Kenza eBookz

Al'amarin maryam Complete - Chapter 32

Al'amarin maryam Complete - Chapter 32

Al'amarin maryam Complete Chapter 32: Al'amarin maryam Complete Chapter 32. Ta gama gyara dakin tana wankin toilet safna iso, xuwanta gidan kenan na farko…

4,412 words

Ta gama gyara dakin tana wankin toilet safna iso, xuwanta gidan kenan na farko tun xuwan Mimi tana shigowa tace "Anty mami memakon ki sauka gidana kya sauka gidan amare?" Anty mami ta bata amsa da cewa "ga gidan Dan uwana wanda nake da iko akan komai xan taho gidanki ina rabe rabe muna hada hanya da mijinki?" sai a lokacin idon safna yakai kan Mimi dake wankin toilet. Cikin mamaki tace "Mimi kece ke wankin toilet kodai shaawa kikai?" "ni nasakata" Anty mami ta bata amsa.

Mimi ta fito bayan ta gama tana cewa "Anty safna nayi fushi fa sai yau kika leqoni? Kuma nasan yanxun ma xuwan Anty mami ne ya kawo ki ba gurina kikaxo ba" kafin safna ta bata amsa mami tace "to inba gurina tazo ba gurinki taxo? Ai tasan dake din da bata shigo ba sai yanxu da naxo don ta nuna miki wata kusan tafi wata" safna ta saurinta tace "a a ni ba haka nake nufi ba, yi haquri matar yaya guri na baku ku gama amarci don innafara xuwa saina gundureku" Mimi cikin jin dadin kalaman safna tace "Allah ya kawoki bazamu taba gundura dake ba, mutum ai baya gundura da nasa" tai waje don kawowa Anty mami breakfast.

Tana bada baya safna ta kalli Anty mami ta fara magana "gaskiya baki kyauta ba, ya daga xuwa gida xaki fara sata aiki wannan abun fa da kike sam be dace ba kuma karkiga mijinta baya damuwa wlh kawai gara yake muki amma kinkacigaba da haka wlh mutunciki zai zube a gurinsu" Anty mami cikin hargowa tace "aishi ba tanbadadde bane irin Audu kuma yana sona yanamun biyayya akan wata banxa Mimi bazai juyamun baya ba" safna ta kuma dorawa da cewa "ai kuwa inkaci gaba da nuna haka akan matarsa wlh zai taka miki burki, dama mumy tanajin ance anan kika sauka tai hasashen matsala xaki zame musu. Hasashenta kuma ya xama gaskiya daga xuwanki kin fara bautar masa da mata" cikin tsananin fushin nuna son Mimi da suke tace "to ai saiki buga ki fada mata abunda ke faruwa taxo ta koreni inkoma hotel tunda kunfison Mimi akaina" safna ta bata amsa da cewa 'ko bakice in fada mata ba nima innaga abun naki ya wuce makadi da rawa zan fada mata don banga dalilin qiyayyarki ga matan qannenki ba don xubar da girma irin haka ta janyo miki raini gurin yasmin"

Mimi ta hado abincin kari a qaton try ta kawo ta tsuguna ta hadawa Anty mami tea kana ta hadawa safna ma duk da ta qoshi amma sai data qarba don karta gwale Mimi. Ta cika musu plate da chips da platain soyayyu tasa musu wainar kwai a gefe da saka musu fork akai ta tura musu, kana ta kuma xuba musu farfeso na kayan ciki tana shirin tura musu ne Anty mami tace "wannan duk abincin ina xamu kaishi? Ko ance miki kowa cikin zani gareshi irinki?" batace komai ba ta fita ta samu Farida kwance gadonta suka fara hira kan gidan abincin Farida da aka bude na Abuja yan kwanakin da suka wuce. Suna cikin hirar ne Farida ta sanyo Anty mami ciki da tambayar abunda tagani dazu. Mimi bata boye mata komai ba ta fada mata tsakaninta da ita a da da kuma yanxu data xama matar qaninta.

