Kenza eBookz

Ajiya a duhu book 1&2 complete by billynabdul - Chapter 196

Ajiya a duhu book 1&2 complete by billynabdul - Chapter 196

Ajiya a duhu book 1&2 complete by billynabdul Chapter 196: Ajiya a duhu book 1&2 complete by billynabdul Chapter 196. 211

3,328 words

211

.......ALLAH sarki, sai ga Momyn Nibras na kuka da neman yafiyar Yaya Fawzan da AA. Suma su Abah ta basu haƙuri. Sannan ta juya wajen Oum ta neman yafiyarta. Ta ce, “Kamila ta gaya min abubuwa da dama a kanki shiyyasa na dinga miki rashin mutunci a baya. Duk da baki taɓa min komai ba ke na rashin dai-dai saima alkairi ga ɗiyata. Tabbas na yarda a yau duk wanda ALLAH ya bama kyakkyawar zuciya ya gama masa arziƙi, da ace Kamila ta nutsu ta zauna da ke da ƙyaƙyƙyawar zuciya itama da taci ribar wannan zaman naku. Amma duk da haka yanzun ma taci riba, dan badan tarbiyyarki da tsayawa akan ƴaƴan data baki saboda wani ƙudirinta ba wlhy da babu na mora a cikinsu. Da yanzu ba wannan maganar ake ba, da bata kallesu a yanzu cikin kamala da mutuntaka ba. Amma sai ALLAH ya dubi zuciyarki, ya dubi zuciyar mahaifinsu, ya jarabceta da baki su halak malak. Kinyi haƙuri da jarabawar rashin haihuwa ALLAH ya sakakanka miki da ƴaƴa masu irin zuciyarki data mijinki. Shekara da shekaru tanata shirya miki mugunta baki taɓa faɗawa ba sai itace ta kasance a cikin ramin data haƙa domin ke. Ta rasa mijin da take burin mallaka ta rabaki da shi, ta rasa dukiyar data so tarawa ta karfin tsiya-tsiya harda yunkurin kisan miji, ta rasa yayan data bada dan samun zuciyar miji. Ta aura masa wanda take so dan ta mallaki ƴaƴan cikin sauƙi. Ta rabasu da waɗanda suke so saboda suna da alaƙa da ke. Yau kuma ga wanda take so ɗin sun tabbatar mata da halaye irin nata data koyar dasu, ke kuma ga mijin a hannunki, ƴaƴan a hannunki, sun auri wanda suke tare dake ɗin batare da tursasawa ba, Fateema miya rage miki banda kita godema UBANGIJI. Tabbas kece kikaga AJIYA A HASKE maimakon AJIYA A DUHU. Yanda ALLAH ya baki duniya ina roƙonsa ya azurtaki da samun lahira mai albarka da rahama. Ki gafarceni akan kuskurena.” Oum dake murmushi ta ce, “Na yafe miki Hajiya Shamsiyya, ALLAH ya yafe mana baki ɗaya. Ba ma ke ba duk wanda ya taɓa min kuskure a zahiri ko baɗini wlhy na yafe masa hatta da Junaid kansa”. Momyn Nibras ta dubi Mamy da kanta ke ƙasa ta ce, “You see, Kamila kinfa ji, ki duba fa Kamila. Dan ALLAH ina roƙonki kema ki sauƙaƙama zuciyarki, ki sauƙaƙama rayuwarki tunda kin dai gane zuwa yanzu wanda ALLAH yace shine-shine. Yaranki na sonki, mijinki ya taka rawar gani a kanki, abokiyar zamanki na miki kallon ƴar uwa ba kishiya ba, dangin mijinki sun taka rawar gani a kanki. Bakici riba ko ɗaya daga abinda kika aikata ba sai faɗuwa ma da ƙasƙanta da ƙarewa da ciwuka kala-kala gasu nan. Miya rage kuma banda jiran sakamakon kabari dana makoma. Karki zama wadda bata da rabo, ki kalla ni'imar da UBANGIJI yay miki da talala na baki lokacin kaiwa zuwa yanzu ki gyara abinda ya rage a cikin rayuwar ki. Da farko naji bazan yafe miki ba saboda kin taka rawa wajen fanɗarar min da yarinya kema duk da nawa laifin, amma kece kika dinga nuna musu suyi komai ba komai a gidan nan har take jin zata iya yin komai ɗin. Amma kalaman Hajiya Fateema na yafiya sun sanyaya min jikina wlhy, yanda bata duba muguntar da kukai mata ba tace ta yafe miki nima na yafe miki. ALLAH ya ganar dake gaskiya ki saduda kafin komai ya ƙarasa ƙarewa. Alhaji Aliyu kaima dan ALLAH ka gafarcemu kai da yaranka. Ku kuma gafarci Nibras abisa ɓarnar data tafka da wadda taso tafkawa. Abu na ƙarshe dazan faɗa itama Saheeba bata da amfanin zama a tare da ku, dan sai kun kakkaɓe su gaba ɗaya a cikin zuri'arku sannan zaku zauna lafiya. Domin kuwa akwai hirarsu da naji randa na dawo da Nibras gidan nan da kuma ana gobe salla ita Nibras taji wani abu itama.” Babu wanda bai ƙara nutsuwa yana kallon ta da mamaki ba. Hatta Mamy sai da ta ɗago tana kallonta fuska share-share da hawaye. Ta cigaba da faɗin, “Nibras taji Saheeba na sanarma ƴar uwarta bazataje idi ba dan tana son aiwatar da aikin da mahaifiyarsu ta turo musu akan Maanal. Suna son su fara salwantar da cikinta sannan su koma kan sauran suma. Dan ita kaɗai zata haihuwa a gidan nan sai Nuratu idan ta shigo kamar yanda mahaifiyarsu ta tabbatar musu ta kuma yi musu alƙawari. Na mata faɗa sosai akan miyasa bata gaya muku ba, sai tace ai tayi niyyar sai kun dawo idi ne kuma sai ta haɗu damu a wajen idin ta bimu, a lokacin da ta gama gaya min na kaɗota dan muzo mu sanar daku muka samu abinda ya faru ya faru na kidnapping ɗinku da akayi. To abinda ban sani ba a yanzu dai shine, miya faru ita ta rasa nata cikin harda cire mahaifa. Manaal ɗin bataci maganin bane ko yaya akai al'amarin ya juya haka?. Wanda naji kuwa Nuratu ce ke waya da bansan waye ba, tana tabbatarwa da alwashin sai ta sakama Kamila cutar ƙanjamau tunda a jikin ɗanta ta samu itama sai ta amshi rabonta, yanda suka rasa Hajiya Turai uwar ruƙonta a dalilin ɗan Kamila, ita kuma ta samu HIV a jikin ɗan Kamila, mahaifiyarsu ta rasa ranta a hannun ɗan Kamila, suka rasa Anum a dalilin dai ɗan Kamila itama dole ƴaƴanta su rasata. Naso yi mata magana na kwaɓi kaina gaskiya, musamman dana ga itama abinda Kamilar ta aikata na son kasheka da tai. Sai naga babu amfani ko nama faɗa babu mai saurarena. To ban sani ba ta aikata, bata aikata ba ALLAHU A'A LAM. Sai kuyi gwaji dan ku tabbatar. Ina sake neman gafarar ku ALLAH ya bamu alkairinsa”. Tsabar tashin hankali Mamy rikitiwa tayi ƙasa. Su kansu su Abah al'amarin ya girgiza su. Su Momyn Nibras na wucewa AA ya tabbatar musu da Mamy nada HIV, ya labarta musu dukkan tattaunawar da yayi da RK, dan haka a take akai kiran RK a waya dan shi yana asibiti. Haka yazo da sakamakon kuwa kowa ya gani. Mamy sai kuka take. Duk da haka Abbu yace suma su Oum sai anyi musu gwajin. Haka aka kwashesu zuwa asibiti har su Saheeba da basu san mike faruwa ba tubda bada su akai zaman ba. Kai su farin ciki ma suke da abinda ya faru a gidan ko yake faruwa. Har addu'a suke ALLAH yasa Maanal ta mutu, dan sun san dai na Nibras kuma ta ƙare tunda harda batun saki biyu. Sun kuma san yanda su Yaya Fawzan ke son junansu bazai taɓa maida Nibras ba. Kaf zuri'ar Aliyu Darma idan ka cire Naufal dake Saudia sai da akaima gwajin HIV har su Inte masu aiki da su maigadi, su