Kenza eBookz

Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul - Chapter 80

Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul - Chapter 80

Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul Chapter 80: Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul Chapter 80. .........Maimakon sake tambayarta…

3,966 words

.........Maimakon sake tambayarta wani sai kawai ya kaɗa kai dan ya fahimci wadda yake hasashen ce. Kansa tsaye ya furta, “Kin san wani ɓoyayyen abu daya shafeta ne dama kafin yau?”. Shiru Maanal tai ta kasa magana. Tsohon minti biyu bata da niyyar cewa komai. RK da yay mata kallo ɗaya ya ɗauke kansa ya ce, “Tsahon wane lokaci kika san ainahin ta?”. Idanu ta ɗago ta kallesa, ganin babu alamar wani wasa a tare da shi a Uncle ɗinsa yake yasata maida kanta ta duƙar, hannunta na wasa da ɗayan hannun ta ce, “Uncle miye amfanin tone-tonen? Taci darajar wanda ya ajiyeta da waɗan da take tada jijiyar wuyan a kansu. Ni harga ALLAH bana buƙatar wani ka-ce-na-ce a kanta. Matsalata da damuwata ɗaya ce ta yanda zan bama Oum garkuwa da ga sharri da tuggunta ita da ahalinta. Amma dama kai kasan ita wacece tuni?”. “Tabbas tun kusan shekara biyu da suka wuce wasu abubuwanta suka fara sakani a shakka. Sai dai akan auren ku na samu tabbacin da nake buƙata a baya gaba ɗaya hasashe ne kawai da zargi”. “Saboda haka ka aikata abinda ya faru?”. “Hakan da nai shine ya kamata. Maanal ki bar wani pretending, kina sonshi kamar yanda yake sonki. Soyayyar da AA ke miki bata wasan yara bace, dan na jima ban taɓa ganin soyayya irin wannan ba. Kuma har abada bazaki taɓa samun wanda zai soki kamar Ajwaad ba....” Ɗagowa tai ta kallesa. Ɗauke kansa yay daga saitin su, ya haɗiye wani abu mai nauyi a cikin maƙoshinsa, yana kuma addu'ar UBANGIJI ya nisantashi da sheɗanin dake kissima masa shi a zuciya. Dan yayima ALLAH alƙawarin har abada bazai sake kallon Maanal da wata siffa ba bayan ta matar ɗan ɗan uwansa. Jinjina mata kai yayi da cigaba da faɗin, “Yes da gaske nake Maanal bazaki samu ba indai a ɓangaren soyayya ce irin ta namiji da mace dake a buri da bigiren zama ma'aurata. Kema kuma kin san haka, idan ma baki sani ba duk randa aka bashi ke zai tabbatar miki nayi imanin hakan. Dan tun farko ƙuruciya dama kece kike kallon tarayyarku matsayin abokai kawai wanda suka shaƙu, amma ga Ajwaad sam ba haka bane, tun asali tun fari sonki yake. Domin tabbatarwa kije da wannan ki karanta, karki bari ya gani dan bai san na ɗauka ba nima shiyyasa na naɗe bayan book ɗin da wannan takardan, zuwa anjima kibama Najma ta kawo min”. Hannunta na ɗan rawa ta amsa, ƙaramin jotter ce an nannaɗe ta da farar takarda ta yanda ba'a ganin ainahin bangon. RK daya ɗauke kansa daga kallonta ya cigaba da faɗin, “Kince kina son bama aunty garkuwa, tofa ta hanya ɗaya ce jal zamu iya yin hakan, amma duk sauran da zaki hanga ko hasashe ba masu yiwuwa bane ba, dan koba komai zamu kalla darajar masu daraja a kanta.” Najma zatai magana dan ita duk sun rikitata RK yay mata alamar zipping, shirun kuwa tayi, tare da saka hannunta ta ma riƙe bakin. Maanal data fara jin nutsuwa da tattaunawar ta ce, “Wace hanya ce kenan?”. “Yafewa Ajwaad, yimasa afuwa daga laifinsa. Duk da nasan abune mai wahala kuma mai ciwon gaske, amma idan aka tuna alkairin baya sai a yafe wannan a kallesa a matsayin kuskure da ajizanci na ɗan adam da kuma jarabawa. Ke da kanki a diary din da kika bani babu inda Ajwaad ya taɓa ko gwada aikata abinda ya aikata a gareki koda da wasa, mizaisa baza muyi tunanin wannan daya faru akwai wani abu a ƙas ba musamman idan muka kalla shan zoɓo kamar daga shi komai ya fara....” Da wani irin mamaki Maanal ke kallon RK. Tace, “Zoɓo Uncle?”. Cigaba yay da faɗin, “Yes dole akwai wani abu a cikin wannan zoɓon da kuka sha, kuma koma minene Ajwaad ya sanshi daga baya ɓoyewa kawai yake yi. Akwai dalilin kuma da yasa ya zaɓi yin AJIYA A DUHU. A yanzu bayan haɗuwarku, zuwa yanzu da kuke ma'aurata ya taɓa tada miki waccan maganar?”. Kanta ta girgiza alamar a'a. “Ya taɓa baki haƙuri koda a wata siga ne balle nuna shi mai laifi ne babba a gareki?”. Nan ma ta girgiza kai. “To wannan ya isa ya zame miki hujja babba. Amma kuma na miki uziri, dan wancan abun ya faru kina da ƙarancin shekaru, shiyasa baki taɓa zama kinyi nazarin komai a kansa ba, kawai dai kinyi jiyyar shock da kika shiga, sannan rabuwarku ta haddasa miki ciwon zuciyar da kika sha fama, sai kuma jin zafin abinda ya farun dan dole ne hakan ga kowacce mace da irin haka zai faru da ita....” Da sauri nan ma ta kallesa. Ya ɗan ɗage kafaɗa ya ce, “Kar kiyi wani musu, shiyasa nace miki kina son AA kema har yanzu. Kin san kuwa ƙarfin da ciwon zuciyarki yayi Maanal? Kinfa je wani mataki ne da komai zai iya faruwa dake. Amma tunda Ajwaad ya dawo rayuwarki bayan farko-farko daya motsa ciwon ya ƙara motsa miki?”. Gaba ɗaya ji Maanal tai kunya ta lulluɓeta. RK daya fahimta ya cigaba da faɗin, “Duk da nasan an ɗoraki a magani mai ƙyau da inganci da ace baki sake haɗuwa da Ajwaad ba a tsakanin tasirinsa kaɗan ne kuma zai zama na ɗan lokaci ne. Amma da yake zuciyar ta samu abinda take so yanzu gashi komai normal ba. Bawai ke kaɗai ba shi kansa AA ɗin ya shiga makamancin halin da kike cikin ne, koma fiye da naki dan sai da ya shiga wani mugun depression fa a shekarun baya da kowa ya fara ɗauka brain ɗinsa ya taɓu ne ma, amma tunda yau akace kin zama mallakinsa kinga ya sake yin wani any cuta data shafi hakan? Bazaiyi ba saboda zukatan sun kasance a tare sun kuma samu abinda suke so. Dan haka ina roƙonki, ina kuma baki shawarar ɗaura ɗamarar bama mijinki haɗin kan zama lafiya, ki kuma ajiye komai gefe ki bashi irin soyayyar da yake so. Wannan shine kawai dafin da zaita cizon matar can ya kuma faranta ran Aunty Dan a duniya aurenku ke da Ajwaad da haihuwar Fawzan ce kawai damuwar dana san tana damunta. Na biyu auren Najma da Fawzan waɗan nan biyun zasusa ta samu cikar burinta na tabbatar”. A wani irin firgice Najma ta kalla RK. Ya harareta, sai tai ƙasa da kanta. Maanal da wani kalar farin ciki ya lulluɓe ta ce, “Uncle da gaske wai?”