Kenza eBookz

Al'amarin maryam Complete - Chapter 37

Al'amarin maryam Complete - Chapter 37

Al'amarin maryam Complete Chapter 37: Al'amarin maryam Complete Chapter 37. Ya isa gurinta da sauri yana cewa "maryam ina xaki haka?" ta cije lebenta na…

4,476 words

Ya isa gurinta da sauri yana cewa "maryam ina xaki haka?" ta cije lebenta na qasa cikin azabar ciwo tace"kirana ake tun daxu bakaji ba?" ta fada tana nuna masa saitin qofa. Ya kalli gurin data nuna yace "ni banji komai ba Mimi, kunnenki ne kawaia" tasa kuka tana cewa "wlh kirana ake kuma mamace ke kirana don muryarta naji" a tsorace ya dubeta yace "mama kuma? Mexai kawo mama nan da yammanan?" dakyar da sudin goshi yajata suka koma suka xauna. Ya dorata cinyarsa yana qara shafa mata maganin hadi da lallashinta yace "maryam kiyi haquri nasan ni na haddasa miki ciwonnnan, sai da kikace bakyaso na kusanceki amma nabi son xuciyata. Nasan dana haqura da kinanan qalau dake, ya marairaice ya riqe hannunta yana furta i m sry Mimi luv, plz forgive me na biyu kenan in shaa Allah baxanyi na uku ba "binsa take da ido bata fuskantar maganarsa ita kawai burinta ya saketa taje kiran da ake mata don har yanxu kiranta ake kuma da muryar mama.

Da yaga bata hayyacinta sai yaqi fita masallaci a gida yayi sallar sukai jam i tare, sukaci abinci ya bata magungunanta tasha xuwa taran dare suka kwanta. Yauma dai kamar jiya gane gane ta dungayi kafin bacci ya dauketa mara dadi da munanan mafarkai, kuma ya tashi da jini fiye dana jiya a jikinsa wanda yau yaga inda jinin ke diga ta kunnen Mimi data kwanta donyin bacci. Wajen 2"30 AM ya tashi yaga tana birgima a qasa tana hawaye, a razane ya taho gurinta yana tambayarta lfy? Ta nuna masa qafarta yakai hannu zai taba tasaki wata gigitacciyar qara da sauri ya janye hannunsa. Ya taba jikinta xafi rau.

Ya dauki towel da ruwan sanyi ya dunga goge mata jikin ya shafa mata maganin ciwon qafa kana ya bata paracetamol tasha ta kwanta, yayi sa azazzabin ya sauka kuma ta samu bacci. Amma shi kam idonsa kyam a kanta tana sharar bacci akan cinyarsa.

Ya xubawa jinin dake diga daga kunnenta ido, diga yake babu tsayawa yayin da Mimi ke bacci. Wani irin tausayin yarinyar yarufeshi yana hawaye yana tunani wannan wane irin ciwone? Ai sai jininta ya qare wace irin lalurace ta samu Mimi haka ga ciki a jikinta? Kodai laulayin ciki ne yaxo mata da haka? Yana kallonta gami da kuka da tunani har garin Allah ya waye tangararau bai sallah ba. Danma yau saturday babu office saida Mimi ta tashi daga baccin kana ya shima ya tashi donyin sallah. Xuwa wannan lokacin jinin daya xuba jikinta bashi da iyaka, dan wandon jikinsa ya jiqe sosai har bed sheet ya baci.

Ya dunga tambayarta ya jikinta ina ke mata ciwo kanta na ciwo? Ta bashi tabbacin babu inda ke mata ciwo sai qafarta wadda yanxu bata iya yakawa sai dai ya dauketa duk inda xataje.

******* ******* ********

Yan kwanakin da suka biyo baya AL' AMARIN MARYAM ya qazanta sosai, kamar jira ake ta dawo gidan matsaloli sukai chaaaa. Xubar jini daga kunne har sun saba da hakan tunda yanxu hartakai inxasu kwanta sai ansaka zani sabida zubar jinin. Abunda suka fuskanta duk sanda Mimi ta kwanta danyin bacci xubar jinin xatace salamu alaikum domin baya dena xuba saita tashi, duk da cewa baccin ba me dadi take ba.

Qafarta ta kunbura tayi suntum har kyalli take kamar a tabata ta fashe, Mimi dai yanxu bata tafiya sai dai a turata a well chair.

Ciwo yayi tsanani bata um bata um um sai dai komai ayi mata. Kuma duk abunda akace tayi yi take babu musu, babban tashin hankalinsa batacin abinci saiya takura mata ko kuma asaka mata drip.

Shi da ishaq Kullum suna yawan asibiti ana aunata amma antabbatar lfyarta lau daga qafar har kunne babu problem. Sai dai Kullum ana bata maganin qarin jini sabida xubar jinin da kuma maganin bacci.

Kwana take kukan ciwon qafa da kuma ita ya barta taje kiran mama, wai ita a lallai mama ke kiranta. Ta fige ta lalace sosai.

Yasha fadawa ishaq cewa indai cikine yasa Mimi wannan abun to shikam a cire cikin domin xai iya xama da Mimi ko bata haihuwa ba. Ishaq na yawan kwantar masa da hankali cewa, babu ruwan ciki lalura ce kawai Allah ya saukar mata, amma cikinta lfy qalau yake. Abun dai gwanin tausayi dan sun daina ta cikin balle a aunashi ko bashi kulawa, kawai ta lfyar Mimi suke.

Xuwa yanxu yan aikin gidan sun gama fuskantar matsalar madam din tasu, suna xuwa dubata kuma kowa yana mata adduar data dace da addininsa. Baqo ya sami Bature da xancen ciwon Mimi bana asibiti bane yana ganin aljanu ke shafarta. Bature ya balbale Baqo da fada kamar ya dakeshi yana cewa "karya qara kirawa matarsa aljanu, shi matarsa bata da aljanu laulayin ciki take in kuma ya kuma cewa tana da iska to a bakin aikinsa." ya sunkuyar da kai yana bashi haquri, a xuciyarsa kuma yayi masa uxuri domin shi kansa Baturen ya xama kamar wani zararre.

Baba me gadinsu yaxo har daki duba Mimi wani yamma daya jiwo ihunta akan ciwon qafar, ya dunga kallonta cikin tausayawa. Ya kwantar da halshe da hikima irinta manya yace da Bature "Alhaji inaga yarinyar nan kamar akwai sammu acikin lamarinta, dan da ace ciwon asibitine xuwa wannan lokaci da ko bata samu lfy gaba daya ba yaci ace ta samu saukin wani abun." Bature ya dubeshi yayi shiru, Baba mai gadi ya dora da cewa "duk wanda yayiwa wannan yarinyar mugun abu yacika marar imani, wannan yarinya meta sani in banda kyauta tawa wadanda suke tare? Lallai duniya taxo qarshe indai har xa a Jefe irinsu haj maryam" Bature ya tsaidashi cikin gaxa sauraran maganganunsa, darajar furfurarsa ya gyaleshi donshi ya tsani ace ciwon Mimi bana asibiti bane. Yace "Baba addua kawai xakai mata Allah ya yaye mata" Baba yace "xan temaka alh dan shine hanyar da xan nunawa madam alherin da tayi mana kenan, xan dunga bada tofi ana kawo mata Kullum tasha a shafa mata a qafar" Bature yace "to angode Baba" ya fita daga falon, shi kuma ya sauke ajiyar xuciya dan dama ya matsu yabar gurin dan ya shafawa Mimi maganinta na ciwon qafar. Ya matsa kusa da Wll chair din ya taba kafadarta, ta dago idonta da suka kuma fitowa sabida ramar da tayi tana kallonsa. Yace "sannu maryam, Allah ya yaye miki ya mayar kaffara ya tashi kafadarki" tace "ya Bature na gurgunce ko?" ya sumbaci bakinta yace "maryam ko da qafa ko babu qafa ina sonki a haka, ki daina maganar gurguncewa kinji" tace "to, amma yaushe mama xataxo? Banaso in mutu ban nemi yafiyarta ba" yace "maryam baxaki mutu yanxu ba in shaa Allah, sai kin haife wannan cikin na jikinki kin shayarmun da Dana nononki yayi koyi da kyawawan halayenki" tai shiru tana kallonsa kawai, yaci gaba da yimata hira me dadi tana murmushi.

Haka rayuwa tacigaba, Mimi ciwo shi kuma damuwa, sau tari a office sai yayi aiki ya tura gaba sai a dawo masa dashi ace da gyara duk kuwa da kwarewa irin tasa. Sai ya xauna ya gyara ko mr Alex yasa a gyara, sarai yasan abunda ke damun sulaiman matsalar ciwon matarsa ne, yana tausayinsa kuma yana yawan kwantar masa da hankali cewa xata warke da xarar ta haihu. Kuma yaje har gida duba Mimi shi da family dinsa. Anata bangaren Hanifa tasan matsalar sulaiman sarai don sunsan Mimi babu lfy ta hanyar wacce suke bawa kudi take musu bincike akan Mimi din. Ta damu kwarai da damuwar da sulaiman ke ciki don duk ya bushe ya xama wani soko danma dan gayu ne me tsafta. Tana labewa tai kukanta ta share hawaye don tasan ciwon Mimi ne silar wannan hali da yake ciki kuma ita tana kukane don sulaiman amma badan halin da suka jefa Mimi ciki ba. Yanxu ta tabbatar sulaiman ba qaramin so yakewa Mimi ba tunda har ya shiga wannan yanayin a dalilin cutarta kawai ina ga tashiga duniya da sunan hauka? Anya shima baxai haukace ba kuwa? Bataso ciwon Mimi ya tsaya anan ba don tasan uwargida cewa tai musu hauka xatai kamar yadda magennan tayi amma kash ya akai abun ya tsaya iya ciwon qafa kawai? Lallai Mimi nada qarfin jini, amma baxatai gajen haquri ba Kullum tana kasa kunne taji yar rahotanta taxo mata da labarin haukacewar Mimi tasan a lokacin dole inyayi haukansa na wucin gadi ya haqura sannan hankalinsa ya dawo kanta, a lokacin xasu faracin duniyarsu da tsinke.

wannan shine tunanin Hanifa a Kullum.

Ya Taheer ya samu Bature da xancen kodai xa a fadawa iyayensu halin da Mimi ke ciki. Sulaiman ya futttuke ya dunga fada shifa a kyale masa matarsa ciwonta ba wani seroius bane just laulayin ciki ne, kuma suna addua suna xuwa asibiti kuma ya saka ana mata sauka Kullum a masallaci. Ya Taheer ya dunga kallon yadda sulaiman ke masa masifa kamar ada can ba girmamawa ce tsakaninsu ba, lallai ciwon maryam dab yake da saka SULAIMAN hauka. Ala dole ya haqura domin bayan ya gama fadan sai kuma ya dawo lallashi da roqon Taheer din karya bari mutan kano suji, a cewarsa in sukaji xasu karbe maryam shikuma bazai iya rabuwa da itaba a halin yanxu don in yarabu da ita yaci amanar soyayyar da sukewa juna, bayan haka kuma besan son Mimi ya masa mummunan kamu ba sai yanxu da take cikin lalura. Ya Taheer ya haqura, haqiqa suna cikin jarraba yana mugun tausayawa yan qannan nasa sulaiman da maryam.

Mai gadi ya fara kawo ruwan tofi kamar yadda yayi alqawari, amma Aisha yake bawa domin ya lura ogan nasu bayason irin wadannan abubuwan. Inya bata ita kuma takan saka pure xuma ta bawa Mimi tasha kuma ta shafe mata qafar dashi. Abun yaxo mata da sauqi don Mimi duk abunda akace tayi yi take babu musu domin brain dinta kamar ta yara ta koma, yaro dan shekara 3 na iya juyata.

