Asanadin makwabtaka book 2 by zee bature - Chapter 64
Asanadin makwabtaka book 2 by zee bature Chapter 64: Asanadin makwabtaka book 2 by zee bature Chapter 64. Bayan sun gama wayar Kawu Amadu ta kira har saida…
4,498 words
Bayan sun gama wayar Kawu Amadu ta kira har saida ta kusa yankewa sannan ya d'aga ta gaishe dashi yana yar dariya yace "Amaryar mu kun tashi lafiya" amsa mashi tay da lafiya lou suma ta tambayi ya suka tashi yace mata lafiya, jin ta d'an yi shiru yasa shi tambayar ta lafiya dai ko cikin yar in ina tace mashi dama don Allah so take ta rok'e shi ya kawo mata jakarta ta makaranta, farko cewa yay shi ba zai kawo ba ta marairaice tana rok'on shi k'arshe sai cewa tay shikenan bari tazo ta d'auka da kanta yana dariya yace ai dama yana cikin shago ya sake ya ganta sai ya zane ta kuma da tsallan kwad'o zai maida ta, itama dariyar take a hankali tace mashi ai yanzu ta wuce wannan a wurin shi yace eh lalle ta isa shi take gaya ma haka ko to ta gwada fitowar zata sha mamaki, rok'on shi ta k'ara yi yace bari ya kawo mata tay mashi godiya ta tambayi gwaggo yace ta na cikin gida, bayan sun gama wayar d'an jimm tay tana son kiran gwaggo amman kunya take ji, can dai tay dialing lambar ta ta fara ringing, bayan ta d'aga a kunyace ta gaishe da ita tana murmushi ta amsa tay mata sun tashi lafiya da tambayar d'anta Haisam Fatun tace mata yana parlor tace to ta gaishe mata da shi tace to, d'an shiru sukai can gwaggon ta ce badai wata matsala ko da sauri tace mata eh ba komai, tambayar ta tay wai ta fad'a ma baffanta zancen gwaggon tay yar dariya tace ta fad'a mashi mana yayi farinciki sosae ma, cikin yar shagwa6a tace amman shine bai kirata ba tace k'ilan ya bari sai an samu natsuwa ne, bayan sun gama ta shiga kiran Baffan nata cikin sa'a ta shiga ya d'aga ta gaishe da shi yana murmushi ya amsa ya tambayi ya take ita da maigidan nata, cike da shagwa6a tace "Baffa shine kasani amman baka kira ni ba gaba d'aya ma ka manta dani" yar dariya yayi "haba ni na isa in manta da inna wuro gaba d'aya, dama zan kira na bari a nutsu tukun, na matuk'ar yin farin ciki da jin abun Alkhairi wllh har bazan iya kwatanta maki ba ashe dai rabon shine mijin naki yasa komae ya faru, kinga sakamakon yi ma iyaye biyayya Allah ya juya komai, Nagode inna wuro ina matuk'ar Alfahari dake matsayin jinina, ina rok'on Allah ya k'ara ma rayuwar ku Albarka ya jikan Mahaifiyar ku" har k'walla sun taru a idanun ta ta amsa mashi da Amin, tambayar ya karatun ta yay tace mashi Alhamdulillah yace Allah ya bada sa'a, bayan ta amsa ta tambaye shi Yadikko yace tana d'aki bari ya mik'a mata tace to, bayan ya kai ma Yadikkon cike da Farinciki tana washe baki suka gaisa tana fad'in Amaryar su, tambayar ya gida da Angon ta tay Fatun ta amsa mata ta shiga yi mata Allah yasa Alkhairi da nuna yadda tay murna da Al'amarin tace Addu'ar da suke tayi ce Allah ya amsa taji mata dad'i sosae wllh da Al'amarin ya juye haka dama haka take ta fata, daga jin yadda take Maganar Fatuu ta fahimci ba k'aramin farinciki take ba, tambayar ta su Mino tay tace basu kaiga dawowa daga islamiyya ba tace to in sun dawo zata kira ta tambayi yaushe zasu zo tace suna nan zuwa in ta Haihu, a shagwa6e tace a'a ita dae bata yarda ba wllh tana dariya tace suna nan zuwa bada dad'ewa ba, bayan sun gama Magana da Yadikkon