. Ƴar dariya RK yayi da faɗin, “Da gaske kuwa. Munafukai suna ɓoyewa ne kawai. Amma ni ina son komai ya fito fili zuwa bayan salla a haɗa da bikinku ayi nasu. To in dai mukai ma matar can wannan dukan zai gigitata ne bana wasa ba. Hakan ne zai bama Aunty garkuwa daga tarkon da take son ɗana mata, dan burinta ai yanzu ta yanda zata ƙwace su Ajwaad ne a hannun Auntyn, bayan kuma ita da hannunta ta bata, tasan kuma aikata hakan zai iya kai rayuwar Aunty ƙarshe ta mutu ta bar mata mijin da ƴaƴan shiyyasa, babu kuma ta hanyar da zata iya hakan sai ta aura musu matan da take so, su kasance kuma daga ɓangarenta yanda ko Aunty ta rasa ranta taci nasara akan yaran suma kansu ta yanda basu isa bijire mata ba ta kowace fuska, ƙaryarta kuma tasha ƙarya, tunda tai wannan ƙyautar har gaban abada bazata koma a hannunta ba wlhy, kuma in sha ALLAHU Aunty da Yaya da yaran nan uku suna tare da juna sai dai ita ta fita a cikinsu”. Cike da farin ciki Maanal ta ce, “In sha ALLAHU Uncle, ai zata sha mamaki dan wannan faɗan mu da ita ne Oum na barci abintama za'ayi sa”. Dariya yayi, tare da faɗin, “Wato tana barci?”. “Sosai ma kuwa. Ai yanda matar nan take ta yaƙar Oum ita kuma bama tasan tana yi ba ai AJIYA A DUHU kenan, babu faɗan daya kai wannan baƙin ciki, kaita zama cikin baƙin ciki da takaici mutum da shirya masa tuggu da mugunta shi kuma baima san kanayi ba kuma yana zagaye da farin cikin da baka ƙaunar ganinsa a ciki, ka kuma kasa cin nasara tako wace fuska wlhy AJIYA A DUHU kenan”. Dariya sukayi yanzu kam har Najma, sai kuma Maanal ta rungume Najma dake ɓoye fuska. Ta shiga jero addu'ar ALLAH ya tabbatar da alkairi ita da Yaya F. RK na amsa mata da Amin. Ɗari bisa ɗari Maanal ta gamsu da bayaninsa. Kuma ita harga ALLAH dama zuwa yanzu ta huce koba duka ba akan jin zafin AA. Kuma tama ranta alƙawarin zata bashi dukkan haɗin kai na kulawa da soyayya bayan tarewarta kodan farin cikin Oum ta kuma baƙantawa Mamy, dan wlhy wannan marin datai mata tayima ALLAH alƙawarin sai ta ramashi a zuciyar Mamy da salon ban mamaki akan AA.... RK ya katseta da faɗin. “Kasancewarku ku biyu Aunty zata samu garkuwa masu tare mata faɗan, dan na fahimci so take itama tai amfani da waɗan nan ƴan iskan yaran da take ta aurama su Ajwaad ɗin wajen tare mata faɗa. Kunga kuma sai ki zuba da su idan tai tsami a tsakanin ku da su sai mu tafi plan c. Abu na ƙarshe kuma Maanal dole ne ki dawo Maanal ɗinki ta asali ta baya, wato ƴar rikici, sarkin takalar faɗa, mai kuma tsiwa. Ki ajiye wannan sanyin da miskilancin, ki kuma ajiye wannan shiru-shirun da noƙe-noƙe, kinyi karatu, kin shiga cikin mutane masu mabanbanta halayya, na tabbata kina sane da komai miskilanci ne kawai ya sa kike nuna kamar baki san komai ba. To dan ALLAH ayi haƙuri a dawo kamar da dan wannan abun da muke gani ƙarami wlhy ba ƙarami bane ba. Babban yaƙi ne, kuma ba'akan komai zai kasance ba sai na kwatar Yaya (Abah) da su Ajwaad. To idan su suna shirin yaƙin hakan, mu zamu shirya na bama Aunty Garkuwa ne kamar yanda kika faɗa, hakan kuma bazai muku daɗi ba sai kun yi fito na fito da waɗan shegun su Nuratun”. Sosai sun gamsu da wannan bayani nashi, sai Maanal taji zuciyarta tai mata wani sakayau, duk wani ƙunci da nauyi ya tafi sai sauke ajiyar zuciya take. Sun sake tattaunawa sosai kafin shi ya fara tashi ya wuce, su kuma sai da suka tabbatar an tafi sallar azhar sannan suka fito a wajen dan yace baya buƙatar kowa ya fahimci komai.....