Ayoyin qur anine na karya sihiri da ayyatushshifa yake mata safe da yamma, kuma Aisha kansata agaba taita karanta mata qur ani da ayoyin korar aljanu. Yarinyar nason Mimi sosai, ita ke kula da ita da duk wani shaaninta, da ita din barauniyace da tayi arxiqi a wannan tsakanin don itake gyara kayan Mimi haka xataita cin karo da kudi tana bawa Bature. Amma abunda Mimi tai mata na alkhairi baxai barta ta saka mata da sharri ba. Domin Mimi ce ta biyawa mahaifiyarta kudin aikin ido wanda ta shekara 8 tana fama dashi sabida rashin gata, sannan ta biyawa Dan uwanta kudin makaranta wanda shima rashin gata yasa ya dena duk kuwa da brain din karatun da Allah ya bashi. Kana ta kwato mata takardar saki gurin mijinta daya saketa shekaru uku amma yaqi bada takadda sai ta tashi aure yace bai saketa ba, in ta kafe ya saketa yace ina sheda?. Abun ya dade yana damunta, amma daga haduwarsu da Mimi ta fada mata duk wannan matsalar daya bayan daya ta dunga yi mata maganinsu. A qarshe ta kai mijin kotu aka rubuta sammaci aka kai masa, dake Dan iskan qaryane yana ganin sammaci ya bada takaddar dan aiken kotu ya dawo da ita. Abu na qarshe wanda Mimi tai mata kwanaki kadan kafin ta fara ciwo shine : kwato mata yaranta guda 2 mata daga hannun ubansu ta danqawa uwar aishan kana ta bata 50k tace tai jari ta kula da kanta da jikokinta.

Wannan abu yayi mutuqar farantawa Aisha rai, kunsan uwa da Da sai Allah kuma dama yayan a wuyanta suke, sannan duk wannan alheri da Mimi tayi batajin ko sulaiman mijinta ya sani ita da aishan kawai suke sirrinsu. Ita kuwa ya xataiwa wannan baiwar Allah wacce tai matá wannan dinbin alheri butulci? Wlh tasan inbata sakawa Mimi ba sai Allah ya tambayeta. Gatan kowa Allah amma Aisha tana kallon Mimi a matsayin itace gatanta kuma babban jigo a rayuwarta, tanawa Mimi duk hidima a matsayin tanawa yayarta uwa daya uba daya.

Farida da su safna, anty Rabi kusan Kullum nan suke wuni kuma suna yabawa da kulawar Aisha ga Mimi.

Dake Qur'ani warakane sai gashi a hankali Mimi ta fara samun sauqi, ta dena digar da jini ta kunne kuma qafar kumburin ya Sabe sosai kadan ya rage sai dai bata takawa. Rashin maganar nan dai shine matsalar da kuma shirmen cewar mama na kiranta.

Bature yafi kowa murnar samun wannan sauki, ya kuma dagewa da kaita asibitin a zatonsa maganin asibitine yasa hakan. Kudi kuwa baisan abunda ya kashe ba Kullum cikin sadaka yake da sakawa ayi sauka Allah ya kawo sauqi. Kuma a hankali sauqin yana samuwa shima kuma ya fara maida hankali kan aikinsa.

Ya Taheer Kullum da safe saiya shigo duba Mimi kafin ya fita aiki, kuma ya yaba da saukin da ake cewa ta samu har yaga gaskiyar Bature daya hanasu fadar bata da lfy wa yan kano, ashe da sun fada da sunyi gaggawa tunda gashi sauqi Kullum samuwa yake.

Su Farida da safna sun dan rage shigowa kowacce ta samu xama a gidan mijinta a dalilin ganin sauqi ya samu. Farida sai a lokacin ta fara awon ciki don da bata faraba tunda babu nutsuwa.

Yammacin asabar liqis tana falo tana kallo da Aisha shi kuma yana cikin dakin batasan me yake ciki ba amma dai ya dade. Ta miqe tsaye tace da Aisha bara in gwada inga xan iya tafiya?

Aisha tace "a a madam bari inxo in riqeki karki fadi" tayi dan murmushi tace 'barni dai in gwada Aisha komai saida gwaji" ta fara takawa a hankali Aisha na binta a baya karta fadi, har qofar shiga bedroom din kana Aisha ta dawo tunda tasan yana ciki.

Ta shiga ciki a hankali take takawa tana dingishi, yana cikin bathroom yaji shigowar mutum yace "waye?" tunda yasan bamai shigowa ciki sai Aisha, a iya saninsa kuma Mimi bata tafiya sai an turata a kujera. Yacigaba da kiran waye? Amma shiru.

Kamar a mafarki yaga Mimi a bakin bathroom din yana cewa "maryam kece ko mafarki nake?" ya tsame hannunsa daga cikin kumfar da yake mata wankin undis dinta (pants da bra) ya dauraye ya matso jikinta yace "maryam ke kadai kika shigo? Lallai sauqi ya samu godia ta tabbata ga Allah." ya kamota ta xauna kan kujerar daya ajiye mata suna dan hira yana wankinsa.

Ta kalleshi xuciyarta cike da tausayinsa da sonsa tace "ya Bature kai kakemun wankin undis?" ta fada tana kwallah. Yace "common meye aciki Mimi luv dan nayi miki? Ada aike kikemun ko? Yanxu Allah ya kawomu lokaci nima ina miki aiba wani abu bane" ta share hawayenta, yana aikin suna jifan juna da murmushin luv har yagama sukai alwalar magrib suka fito.

Sosai sauki ya samu, kowa ya saki jiki don abunda ya rage kawai dawowar walwalarta.

Ranar monday da wuri ya fita aiki sabida suna da meeting, kuma Mimi tayo masa rakiya har bakin mota da dingishinta sai dayaga ta koma sannan ya shiga suka tafi.

Batare data xaunaba ta shiga bedroom ta koma bacci, Aisha tanata aikinta hadi da leqawa taga ko Mimi ta tashi ta kawo mata abinci amma taga bacci take. Har tagama komai Mimi na bacci, ta fitowa da mimin kayan da zata saka dan a tsarinta tana tashi take wanka kana ta yi break fast. Doguwar rigar atamfa mai laushi ta dakko mata, bataga Dan kwalin rigar ba so saita dakko mata kashka medium irin wanda ake dorawa saman doguwar rigar ta hada mata da atamfar ta ajiye a kusa da Mimi gefen gado. Kana ta fita gurin kitchen gurin moses inda suke haduwa gaba daya da ragowar ma'aikatan suna ganin yadda yake girki suna hira.

Dake hausawa sunce baya bata da kadan, Mimi cikin baccinta taji ya Bature na tashinta, ta farka a firgice ta kalleshi tace "harka dawo?" yace mata "eh" kawai ya zarce dayi mata wasannin soyayya. Ta xare jikinta don batason wannan harkar sam a halin yanxu tace masa bari nai wanka, ta dingisa ta wuce bathroom. Tana wanka tana tunanin meya dawo da ya Bature gida yanxu shi da yace mata yau meeting garesu? Da wannan tunani ta fito wankan, abun mamakin sai ta samu dakin wayam babu kowa, da sauke ajiyar xuciya a fili tace "dama nasan bazai dawo yanxu ba, May be mafarki nayi"

Ta shafa mai tana saka riga ta hangeshi kwance ta cikin madubi tsirara akan gado, gabanta yayi wata irin faduwa. Ta juyo taga gurin wayam, ta kuma kallon madubin ta hangoshi kwance. Hankalinta yayi wani irin tashi tayi yunqurin ihu amma ta kasa don bakinta ya sarqe.

