Kenza eBookz

Ajiya a duhu book 1&2 complete by billynabdul - Chapter 32

Ajiya a duhu book 1&2 complete by billynabdul - Chapter 32

Ajiya a duhu book 1&2 complete by billynabdul Chapter 32: Ajiya a duhu book 1&2 complete by billynabdul Chapter 32. A ruɗe Oum tacema Babban yaya yay mata…

3,132 words

A ruɗe Oum tacema Babban yaya yay mata kiran Uncle ɗinsu yana sashenta. Fita yay kuwa da sauri, sai dai yana fitowa motar RK na fita a gidan da gudu. Dan dai-dai ya nufo sashen AA da nufin jin damuwarsa saboda tunaninsa Oum na wajen mijinta kamar yanda tace masa zataje, sai dai yana gab da shiga sashen ne Dr Ranjet yay kiransa cewar gafa Maanal an kawo asibiti. Shine ya juya a guje ya faɗa mota ya fice. Fitar tasa dai-dai da shigowar motar Fawzan shima daga wajen aiki. Matarsa na a gefensa dan itama tana fita aikin, motarta ta samu matsala ne ta barta a office tai kiransa ya biya ya ɗakkota suka nufo gida. Ganin babban yaya ya sasu fitowa da sauri Fawzan na tambayar ko lafiya yaga Uncle Rafeeq ya fita a guje?. “I don't know why! Na fito kiransa ne nima fa”. “A da alama gaskiya babu lafiya, dan kamarma waya yake hankali tashe. Maybe asibitine suka kirashi kasan Uncle da patient ɗin nan nashi. Amma lafiya kuwa?”. “Auta ne babu lafiya”. Ai Fawzan ma bai samu damar sake cewa komai ba suka nufi sashen AA su duka ukun. Sai dai Babban Yaya na ƙoƙarin kiran layin family doctor ɗinsu a waya da shima ke aiki a KK HOSPITAL ɗin. Kafin doctor ya iso su duka sun rufu a kansa hankalinsu duk a tashe. Kallo ɗaya zakaima wannan taron kasan AA ɗin ɗan gatan dangi ne. Dan amaryar Abah ce kawai babu a wajen. Sai da matar babban yaya ta ɗaga waya tai kiranta sannan sai gata ta iso. Kusan tare suka shigo da doctor. Itama dai macece ƙyaƙyƙyawa, tana da ɗan jiki na ƙiba dan har tafi Oum ma. Sai dai Oum ta fita tsayi da haske dan ita fara ce kamar yanda Abah ke fari tas. Kai hasalima suna kama sosai da Abah ɗin tabbacin auren zuminci ne a tsakaninsu. Hakama duk yaran kama suke dasu, idan ka cire AA da yake da duhun fata sai dai kamanin fuskar Oum da Abah ɗin na tare da shi shima. Duk fitowa sukai aka bar Oum da Doctor yana duba shi. Duk da cikin faɗa yake mitar shi abarsa kar doctor ɗin ya taɓasa. A barshi haka baya buƙatar kowane magani. Hawaye Oum take tana ƙoƙarin tausarsa da shafa lallausar sumarsa daya tara take cin kuɗaɗe. Yayinda idanunta ke zubar da hawayen tausayin yaron nata dan gaba ɗaya yanayinsa ya nuna alamomin tashin ciwonsa. Sam bata fatan hakan, bata son abinda ya shuɗe suke murna ya dawo. Sun azabtu matuƙar azabtuwa da halin da AA ya shiga a shekarun baya. Da ƙyar da addu'oi abubuwa suka sassauta. Sai tabon dake zuciyarsa da sun san har ya koma ga ALLAH bazai warke ba kamar yanda suma nasun yake zaune daram. Sai kuma gashi ƙaddara na neman sabunta abubuwa cike da ban al'ajabi da mamaki a duka ɓangarorin biyu.........✍️

✨ZAFAFAN DAI ✨

1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull)

Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000

0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070

Kati MTN:- 09032345899

Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*

*_💞AJIYA A DUHU....💞_*

*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*

*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

*_My TikTok account 👇_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram👇🏻_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30