ta ba Baffan wayan suka cigaba nan yake tambayar ta Haisam yace bai da Lambar shi yana son yi mashi godiya tace ai yana nan ko a kai mashi yace to, mik'ewa tay da sauri ta nufi hanyar fita, Yana kishingid'e kan kujera ta tunkaro shi Wayar kare a kunnanta, tana zuwa daga gefe ta tsaya ta cire wayar daga kunnan ta a hankali tace mashi Baffan ta ne yake son Magana da shi ya d'an d'aga mata kai ta mik'a mashi wayar ya amsa, gyara zama yay a nutse ya gaisa da shi nan ya hau yi mashi godiya sosae da Addu'oi, k'asa k'asa yake amsa wasu wasu kuma yay shiru daga baya sukai sallama ya mik'a mata phone d'in idon shi cikin nata da d'an murmushi ta amsa ta maida ta kunnan ta, har ta juya kaman zata tafi sai kuma ta dakata tana tambayar Baffan yaushe zasu zo to jin yana mata sallama yace mata ba yanzu ba sai an d'an jima, aikuwa cike da shagwa6a ta hau Jujjuya jiki tana ita dae bata yarda ba don Allah su zo kwanan nan kai kace da gayya take juya jikin saidae ita bata ma san tana yi ba kuma da alama ma ta manta da a gaban Haisam d'in take, shi kuwa kafe bayan nata yay da ido da wani kalan expression mai wuyar fassaruwa yake kallon nata, bayan sun yi sallama ta juyo suka had'a ido ta sakar mashi d'an murmushi shima ya d'an yi mata, juyawa tay zata tafi taji yace in ta gama abunda take zasu gaishe da Hajiya ta juyo tace mashi to sannan ta tafi, tana komawa Bedroom d'in bada jimawa ba akai knocking kopar ya bada izinin shigowa, Amadu ne ya shigo ruk'e da jakar Fatun da d'an murmushi ya nufi cikin parlon ya tsaya daga gefe yana gaishe da Haisam d'in, bayan ya amsa ya nuna mashi armchair yace ya zauna mana, mik'ewa yay ya nufi hanyar Bedroom d'in da alama kiran ta zai yi, yana tura kopar daidai ta kawo bakin kopar zata bud'e ta yafo mayafi golden da ta sa jiya da yake a atamfar akwae golden brown harda takalman da ta saka jiyan mahad'in gyalen half cover masu tsini sun k'ara mata tsawo ta tattara gashin ta a baya ta sa red ribbom sai yayi kaman ta saka hular gashi don ya rufe gefe da gefen fuskar, tura kopar da yay ta buge mata goshi da sauri taja baya had'i da sa hannu guda ta dafe wurin da ta bugen, bai yi zaton tana a bakin kopar ba yay moving zuwa inda take tsaye ya kai hannu ya cire hannun ta da ta dafe goshin wurin har ya d'an canza kala, bin wurin yay da kallo ya kasa furta komae don gaba d'aya wata irin kasala yaji ta fara saukar mashi sakamakon K'amshin ta da ya cika mashi hanci, jin yayi shiru yasa ta d'aga ido ta kalle shi suka sauka cikin nashi nan take gabanta ya fad'i ganin irin kallon da yake mata da sauri ta sauke idon ta k'asa, d'ayan hannun nashi slowly ya zagaya dashi bayan ta ya matso da ita suka had'e da juna nan take wutar Fatuu ta d'auke ta fara shiga wani irin yanayi dama kuma a tsume take har saida ta d'an runtse ido, jikinta ne ya canza wata irin kasala ta baibaiye ta wani abu ya fara mata yawo a jiki ga k'afafuwan ta na neman kasa d'aukarta, sauke gudan hannun shi da ke ruk'e da natan yay k'asa ya d'an sunkuyar da face d'in shi Slowly ya d'an fara matsawa da ita saitin tata, jin saukar breathing d'in shi a gab da Fuskar ta yasata d'agowa da sauri har saida gabanta yay wani irin bugu ganin fuskar shi kusan saura kad'an ta had'e da tata, wani irin kallo mai wuyar fassarawa suka shiga bin juna da shi, da k'yar Fatuu ke daurewa