Tana cikin wannan haline taga ya dunfarota, ta runtse ido tana so tayi ihu ko addua amma bakin ya rufe gam, dalilin ihunta kuwa ganin wannan mutumin mai nufota tsirara da nufin sex da ita al'aurarsa har qasa take wato takai gwiwarsa kuma wai sex xeyi da ita. A fuskarsa dai kamannin mijinta sak, amma tasan mijinta bashi da wannan mummunar Al aurar. Allah ya temaketa ta yunqura ta miqe tare da xarar mayafinta tai waje da gudu. Tafiya take tana waige amma ga mamakinta binta yake tsirara yana dariya.

Ta nufi gate dake brain din irinta yarace wai saita nufi office din su Bature a nufinta taje taga shine wanda ke binta koba shi bane. Me gadi ya bude mata gate yana cewa 'sannu madam jiki yayi kyau, gidan alh ishaq xaki leqa kenan?" ta fita ba tare data tankashiba sabida hankalinta yayi gaba.

Ta tari napep a layin ta fada masa yakaita Company din NNPC. Ya fara tafiya da sauri don yaga alamar sauri take don suna tafiya tana waige. Ita kuma anata bangaren ya Bature take gani har yanxu yana binta kuma tsirara yana dariya ga mamakinta kuma sauri yake har yana wuce ababen hawan dake gudu kan titin.

Yana ajiyeta ta shige cikin ma aikatar da gudu, yana cewa hajia kudin bata saurareshi ba ita kawai burinta ta gujewa wannan dake binta kuma taje office din ya Bature taga shine koba shiba.

Sai dai abunda yayi mata cikas bata San office din nasa ba tunda bata taba xuwa ba, dan haka ta nufi babbbab hall din da suke meeeting inda ta hango jamian tsaro jibge gurin suna gadi.

Ta nemi shiga suka hanata tare da tambayar wacece ita, ta dunga nuna musu mutumin dake binta tare da ce musu gurin mijinta xata. Sukace ta tafi tabasu guri su basuga kowa ba, daya daga ciki yace "su kyaleta da alamar mahaukaciya ce"

Suna ta dauki ba dadi tsakaninsu da ita, su sun hanata shiga, ita kuma ta kafe saita shiga sabida wanine ke binta.

Daga cikin dakin meeting din suka farajin hayaniya tayi yawa, mr Alex ya tura Hanifa taje taga meke faruwa. Ta miqe dan cika umarninsa

Duk da tanada masaniyar abunda ke going amma sai datayi mamakin ganin Mimi anan tana fada da sojojin. Direct tace "ku barta ta wuce matar Eng SULAIMAN A AZEEZ ce, tana da tabin hankali" ta bawa Mimi hanya ta wuce tana wani shu'umin murmushi na cikar buri.

Tana shiga gurin ta fara cewa "ya Bature! Ya Bature!! Kana ina? Kaxo xai kasheni, ko kaine ka turoshi ya tsoratani?" Bature kansa sunkuye yana rubutu ya tsinci muryar Mimi tana fadar haka.

Ya tashi da sauri ya nufeta, tuni ta fita hayyacinta sai maganganu take wanda rudi yasa baya gane abunda take fada. Duk gurin yayi shiru ita kawai ake sauraro, Hanifa na tsaye jikin qofa tana murnar Mimi fa lokaci yayi domin da alama hauka ya kankama.

Yaje ya riqeta yana girgixata da cewa "Mimi ki dawo cikin hankalinki plz, waye xai kaaheki? Meya kawoki nan?" ta dubeshi ta kuma dubi me kama dashi wanda har yanxu take ganinsa yana mata dariya tare da kiranta da "taho Mimi luv nine ya Baturenki" ta dunga kallonsu a tare, ta rasa waye na gaskiyar, take anan kwakwalwarta ta juye ta kwallah qara ta xube qasa sumammiya.