Farida masifa ta dunga yiwa Mimi akan wannan sanyin da kwantar da kai baxai kaita ba gara ta horoncewa Anty mami irin yacce yasmin tayi. A fadar faridan in itace wlh saita casa Anty mami da qafarta xatabar gidan. Mimi ta bata tabbacin baxata iya ba sabida xumunci da kuma mumy, xatai haquri da Anty mami darajar wadannan abubuwa. Farida ta watsa mata harara tace "ai saiki xauna kita hadiyar baqin cikinta" Mimi tana dariyar daukan dumi irin na Farida tace "xo muje kitchen din mu dora girkin kar kuku ya rigani" suka nufi kitchen Farida ta xauna kan stool Mimi ta hadata da yankan salad ita kuma ta dora wake.

Acan daki kuma Mimi na fita safna tahau Anty mami da fada tana nuna mata kuskuren takura Mimi da taxo tanayi har gidan mijinta duk kuwa da biyayyar da Mimi ke mata. Anty mami ma tahau sai cacar baki suke kamar saanni daga qarshe dole safna ta bar mata tunda ita din ba gwanar masifa bace. Daga qarshe Anty mami ta share safna ta dakko system tana dannawa wai ita a dole tana fushi safna tai mata rashin kunya akan Mimi. Ta gaji da xaman jugum jugum ta nufi kitchen maida kayan da suka karya anan ta tarar da su, tasa hannu jin rice nd beans ake suka ida sukaje sallah sannan suka xuba a try su ukun yaji manja da yaji salak da tumatur da gurji da dafaffen kwai suka baje a falo sukaci sukai qat suka dora da coke. Ita kuwa wacce ta sawa kanta kunci tana qunshe a daki.

Sai dawowar mai gidan suka tafi, yace da Mimi yunwa yakeji bata gama abincin dare ba hakan yasa ta dakko masa guntun wake da shinkafar da yayi ragowa ta xubo masa hadin salad akai. Ya xauna yaci yana santi har yana tambayarta ta aikawa ishaq? Tace "eh Farida ta diba masa" Anty mami ta fito daga daki yana dariya yayi mata barka da gida. Bata amsa ba ta xarce da qorafin Mimi tasan tananan amma tayi wake da shinkafa, ita kuma bataso. Ya dubi Mimi dake xaune gefensa yace "Mimi luv ya akai abincin da Anty mami bataso" cikin kwantar da kai tace "yi haquri ranka ya dade, bansan bataso ba Farida ce take shaawa shine nayi a gidan gabadaya" ya juya gurin da Anty mami ke tsaye "to Kinji uxurinta Anty mami amma kiyi haquri" cikin fusata ta fara magana don ta farajin haushin tufkar da take Mimi na warwara duk yacce taso haddasa rigima tsakaninsu sunki bata hadin kai "to saiki fadamun da Farida da ni wayafi matsayi da iko a gidan?" Bature yayi saurin tareta da cewa "a a Anty duk abun bai kai haka ba, yanxu ya kikeso ayi?" cikin izzah tace "ta dafamun abunda xanyi don yunwa nakeji, don zalunci tasani yini da yunwa ni da gidan Dan uwana" ya kalli Mimi yace "Mimi luv dan daure ki samawa Anty mami abunda xataci me sauki" ta haskeshi da murmushi tace "to yaya luv" ta miqe ta nufi kitchen. Anty mami taja dogon tsaki kodai xatabi shawarar safna ta fita harkarsu? Amma kishin Mimi take sosai akan Bature.

Ta dora mata farin couscous wanda ta yanka koran tattasai ta xuba mai a dahuwar sai green beans. Gefe kuma tana duba girkinta na dare data dora (tuwon shinkafa da miyan kuka) babu jimawa ta gama ta dumama mata stew din da take da ita a fridge ta hada mata ta kai mata har daki.

Ta kalli couscous din bayan fitar Mimi, batacin couscous don haka ta dibi wake da shinkafar da aka ajiye mata tun rana taci ta barbaza kamar bata diba ba don dama tanaso don san haddasa fitini tace bataci.

Da daddare gurin dinner Mimi bata xauna cikinsu ba sabida abunda ya faru jiya. Anty mami bataiwa kanta ba wannan karon sakin jiki tayi ta kwashi tuwon shinkafa miyar kuka don ko tayi akai mata bata qin ci, tanason wannan cimar kwarai kuma sabida ita Mimi ta dafa, duk sai taji kunyar abunda tayi dazu. Ragowar tuwon tace Mimi ta ajiye mata xataci dumame. Yauma can ta barsu suna hira a falo taje baccinta.

Ranakun da suka biyo baya ta dan samu saukin takurar Anty mami sabida ta fara halartar aikin da ya kawota, sukan yini da Farida a gidanta ko ita taje gurin Faridan. Sai dare Anty mami ke dawowa, inta dawo kuma a gajiye take amma dan kishin kar Bature ya bawa Mimi lokacinsa haka xata tareshi da hira yana hamma tana hamma har sai lokaci yaja wanda takega koya koma gurin Mimi bacci kawai xaiyi.

Akwana na hudu da xuwan Anty mami gidan da yamma Bature ya dawo ya sami Anty mami gida, yau ta dawo da wuri. Mimi tamai barka da dawowa ta cire masa jacket din saman suit dinshi tada fara jiqewa saboda ruwan saman da ya sauka babu jimawa ta shige cikin daki don ajiyewa ta barsu shi da Anty mami suna hira. Shiru shiru yana jiran Mimi ta fito daki ta kawo masa abun sha kamar yadda ta saba inya dawo amma bata fito ba. Yace da Anty mami yana xuwa ya tashi yabi Mimi daki.

Ya sameta xaune kan kujerar gaban madubi riqe da rigarsa data cire masa tana hawaye, dakin da dan duhu kadan sabida hadarin daya lullube sararin sama kuma bata kunna haske sosai ba. Jin takun mutum yasa tayi saurin qudundune rigar ta boye a jikinta, sai dai ta makara don ya riga yaga abunda tayi yana xuwa yasa hannu ya ciro rigar ya qurawa rigar ido da nufin gano abunda yasata kuka ajikin rigar. Sai da yayi amfani da fitilar jikin wayarsa sannan yaga shatin lebunan mace da jan janbaki (💋)radau a jikin light ash din suit dinshi. Jikinsa yayi sanyi qalau don yasan ba Mimi bace don ita da wuya tasa jan jambaki indai ba period take ba ko kuma tasa kayan da suka dace da kalar ja, tafi saka pink ko dark purple.

Tunani take a xuciyarta tun sanda ta shigo dakin ajiye rigarsa ta dagata tana yarfe ruwan jiki da nufin ta dan shanya idonta yakai kan 💋 wannan, wato kenan Bature yawan bin mata yake shiyasa kwanaki yake yawan fitar bayan isha sai wajen 10 ya dawo? Shiyasa Kullum yake cikin yin waya babu dare ko rana kuma intana gurin baya amsawa? Lallai ita din banxa ce tun a lokacin ya kamata ta gane ba sai yanxu da abun ya girma ba har ya fara nuna mata shedar yana bibiyar mata. In kuwa ya Bature neman mata yake tabbas ya cuceta cuta ta har abada kuma wlh xata iya haqura dashi duk soyayyar da take masa don ita batason fasiqi tun farko abunda tai gudu kenan ya Faty ta kakkareshi kyakykyawan namiji kamarsa ba a rabashi da yan mata bare shi bayan kyau ga kudi. Wannan dalilin shi yasa ta riqe rigarsa tana kuka har yaxo ya sameta.

Shi kuma anasa bangaren tunanin yadda akai wannan janbakin yaxo jikinsa yake, inyaje office yakan cire jacket dinsa a rataye wasu lokutan baya sakawa sai antashi ya mai da abarsa jikinsa. Babu shakka Hanifa tayi amfani da wannan dama xata haddasa masa fitina da xargi tsakaninsa da iyalinsa tabbas sai ya dau mataki akan hakan.

Tunaninsa ya katse lokacin da yaga Mimi na shirin fita ta bar masa dakin, yayi saurin isa inda take ya riqo hannunta yana bata haquri. Bata da niyyar sauraranshi don sai kici kicin kwace hannunta take, ganin haka ya kai gwiwoyinsa qasa ya tsuguna gabanta ya riqo hannayenta. Jikinta yayi sanyi ganin mijinta a haka tace "ya Bature me haka? Ka tashi don Allah" ya katseta da cewa "MARYAM wallahil azeem ban taba aikata abunda kike zargina akai ba, kuma ni kaina bansan yadda akai jambaki yaxo rigata ba, amma na miki alqawari indai ni SULAIMAN aurene ya haifeni baxaki qara ganin haka ba" idonta cikin nasa tana xubar da kwallah tace "ya Bature basai kayi wannan rantsuwar ba, na yadda da kai da kuma abunda ka fada don Allah ka tashi" bai tashinba sai matsowa yayi kansa dai dai mararta ya kwantar da kan nasa a cikinta, ita kuma tasa hannu tana shafa masa. Yace "indai kin huce kiyimun dariya" ta washe masa fararen haqoranta kana ya miqe ya rungumeta suka fito saqale da juna.

Da daddare be zauna hira da Anty mami ba kamar yadda suka saba, yayi mata qaryar kansa na ciwo ya nufi gurin Mimi. Yana hawa gadon ya amshe wayarta da take chating ya ajiyeta gefen gado, ya fara balle mata botiran gaban shirt din jikinta. Shauqin son Mimi din ne yau yake damunsa kuma dama anjima ba a hadu ba, ya fara binta da hot romance dinsa kamar yadda ya saba, sosai yakeson wankewa Mimi zuciya saboda bacin ran da tayi dazu.

Taga abun nasa na neman zarcewa ta riqo fuskarsa ta qura masa ido ya fara futa hayyacinsa, taji tausayinsa tace "ya Bature bani da tsarki fa" bai kulata ba sai maida fuskarsa da yayi yana lasar wuyanta kana yace "haba Mimi ni xaki yiwa wayo?" ganin da gaske be yadda ba taci laya "ya Bature wlh da gaske nake" ya dago ya bar abunda yake jin ta rantse yace "yaushe hakan ta faru bansani ba?" tace "yau da asuba na tashi dashi, nima nayi mamaki don banji ciwo ba ko kadan sai ganinsa nayi" ya danne abunda yake taso masa yace "to Allah yasa ciwon ya rabu dake kenan" ta amsa adduar da yayi. Ya matseta tsam a qirjinsa tana shafa kansa har ya samu relief.

Allah Allah yake ya isa office ya samu Hanifa yaji dalilin abunda tayi masa a jikin rigarsa jiya, yace da driver ya qara sauri don yaso makara tunda sai da suka kai Anty mami.

Hanifa ta shigo gaisheshi kamar yadda ta saba, bai amsa ba sai tambaya yayi mata cikin daure fuska "mesa kikasa min lips dinki jikin rigata jiya?" tayi tsit kanta a qasa, ya kuma maimaita tambayar yana waro mata idanu. Cikin firgita da yanayinsa tace "Sir, ba ba ba nice ba" ta fada tana qiqina. Ya buga table din gabansa cikin tsawa yace "to uban waye inbake ba? Nine kenan? Tunda daga ni sai ke a office din" tai tsuru tsuru a tsorace take dashi sosai don fada yake kamar ya daketa. Ya qarashe fadansa da cewa "to inma kinyi donki haddasa fitina tsakanina da Mimi ne to kinyiwa kanki don bakison darajar aure bane shiyasa kikai haka, kuma fitinar da kikai niyya ba ayiba don muna da fahimtar juna da matata. Wlh Hanifa kika kuma yin abunda kikai sai kin bar office din don canjaki xansa ayi, da bacin ran Mimi gara in rabu dake har abada" ya qara watsa mata kallo "get out of my sight"

Ta fita wajen office din tana hawayen baqin cikin cewar da yayi da bacin ran Mimi gara rabuwa da ita. Ta ciro waya ta kira gwaggoriya ta fada abunda tasa tayi tayi amma ba a dace ba don hakan ya janyo mata cin mutunci. Gwaggoriya ta bata haquri da cewa karta kuma hakan tunda zai dau matakin korarta a office dinsa, ta kwantar mata da hankali da cewa indai da malamai a duniya bazasu watsar da makamansu ba sai ta auri sulaiman.

******* ******** ********

Tun daga ranar Anty mami ta tsiri indai taje office ta dawo da daddare sai ta bawa Mimi aikin lecture din da sukai ta shigar mata a system, Mimi kan shafe tsahon dare har xuwa 2 na dare tana typing kuma ko xata kwana a xaune Anty mami baxata tausaya mata tace taje ta kwanta ba har sai ta gama, wanda a lokacin mami takai wajen kai 10 na baccinta. Kuma tayi hakanne don ta hana Bature da Mimi damar kebewa suyi soyayyarsu tunda Baturen ya fara bijirewa hirarta ta dare yana mata qaryar ciwo.

Ranar data farasa Mimi wannan aiki Mimi sauri ta dungayi don ta gama ta tafi gurin mijinta wanda tasan baya bacci sai a jikinta. Tana gamawa tai wa Anty mami dake gyangyadi sallama, anty mami ta wartsake jin Mimi har ta gama shigarda uban aikin data bata a syatem. Tace cikin mamaki "kai amma kinyi sauri kina da saurin typing, bari inbaki ragowar ki shigarmun" Mimi cikin kunya tace "Anty mami bari inje in kashewa ya Bature fitila in dawo, nasan yayi bacci da fitila a kunne" Anty mami ta daure fuska tamau tace "Dallah zauna kimun aiki, jarababbiyar banxa inda shi ya damu dake yadda kika damu dashi ai da tuni ya biyo sahunki" ta xauna jiki sanyaye ta fara aikin data bata.

Acan bangaren kuma Bature yagaji da jiran Mimi ya kasa bacci sai juyi yake, ya dubi agogo 12:48 AM, ya miqe ya nufi dakin Anty mami.

Ya tarar da Anty mami na bacci Mimi na gefen gado tana mata aiki kamar tare zasu raba kudin, shigarsa yasa mami ta tashi. Abun dariya wai saita dubeshi tace "lfy?" yadanyi dariyar jin abunda yace "Mimi na biyo taxo muje mu kwanta naga daya saura" ta basar dashi ta koma xata kwanta, Mimi ganin haka tace " Anty mami in bishi?" jin furucin Mimi ta miqe tace da Bature "fita kaban guri, inta gama xata dawo ai basai ka biyota ba ko so kake ka nuna mun ban isa da ita ba" ya fita waje jin abunda tace. Ta juya gurin Mimi tace "ke kuma aikin nawa xaki bari ki tafi gurin miji ko? Ke ko tsoronsa bakyaji? Dubeshi qatoto dashi kita binsa yana daddanneki" Mimi dai sunkuyar da kai tayi tacigaba da aikin. Bata gama ba sai 1:26 ta miqe a gajiye tabar dakin donkar Anty mami ta kuma sakata wani aikin.

Ta sameshi ya jera fululluka a gabansa ya rumgumesu abun tausayi ta shige jikinsa, jinta jikinsa yasashi tashi xaune. Ya jawota yace "Mimi kiyi haquri nasan duk Anty abunda Anty mami ke miki inajin babu dadi kawai ina haquri da itane" idonta yadan kawo ruwa, tace "ya Bature ada Anty mami tana sona amma tundaga bayyanar maganar aurenmu ta tsaneni ta kuma canjamun." yana share mata hawaye yace "bakece Anty mami bataso ba, nine bataso na aurin qayatacciyar mace irinki ba. Ta fiso ta aura miki dattijo irin Dr. Mijinyawa yadda xaki xama sillar samun kudinta a koda yaushe ta buqaci hakan. Shiyasa ta ke miki hakan" ya canja salon maganarsa xuwa wasa da xolaya don ya cire mata damuwa yace "kuma abunda bata saniba shine; inda kike jarababbiyar nan data aura miki wancan tsohon ai da baxai iya miki ba, nidin dai nike iyawa jarabarki"😆 jin haka ta juyo ta dau filo tana masa dukan wasa da cewa "nice jarababbiyar ko?" shima ya dauka yana dukanta suna dariya.

Cikin sati biyun da Anty mami tayi a gidan Mimi taci gwagwa a hannunta ta hanyar sata duk wasu ayyukata na office ga kuma hantara da gyara koda agaban yan aikin gidan bata lura hakan kan iya ragewa Mimi daraja a gurinsu. Inkuwa weekend ne tana gida komai Mimi tayi bata iya ba, gashi Kullum dare bata barin Mimi sai kusan qarfe biyun dare take komawa gurin mijinta tun be saba da hakan ba har ya haqura ya saba.

Mimi sai yanxu tagane abunda ke hada Anty mami da yasmin fada, babu shakka irin wannan abun da take mata yanxu ta nemi yiwa yasmin ita kuma ta bijire.

Shikansa Bature duk ya fara gundura da xamanta duk kuwa da irin qaunar da yake mata sabida yadda ta takurawa matarsa da kuma hanashi sakewa da ita.

Ranar monday ta tafi wanda yayi daidai da kwananta 15 a gidan, harda kukanta duk yadda Mimi tagaji da wahalar Anty mami saita tsinci kanta da kewarta, lallai ranar naka sai naka dadin xama kuma sai bare.

Ranar da wuri suka kwanta ita da mijinta abunda suka dade basuyi ba, duk jikin rawa yake akanta kamar bai taba saninta ba. Ta katseshi da nuna masa batason abunda yake shirinyi. Ya marairaice mata sosai da magiya kuma dama shidin yakan dade bai buqaci mace ba, amma duk randa buqatar taxo masa baya iya haquri ko kadan. Ita kuma yau sam she is not in d mood.

Ya fara mata dadin baki "haba Mimi ninefa in wasa kike don Allah ki dena kinsan bana iya haquri innakai haka" yayi mamakin ganin ta bijirewa duk wani sweet mouth dinshi. Ya riqe kafadunta yana kallon kwayar idonta "Mimi tunda na aureki yauce rana ta farko ta kika bijirewa shinfidata, nasan laifi nai miki shiyasa xakimin wannan hukuncin amma Dan Allah kiyi haquri bazan iya juraba kinga bani da wata matar sai ke ki bari insami nutsuwa sai ki fadamun laifina kinji Mimi na a yafemun" ta cire hannunta daga nasa ta sauka akan gadon ta koma kan sofa ta kwanta, ta lura duk yadda xatai masa bayani idonsa ya rufe baxai fahimta ba gara ta canja makwanci inyaso ya haqura dole don yau gani take ko mutuwa xaiyi baxata bashi jikinta ba don sam bata raayin abun kuma ita kanta batasan dalilin hakan ba.

Baki sake kamar sabon shashasha yake kallon Mimi da sabon salon raba musu makwanci yau. Ya tashi ya nufita halin da yake ciki yasa har tsigar jikinsa na tashi. Ya riqe dantsen hannunta yace "Mimi wani abun kika koyo na guduna a shimfida?" ta fusge hannunta a xuciye itama tace "tunda nace banaso ka rabu dani mana ko dole ne?" ya tsuguna gabanta jiki a sanyaye ganin Mimi yau ta canja masa yace "maryam kodai abunda Anty mami tai miki ne kike daukar fansa a kaina? Naga ai na baki haquri ko kuma nima ba a sona take miki hakan ba" jin abunda yace itama nata jikin ya danyi sanyi tace " ba wannan bane xan iya cemaka na manta da abunda tayimun kuma Anty mami ai yar uwata ce dole nai haquri da ita tunda inason qaninta. Kawai dai abun ne banaso Don Allah ka haqura"

Ya miqe yaje ya kwanta akan gado ruf da ciki yana runtse ido. Ita kuma ta kwanta kan sofa. Kusan awa daya da kwanciyarsa ya kasa bacci sai juye juye yake, yayin da ita tuni ta sami bacci. Yaga alama indai yanason ya runtsa a daren nan to saiya fitar da abunda ke cikinsa, ganin bashi da xabi ya tashi ya nufi Mimi.

Cikin baccinta ta jishi ya turmusheta iya qarfinsa, ta bude ido ta fara kai masa duka da hannunta a qirjinsa iya qarfinta tana kuka tana cewa "banaso, nace maka banaso inkayi mutuwa xanyi ka rabu dani" ya hada hannunta ya riqe tsam ya fara shigarta a hankali don bata bashi hadinkan yi mata romance ba. Tana jinshi jikinta tayi shiru tsit tabar kukan, matar da tace bataso sai gata tana nunfarfashi. Sun dau tsawon lokaci suna abu daya sannan ya gyaleta ya dauketa ya mayar kan gadon suka kwanta.

Sai dai a wannan daren basu rintsa ba don kwana tayi bata da lfy, xaxxabi take me zafin gaske harda rawar sanyi. Ya kashe AC ya kulle Windows ya rufeta da jibgegen blanket amma bata daina jin sanyin ba. Gashi kusan duk minti biyar saiya rakata bandaki fitsari, haka suka kwana har ya fara zargin kansa da haddasa mata ciwo, wane haukane ya kaishi yin sex da mace bataso kamar wani bagidaje? Ga abunda ya jawo nan.

Haka suka kwana da asuba ma a gida yayi sallah, ita kuma a xaune. Tana idarwa ta fara bacci, shikam ko falo bai fita ba bare wani office yananan bakin gado yana gadinta tana bacci shi kuma ya na gyangyadi. Yayiwa mr Alex waya yadau excuse ya fada masa madam ce babu lfy.

Sai 11 safe ta farka ras da ita kamar batai ciwoba jiya cikin dare ya hada mata ruwa tayi wanka, suka fita cin abinci a dining itace ma kedan kunyar abunda tai mai jiya, ya nuna mata babu komai ajixanci ne irin na Dan Adam shima ya bata haqurin hakke mata da yayi ya fada mata ba halinsa bane jiyanma ya rasa abunda yasa haqurinsa ya gaxa. Bayan sun gama ta shiga gidan Farida, shi kuma bacci ya koma.

Mrs Hajia 😊 [9/30, 1:05 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 5⃣6⃣

Babu jimawa babbar sallah taxo, hutun babu yawa kwana hudu ne kawai. Ranar arfa suka isa da safe kuma a ranar suka kewaye yan uwa da daddare bayan sunsha ruwan axumin arfa da akai. Kamar yadda suka saba ko ina maraba ake dasu, mama harda bawa Mimi kayan qamshi irunsu kanumfari da citta wanda xatai aikin naman sallah. Mumy kuwa da sukaje cewa tai da Mimi karta bawa kanta wahalar aiki irin na wancan sallar ta samo mata yar tayin aiki kuma ga Aisha nan yar aikinta ta yarda da ita sosai ta bawa Mimi. A gidan hajja kam sun shafe kusan 11 dare suna hira da kakanninsu cikin nishadi, Mal manu adduoi yadunga bawa Mimi kamar yadda ya saba yana cewa ta dunga yiwa kanta da Bayahuden mijinta. Su Faty har sun rufe gida suka buga musu, ganin sune har sun kwanta Ahmad ya taso Faty wacce cikinta yayi wani irin mugun girma don har ya wuce watanninsa na haihuwa ta kumbura suntum. Ta tausaya mata sosai lallai mata suna wahala da ciki, Faty tana dan dariya tace da Mimi "karki damu an tabbatar da lfy lau muke ni da Baby kawai lokacin da Allah ya dibar masa na xuwa duniya ne beba" haka dai suka rabu cikin kewar juna tana fadawa Faty tana haihuwa ta fara fada mata ranar xata taho kano ya Ahmad yace "to unguwar xoma"

Washegari idil adhha, suna sakkowa idi yayi layya sa da rago ya yanka, kuma nan take ya rabar da naman san gaba daya ga maqota da danginsa akaita kaiwa. Kayan ciki kawai ya bari da naman rago, maaikatan da mumy ta samo mata su sukai gyara naman (kayan ciki) jikin ragon kuma aka ratayeshi. Ta tsaya ta kula da suyar akai mai kyau da tsafta. Rana ta biyu da sallah da daddare sukaje gidansu Farida gaishesu, Mimi ta dibarwa ummansu soyayyan nama. Acan suka tarar da Farida sai shagwaba take xubawa. Umma taji dadi ta bawa Mimi danbum nama ita da Farida cikin bokitai da kilishi, washegari uku ga sallah suka koma Abuja kamar yadda sukaxo su 4 sabida washegari talata xa a koma aiki hutun da federal ta bayar ya qare.

(Eid Adha Mubarakh, Taballallahu minna wa minkum)

******* ***** ******* ****

Sati biyu kenan da yin sallah, suna kwance bayan sallar asuba wata irin yunwa ta tasheta. Ta tashi zaune baya kan gadon, ta nufi dakin motsa jiki dake can qarshen falon. Acan ta taddashi kan gym yanata motsa jiki sai zuffa yake. Ta kalleshi "yaushe ka tashi bansani ba?" ya bata amsa "aini ban kwanta ba ina ganin kinyi bacci na fito tunda naga yanxu ke bakyason motsa jikin kin xama malalaciya" ta yamutsa fuska "wlh ya Bature ni kaina bansan abunda ke damuna ba these dayz in nayi haki nake nafi gane inta bacci" yace "inaga gajiyan tafiyane har yanxu bai barki ba" batace komai ba ta nufi kitchen samawa kanta abunda xataci.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull