaji saboda abin yazo masa a bazata..........✍️
🤣🤣 An dai ji kunya AS da tsoro.😂
09032345899
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_💞AJIYA A DUHU....💞_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
*_My TikTok account 👇_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram👇🏻_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_Arewabooks_*
Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30
*_WhatsApp channel_*
https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R
_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_
🅿️➖8️⃣5️⃣
______________
.........A nutsensa ya turo ƙofar ya shigo. Ya kuma maidata ya rufe sannan ya shiga takowa cikin office ɗin. Duk da ƙamshinsa da motsinsa bai sa ta motsa daga tsayen da take ba. Sai ma sake kumbura take yi taf har ya ƙaraso bayanta daf ya tsaya. Tsabar yanda ya fita tsaho har tsakkiyar kanta yana gani tsaf, gently ya ranƙwafo a bayan nata batare da jikinsa ya taɓata ba ko kaɗan, fuskarsa a saitin kunnenta yana busa mata numfashinsa saman dokin wuya cikin raɗa ya furta, “Ko sai na ƙarasar dake ɗin ne dai saman kujerar?”. A wani irin zabure Maanal tai gaba camak kamar wadda aka sarrafa da remote. Sai kawai hangota yay a saman kujerar. Murmushi ya saki da wani lumshe idanu sai kuma ya buɗe su yana miƙewa tsaye sosai ya shafo kwantaccen gashin sajensa zuwa wanda ya zagaye madaidaicin bakinsa. Maimakon yaje ya zauna a kujerarsa sai ya zauna visitor chair ɗin shima dake kallon wadda ta zauna. Basket ɗin saman desk ɗin nashi ya jawo, ya ciro ƙyawawan kulolin da aka shirya abinci. Tuni wani irin ƙamshi ya cika mata hanci, duk da shekaru sun shuɗa, ƙamshin girkin Oum bazai taɓa shuɗewa daga zuciyarta ba sam kamar yanda tasan shima kansa Ajwaad bazai taɓa manta na Ammienta ba. Dan haka ta fara satar kallon abincin. Sai da ya gama zubawa dai-dai cin mutum ɗaya sannan ya sake matsowa sosai da kujerar, sai dai duk da hakan sam jikinsu bai taɓa na juna ba akwai ɗan space. Abincin ya ɗebo a spoon ya kai bakinta. Ƙin buɗe bakin tayi, shiko ya wani zuba mata idanu. Hawaye ne suka fara taruwa a nata idanun, dan haka ta kauda kanta gefe a hankali tana mai haɗiye abinda ya tokare maƙoshinta. Shima idanun nasa ne suka kaɗa sosai, amma da yake namijin duniya ne sai ya saki ɗan murmushi irin na danne damuwar nan. Muryarsa da wani kalar sanyi da kulawa ya furta, “Karfa na cinye ki dawo kina min rigima”. Shuuuuu hawayen da take faman riƙewa suka ziraro daga idannunta tai murmushi, wasu abubuwa ne masu nauyi da suka shuɗe ke tsikarin zuciyarta, ƙirjinta ya mata nauyi matuƙa. Slowly ya kauda nasa kan shima daga kallonta, idanunsa sun sake masifar kaɗewa. Kusan minti ɗaya suna a haka kafin ya juyo, tissue dake saman desk ɗinsa ya zara biyu ya miƙa mata batare daya kalleta ba. Itama bata kallesan ba ta amsa tissue ɗin, hawayen ta share, tare da dunƙule tissue ɗin cikin hannunta taƙi zubarwa. “Ka kori Abideen ne?”. Ta faɗa batare data kallesa ba har yanzu. Shi kam juyowa yay ya sauke nauyayyun idanun nasa a kanta, sai kuma batare da ya bata amsa ba ya furta, “Ci abincin first”. “Ni bana jin yunwa.” “Na sani”. Ya bata amsa a taƙaice yana sake kai spoon ɗin bakinta. A hankali ta furta, “Bani zanci da kaina” tana kai hannu zata amsa spoon ɗin. Matsar da hannunsa yay kaɗan yana zuba idanunsa sosai cikin nata. Dole tai ƙasa da nata ta buɗe bakin kaɗan. Ƙaramar ajiyar zuciya sukayi a tare bayan ya zare spoon ɗin ita kuma ta fara tauna abincin a hankali... Lips ɗinta kawai dake motsi yake kallo, sai kuma ya ɗan murmusa kaɗan da faɗin, “Kin tuna ranar da kika fara girki, da irin abincin nan kika fara har na samu wannan ciwon?”. Yay maganar yana kallon gefen babban yatsar hannunsa na dama gab da wajen tafi. Itama hannun ta kalla, dai-dai wajen akwai madaidaicin tabo da akallo ɗaya zaka fahimci sanda aka jisa ba ƙaramin ciwo bane. “Oum!! Mamy!! Babban yaya ku kawo taimako hannun Besty ya gundile, ya gundile Abah kalla jini, wayyo Yaya F mun bani Besty ya zama mara hannu”. Ya faɗa yana kwaikwayon ƙaramar muryarta a wancan lokacin. Ai bama tasan ta sanya dariya ba. Taja mayafinta ta rufe fuskarta tana mai kifeta a desk ɗinsa komai na dawo mata kamar a yanzu yake faruwa. Shima dariyar yake sosai kamar ba shi ba. Ya ɗan girgiza kansa... “Kai yarinyar nan kinyi rashin ji wlhy. Kefa kika jimin ciwon, amma kika fini ihu da raki da cika kunnen mutane, ban isa kuma nace kece ba ki isheni da rigima da tsiwa. Ai naci girkinki na farko da wuya dai”. Batare data ɗago ba ta ce, “Amma ai kaine kasa na ji maka ciwon ko, ba kaine kace na yanka albasan a hannunka ba”. “Amma sai nace ki yanka ni? Anya bazan ramaba ma yanzu?”. Da sauri ta ɗago tana waro dukkan idanunta a kansa, fuskarta tuni ta ƙwaɓe da shagwaɓa ta ce, “Kuma sai ka rama ɗin?”. Shima kallon nata yake sosai cikin ido, sai kuma a hankali ya rissinar da nashi yana mai girgiza kai. “Zanyi tunani, idan da yiwuwar na yafe to”. Baki ta tura tare da masa harara, shi kuma ya taɓe nasa yana sake kawo mata abincin daya ɗibo a spoon saitin baki. Kafaɗa ta maƙe masa zatai magana ya ce, “Shiiii”. “To ka bani zanci da kaina”. “Kin tabbatar?”. Da sauri ta jinjina masa kai. Plate ɗin ya miƙa mata babu musu. Dan shima dai ya fahimci idan bai batan ba za'a iya samun matsala. A hankali ta cigaba da cin abincin, sai kuma ta sake ɗakko masa batun Abideen kodan kauda wannan kallon da yake mata. Idanun nasa kuwa ya janye, sai kuma ya a harɗe hannayensa a ƙirji da kwantar da jikinsa a kujerar sosai. Tsohon minti ɗaya kafin ya amsa mata da. “Miye damuwarki wai da zancensa? Ko shima saurayin naki ne? Dan naga ke samarin naki basu da adadin ƙirga”. “Eh mana, farin jini ai kenan, ko kuma kana kishi ne?”. “Mizai sa nayi kishi kuwa ina matsayin Yaya. Kidai sani sai na tantance wanda ya dace kozan bashi ke”. Har ƙarƙashin rai zancen nashi ya soki zuciyar Maanal. Amma sai ta dake itama cike da basarwa ta ce, “Ba damuwa Yayana, ai duk yanda kayi dai-dai ne. Amma dai inada zaɓina gaskiya, nasan kuma bazaka min auren dole ba, kaima shine zai kasance zaɓinka ai ko?”