Wadanda ke gurin suka taso xasu tayashi daukarta, ya tsaidasu da cewa xai iya. Ya ciccibeta cikin rashin sa a mayafin dake rufe kanta ya xame ya fadi qasa, tsautsayi yasa ya takashi bai saniba aikuwa satsin tiles dana mayafin ya kwasheshi yayi qasa ya fadi Mimi dake hannunsa kuma ta fadi gefe wanwar kan cikinta.

Qarar faduwarta da kiran sunanta da yayi a tare suka fito, beyi ta nasa faduwanba ya nufeta a gigice yana girgixata da fadin "maryam ki tashi, maryam ki taimakeni ki bude ido" duk wanda ke gurin sai da ya tausaya masa ciki kuwa harda Hanifa da itace silar faruwar komai.

Akayo kansu gaba daya ana masa sannnu cikin sauri ya dakko wayarsa ya kira ya Taheer da ishaq a taqaice ya fada musu abunda ke faruwa.

Suna tsaye cirko cirko yayin da Bature ke tsugune gaban Mimi da bata motsi yana kuka haiqan ya Taheer ya iso. Ya dudduba Mimi shima take ya fara hawaye don gani yake Mimi ta mutu. Isowar ishaq yasa suka tsagaita da kukan, ya tsuguna ya dinga chaje Mimi, ya dago yace musu tana da rai tabbas. Ya Taheer cikin hanxari yace "to sulaiman inaga a sada yarinyar nan da iyayenta tunda har abun yakai haka ta fara fitowa." ishaq yace hakane yafi dacewa.

Bature badan yaso ba ya yadda, Taheer yace bari yaje ya samo tiket. Ishaq kuma ya fara bata taimakon gaggawa don numfashinta ya dawo.

Mr Alex ya matso cikin tausayawa yace "ya bada jet dinsa akaita" Bature yaji dadi sosai sukai godia, nan take ya kira pilot din yazo da jet din, Aka dora Mimi kan gadon marasa lfy ishaq ya juna mata drip da oxygen Taheer da Bature suka shiga jet din ya daga xuwa kano.

Meeting din daba a qarasa ba kenan, akaita jimamin halin da matar Eng sulaiman ke ciki.

Ishaq be koma asibiti ba gida ya nufa.

Hanifa kuma gwaggoriya ta kira ta fada mata abunda ya faru cikin farinciki amma bataji dadin tafiya da Mimi kano da akaiba. Gwaggoriya ta kwantar mata da hankali cewa ai a kano sai tafi nesa da sulaiman don tasan yana kaita zai juyo ya dawo Abuja sabida aikinsa ita kuma acan xata sulale ta gudu ta shiga dawa. Hankalin Hanifa ya kwanta da jawabin gwaggoriya ta bar damuwa data fita har sadaka tayi murnar aikinta yaci, kuji kwaba yan uwa wai layya da kare.

Mrs Hajia 😊 [9/30, 1:05 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

Writing & story by Rahmatullah Muhammad (hajia)

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 6⃣0⃣

Ishaq yana isa gida ya samu Farida har bed room tana shirin wanka daure da towel. Babu sallama ya balbaleta da masifar cewa tana ina har Mimi ta fita taje office din sulaiman sabida tsabar shashanci da sakaci irin nata?

Farida ta tambayeshi cikin rudewa da neman maimaita mata abunda yace Mimi tayi. Cikin masifa kamar xai daketa ya fada mata duk yadda akai.

Ya dakata da fadan da yake dai dai lokacin da yaga Farida tayi xaman yan bori tana ihun kukan kiran sunan Mimi dan Allah a temaketa a dawo da mata da Mimi.

Ai tuni ya dena fadan ya dawo lallashin Farida da fada mata Mimi yanxu an wuce da ita kano kuma xata samu sauqi in shaa Allah. Shima dai a ranar aiki ya sameshi don farida taqici taqi sha sai kuka da kiran sunan Mimi da kuma cewa lallai saiya kaita kano itama dan gani take Mimi mutuwa tai suke boyewa. Haka ya yini lallashinta har bayan sallar asr.

Ya yiwa Baqo waya yace ya tattaro masa duk masu aikin gidan su sameshi anasa gidan.