*_WhatsApp channel_*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R

_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_

🅿️➖4️⃣5️⃣

______________

.........Sai da Doctor yay masa allurai masu matuƙar ƙarfi a cikin drip ɗin da aka saka masa har kala uku a tare sannan barci ya ɗaukesa. Cikin kwantar ma su Oum da hankali yace musu karsu damu in sha ALLAHU komai zaiyi normal. Dan dama akwai malaria ne a jikinsa sai kuma damuwa data saka jininsa haurawa sama sosai, kuma da alama ya kwana biyu da damuwar a ransa amma ya cigaba da jigata kansa da sabgogi kuma. Hankalinsu ya ɗan kwanta jin abun da sauƙi, sai dai a ƙasan ran kowa maganar damuwar da yake ciki ta damesu. Oum da Fawzan ne kawai da suka fahimci musabbabin damuwar zuciyarsu ke suya. Sai dai basuce komai ba akai dan ko Babban yaya daya dawo Kano basu gaya masa zuwan Maanal gidan ba. Bayan sun shiga sun gaggansa yana barci fuskar nan fayau sai dai a takure na rashin wal'wala tamkar yana ido biyu. Yayinda Oum ke zare masa takalman ƙafarsa a hankali. Amsa Babban yaya dake kusa da ita yay ya ajiye gefe, batare daya zare masa socks ɗin ba ya maida duvet ɗin ya rufe masa ƙafafun a yanda suke. Tie ɗinsa da tuni ya sassautoshi da kansa dama Oum ta ƙarasa zarewa shima. Sai ƴar rigar saman long sleeve shirt ɗinsa itama ta ɓalle botiran. Itama shirt ɗin ta rage botira uku na sama. Su dai sauran duk suna tsaye suna kallonta, musamman Abah dake mata kallo cike da so da ƙaunarta. Matarsa dabance a cikin mata, idan yace daban yana nufin daban ɗinne a cikin daban. Har yanzu bai iya samun abinda zai kwatanta Fateeman sa da shi ba. Murmushi ya saki mai sanyi sakamakon haɗa ido da sukai da babban yaya da shima ke murmushin, sai kuma duk suka janye ya ɗan kalla amaryarsa itama. Itama dai Oum ɗin take kallo fuskarta da ɗan murmushi. Jiyay itama so da ƙaunarta na sake dasuwa a ransa. Kai shi kam ya gode ALLAH da samun mata nagartattu na ƙwarai. Su ɗin aljannar duniyarsa ne. Sallar magrib ce ta fita da su a sashen, amma Oum bata fitan ba sai ma umarni ta bama Fawzan akan ya kawo mata kayan sallarta nan. Da girmamawa ya amsa mata yana fita. Yayinda Abah dake kallonta cikin marairaice fuska ya furta, “Amma baiwar ALLAH tunda ɗan naki ya samu barci ai ƙyaji tausayina kizo ki bani abinci”. Ɓata fuska Oum tayi tana girgiza masa kai, “Ni dai gaskiya babu inda zanje nabar yarona a wannan halin, in dai abinci ne ai na kammala Mamy ta shirya maka kuje ku ƙarata”. Dad daya rasa ma abin cewa juyawa yay yana kallon Mamy, murmushi ta masa kawai da faɗin, “Kaima kasan ba kulamu za'ai ba ɗan gwal babu lafiya. Mu rufama kammu asiri muje muci abinci dan nikam har uku huɗu nake ganin mutane”. Ɗan hararar wasa Oum tai musu tana murmushi. “Eh kwaji da gulmarku dai, dan kawai kanwa na kawo sai na bar yarona a halin ciwo na koma kanku”. Dariya sosai Abah ya kwashe da shi, sai kuma ya nunama Mamy hanya yana faɗin, “Kinga Kamilah muje dan na kula itama uwar ɗan sai a hankali. Dama haka ɗan ya ɗakkomu a airport yana mana mazurai kamar sabon dan doka da mai laifi.” “Kwaji dai da shi, ba kulaku zamuyi ba sai mun warke”. Oum ta faɗa tana murmushi. Ficewa sukai suma suna dariya. Dama tuni matan su Fawzan sun fice. Dai-dai nan Fawzan ɗin ya shigo da kayan sallar Oum. Ajiye mata yay shima ya fita dan kar ya rasa jami'a.