__________★

Sosai Nuratu ta fasa lips, goshinta kuwa yayi irin ƙullutun nan abin dariya. Yanda take kuka da rantsuwar sai ta kashe Maanal yau a gidan nan ya saka Saheeba kiran uwarta a waya. Dan Mamy gaba ɗaya ta kasa dawowa a hanyyacinta, kalaman Maanal da marin data ma Nuratun ne kawai ke mata kai-kawo a cikin idanu. Eh tasan Maanal dama tun tana mitsitsiyarta bata da kunya yarinyar, amma bata taɓa kawowa a ranta fitsararta zai iso gareta ba. Lallai tayi sake, matuƙar sakacin da har yarinyar nan ta zauna a gidan na wannan lokacin har ma da ciki. Gabanta ya faɗi tuna zancen ciki... Dai-dai nan Saheeba ta miƙa mata waya dan tunanin da tai nisa a ciki yasa bama tasan su Saheeban na waya da uwarsu ba........✍️

*_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_*

*09032345899*

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*

*_💞AJIYA A DUHU....💞_*

*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*

*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

*_My TikTok account 👇_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram👇🏻_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30

*_WhatsApp channel_*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R

_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_

*_BOOK 2_* 🅿️➖5️⃣6️⃣

______________

.........“Maman Saheeba ta ce, “Aunty miyasa kikai haka? Ni da kinyi shawara dani wlhy bazaki kira yarinyar nan har sashen ki ki wani mareta ba.” “Raina ne ya ɓaci Nana, babu kunya fa a gabana agaban kowa Ajwaad ya wani rungume yarinyar nan jikinsa na rawa, ya kuma ɗaga hannu ya mari Nuratu, Fadeel ya amshe kayan hannunta, yabi yarinyar nan da zagi shima. Haka ma Fawzan. Yanzu kodan ganin idona yaran nan bazasu raga ba. Su dukansu suka nuna goyon bayan ƴar iskar yarinyar nan......” “Na fahimceki, amma da kema kinyi pretending kawai a wuce wajen. Dan wannan faɗan ba naki bane na tsakanin su yaran ne ai. Yanzu kuwa abinda kuka kira yarinyar kukai mata kamar kin buɗe mata cikinki ne kai tsaye. Karki manta yarinyar nan idonta a buɗe yake, tunda kema shaida ce akan halinta na baya, dan yanzu ta koma wannan sum-sum ɗin bai kamata ki sakankance da yawa haka ba. Rainon Fateema da Ajwaad ce fa, sannan jinin Asiya ce. Dole fa ki dinga ƙoƙarin control ɗin fushinki Aunty idan ba haka ba zamuyi wahalar banza, dan in dai mutanen nan suka gane akwai wani abu a tare dake wlhy auren nan bazai yiwu ba na Nuratu da Ajwaad, balle kuma akai ga Fawzan, kuma na tabbatar bazasu cigaba da barin Fawzan a haka ba zasu nema masa matar aure, Ajwaad na auren yarinyar nan, mi kike tunani, ke da Saheeba kaɗai zaku iya wasan ne? Bayan sun rinjaye Ku? To dole fa ki cigaba da yin kamar yanda kike yi, shi wannan faɗan ki barma yaran suyi, suma kuma a yanzu karda su sake cemata komai su barta sai ta sakankance sannan dan wannan marin sai Nuratu ta rama shi. Haba Aunty kamar bake ba, ke da na sanki tamkar ƙuli-ƙuli babu mai iya gane gabanki balle baya. Karki bari abubuwa suyi miki yawa ki fara sakin layi dan ALLAH. Yarinyar nan kuma ki fita a sabgarta in ba hakaba zata zame mana ƊAN HAKKIN DAKA RAINA tunda bata da kunya sam, kota zame mana RAINA KAMA KAGA GAYYA”. Ajiyar zuciya mai nauyi Mamy ta sauke, cike da gamsuwa ta ce, “Hakane kuma Nana na fahimceki. Amma maganganun yarinyar nan sun min zafi, dan tabbas bada su Saheeba take ba dani take, amma lokaci ne, zan nuna mata uwarta ma da Fateemar da suke taƙama da ita basu kai ba balle ita haihuwar jiya.” “Karki wani damu lokacin cin ubanta na zuwa. Wannan cikin nata kuma na amso maganin zubar da shi amma sai zuwa bayan salla zai iso, dan so nake mu zubar da shi dai-dai sanda ake hidimar bikin Ajwaad da Nuratu”. “Miye ma'anar yin hakan? Ni gwara kawai ya ɓare yanzu dan idan na kalleta wani irin zafi nake ji a ƙirjina wlhy Nana”. “Karki wani damu ki kwantar da hankalinki Aunty, hakan da zamuyi nada ma'anoni masu yawan gaske. Ai gara cikin yay kwari ta yanda zataci azabar fitarsa, a kuma lokacin mu nuna tayi hakan ne dan kishi Ajwaad zai ƙara aure. Kai idan ma ta kama har Fateema sai tuggunmu ya shafa akan zubar da cikin nan”. Wani sassauci Mamy ta ɗan ji a ranta, ta sauke numfashi da faɗin, “Shike nan hakan ma yayi, ALLAH ya kaimu”....