Bola kaf su Uwangale dama bata jima a gidan ba. Babu jimawa aka fidda results dan awa ɗaya tak akayi. Gida suka tattaro kaf suka dawo dan bama bari ake kowa na shiga wajen Maanal ba sai idan za'a bama yara abincinsu Oum da Ammie ke shiga kawai, sai AA time to time dake goge mata jiki. Dole kuma akai kiran Baba Sardauna da Baba a video call dan babu abinda akeyi bada yawansu ba a family ɗin. Suna kallon kowa suna kallon komai Abbu ya fara buɗe results ɗin ɗaya bayan ɗaya. Dana masu aiki aka fara, kaf ɗinsu babu mai HIV a ciki. Kowa aka bashi result ɗinsa ya fita da farin ciki. Sai na Abah, shima normal, Oum, itama dar, Babban Yaya, shima dar, Yaya Fawzan, Alhamdullah, AA, shima dar. Maanal, Ameerah, Saheeba, Najmah babu mai ita. Nuratu, Mamy sune masu ita. Nuratu nata kuka dan bata taɓa sanin haka zata kasance ba sai a asibiti da taga za'a ɗiba jininta ta rikice. Amma AA yay mata buyagin data nutsu, taso ta gudu tun daga asibitin aka saka mata ido, dan babu yanda ta iya har akazo gida. Mamy dake kuka tana zagin Nuratu ta shaƙure ta. Da ƙyar aka kwaci Nuratu a hannun Mamy. Aunty kanta kuka take kamar ranta zai fita. Saboda yanda makomar zuri'arsu ta ƙare. Ta kuma tabbatar tun farko tun fari komai ya faru ne daga kuskuren mahaifiyarsu. Abah da gaba ɗaya komai ya kwance masa ya fice masa a rai yace, “ALLAH ya ƙyauta, shi batun son zubarma Maanal ciki fa Saheeba yaya akai abin ya koma kanku?”. Saheeba dake kuka ta kasa magana. Sai da Babban yaya yay mata tsawa sannan ta ce, “Wlhy ban sani ba Abah, na dai san tabbas na saka mata magani kuma taci abincin amma ban san tayaya al'amarin ya juye a kaina ba. Ban kuma taɓa tunanin reshene ya juye da mujiya ba sai yau ɗin nan?”. A hankali Ameerah tace, “Bazaki sani ba, domin kuwa ni ce nan na maida komai a kanki”. Babu wanda bai kalla Ameerah ba da sauri..........✍️212

........Babu ko ɗar Ameerah ta cigaba da faɗin, “Tun washe garin gama bikinmu naji wayar da Hajiya Turai tayi da wanda ban sani ba, sai daga baya na fahimci Sille ne. Daga nan na sanya muku ido da kowane motsinku. Daren salla kamar yanda Momyn Nibras taji abinda kuke faɗa nima naji, dan haka na kira Inte na roƙeta zatai min wani abu amana. Tace min zatayi. Na sake jaddada mata tace wlhy zatayi in dai ba abinda zai cutar da wani a gidan bane ba. Ban ɓoye mata ba nace duk abinda Saheeba zatayi ta saka mata ido idan mun tafi massallaci. Tace min to. Muna a massallaci ta kirani ta sanar min taga tana zuba magani a abincin da Maanal tace a dafa mata. Nace duka ta ɓata? Tace eh. Nace to su sake mata wani. Tace min to. Bayan mun dawo massallaci nacema Inte ta zubama Saheeba wanda ta zubama maganin a gabanta. Haka kuwa akayi, na tabbatar kuma Saheeba taci abincin ne dan hankalinta nakan ganin Maanal taci batare data fahimci ma irin wanda Maanal ɗin tace a dafa mata bane itama. ALLAH kuma ya ƙaddara akanta al'amarin zai koma ba Maanal ɗin zai sama kamar yanda suka shirya ba. Amma wlhy ni ban san munin maganin ya kai har yanda yay mata illa ba” Sosai Babban Yaya yayi murmushi, babu wani kauce-kauce ya ce, “ALLAH yay miki albarka Ameerah. Ke kuma azzaluma kinga sakamakonki right.” yay