__________★

Alhamdullah washe gari su dukansu jikin nasu da sauƙi. Musamman ma AA da Oum ke faman riritawa kamar wani ƙwai. A yanzu haka tana zaune ne bakin gado kusa da shi tana bashi breakfast, sai faman mata shagwaɓa yake ita ko tana lallaɓashi. Su Fawzan duk sun wuce aiki bayan sun shigo sun duba shi, hakama Abah tunda ya shigo ya gansa ya fita dan yana da uziri. Mamy ma ta shigo ita da matar babban yaya. Sai dai bata wani jimaba ta tafi tabar Oum da matar babban yayan dan ita bata aiki Bussines takeyi na kawo kaya daga Chaina tana rabama ma'aikata. A yanzu haka ma da Oum ke faman lallaɓa shi tana zaune tana faman musu dariya. Shi dai ba wani kulata yake ba dan tsakaninsa da matan yayyan nashi gaisuwar girmamawace da mutuntawa. Amma ka gansa yana hira dasu ko wani wasa da dariya abune mai wahalar gaske dan duk ƙanne suke a gunsa. Kai shifa mai ganin dariyarsa yanda ya kamata daga Oum sai ƴan uwansa, musamman Fawzan ma da suke kamar wasu friends ba brothers kawai ba. Dan shi Fawzan akwai barkwanci kamar Abah, saɓanin babban yaya da kusan halinsa ɗaya da AA ɗin. “Oum Please ki bari haka zanyi amai”. AA yay maganar a hankali yana kwantar da kansa a kafaɗar Oum ɗin cike da shagwaɓa. Murmushi itama tayi da kai hannu ta shafa kwantaccen gashin kumatunsa dake luf-luf duk da yau ko gyara bai samu ba. “To shike nan an barsa haka, ai kamayi ƙoƙari, kaida in baka da lafiya abinci ya zama maƙiyinka duk sonka da shi. Yanzu sai mi kake buƙata?”. Cikin lumshe idanu da sake maida muryarsa can ƙasa ya ce, “Barci”. “To Alhamdullah karɓa wannan ruwan addu'an kasha, Mamy ce tayo maka”. Ɗan jim yay yana kallon kofin, sai kuma ya ɗauke kansa da faɗin, “Oum ga naki ma ban shanye ba. Ki bari saina gama da shi”. “No naƙi wayon, shima kasha ai ba'asan inda za'a dace ba”. Fuska yaso ɓatawa amma dai ya amsa yasa kofin a baki, bayan yayi bismillah ya shanye yana miƙa mata kofin. “Yauwa ko kaifa ɗan albarka. Shike nan kwanta abinka ka huta nima bara naje na idan abinda ya rage kafin ka tashi na nema maka lunch”. Kansa kawai ya gyaɗa mata yana zamewa a gently ya kwanta. Dai-dai tana tattara kwanikan matar babban yaya mai suna Saheeba na tayata. Knocking akai tare da sallama, Oum ta amsa tana bada izinin shigowa dan su duka sun gane mai muryar. RK ne ya shigo cikin takunsa na nutsuwa, suna haɗa ido da AA ya saki murmushi cikin tsokana ya furta, “Ayya my son ashe an kusa a gangara”. Harararsa AA ɗin yay yana ɗauke idanunsa a kansa. Yayinda Oum ke dariya Saheeba na tayata. Sai da ya kai zaune a bakin gadon ya gaida Oum, Saheeba ta gaisheshi da tambayarsa aiki ya amsa mata da kulawa da tambayarta ina yara. Amsa ta bashi da cewar suna Kano basu dawo ba sai gobe da sassafe zasu taho da mamanta. Ya jinjina mata kai kawai yana maida hankalinsa ga AA. “Sorry my dear Son ai ban san abun haka ya kasance ba, sai ɗazun Fawzan ke sanar min ashe jiya ina ƙoƙarin fita ana kirana na dubaka. ALLAH ya ƙara sauƙi yasa ya zama kaffara”. Batare da AA ya buɗe idanunsa ba ya jinjina masa kai kawai. Dai-dai nan Oum ke faɗin, “Ai na kira wayanka da dare ma bayan ya samu barci switch off, ALLAH yasa dai lafiya dan fitan naka a jiya duk sai da ya dame mu”. “Wlhy tashin hankali yasa har cajin wayar ya kare ban kula ba Aunty, dama saura kaɗan sanda nazo nan jiya. Ƴarki ce babu lafiya sukai kirana gata an kawota asibiti, shine fa na tafi hankali tashe kin san ciwon nata nada haɗari”. A rikice Oum ta ce, “Wai kana nufin Maanal?”. Da wani irin mugun sauri AA ya buɗe idanunsa a karo na farko tun shigowar RK ɗin. Idanunsa masu kaifi da masifar haske kamar an watsa madara duk da halin ciwo da yake a ciki ya zubama bakin RK dake faɗin, “Yes ita Aunty, wai daga wajen aiki ta koma kawai ta yanke jiki ta faɗi”. “Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un yaya jikin nata?”