_😂Wannan ciki dai da ake son a zubar kota ina aka samo shi. Koda yake AA ɗan baiwa ne maybe a mafarki ya lallaɓo🥱😜😆🏃._

________★

Wannan tattaunawa ta RK da su Maanal ta taka matuƙar rawar gani akan abubuwa da yawa. Duk da tako wane ɓangare kowa akwai abinda ya damesa. Aranar dai Mamy da su Nuratu basu je aiki sashen Oum ba. Nuratu kuwa tasha uban bori akan sai taje har sashen Oum ta daki Maanal. Da ƙyar Mamy da Saheeba suka lankwasata bayan an kira Hajiya Turai a waya itama ta sake yin nata. Sai da Oum taje har sashen Mamy ta bata haƙuri da lallashinta sannan tace ita fa ba wannan bane ya ɓata mata rai bata jin daɗi ne. Ita dai Oum ta sake bata haƙuri ta taho. Sai kuma hakan ya damu Mamy ɗin, dan da ciwo kaga kanata hauka akan mutum shi ko'a jikinsa, (kamar dai yanda Maaanal tace AJIYA A DUHU kenan😂) washe gari suka fito akaje tafsir tare aka kumayi girki tare. A ɓangaren Fawzan shima dai ransa danƙare yake da al'amarin Mamy dan abin sai ya zame masa biyu. Wanda tai masa, da wanda ya faru akan marin Nuratu da AA yayi. Shi ko babban Yaya iya na marin Nuratun ne kawai ya bashi mamakin. Sai kuma ya ɗauka kawai Mamyn ta fusata ne saboda Nuratu na jininta. A ɓangaren Mamy kam abin da ya tsaya mata a zuciya Abah ne. Dan daga wannan nasiha bai sake cemata komai ba, hatta borin kin zuwa aiki da tayi na kwana ɗaya da ƙin zuwa shan ruwa sashen Oum ko'a fuska bai nuna mata ba balle ya tanka. Sai hakan ya girgizata ya kuma tsaya mata a zuciya taketa hasashe-hasashe ta kasa gane komai. Gefe ga tsanar Maanal da maganganun data gayama su Saheeba yana ƙara yima Mamy ciwo bama su Saheeba ɗin kawai ba. Sun kuma rasa ta yanda zasu rama duk da sun ɗauki alwashi kala da iri Saheeban da Nuratu. Na ƙarshe AA, matuƙar ciwo abinda ya farun yay masa. Dan haka ma a jiya ya shirya tafiya Lagos ya bar musu gidan. Dan baya buƙatar yin wata magana da Mamy in ba hakaba ALLAH sai zuciya ta kwashe shi yama Nuratu dukan mutuwa ya kuma koreta a gidan duk da Oum ta masa faɗa da nasiha sosai a washe gari. Itama Maanal karanta jotter ɗin da RK ya bata ya sakata kuka sosai jikinta kuma yayi sanyi matuƙa, dan haka ta ɗauka ɗammarar gyara abubuwa da yawan gaske...