maganar yana kallon Saheeba dake kuka kamar ranta zai fita. Cikin ɗacin murya ya cigaba da faɗin, “Kuka baki fara ba ai, sai yanzu ne zakiyi shi daga ke har wannan azzalumar ƙanwar taki, kunga dai yanda uwar taku ta ƙare kanta fal haƙƙin mutane, ya rage naku kuma ku dawo hankalinku ko kuyi irin mutuwarta koma wadda ta fita. Dan basai mutum ya wulaƙanta a duniya bane ake gane ya shiga uku, tafiyarsa lahira da hakkin mutane shine babban shiga uku. Kunyi abinda kuke so, UBANGIJI kuma ya nuna muku yanda ya tsara. Nayi nadamar haɗa zuri'a dake, kai Alhmdllh da Anum ma taru, inama Naufal ɗin ya bita na tabbatar banda sauran alaƙa dake jaka jahila kawai..” Riƙe Hannunsa Yaya Fawzan yayi cike da lallashi, dan muryarsa ta farayin sama alamar fusata, kuma tabbas idan yakai maƙura sai Saheeba ta ɗanɗana irin abinda Nibras ta ɗan ɗana a hannun AA. Aunty dake share hawaye tace, “Saheeba kun cucemu ku da Kamila, dama wannan abun ne Nana ke son faɗama su Fadeel? Fadeel halan baku duba video ɗin dana baku ba”. Kai tsaye Babban Yaya yace, “Aunty bama buƙatar dubawa, bama buƙatar jin komai daga gare ta. Kiyi haƙuri, amma wlhy na tsani azzaluman cikinku. Ita tana son salwantar da jininmu, mahaifiyarmu na son kashe mana mahaifi. Ɗanta na son kashe mu. Saurayinta na son kashe mana Oum. Wannan wace irin rayuwa ce dan ALLAH, wai minene a duniyar nan da har idanu da zukata ke rufewa wajen aikata zalunci. Yanzu da kenan so sukai su kashe abinda ke cikin Maanal, su lalata mata mahaifa kamar yanda akama Oum? Wane irin zalunci ne wannan da bushewar zuciya dan ALLAH. Mata, mata da suka san ciwon yan uwansu mata, cikin ne fa a jikinta, shekaru ta ɗauka tana haukan neman sake samunsa amma har ake shirya sharri a lalata ma wata nata daya kasance na farko haba-haba idan naso zuri'arku na zalunci kaina ai..” kawai ya tashi ya ɗauke Saheeba da maruka, itama Nuratu ta samu rabonta. Aunty suka ruƙunƙume suna kuka da Mamy, sai da Oum ta tashi ta kama hannun Babban Yaya dake huci. Da ƙyar aka samu falon ya lafa. Baba Sardauna dake ta video call yay gyaran murya, duk hankalinsu suka maida a kansa. Cikin son danne ɓacin ransa ya ce, “Tone-tonen ya isa haka. Sannan batun cigaba da zama da su a gidan nan gaskiya bazai yiwu ba kamar yanda Fateema da Maanal suka roƙa. Dan nakai wata gaɓa da a yanzu ko canjawa sukai suka koma aikata alkairi zuciyata bazata nutsu ba zanta kallonsu ne da zargin zasu sake cutar min da zuri'ata ta wata hanyar kuma. Kamila bazamu taɓa wulaƙantaki ko tozarta ki ba saboda darajar waɗan nan yaran uku da kika haifa mana, duk da da hannunki kika ɗauka kika bama Fateema tuwo dai sunansa tuwo ba'a canja masa suna. Kece dai uwarsu ta haihuwa kuma kina da hakki a kansu suma suna da hakki a kanki. Dan haka bazamu rabaki da suba, suma bazamu rabasu da ke ba. Aliyu ya sanar mana ya sakeki tun bayan rikicin farko daya zaƙulo Dr Tofa ya masa bayani akan abinda ya faru game da zancen fyaɗen da kika saka aima Maanal. Ya tabbatar kece kika ce ace an mata fyaɗe saboda baki san Ajwaad zai amsa shine yayi ba a gabanmu. To wannan ya riga ya faru ya wuce ina sha ALLAHU, amma tun a lokacin ya tabbatar mana bazai