. Ta ƙare maganar cikin salon waro idanunta a kansa. Wani hayaƙin takaici ne ya turniƙe sa, dan har launin idanunsa sun sauya. Janyesu yay daga cikin nata batare daya amsa mata ba. Itako saita wani ɗage kafaɗu da ɗan taɓe baki. Ta ce, “Koda yake ai kasan zaɓin nawa ma. Kai dai kawai ka fara shiri nan da wata biyu zaka aurar da ƙanwarka in sha ALLAHU. Dan Rafeeq ya tabbatar min baya son ya wuce hakan, nima kuma hakan nafi so. Dama ya kawo min ƙararka daren jiya”. Da ace Maanal na kallon kalar mugun kallon da AA ke mata data tsuke bakinta, koda yake tana jinsa a jikinta. Amma ta daure ta danne abinta. Karo na farko yaja tsaki. Kallonsa tayi, amma shi kuma sai ba kallonta yake ba yanzu. Hasalima ya jawo laptop dake a saman desk ɗinne kamar a fusace. Gabanta ya tura, babu wasa a muryarsa ya furta, “Ki duba za'a tura miki saƙo a email ɗinki. Next week akwai tafiyar da kamfani zai yi har da ke ciki zuwa ƙasar Chaina. Tafiya ce ta kwana goma zuwa sati biyu. Wannan zanen nake son ki duba min shi kafin lokacin tafiyar, kije da laptop ɗin”. Da mamaki ta ce, “Kamar ya? Amma dai kasan baza'a barni a gida ba, dan mi zaku saka sunana?”. “Saboda dolene kiyi tafiyar”. Dangwarar da plate ɗin abincin hannunta tayi, tare da faɗin, “Idan na ajiye aikin gaba ɗaya fa?”. “Wannan ne baki isa ba ai”. “A matsayinka na wa?”. “Mi kike ci na baka na zuba”. “Ajwaad kana shigar min hanci da yawa fa”. “Ki fyatoni kawai ki huta mana”. Rasama abin cewa tayi dan takaici. Shi ko da yasan ya kaita maƙura idanu kawai ya zuba mata cike da kallon ƙurullar daya saka illahirin jinin jikinta yamutsawa. Zuciyarta ta shiga kumburowa kamar ƙwaɓaɓɓiyar fulawar burodi bugun ƙato. Da ƙyar ta danne rawar da muryarta ke neman yi cike da masifa ta ce, “Wai wannan wane irin haramtaccen kallo ne dan ALLAH. Nifa wlhy ana takura rayuwata, ana shiga haƙƙinna, idan ba'a son aikin nawa a koran a kamfanin mana.....” daga ƙarshe ma harshen nata ya harɗe ta yanda ita kanta bata ma fahimtar abinda take faɗa. Shi dai ya zuba mata ido kawai yana hukuntata da su. Sai da tayi mai isarta ta gama sannan ya tura mata goran ruwa gabanta. “Ai bance ina so ba”. Ta faɗa cike da tsiwa. “Hakane”. Ya bata amsa shima baki a taɓe. Sai kuma ya tsuke fuska kamar bashi ba ya gyara zamansa ƙafafu a harɗe hakama hannuwansa harɗe a ƙirjinsa. Babu alamar wasa a tattare da shi ya furta, “Kinyi abinda na saki?”. Harrarsa tayi, duk da yanayin nashi ya sa zuciyarta shiga tsoro, amma a dake ta ce, “Kai ka isa ne ka sakani abu nayi?”. “Oh haka kika ce?”. Baki ta murguɗa masa kawai. “Hummm ki cigaba da min wannan gatsinan zanyi maganinki soon. Na kuma baki nan da gobe ki dakatar da Rafeeq daga yaudarar da kike son masa. Idan ba hakaba zan baki mamaki”.. Murmushi tayi mai ciwo da zuba masa idannunta da suka kaɗa. “Oh mamaki? Ai ka daɗe da bani mamaki tun shaiɗan na baƙauyensa. Ajwaad ka daina wahalar da kanka da tunanin wannan abubuwan da kakeyi zaisa na ji tsoronka. Kasa a ranka ni Maanal matar Rafeeq ce in sha ALLAHU. Ina raga maka ne saboda Oum da Abah da Mamy, amma wlhy idan ka cigaba da shiga sabgata zaka sha mamaki na”. Daga haka ta miƙe tana ajiye masa key ɗinsa tai ƙoƙarin wucewarta. Amma sai ya saka mata ƙafa babu shiri ta koma cikin kujerar daɓar ta sake zama. Cike da isa ya ƙara jawo tashi kujerar gabanta ya wani tattare ko'ina ta yanda ko space ɗin fitar numfashi mai ƙarfi bai rage mata ba. Idanunsa da suka juye gaba ɗaya ya sauke a cikin nata, ya kuma hanata janyewa duk da ƙoƙarin hakan da take yi. Sai kawai taji kamar ta saki kuka ta huta. Wani ɗan iskan murmushi ya sakar mata, batare da ya sake cemata komai ba ya kamo hannunta ya ɗaura mata ƙaramar shopping bag mai tambarin apple a jiki, ya sake ɗakko key ɗin motar nan ya saka mata shima, ya ɗauka laptop ɗin itama ya ajiye a saman ƙafarta. Har lokacin idanun nasa a cikin nata yaja kujerar baya ya miƙe abinsa cike da takunsa na isa ya zagaya ya koma kujerar zamansa, desk ɗin ya dafe da duka hannayensa biyu ya ranƙwafo, duk da ba kusa suke da juna ba sai da taji wajen ya sake mata nauyi da matsatsi. “Fatan nasara”. Ya faɗa a hankali sannan ya kai zaune a kujerar ya hau ayyukansa. Tsuru kawai tai tana kallonsa na tsawon lokaci. Shiko ya cigaba da aikinsa kamar ma ya manta da ita, dan kalamanta wani mugun saka zuciyarsa tafasa suke ainun. Itama kasa cewa komai tayi, sai kawai ta miƙe tana mai ajiye masa key ɗin motar ta wuce abinta da shopping bag ɗin da laptop ɗin kawai. Dan wadda ya bata ranar ce ta kuma fahimci wayace. Tana buƙatar wayar ne a yanzu dan har sim cards ɗin suna a hannunsa dama, bata sani ba kuma ko ya haɗa mata da su. Sai da ta fice ta maida ƙofar ta rufe sannan ya ɗago a hankali ya sauke idanunsa akan key ɗin. Janyewa yay ya maida kan ƙofar kamar yana hangota har yanzu a wajen. Sai kuma ya furzar da iska yana mai ajiye document ɗin hannunsa da ɗan ƙarfi ya tura duk hannunsa biyu cikin sumar kansa ya shiga yamutsata, tare da kwantar da bayansa jikin kujerar yay sama da kan nasa yana furzar da zazzafan huci. Tsohon lokaci ya ɗauka a haka da shima bai san adadi ba, kafin ya sake sauke numfashi mai nauyi ya cigaba da aikinsa...........✍️
_😂Jaraba, idan aka haɗu kamar abin arziƙi, amma daga ƙarshe da wahala a rabu lafiya sai da bala'i🤣, wai mike damun gayun nan ne😆😆? Maga dai yanda za'a ƙare da batun zuwa chaina😌🥱. 🏃🏃_
09032345899
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_💞AJIYA A DUHU....💞_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
*_My TikTok account 👇_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram👇🏻_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_Arewabooks_*
Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30
*_WhatsApp channel_*
https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R
_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_
🅿️➖8️⃣6️⃣
______________
.........A Kaduna kam shirin biki ake sosai, dan a yau laraba akai gagarumin kamun amarya daya zaga ko'ina na media. Waje suka kama yasha ado da kwalliya kamar yanda itama amarya tasha ado. Dj ya warware sauti ƙawayen amarya da amarya da ƙawayen uwar amarya da ƙannen ango har ma da gayyar soɗi suka cashe gwargwadon iko. Amarya tasha turare har yana hawar mata kai. Ango dai baima ƙaraso ba sai bayan sallar isha'i. Shima a media ya tsinta shagalin kamun. Tsaki kawai yay ya dinga wuce videos ɗin dan shi a nasa tsarin baya buƙatar duk waɗan nan bidi'oin. Amma yasan bai isa cewa baza ai ba Mammah ta hargitsa masa hazo. Yau ɗin ma itace ta kafa masa dogon gargaɗi akan ya dawo Kaduna domin halartar events ɗin da za'ayi. Duk da dama dai yayi niyyar hakan shima bisa umarnin Daddy. Yaso fara tsayawa Abuja wajen Maanal amma sai aka samu akasi, dole ya haƙura ya wuce akan zuwa gobe zai koma Abujan, dan baya tunanin Maanal zata zo wajen bikin nan. Shima a karan kansa baya son ma tazo ɗin... Ammie da Nene da surukan Nene da Sakina sunje wajen kamun, duk da da dai Ammie batayi niyyar zuwan ba Hajiya Majdiya tace suje. Dan zuwa yanzu kam sun ƙulle da Ammie sosai bisa umarnin Oum da tuni ta zayyanema ƙanwar tata komai dake tsakaninsu da su Maanal. Su Ammie sun sha habaici, dan har Hajiya Yaya ma taje wajen kamun. Amma kamar yanda Ammien ta saba sai ta nuna bama tasan suna yi ba. Su Hajiya Basariyya dai anata safa da marwa su amarori. Ta shige taro tayi damal-damal dan ta san sirrin komai da takun komai, gefe kuma ta gogama Ammie kashin kaji da bata haushi. Sai dai kuma hakan bai samu ba, dan ta firgita da ganin su Ammie a taron kamun batare da tayi tunanin zatazo ɗin ba. Duk sai jikinta yay sanyi. Itako Ammie bama ta nuna ta san da zamanta a wajen ba. Sai da tsabar munafuncin Hajiya Basariyyan ya sata zuwa ta wani ranƙwafo tanama Ammie magana a cikin kunne. Ba wata magana bace mai ma'ana, amma mutane sai su ɗauka wani sirrin ne akeyi irin na iyayen biki. Nan ko tambayarta tai kawai wai mi za'a kawo ma baƙinta. Murmushi Ammie tayi tana sake jinjina makirci irin na Hajiya Basariyya, itama sai kawai ta amsa mata da komai ma a basu zasu ci. Daga haka ta maida hankalinta ga wata ƴar uwar Daddy da yaranta da suka ƙaraso wajen, dan suna ɗasawa sosai da Ammien....
______★
A media su Manaal sukai kallon kamun, sai kuma ga Amal ta kira Shahidah. Nan suka ɓige da zancen suna dariya. Dan sun fahimci duk anayi ne wai a basu haushi. Ita Maanal ma tunda suka fara wannan zancen sai kawai tai shiru ta maida hankalinta ga saita wayarta. Dan tunda ta dawo ta cireta a kwali ta sanyata a caji. Ganin ta cika ta ciro ta dan ta saka sim card ɗinta, ɗayan kuma ta ajiye akan gobe in sha ALLAHU zata sayo wata wayar dan riƙe waya biyu ya kamata kenan. Shiyyasa bata taɓa damuwa da wannan iPhones ɗin banzar ba ita kam. Bayan sun gama wayar ma tashi tai ta nufi ɗaki domin kwanciya....
_____________★