Kwanakin azumi sun cigaba da tirzawa, wasu na ibada wasu zukatansu cike da burikan sharri. A randa aka shiga goman ƙarshe AA ya dawo gidan, zuwa dare kuma ya sake barin gidan acewarsa ya shiga ittikafi. Bai yarda wata keɓantacciyar gaisuwa ta shiga tsakaninsa da Maanal ba itama kuma bata nuna ta damu ba a zahiri duk da hakan ya mata ba daɗi, dan yanzu so take su daidaita sosai. Ita kanta Oum bataji daɗin yanda AA yayi ba amma batace komai ba. Shi kuma a ganinsa hakan da yay zaifi alkairi dan a cikin wani irin matsananciyar buƙata yake shiyasa ya zaɓi duk hanyoyin hana keɓancewarsa da Maanal sam. A ɓangaren Abah da Uncle RK da su babban yaya kam suna ibada suna kuma shirya biki batare da sanin kowa ba. Yayinda suma dai ta ɓangaren Mamy bikin suke shiryawa acewarsu babu ɗaga ƙafa sati ɗaya da salla. A kwana a tashi babu wahala wajen UBANGIJI, azumi nata bankwana su Maanal nata ƙara dagewa a yin ibada. Duk da ita ma a farkon goman tai period, ALLAH dai ya taimaketa kwanansa uku ya tafi ta cigaba da azuminta. Tun azumi na goma sha biyar tela yazo ya gwada ƴan hutun su Oum bisa umarnin AA. Batare da kowa yaga kayan da za'a ɗinka ɗin ba kuma. Yau da azumi ke ashirin da bakwai ana saka ran salla nan da kwana biyu ko uku sai ga ɗinkuna sun iso kowa da sunansa. Zokaga murna da tsalle wajen yaran. Abinda ya ƙona ran Mamy babu Nuratu a ɗinki, duk da taga babu Maanal itama hakan bai dameta ba. Tako ƙara ƙullatar AA sosai a ranta, gashi dama ta fassara barin gidansa da wai yana haushi da ita ne. Bata san bawan ALLAH abinda ya damesa daban ba. A ranar shima Yaya Fawzan ya kwashe su da dare yin shopping na takalma da sauran tarkace. Harda Maanal da Oum akaje, nan ma baƙin ciki kamar zai kar Mamy. Duk da dai ta danne bata nuna ba a fili, harda kuma su Saheeba da Nuratu da Nibras. Kowa kuma ya zaɓo ra'ayinsa, Oum kuma ta zaɓo nata dana Mamy data ƙi binsu wai ita kawaici sai na Aba. Fawzan ya ɗauka musu shi da Baban yaya da AA dan Uncle RK ya fece Kano yace kansa bazai murfi ba ranar salla sabon amarcin shi da Nuwaira 🤣. Shi kuma babban yaya washe gari ya lodo uban cefane da kaji gyarru sai uban jan nama. Tuni sun hutar da Abah yin komai a gidan nan. Dan shi kansa bai san yaushe ne last da ya sai wani abu na abinci ko sutura ba koda ma kansa a gidan. Hatta da ƴan uwansa duk salla sai su babban yaya sun aika musu da kaji da cefane na abincin salla. Wannan sallar ma hakan ce ta faru, tuni nasu sun wuce Kano. Batare da sanin kowa ba kuma AA ya tura Kaduna da uban kaya ma Daddy kamar yanda suma su Babban yayan kanyi ga nasu surukan duk shekara... Tunfa a daren masu aiki suka iso, dan duk salla su Oum na ɗaukar masu tayasu aiki saboda abinci akeyi bana wasa ba kasancewar ana fita da wani wa bayin ALLAH, kuma a cikin azumin ma akwai inda ake dafa abinci a raba duk lokacin shan ruwa batare fa kowa yasan daga su bane. Bayan ɗanyan abinci da shi kansa AA ke rabawa duk shekara shi da sauran ƴan uwansa. Dan asusu garesu na tara kuɗaɗe domin hakan kawai sai shekara ake ciresu ai hidimar taimakon bayin ALLAH. Oum kuma kaɗai tasan suna yin hakan. Masu aiki sun kama aiki, Oum ta kaɗa ƴammatanta saloon da kitso. Mutuniyar taku dai nata daru, Oum tace babu fashi sai an mata. Itako aka fara wanke ma kan sannan akai kitso bamai yawan ba. Dan Oum tace a mata kaɗan tunda za'ai na tariya kwanan nan. Haka ma ƙunshi a yatsu kawai akai mata ja shike nan. Ta koma gefe yana sauke ajiyar zuciya ga haushin AA dama na cimata rai. Suma sauran duk an musu harda Oum, basu dawo gida ba sai la'asar, babu ɓata lokaci suka shiga haɗa abincin buɗa baki...........✍️