iya cigaba da zama dake ba dama zaman haƙuri kukeyi da yima Fateema kawaici. Dan haka ya bamu takardar sakinki har biyu, bayan nan kuma kika sake tafka wannan kuskure na son kashe shi, duk da harga ALLAH munyi shirin gyara komai batare da kin ma sani ba da sauran igiya ɗayan data rage tsakaninku. Amma batun kisa daya shigo ciki yasa muka fahimci babu amfanin yin hakan. Ga shi itama ƴar ƴar uwarki ta sake tafka wata kwamacalar, kuma wlhy ta godema ALLAH abinda ta ƙudira bai faru ba, dan da ace ta samu nasarar cutama Maanal ALLAH sai na shiga kotu da ita. Amma tunda ALLAH ya kiyaye hakan shawara ɗaya zan bama Fadeel ya saketa shima. Daga ƙarshe akwai gida anan Kano na mallaka muku shi ƙyauta ke da su Ku dawo kucigaba da rayuwa a ciki ku barmin zuri'ata ta huta haka nan. Ina son su kasance happy family ya Isa haka ai an wajigu”. Kuka sosai Mamy take tana kallon Abah, ashe ya daɗe da sarkinta shiyyasa ya daina saurarenta, innalillahi wa-inna ilaihiraji'un, shike nan abinda tayi fata ga Fateema ya tabbata a kanta. Ta rasa komai, komai da komai ta rasa ita Kamila ta shiga uku ta lalace. Babu wanda ma yasan tanayi, kowa kuma ya gamsu da hukuncin Baba Sardauna. Oum ce taso yin magana Baba Umar yace mata “Kull babu neman alfarma, abinda Yaya ya yanke ya zartu”. ALLAH sarki su AA hakan bai musu daɗi ba amma bazasu iya magana ba tunda sun san Mamy ta riga tayi kuskuren da ahalin Darma bazasu sake aminta da ita ko kallonta da daraja ba. Suma da ta haifa suke jin zafin yanda taso kashe musu mahaifi balle su dake mata kara. Damma su Baba Sardauna sun shiga sun fita ne aka kashe maganar kisan Abah a wajen hukuma suka saketa da yanzu ba wannan maganar ake ba ai. A take shima Babban Yaya ya bama Saheeba saki ukun ta. Babu kuma ɓata lokaci aka samo kamfanin masu kwashe kaya aka fara haɗa kayan su Mamy da su Saheeba dan Abah yayi alƙawarin bazasu sake kwanar masa cikin iyali ba. Har kayan Nibras ma ya saka a tattare komai. ALLAH sarki Oum kuka take sosai, dan wlhy har zuciyarta son Mamy take yi, sannan ita har yanzu bata kallon cutarwar Mamy alkairinta na bata ƴaƴan nan uku kawai take kallo da girmamawa. Abinka da kamfani kuma aiki bana mutumin ɗaya ba kafin azhar sun gama komai an lodesu a manyan motoci, masu wucewa Kano suka ɗauki hanya, na Nibras aka wuce gidansu da su. Su Mamy jirgi zasu bi dan shi Uncle Mahmud ya biya musu, Uwangale kuka take da rokon ita dai a barta nan gidan bazatabi su Mamy ba. Ita bazata iya rabuwa da wannan daula ta koma Kano ba. Amma babu wanda ya kulata. A mamakin kowa Mamy ma kuka take mai ban tausayi, sai dai bataima kowa magana ba. AA, Yaya Fawzan, Babban Yaya da kansu zasu mata rakkiya airport. Yaya Fawzan ya zauna mazaunin driver idanun nuna sun kaɗe sun tara ƙwalla. Babban Yaya na kusa da shi, AA da Mamy a baya da kansa ma ya sakata motar. Idanunsu sunyi jazur, kallo ɗaya zasu baka tausayi amma yaya zasuyi, Mamy itace ta jama kanta, duk da babu shaƙuwa a tsakaninsu da ita ganinta a kusa da su ma ai wani abu ne mai girma. Haka Yaya Fawzan yaja motar Oum na kuka sai da Abah ya rungumeta. Nuratu, Saheeba da Aunty sai Uwangale motarsa daban suma driver ya jasu.....

Motar shiru tunda suka ɗauki hanyar airport har suka iso. Yaya Fawzan ya samu waje yay parking. Basu fitoba kowa yayi shiru kusan minti biyu babban Yaya yay gyaran murya. Duk kallonsa sukayi har Mamy data sha kuka harta godema UBANGIJI. Muryarsa da rauni sosai ya ce, “Mamy bazamu ƙiki ba. Dan duk abinda kika zama ke mahaifiya ce, muna kuma sonki muna ƙaunarki duk da kin ɗaukemu tun muna ƙanana a zanen haihuwa kin bama Oum saboda biyan buƙatar kanki. Alhamdullahi Oum ta mana riƙo irin na uwa mahaifiya ba uwar riƙo matar uba ba. Muna alfahari da wannan kamar yanda muke alfahari da haihuwarmu da kikayi. Komai daya faru mun yarda mun karɓesa matsayin jarabawarmu kuma ƙaddararmu. Amma dan ALLAH muna roƙonki a karo na farko kije kiyi nazarin komai da ya faru. Tun daga aurenki da Abanmu har zuwa yau minene suka aikata miki na cutarwa? Wanne kikai musu ke na cutarwa?. Mu wanda kikai mana mun yafe miki shi kuma muna roƙon ki yafe mana wanda muma muka aikata miki ko ƴan uwana?”. A tare AA da Yaya Fawzan suka jinjina kawuna. Ya cigaba da faɗin, “Idan har kece mai laifi Mamy ki zauna ki nazartu da yanda ƙarshen yazo, ki daure ki shirya canja zuciyarki zuwa kyakkyawa kamar yanda matar can ta faɗa. Ba zamu so rayuwarki ta ƙare da hakkin kowa ba musamman iyayenmu Abah da Oum da suka kyautata rayuwar. Ki koma ga UBANGIJI Mamy shi mai gafara ne, kiyi tuba na gaskiya ALLAH zai yi alfahari dake. In sha ALLAHU zamu cigaba da sauke dukkan hakkinki dake a kammu. Zamu dinga zuwa dubaki a kai a kai, duk abinda kike buƙata ki gaya mana zamuyi miki shi in har baifi ƙarfinmu ba. Idan kun sauka in sha ALLAHU muma zuwa jibi yanda jikin Maanal ya kasance zamu biyo bayanku muga mazaunin naki. Ki riƙe a ranki muna sonki, muna kuma yi miki fatan shiriya, za kuma mu cigaba da roƙon ALLAH ya baki ikon neman gafarar duk wanda kika cutamawa”. Ya kai hannu ya ɗauke hawayen da suka cika masa idanunsa. Yaya Fawzan kam share-share suke zuba. Shima AA hawayen da suka ciko masa idon yasa yatsa ya ɗauke. Sannan ya kamo hannunta ya matse a cikin nashi, kafin a hankali ya kaishi wajen bakinsa ya sumbata. Daga haka ya buɗe motar ya fita. Suma su Babban Yaya duk suka fita. Haka suka kamata suka saka a wheelchair ɗin. Kamar yanda AA yay mata Babban Yaya da Yaya Fawzan ma haka sukazo suka kama hannunta duk suka sumbata. Sannan Aunty ta kama keken nata suka shige dan jirgin su zai tashi nan da mintuna..........✍️213

Readers Also Read