. Oum ta faɗa tana kallon AA, suna haɗa ido yay wani saurin lumshe nashi ya juya musu baya. “Da sauƙi Alhmdllh, dan yanzu haka ma na barta tana barci. Shiyyasa nace bara nazo naga Autan ki shima”. Addu'a sosai Oum take ma Maanal, yayinda Saheeba ke amsawa zuciyarta na kai kawo da maimaita sunan Maanal ɗin. Can dai taga zata gaza ta tattare kayan data kwashe tana faɗin, “Oum bari naje dasu a wanke, ki huta zan masa lunch ɗin kawai”. Kai Oum ta gyaɗa mata da sanya mata albarka. Daga haka ta fice da ɗan saurin da su Oum ɗin sam basu lura ba. Kai tsaye sashen Mamy ta nufa, shima dai komai ya haɗu ga wani ƙamshi na musamman na tashi, tana a falonta na biyu zaune da waya a hannunta alamar magana ta gama yi. Shigowar surukar tasu kuma ɗiya a wajenta dan Saheeba ƴar yayarta ce uwa ɗaya uba ɗaya, zama a iya cewa itace ta haɗa aurenta da Fadeel ɗin. Ɗan ɗagowa tai ta dubeta sai kuma ta maida ga wayar tata tana faɗin, “Saheeba lafiya kuwa?”. Zama Saheeban tai kusa da ita gab fuskarta na nuna matuƙar ruɗani. “Mamy inafa lafiya. Kin san ina can wajen Yaya Ajwaad kamar yanda kikace naje na zauna komai ayi a gabana, sai ga ƙaninta yazo shine naji wata magana data ban mamaki.....” tsaf ta zayyane mata duka abinda aka tattauna a sashen AA ɗin. Cikin matuƙar mamaki Mamy ta sake maimaita sunan. “Maanal kuma Saheeba?”. “Tabbas Mamy sunan nan naji, duk da nasan akwai Maanal da yawa a duniya zuciyata ta kasa yarda ba waccan yarinyar bace da Yaya Ajwaad ke ƙula fuci. Kin dai san makirci da munafuncin matar nan, musamman idan kika duba ƙaninta ne yazo da labarin da mai sunan”. Wani ƙayataccen murmushi Mamy ta saki tare da gyara zamanta na ƙasaita. “Lallai lokaci yayi ashe, lokaci yayi da za'ai fito-na-fito na haƙiƙa tsakanina da Fateema akan ƳAƳANA. Saheeba! Ki ajiye wannan batun zamuyisa daga baya, amma ki tabbatar kin bibiyeta idan har zataje asibiti duba yarinyar kuje tare. Yanzu haka Abdull ne yay kirana zasuzo da matarsa da wata yarinya wai budurwar Ajwaad ɗin”. Wani mugun faɗuwa gaban Saheeba yayi, har sai da ta waro idanunta waje sosai sannan ta furta, “Budurwar Ajwaad Mamy? Ajwaad ke da budurwa kuma?”. “To nima abin dai ya ban mamaki gaskiya. Amma dai mu jirasu suzo ɗin. Kisa ai abinci daga ɓangarenki dan bana son ƴar tsirkun ta fahimci komai kin santa da bin ƙwaf. Yaya yasha ruwan rubutun?”. Da ƙyar Saheeba da gaba ɗaya take a birkice ta amsa mata da, “Eh ya sha amma da ƙyar, dan sai da taita lallaɓashi wai shi nata kawai zai sha”. Ƙwafa Mamy tayi ranta na ƙuna, sai dai batace komai ba akan haka. Itama Saheeban saita miƙe dan zuciyarta gaba ɗaya a ƙuntace take. Da haɗa hanya ta isa sashenta, kai tsaye bedroom ta afka tana rarumar wayarta dake a saman mirror. Bata ko damu da tarin miss calls data samu ba ta shiga laluben layin mahaifiyarta. Bugu biyu kuwa aka ɗaga. Ko gaisheta batai ba ta ce, “Mama akwai matsala fa, dole ki baro Kano a yau ɗin nan gaskiya. Sannan Nuratu ta taho Kanon ne?”. “Ke lafiya kuwa kike min maganganu a gwame? Mike faruwa ko yake shirin faruwa?”. “Abubuwane da yawa Mama, amma yanzu ina son sanin ina Nuratu take?”. “Nuratu tana Keffi kema kin san shiyyasa batazo bikin nan na Kano ba, zasuyi bikin birthday ɗin ƙawarta”. “Mtsoww wlhy wannan yarinyar gantalinta ya fara isata, tana can wataran zata ji an ɗaurama Ajwaad aure tunda ita bazata nutsu ba”. “Aure?”. “Sosai ma kuwa Mama. Tunda ita wawuyar yarinya ce. Ita tasan wlhy badan faɗi tashin da muke ni da ke akan batuntaba da tuni Mamy ta canjata da wata. Yanzu dai ki kirata idan taga da hali ta maza ta dawo Abuja dan Ajwaad baida lafiya tun jiya ko aiki bai fita ba yau. Ga Abdull nan kuma shida ƴar iskar matarsa ɗin nan mara kunya daya kawoma mutane cikin family bisa ra'ayinsa shi kaɗai wai zasuzo da wata budurwar Ajwaad ɗin ce, kin san kuma Mamy ita kaɗai ke goyon bayan auren nan nasa dama. Ga kuma wani batun a gefe da bamu gama tabbatar da shi ba”. A matuƙar rikice Maman nata ta ce, “Na shiga uku ni Gambo, wane kuma batu ne haka Saheeba?”. “Humm Mama ke dai kawai sai kin dawo”. “Dawowa kam ta zama dole dan yanzun nan zan baro kano, yaranki ma sa biyo jirgi gobe dan ni ko ban samu jirgin ba zan biyo mota kawai”.........✍️