*_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_*

*09032345899*

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*

*_💞AJIYA A DUHU....💞_*

*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*

*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

*_My TikTok account 👇_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram👇🏻_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30

*_WhatsApp channel_*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R

_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_

*_BOOK 2_* 🅿️➖5️⃣7️⃣

______________

.......Alhamdullah ƙarfe biyar akace anga wata a saudia, yara suka fara murna da fatan ALLAH yasa a Nigeria ma a gani. Hakan kuwa akai, kafin ma tara sanarwa ya iso kunnen kowa daga Sarkin Musulmi cewar anga wata muma a Nigeria gobe salla. Ai fa tuni gida ya yamutse da murna. Zuwa tara sai ga AA ya dawo gida. Tunda ya shigo Maanal kallo ɗaya tai masa ta ɗauke kai, yanda ƙannensa suka gaishesa itama ta gaishesa ne ta basar. Shi dai kallonta kawai yake ta ƙasan ido, Oum tace mizai ci ya miƙe yana faɗin, “Komai ma na samu amma mara nauyi, bara naje na watsa ruwa Besty ta kai min can dan zata amshi saƙonta daga can, idan kinzo ina sama”. Ya faɗa maganar ta ƙarshe idonsa akan Maanal Cikin rashi damuwa Oum data san da saƙon tace to. Shima sai ya fice bayan ya ɗan kalla Maanal ɗin karaf kuwa yaga hararar da take masa. Da sauri ya janye idanun yay gaba yana cije lips. Umarni Oum ta bata nata tashi ta haɗa masa abincin. Badan taso hakan ba ta amsa da to tana miƙewa. Shi ko AA sashen Abah ya nufa, acan ya samu Mamy tare da shi, ƙin yarda yay su haɗa ko ido. Kansa a risine ya gaisheta bayan ya gaida Abah. Idon Abah ya sakata amsawa kamar babu komai a ranta, amma ta ciki na ciki. Bai wani jima ba yace ma Abah zai je ya watsa ruwa yayi aski yana jin gashi duk a jikinsa. Abah ya sanya masa albarka ya fito. Sai da ya kalla sashen Oum sannan ya wuce nashi sashen.

Readers Also Read