gudun kada ta zaqe don ta kai wata ga6a da take neman rasa control idanun ta har sun fara lumshewa sai k'ok'arin daidaita su take amman abun yaci tura kawae sai ta rufe su gaba d'aya, bin dogayen eye lashes d'in ta yay da kallo sai d'an far far suke sakamakon idanun nata dake motsi, numfashin ta ne ya nemi tsayawa jin ya had'e faces d'in su nan take jikinta ya fara d'an rawa ta koma yin numfashi da sauri da sauri shima nashi da d'an k'arfi yake fita yana had'uwa da nata, sun d'an d'auki lokaci a haka suna ta shak'ar scent d'in juna, can ya janye fuskar ta shi a hankali ya maidata gefen tata ta yadda kwantaccen sajen shi ya had'e da gefen tata fuskar cikin wata irin murya mai fuzgar mai sauraro ya furta "am sorry, bansan kina a wurin ba...." Kasa ko d'aga mashi kai Fatuu tay idonta still na a rufe taji ya k'ara furta "Uncle d'in ki na jiran ki a parlor" yana yin Maganar ya d'ago ya cire hannun shi dake tallabe da ita ya juya ya nufi hanyar Laundry ba tare da ya ko kalleta ba, da k'yar ta d'an bud'e idanun ta da suka gama canza kala tabi bayan shi da kallo kar ya shige ya rufe kopar, kasa cigaba da tsayuwar tay don gaba d'aya jikinta ya gama mutuwa da k'yar ta ja jiki zuwa bakin gado ta zauna dabas still breathing heavily, hannu tasa ta dafe goshin ta ta d'an sadda kai, ita kad'ai tasan mi take ji a jikinta, da k'yar ta fara k'ok'arin daidaita kanta tunowa da yace Kawu Amadu na a parlor, mik'ewa tay jiki a mace ta nufi kopar ta bud'e, bayan ta fito saida ta k'ara tsayawa a cikin Corridor ta k'ara daidaita natsuwar ta sannan ta nufo cikin parlon, tana shiga suka had'a ido ta fara mashi murmushi wanda yafi kama dana yak'e shima d'an murmushin yake mata ta nufi inda yake, a d'ayar armchair d'in ta zauna ta gaishe da shi ya amsa shiru ta biyo baya don sai taji kaman muryar ta ba a daidai take ba, hannu ya kai ya d'aukko bag pack d'in daga k'asa ya d'auro ta kan hannun kujera yace mata ga ta nan da k'yar tace mashi ta gode, ganin ya mik'e alamar tafiya zai yi yasa cikin yar rawar murya tace don Allah ya tsaya yay breakfast yay mata wani kallo mai kaman harara ya juya ya tafi ta k'ara ce mashi ta gode ya d'aga mata kai kawae lokacin ya bud'e kopar ya fita, zaune tay turus tama rasa mi yake mata dad'i a hankali ta d'aga ido ta kallo kopar Bedroom d'in ta shiga tunanin zuwa zatai tay mashi magana su tafi ko kuwa, ji tay bazata iya zuwan ba tay zaune zuciyar ta na tariyo mata abunda ya faru a tsakanin su, tana haka bayan wani lokaci taji k'arar bud'e kopar Bedroom d'in aikuwa da sauri ta sunkuyar da kanta k'asa, nufo cikin parlon yay idon shi akanta ya tsaya daga gefen ta taji yace zasu iya tafiya sai lokacin ta d'ago ta kalle shi ta d'an d'aga mashi kai, mik'ewa tay har zai juya sai kuma ya dakata ya juyo yana kallon ta ta d'an kawar da fuskar ta, "How are feeling, ko wurin na ciwo muje Hospital?" D'an kallon shi tay had'i da girgiza kai a hankali tace a'a yama daina zafin ya jinjina kai yay gaba ta bi bayan shi a ranta ta shiga raya kenan duk abunda yay mata d'azun ban hak'uri ne Saboda ya buge ta, yana gaba tana biye dashi suka shigo harabar gidan, suna cikin tafiyar ta kai idon ta can gefe wurin parking space ta hangi d'awisu ya bud'e jikin shi yana kuka gwanin burgewa, murmushi Fatuu ta saki tunowa da can baya lokacin da ta kawo ma shi Fruit na karin ciwo ta iske zashi Masallaci har suka fito tare ta tsaya a harabar tana ma d'awisun wasa shi kuma ya nufi hanyar Masallacin yana d'an d'angyasa k'afa Saboda raunin da yaji da kwalba, gab da zai shiga ta kware murya tace Ya Handsome kayi man Addu'a Allah yasa in zama likita ya d'aga mata kai ba tare da ya juyowa ba, fad'ad'a murmushi tay bata ta6a kawo wa a ranta wai zasu yi aure ba don ita auren ma bai gabanta a lokacin duk da kuruciya, ko ba aure a tsakanin su Haisam nada daraja a wurinta ta silar shi ne ta san kanta ko lokacin da ta kasa mashi uzuri da abu ya Faru tsakanin su harda girman da yake da shi yasa duk da tana tunanin laifi yayi mata amman bata son girman shi ya fad'i ne gashi hakan ba K'aramin karya mata zuciya yay ba don tana ganin ita tana k'aunar shi shi kuma sha'awar ta yake ashe duk ba haka bane, Kallon bayan shi taci gaba da yi wata irin k'aunar shi na ratsa mata zuciya har tana d'an yin murmushi a haka har suka k'araso part d'in suka shiga,
lokacin da suka shiga basu samu kowa a cikin parlon ba an dai gyara shi fess sai k'amshi ke tashi, Hanyar Bedroom d'in ta ya nufa ta bi bayan shi, knocking kopar ya d'an yi daga ciki ta bada izinin a shiga ya tura da yar sallama ya shiga, tana zaune a bakin gado idanunta sanye cikin glasses hannunta ruk'e da Littafin Addini tana dubawa bata dad'e da komawa cikin d'akin ba bayan ta yi Breakfast, d'ago ido tay ta kalle shi tana niyyar yin Magana Fatuu ma ta shigo da sallama Hajiya ta saki murmushi tana amsa mata kafin tace "Maraba da Amaryar mu" d'an sadda kai tay Hajiyar ta nuna mata gefen ta da hannu alamar tazo ta zauna, tsaye Haisam yay daga gaban gadon bai zauna ba ya gaishe da ita ta amsa tay mashi an tashi lafiya, kai idon ta tay kan Fatuu da ta d'an sunnar da kai da murmushi tace "Amarya an tashi lafiya ya bak'unta kuma?" a hankali tace Lafiya lou,
"Ba dai yar kunya muka fara dake ba" Hajiya ta tambaya tana murmushi hakan yasa Fatun d'agowa itama murmushin ne akan fuskar ta a hankali tace mata a'a, "Yauwa to, ni ba surukar ki bace Kakar kice a hakan zaki cigaba da kallo na muci gaba da wasa da dariya kaman da, don ma yanzu anyi hankali natsuwa tazo an rage sani nishad'i" yar dariya Fatuu tay ba tace komai ba, kallon Haisam tay "Kai kayi tsaye kaman wani Security ka samu wuri mana ka zauna, ko gadin Matar taka kake?" Fuskar shi a sake kaman zai murmushi ya kalleta ta nuna mashi Stool a gaban mirror tace ya d'aukko shi sai ya zauna, yin yadda tace yayi suka d'an yi shiru kafin ta fara magana,
"Alhamdulillah, duk abunda Allah yayi mai kyau ne, a koda yaushe muna rok'on Alkhairi so duk abunda muka ga ya faru damu in ma mai kyau ko akasin hakan Alkhairi ne, Fateema ina maki barka da shigowa wannan Family don a yanzu kin zamo wani 6angare nashi, ina fata zaki d'auke mu a matsayin dangin ki, ki rungumi kowa matsayin dan'uwan ki duk da bani da shakku akan ki nasan ki farin sani nasan baki da matsala to sai kinyi hak'uri don shi mataki ne nasara ba kamar a yadda Auren naku ya kasance, dole daga baya za'a iya fuskantan yan matsaloli bama fata in sha Allahu muna fatan Allah zai shige mana gaba, sannan ina son ki saki jikin ki kada wai ko don kiga ga yadda akai auren naki ki takura kanki Ki k'i yin walwala, duk aure aure ne duk kuwa yadda aka yi shi ki walwala ki farinciki ki Alfahari da Auren, gidan mijin ki naki ne so ba buk'atar takura kai, duk yadda bani da haufi akan mijin ki ance wai zo mu zauna zo mu sa6a, so a duk lokacin da yay maki wani abu da baki ji dad'in shi ba ki k'ok'arin yi mashi Magana kada kice zaki bar abun a ranki duk d'an Adam ajizi ne zai iya yi maki laifi ba tare da ya ankare ba, ta hanyar yi mashi magana ne zai gane har ya gyara laifin shi, in kuma bai gyaran ba wanda bana tunanin hakan ni kizo ki sanar dani kar kiji wani abu, duk yay maki wani abun da kike tunanin fad'i ma wani don neman mafita ko shawara kizo wuri na kar kice zaki kai k'ara gidan ku hakan ba komai yake jazawa ba face matsala, zai iya maki abu kije ki fad'a daga baya ku shirya ki manta ma amman su kuma abun na nan a ran su watak'il su k'ullace shi ko makamancin hakan, don haka k'opa ta a bud'e take duk in kina da wata matsala kizo gun Hajiyar Sanata ki fad'a mata ni kuma in sha Allahu zanyi k'ok'arin ganin na daidaita komai, ina Fatan zaki cigaba da yi mashi biyayyar dana san kina mashi kada don ya zama mijin ki kice zaki rage kan hakan a'a a yanzu k'arawa ya kamata kiyi don muhimmancin shi a yanzu yafi na da ya tashi daga Yayan ki Handsome ya koma Mijin ki wanda Aljannar ki ke a tafin kafar shi" d'an dakatawa tay kan Fatuu a k'asa haka Haisam d'in Fuskar shi na a gefe,
"Na dawo gare ka Zakee manyan dawa, ga Fateema nan Amana ce a wurin ka duk da nasan kasan da hakan amman ina fad'a maka ne don kada ya zama ba wanda ya fad'a maka hakan, ka ruk'e ta Amana dama can kai kamar guardian ne a gare ta to yanzu matsayin ka ya koma biyu don haka sai ka linka komae, kuma don ta zama taka ba yana nufin ta zama baiwar ka ba duk kyautatawar da zaka yi mata lada zaka samu haka in har kaci zarafin ta ka munana mata tabbas zaka samu zunubi don haka ta zama taka ne don ka kyautata rayuwar ta, sannan ina son jan hankalin ka kayi k'ok'arin zama adali ga matan ka nasan ba sai nayi maka bayanin yadda zaka zama adali ba kasan miye yin Adalci tsakanin mutane, idan har ka za6i yin rashin Adalci to ka bud'e ma kanka da kanka kopar matsalolin da zasu hana maka kwanciyar hankali ga kuma zunubi a wurin ubangiji, a k'arshe ina Addu'ar Allah yasa Albarka a Auren ku ya kauda duk wata fitina, yasa ya zame maku silar shiga Aljanna gaba d'ayan ku, Amin ya Rabbi" a hankali Haisam ya amsa da Amin Fatuu kuma a cikin rai ta amsa Hajiya ta kai hannu ta d'an bugi shoulder d'in ta tace ita bazata amsa ba ta d'ago tana yar dariya tace ai ta amsa,
"Oh Fateema ni wannan in nayi sakaci ban yi da gaske ba yar gaisuwar da nike samu yana zuwa ma ai sai ki hana shi ya tattara ni ya zuba a dustbin" cikin rashin Fahimta Fatun ta d'an waro ido Hajiya taci gaba "eh mana, kina irin wannan kwalliyar ina zai rink'a tunawa da wata tsohuwar matar shi..." Tun kan ta rufe baki Fatun tasa tafukan hannuwan ta ta rufe fuska Hajiyar nata dariya, a hankali Haisam ya d'ago ya kalli Fatun suka had'a ido da Hajiya ta d'an harare shi cikin wasa yay d'an guntun murmushi ya juyar da fuskar shi gefe,
"Yanzu dae ki bani cin hanci sai in yafe maki shi in kuma fad'a maki abubuwan da zasu sa ki kama shi a hannu" cire tafukan hannuwan tay tana murmushi bata ce komai ba, mik'ewa yay yace ma Hajiyar zai d'an je G.r.a tace a dawo lafiya ya nufi hanyar fita, kallon Fatuu Hajiya tay ta d'an kai mata bugu tace bazaki tashi ki raka shi ba yaran zamani duk baku san abunda ke sa ana kama miji ba, mik'ewa tay a kunyace ta nufi hanyar fita Hajiya ta bita da ido tana murmushi a ranta ta ayyana Allah kenan gwanin hikima, wasu mutanen na shigowa rayuwar mu ne in ma su amfane mu ko mu mu amfane su, wasu su tsaya wasu kuma su tafi bayan sun taka rawar da zasu taka, a fili ta furta "Allah kasa Mudace", tana fitowa har ya kusan fita daga parlon taja ta tsaya a bakin corridor, kamar yaji a jikin shi ya juyo suka had'a ido, dakatawa yay ganin haka yasa ta nufe shi walking slowly, a d'an gaban shi ta tsaya tana bin shi da kallo ganin ya kafeta da ido yasa cikin yar inda inda tace "D...dama Hajiya ce tace in rako ka" da k'yar ta kai Maganar Saboda kallon da yake bin ta dashi ba Arzik'i ta sunkuyar da kanta,
"Ok thanks, ki koma" taji yace ta d'ago, kai ta d'an d'aga mashi yana shirin juyawa tace "Sai ka dawo Allah ya tsare" dakatawa ya sake yi ganin yanayin fuskar shi kaman zai murmushi yasa itama ta d'an yi mashi, "Do you need something?" da sauri ta girgiza mashi kai alamar a'a ya d'aga kai ya wuce, saida taga fitar shi sannan ta juyo tana d'an sakin Murmushi ta nufi komawa Bedroom d'in Hajiya..............
*ASM Bk2064*
_Destiny may be delayed but cannot be changed...._
*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*
..........tana shiga tace mata ya tafi ta d'aga mata kai kafin tace eh a hankali , a inda ta tashi ta koma ta zauna Hajiya ta fara magana "irin nuna kulawa haka yana k'ara dank'on k'auna tsakanin ma'aurata, yanzu kinga kece abu na k'arshe da ya gani kafin ya fita to zaki ga kin tsaya mashi a ran shi yana tafiya yana tunanin ki har ma kiga yana d'an murmushi kaman ta6a66e, ba kamar yadda kika ci gayun nan" Dariya Fatuu ta saki ba kaman da tace kaman ta6a66e ta bata dariya sai Maganar ta tuno mata da Maganar Aunty Mareeya, itama hajiyar Dariyar take taci gaba "naji dad'i dana gan ki haka tsaf kin sha gayu wannan ma zai taimaka wurin siye zuciyar shi don shi mutum ne mai tsananin son tsafta nasan kin san da hakan, ga son k'amshi don haka ki dage da tsafta, amman fa kuma kar tay yawan da zaki janye man hankalin shi gaba d'aya" ta d'an ta6e baki, sosae Fatuu ta saka dariya, cigaba tay bayan ta d'an murmusa,
"Komai nashi Sak kakan shi wllh, yana tuna man dashi a koda yaushe shiyasa bazan 6oye ba a duk jikokina nafi jin shi a raina kowa ma ya sani, hatta y'ay'an cikina ban jin su kaman yadda nake jin shi, Duk irin halayen shi na kakan shi ne, koda ake ganin Sojoji kaman basu da kirki basu da tausayi ba haka bane kowa da irin halin shi kaman dae a sauran mutane....." D'an dakatawa tay tana kallon hoton Gen. Adamu Zakee dake a jikin bango cikin shiga ta Alfarma, da gani akwae k'auna mai k'arfi a tsakanin su kuma rashin shi ba k'aramin ta6a mata zuciya yay ba,
"Shima haka yake da son K'amshi, ko 6ata mashi rai kikai in dae zaki je bashi hak'uri ya kasance kina sakin k'amshi to Magana ta k'are tuni zai yafe maki, koda ma ba ke kika 6ata ran ba in dae zaki rarrashe shi kina k'amshi yanzu ya saukko" idonta akan hoton take Maganar, tausayin ta ne ya kama Fatuu itama ta kai idon ta kan hoton ta d'an girgiza kai, bayan d'an wani lokaci Hajiya ta sauke idon ta tare da ajiyar zuciya, kallon ta Fatuu tay da d'an murmushi tace "Allah ubangiji ya jik'an shi da rahama yasa ya huta, Allah ya h....had'a ku a Aljanna" tana murmushi ta amsa da Amin sai kuma tace "muci gaba da soyewa acan ko?" Dariya Fatuu tay suka d'an yi shiru, can ta kalle ta tace bari taje wurin Aunty Saude ta taya ta aiki,
"to ke waya fad'a maki Amarya na wani aiki, ki zaman ki ki huta, ki k'yale ta tayi aikin ta lokacin yin aikin zai zo sai kita yi" shiru tay ta maida kanta k'asa, "in kina son zuwa kije k'yama k'ara koyon wasu abubuwan tunda Saude ba daga baya ba wurin iya girki tasan hannun ta, sai ki dage ki k'ara koya duk da ma Mijin naki ba gwanin cin Abinci bane, amman k'ilan ya rink'a cin na Matan shi" tana d'an murmushi ta mik'e zata tafi, har ta juya Hajiya ta dakatar da ita, "Yauwa na tuna, Maganar gyaran part d'in naku Tukur ne ke yi, to tun kafin ki tare yayi man magana kan zai cigaba ne ko a'a nace ya bari ki zo duk da dai shi Namiji ne ina ganin baida Matsala, amman ke ya kike so" d'an jimm Fatun tay ta rasa mi zata ce Hajiyan tace ta bud'e baki tay magana, a sanyaye tace duk yadda ta yanke yayi,
"Shi d'in ne ya nuna yana so, tun farko ma ni ba shi naso yayi aikin ba bayan Haisam d'in ya dawo sawa nayi ya nemo wani amman ya matsa, kwanaki har zaunar dashi nayi nai mashi Magana kan hakan tunda ko ni bai bari akai kayana wurin wanki ga Karatu lokacin amman sai cewa yay wai baida abunda zai saka mana sai dai hakan kawai, nace to mu duk abunda ya ga an yi masa ai don Allah ne ba wai don ya saka mana ba, dama can Allah ya k'addaro akwae rabon shi a tare da mu" ta k'arasa tana murmushi itama Fatun shi take yi, "Yanzu tunda naga ya nuna yana so ke ki rink'a gyara Bedroom da Kitchen ala bashshi shi sai ya rink'a gyara maki parlon tunda dama yana da girma ko in kin tafi Makaranta sai ya shiga ya gyara, Wankin k'ananun kayan mijin naki kuma kyaci gaba in zai mashi na manyan kaya sai yazo nan yay amfani da injin d'in nan, koma kawae bari na mashi magana tunda ga naki sun k'aru ya bari a rink'a kaiwa dry cleaning kawai", kallon Fatun tay "lafiya lou zaki rink'a gyara Bedroom d'in da Kitchen d'in ba takura tunda naga karatu kike?" Da sauri tace mata eh, a ranta ta raya ita da ke yin fin wannan aikin a gida wannan ai ba wani aiki bane, ce mata tay taje tayi mata godiya ta juya ta fita, Kitchen ta nufa a ciki ta iske Saude na shirye shiryen d'aura girkin rana, da yar sallama ta shiga ta juyo tana murmushi ta amsa mata ta nufi gefenta gaban drawer ta jingina fuskar ta da murmushi tace "Sannu da aiki Aunty Saude",
"Yauwa Amaryar mu kun shigo" kai ta d'aga mata suka d'an yi shiru,
"Aunty Saude aiki na zo taya ki" d'an waro ido tay "aiki kuma Fateema keda kike Amarya, ki rufa man Asiri kar nayi laifi" tana murmushi tace "kai Aunty Saude daga taya aiki sai yin laifi ai na fad'i ma Hajiya zan zo in taya kin" tace "to amman ai ina iya yin laifi wurin Angon naki yaga duka daga kawo mashi Amaryar shi jiya yanzu na saka ta aiki" d'an tura mata baki tay tana murmushi "Kai Aunty Saude shi ina ruwan shi kuma ma ai ya fita bai gidan"
"Ya kamata dai kije ki huta don kina buk'atar shi ansha hidima" still tura bakin ta k'ara tana kallon ta itama Sauden kallon ta tay tana yar dariya, Fatuu tace "ni dae na huta har na gaji ma" kafewa tay kan sai ta taya ta aikin girkin tace ai ta k'ara koya ma Sauden tace shikenan tunda ta kafe,