Humm, tofa🤔🥱🤨😌

✨ZAFAFAN DAI ✨

1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull)

Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000

0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070

Kati MTN:- 09032345899

Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*

*_💞AJIYA A DUHU....💞_*

*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*

*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

*_My TikTok account 👇_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram👇🏻_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30

*_WhatsApp channel_*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R

_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_

🅿️➖4️⃣6️⃣

______________

.......Tunda Saheeba ta fita a sashen taketa faman kai-kawo. Wani irin watsal-watsal zuciyarta ke faman yimata. Tun tana jin zata iya daurewa harta kasa. Fitowa tai a sashen nata ta nufi sashen AA. Yanda ta shigo fuuu sai kuma tai laƙwas ganin doctor da RK da Oum a ɗakin. A take ta gyara yanayinta ta ƙawata fuskarta da murmushi. Sai kuma ta kalla Oum tana faɗin, “Na sake zuwa ne kar'a sakani a black list”. Dariya Oum tayi itama, zuciyarta fes ta ce, “Kamar kin san na fara ayyana haka a raina, tun shigowar safe ban sake ganinki duba mu ba”. “To ALLAH ya baku haƙuri na ɗan tsaya kan masu aikin nan ne kin sansu da aikin algus idan basu gadama ba. Yaya jikin naku?”. Kallon AA Oum tayi da faɗin, “A jiki Alhamdullah”. “To ALLAH ya ƙara afuwa”. Mamyn ta faɗa tana kallon AA itama da yay kamar bai ji shigowarta ba. Sai lokacin ya ɗan ɗago idonsa ya dubeta, da Muryar nan tasa ƙasa-ƙasa ya ce, “Ina kwana”. Wani irin motsawa zuciyar ta tai na takaici, amma sai ta danne ta sakar masa murmushi da amsawa da, “Lafiya Lau, yaya jikin naka?”. A hankali ya amsa da, “Alhamdullah”. Gaisheta RK yayi shima da girmamawa. Itama ta amsa da kulawa tana tsokanarsa wai shi da ɗan nasa ba'a san wazai riga wani aure ba. Ƴar dariya RK yay da kallon AA, sai kuma ya bata amsa da, “Karki damu Aunty muna tafe, dan gara ni na farayi kafin a fara kirana Baba na zaure”. “Ato ya kamata dai, dan zaman ya isa haka Uncle tururu ɗansa tuzuru”. Dariya kawai RK yake cike da jin nauyi, dan yana matuƙar girmama matar da ƙaunarta kamar yanda yasan ita da ƴar uwarsa suna ƙaunar juna. Dan in ba faɗa maka akai ba bazaka taɓa ɗauka kishiyoyi bane. Oum ma dai dariya take kawai doctor na tayata, gogan kuwa yama lumshe idanunsa dan ruwa doctor ya sake saka masa saboda sake samun ƙarfin jikinsa. Sallama tai musu ta juya ta fita tana sanarma Oum zataje taɗan kwanta ta huta. Oum tai mata godiya...

Readers Also Read