Cikin qanqanin lokaci sukaxo suka sameshi, ya dunga binsu da kallo yana kada qafa, mugun haushinsu yakeji kamar ya tashi ya rufesu da duka.

Ya fara magana cikin qunar rai "abun takaici ne ace duk yawanku a cikin gida har maryam ta sulale ta fice baku sani ba, bayan kudin kunsan tana da lalura ba a rufe muku ba" suka rude da jimami da kalaman kare kansu na basusan fitar madam ba.

Ya daka musu tsawa da cewa suyi masa shiru, sukai tsit suna sauraransa yace "sakamakon abunda sakacinsu ya haifar antafi da maryam kano, dalilin haka ni kuma na koreku aiki gaba dayanku." falon ya cika da koke kokensu, farida tana zaune tana jinsu batasa baki ba idonta yayi jajur sabida kukan data yini yi.

Ya daka musu tsawar cewa su bace mai da gani, suka tashi jiki a sanyaye suka dunga fita Aisha ce kadai ta rage. Ishaq ya kalleta yace "ke xaman me kike?" ta matso kusa da qafafunsa cikin kuka tace "Dan Allah Alh kayi haquri, wlh lokacin dana bar madam bacci takeyi, sai yanxu da kaxo da lbrin abunda ya faru. Nidai kasani motar kano yanxu in bita can in tayasu jinyarta badon a bani kudi ba, sai don rama dinbin alkhairin da tayi yimun" ishaq yayi dan jim, Farida ta dafashi "ya ishaq ka kyaleta ita, amanace sosai tsakaninsu da Mimi" yace "to shikenan kije xuwa da safe sai inkaiki tasha ki tafi kano dan yanxu dare yayi."

KANO

Isarsu direct Aminu kano teaching hospital (AKTH) suka sauka. Dake abun na manya ne da gaggawa aka amshesu aka wuce da ita A&E. Likitocin emergency suka rufu kanta a qoqarin neman numfashinta.

Ya Taheer shi yayi waya ya sanar da gidajensu halin da ake ciki dan Bature bashi da nutsuwar haka, duk nacin likitocin da ya fita ya basu gurin suyi aikinsu amma dole suka kyaleshi domin yaqi fita qememe.

Faty wacce ta zama metro a halin yanxu ta riga kowa isowa don tana cikin asibiti wayar mama ta sameta tana kuka ta fada mata ankawo Mimi yanxu bata da lfy.

Ta tsaya akan Mimi tana taya likitocin aikinsu, suma sun qara bawa Mimi kulawa da suka gane sis din metro Faty ce. Aka bawa Bature takaddar biyan kudin gado da sauran charges din yaje ya biya. Amma qememe yaqi fita sai ya Taheer ne yaje ya biya aka bata gado.

Likitocin suka fito dan ansamu komai ya dawo normal amma tana bacci. Lokacin mumy, mama Dady da Baffa sun iso hankalinsu tashe. Faty ke musu bayanin Mimi ta samu bacci yanxu.

Suka dunguma dakin hankalinsu tashe yake har yanxu, mumy keta tambayar Taheer wane ciwone wannan farat daya Mimi tai wannan uwar rama kuma har aka kawota gida?

Sun sami Bature a dakin yana zaune gefen gadon hannunsa riqe hannun Mimi. Sai da suka xauna suka nutsu kana ya Taheer ya bude musu komai tun farkon ciwon har kawo yau.

Sukai jugum jugum suna sauraransa, mumy ta kalli ya Taheer tace "amma Taheer kaci amanarmu a matsayinka na babba a tsakaninsu, don sulaiman bashi da hankalu kaima baka dashi kenan? Marainiyar Allah bata da lfy kusan 3wks ku hada baki ku rufe mana? Nagode kwarai Taheer wlh in maryam ta mutu saina daureku kaida sulaiman"

Taheer ya gigice yana bawa mumy haquri, bai zaci xata dau abun da zafi haka ba.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull