Kenza eBookz

Auren huce haushi complete - Chapter 18

Auren huce haushi complete - Chapter 18

Auren huce haushi complete Chapter 18: Auren huce haushi complete Chapter 18. "Ashe zan Miki dura wlh, sai kinci kuji min yarinya da kinibibi Wai so kike…

3,937 words

"Ashe zan Miki dura wlh, sai kinci kuji min yarinya da kinibibi Wai so kike da karfi sai kin koya min surutu ne? Kin iya kalato abin magana da wani bakinki chut". Ya fada yana shafo pink din lips dinta. Taci Amman ba wani na kirki ba da gaske abinci Bai dameta ba barta dai da 'yan ciye-ciye. Bayan sun gama ne ta kwshe kayan ta gyara gurin duk Yana kallonta komai tayi kyau yake mata gata ba wata babba ba sai dai akwai Sama da kasa masha Allah. Lokacin data gama ne ya yafito ta da hannu,a hankali ta nufo shi kamar me counting steps sai rausaya take, wani yawu ya hadiye, Dan risinawa tayi a gabansa duka hannuwanta ya kamo ya zaunar da it kusa dashi. "Zaki rakani unguwa?" Ya fada Yana zame Mata veil din da tayi rolling gashinta ne ya bayyana biki sidik dashi sai walqiya yake yasha gyara ga kamshin hair spray Yana tashi. "Eh zani Bari naje na shirya". ta fada Tana kokarin zare jikinta daga nasa. Duka hannuwansa yasa ya riko kugunta ya hade ta da jikinsa. "Ina zaki?wane irin Shiri zakiyi kinsan inda zamu ne kike sauri?". Lakwas tayi a jikinsa da karfi da yaji so yake ya Saba mata da Zama a jikinsa gashi baya ko Jin jauyin taba Mata jikin sai dai idan Bai soba. "Bazaki tambayi inda zamu ba, kina Neman sake canza Kaya". "Nasan gida zamuje Mana". "Ai kece gidan, kinaji da so nake muje gidan da gaske mu roki alfarmar a bamu aron me aiki daya Wadda zata zauna min dake kafin na dawo". "Kafin ka dawo? Ina zakuje?". "Au Ashe ban fada Miki ba, aikin NGOS din Nan ne ya taso suka gayyace mu zuwa meeting da zasuyi a UK Kinga ai bazan zauna ba da dollars ko stalling founds suke biyan mu, idan Allah yasa na samu da Dan auki Kinga na Kara jarina tunda Naga Nima Ina sha'awar siyar da materials har munyi magana da Abba yace ze bani rumfa daya a Muda lawal market na gwada ko ina da nasibi a cikin sana'ar, sannan Habib ma munyi magana zamu Fara siyar da spare parts na motoci a nan Muda lawal market din dai". "Allah ya bada sa'a, Kuma idan ka tafi sai yaushe zaka dawo? Ko kaima shike Nan abinda yake faruwa Dani ze faru a kanka kaima, kada ka tafi ka barni Dan Allah tunda nasan ba Sona kake ba baka ni akayi sadaka, Dan Allah ka taimaka ka kaini Jordan tunda Ina kudin flight kawai ka taimaka ka fitar Dani daga kasar da sunan Kai zaka tafi dani, bana son Ammah ta qara shiga cikin damuwa a kaina wlh Batasan tashin hankali ba Sai Dana isa aure Kullum idan kaga Ammah a cikin tashin hankali to a kan lamarina ne ni Kuma yanzu bana fatan na qara ganinta cikin bacin rai ta dalilina, kaje ka fada musu zaka tafi Dani ko Kano ne ka Kaini na zauna gidan su bestie kafin na samu visa, nagaji da Kasar nan wlh Ina da gata Amma sai walagigi rayuwa ta takeyi anan Dan Allah kayi min wannan alfarmar Koda ita kadai zakayi min ta karshe a zamana da Kai". Ta kifa kanta a jikin kafad'arsa ta saki wani kuka Mai tsuma zuciya. Bai hanata ba ya dai Kara matseta a jikinsa Yana shafa bayanta yasan abin Yana cin zuciyarta ne bata rasa komai ba amma an dabaibaye Mata Jin dadin rayuwa kamar yanda Baba malam ya fada masa. Sai da tayi Mai isarta ya dago kanta daga jikin kafadar tasa. "Kiyi hakuri kowa da irin tasa jarabawar ke taki a haka tazo, Kuma waya fad'a Miki zan tafi na barki bazan dawo ba? Waye kuma yace Miki bana sonki? Kinsan tun tsawon lokacin da nake dakon soyayyarki kuwa? Tun Baki san meye son bama yarinya share hawayen ki Mahmud naki ne har abada, dole kije Jordan ke me gida sukutum a can.Amma yanzu kiyi hakuri nema zani idan Kuma na zauna bakya son tafiyar saina fasa Sameer yayi komai kawai nace madam ta Hana". "Kaje kawai idan baka dawo ba nasan abinda zanyi". "Keh! kina da hankali kuwa me zakiyi wlh zan turaki gurin Hajiya Inna duk da ban shirya zuwa yanzu ba kawai ki Kira min ruwa, zaman Allah nakeyi zamanki nakeyi badan ke ba Dana Dade da barin garin Nan". " Ni Kuma?" "Off course" Ya fada da karfin gwiwa. "As how?" Share ta yayi kamar bai jita ba. "Tashi ki rakani kada dare yayi, dauko Mana key din motarki na dana kada na tafi ban Sanya albarka ba, ki canza shiga kada a kalle min kayana" fada Yana mikar da ita daga jikinsa. Duk kin haye min cinya kinsa sai ciwo take min". Ya fada Yana Mata wani smile. Bata kula shi ba tayi gaba abinta duk zuciyarta ba Dadi sannan tana jujjuya maganganunsa a zuciyarta, kinsan tun lokacin da nake sonki? Danke nake zaune a garin Nan gasu Nan dai da yawa. Saida ta sakarwa Kanta ruwa sannan ta shirya agurguje ta saka wata Riga da siket na atamfa super dinkin ya zauna das a jikinta ta saka mayafin da yayi matching da atamfar ba tayi amfani da turaren kaya ba body mist kawai tayi amfani dasu a jikinta kusan kala uku, sai ya bada wani sansanyan kanshi Mai dadi. Tana gyara gyalen ya shigo dakin tsayawa tayi tana kallonsa shida yace unguwa zata raka shi sai gashi da Riga armless da wandon ta farare tas na kamfanin Adidas sai taga kwata kwata ya canza Mata ya koma irin 'ya'yan hutu din Nan na gaske wadanda Jin Dadi ya gama ratsa su yayi wani irin fresh da shi. Matsowa yayi kusa da ita Yana Dan watsa hannu irin dai na isassun yaran. Mayafin ya kama ya ida rufa Mata a kanta. "Kallon fa na menene? Kona canza Miki ne?". Kai ta girgiza Masa. "Baba son body language fa ki bude Baki kiyi min magana". Yana janyo ta jikinsa. "A'a kawai dai da naji kace unguwa zan rakaka kuma na ganka da......" Sai tayi shiru. "Karasa Mana sai Kika ganni da shigar nigas ko?" Shirun dai tayi. "Idan Ina tare da iyalin dole na sake, kema da nace ki canza ai na Shan iska nake nufi ba Wai irin wannan ba, zo muje ki canza yawon Shan iska zamu ki min hira ki bani labarin ki tunda ke bakya bukatar nawa ki bani happiness a wannan Daren yanda duk inda nake na rinqa Tino da abubuwan su zamar min kamar kina kusa Dani". "Ni dai Dan Allah ka barni haka muje kawai" "Dauko key din to muje dare nayi Kuma Ina son ganin Baba malam da Abban mu, ko ba namu bane?" Ya fada Yana kallon ta, an samu cigaba, tunda ko banza tunda ya mamnatse ta take iya kallon idanunsa ba kamar da ba da Bata yarda ta kalleshi. "Namu ne". Ta fada a hankali, badan Yana very closer to her ba da ba lallai yaji me take fada ba. "Oya let's go". Ya fada Yana nufar kofa, saida ya kashe electronics na gidan sannan suka fito Yana time da karamar luggage a hannunsa,Kati ya curo daga cikin wallet dinsa ya saka a kofar ya rufe, daga nesa Mai gadi ya hangesu sun nufi parking lot din gidan inda motar daya take ajiye, a ransa yake fadar "duk inda wannan Dan ya fito Dan mafita ne ba irin yaran Nan bane lalatattu kamar yanda aketa surutun abun masu kushe da ganin rashin kyautatawar su Alhaji nayi masu gani kyautatawar nayi". Yana can Yana tunani Bai ankara ba yaji Karan Horn alamun har sun karaso Yana can Yana nashi zarafin. Da gudu ya tashi Yana fadin Ayi hakuri nayi zurfi gurin tunani ne, a dawo lfy Allah ya tsare". Horn ya yi Masa suka fice daga gidan. Suna barin gidan sun hau babban titi sosai motar su mama ta doso kofar gidan. Dan saida suka hada turaren wutar ya kammala aka zabga Masa turarika masu mahaukatan kanshi da mazubai Wanda dole yayi attracting mutum. Daga Dan besa direban ya tsaya Mama da Asabe suka fito Asabe na rike da ledar Mai tambarin gurin Saida turarukan wutar dasu humra suka nufi gate din gidan, Asabe CE tayi knocking ta 'yar karamar kofar jikin gate din ya leko ya gane Mama tunda ya jima a unguwar sai dai ita ba lallai yasan shi ba. Da sauri ya bude kofar Yana fadin. "Hajiya kune haka barka da zuwa ina wuninku". Ta rusuna ya gaishe su. 'yar dariya Mamar tayi tare da amsawa kafin tace masa. "Munzo Kara duba Zahra ne tunda tazo ban samu mun shigo ba sai yau" Cikin nuna girmamawa malam Sani yace. "wallahi kuma anyi sabani yanzu ba dadewa suka fita da Mai gidan da kun lura ma inaga kunyi kiliya dasu a lokacin da zaku shigo su Kuma sun fita". Turus sukayi wannan ta kalli wannan. "Ina suka fita daga kawo yarinya ko sati Bata rufa ba?" Ta fada da alamun bacin rain a maganar ta ta. "Wlh nima ban Sani ba tunda ba hurumina bane sanin hakan ba, sai dai ko Zaki Kira ta a waya idan basuyi nisa ba sai su dawo". Mama Bata taba danasanin rashin karbar number zahrar ba irin yau. "Ba komai ga sako Nan ka aje mata idan Allah ya kaimu gobe Asabe zata dawo tayi Mata bayaninsa"

Ta fada tana kallon Asaben, Wadda ledar ke Hannunta, da sauri ta mikawa Mai gadin tana fadar "in Sha Allah zan shigo Amma a fada Mata". "In Sha Allah za'ayi fada kin gaida gida". Ya juya da ledar a hannunsa, want abu Asabe ta radawa Mama a kunne tayi saurin tsayawa tana duban kofar da Mai gadin ke kokarin turowa. "Malam Bismillah". Ta fada Tana komawa tare da dauko Abu a cikin Jakarta. Dawowa yayi Yana Dan sadda kai, kudin da Bata San ko nawa bane Mika masa. "Ga wannan ba yawa Dan Allah a tabbata sakon ya shiga Hannunta komai dare" "In Sha Allah Hajiya da shi zata shiga ciki, Allah ya Kara sutura na gode madallah". Ya fada Yana qara gyara rikon ledar da kyau. "Hajiya ta haka akeyi Nan gaba ko wani aikin kike bukata da gudu zeyi Miki kinsan su bugun Abuja ba bayanin da basa ganewa in dai kina ungo to zance ya Kare Abu sai dai in Baki nema ba, ai Nima goben da sako zan taho Masa Naga alamar kamar zeyi son abin duniya jifa yanda yayi caraf ya karbe kudin daman kamar jira yake. Dariya sukayi gaba daya harda tab'awa, suka nufi motar data kawo su.

******

Tafiya suke yi Yana rike da Hannunta da nasa dayan, dayan Kuma Yana tuki cikin kwarewa lokaci lokaci Yana Dan matse hannun, ganin sun dauki hanyar barin garin yasa Zahra ta Dan dube shi. "Wai Ina zamu ne?". "Siyar dake zanyi, kinji yanda nake samun makudan kudina cikin sauki, duk garin da naje haka nakeyi na duba kyakykyawar mace na aura idan an sake Dani sai nabi dare na gudu nabar garin daman ba Wanda yasan daga inda na fito, bare ke yanda Allah ya surantaki da sura ai ke sai nafi samun alheri a jikinki". Ya fada Yana wani daure fuska. Zuruzuru Zahra tayi ganin fuskarsa ba annuri ko misqala zarratin Nan da Nan jikinta ya dauki rawa, duk sanyin ACn dake motar Saida gumi ya rufeta, kallonsa ta Karayi still dai fuskar kamar bai taba fara'a ba a duniya. Jikinta tsumar ya karayi kamar ana kada Mata gangi, cikin sarkewar murya ta Fara magana bakinta Yana rawa. Me nayi maka zaka cutar Dani?". Rage gudun motar yayi cikin duhu, a hankali ya tssyar da motar, Zahra rufe idonta tayi take hawaye suka wanke mata kumatu.

✨✨ ✨

AUREN HUCE HAUSHI

Maman Fateemah

Page 26.

________Sai da ya gangare sosai sannan ya kashe motar, chak ya daukota kamar 'yar Baby ya rungumeta, dai dai kunnenta ya kai bakinsa ya hura Mata iska duka tsikar jikinta ta tashi duk da tana cikin halin rudu bai Hana sakon zuwa ba. "Ki rufa min asiri ada ace satoki nayi Nan da Nan kin rikice nayi Miki Kama da masu irin wannan d'abi'ar? Wlh zolsyarki nakeyi haka Zaki shide min ki Kira min ruwa daga fita unguwa mu bige da kwanan Asibiti cool down idan na sayar ai Nina kashe kaina". Ba zato taji ya saka harshensa Yana lashe hawayen Yana Wasa da harshensa a saman idanunta, qanqameshi tayi, "Dan Allah ka bari". "Na bar me?" "Hakan ba Dadi". "To da cewa nayi kiji Dadi? Ni nasaka kukan Kinga ai shanye hawayen ya kamani kada muje inda zamu a juya min baya". Ya fada yana shinshinar gefen wuyanta. " Kiyi hakuri bazan Kara ba tunda wannan idon naki Mai arahar kuka ne Ni zanga yanda za'ayi idan abin kukan ya samu". "Cewa fa kayi ka Saba halinka ne ka Saba yin hakan Kuma fa fuskar ka ba Rahama a ciki kamar Mai tsaron gidan wuta". "Kai innalillahi! Mai tsaron wuta ni din?" ya fada yana fiddo idanu waje "A'a ba Kai nace ba kamar nace". "Ba cinya ba kafar baya" " Nifa nayi ne Dan Naga idonki, idan kina cikin halin tsorata yana sakani nishadi". Wayar sa ce ta Fara vibration a jikinsa, Dan zameta yayi daga jikinsa ya dauko wayar ya duba tsaki ya d'an Yi. "Dan matsala kawai". Ya fad'a yana saka wayar a handsfree. "Ya akayi Hayatu". Dariya ce ta kwacewa Sameer Wadda Bai shirya Mata ba. "Wlh zan kashe, wato abin dariyarka na Zama ko?". "Sorry sir wlh ji nayi gaba daya tazo min, Kuma ko sallamar da nayi baka amsa min ba".

"Ka Fadi abinda zaka Fadi Kona kashe da gaske Kuma sallama na amsa Kaine dai bakaji ba, duk safiyar Allah baka tashi kirana ba sai yanzu da tsohon dare salon ka Hana mutum rawar gaban hantsi, na fada maka idan Ina bukatar Abu ni zan nemeka Amma tsabar saka ido sai ka kirani ni, to fad'i meya faru? Ina jinka". Ya fada Yana maido ta jikinsa. "Game da maganar tafiyar Nan ce anya zanje kuwa wlh jiya danaje sokoto daukar wadannan hardcopy din na shiga gurin Hajiya Inna muna cikin magana saiga uncle Mustapha ya shigo a sukwane bansan wane minafikin bane ya fada Masa nazo garin ba tunda bana zuwa lokacin da suke gida, ya tasani gaba da sababin nasan inda kake ina kallon su suna walaqiqin nemanka Amma nayi mirsisi naki fad'a musu komai, Ni Ina ta faman lallaba mutuniyar taka amma Saida Uncle mustapha ya Bata lamarin Dan wlh kuka take da hawayen ta bibiyu tana fadin Dan Allah na fada Mata idan mutuwa kayi saita hakurw tasan ita kadai zata nesanta ka da ita, wlh yanda ta bani tausayi da bude aiki kawai zanyi sai Kuma na tuna da warning dinka kawai na fasa, Kuma wlh yanda uncle yayi ba abinda ze Hana shi bibiyata ta karkashin kasa ban sani ba a gida da waje amma ya kake ganin za'ayi? Numfashi ya sauke me karfi yana Kare matse zahrar a jikinsa har Saida tayi 'yar karar Jin zafi.

"Karar me nakeji a kusa da Kai ne?".

"Ina ruwanka tsabar saka ido, to madam ce a kusa Kona baka ita kaji for confirmation, a'a Barta a gaisheta". Tana jinka a speaker wayar take, ka Bari kawai Zancen baze yuwu ta waya ba idan Allah yasa na shigo sai mu tattaunawa Kuma ka tabbata komai ya kammala kafin na shigo goben in Sha Allah" "Noted, in Sha Allah a gashe min da ita sosai a fada mata Batool tayi ta kiranta dazu ba'a dauka ba". "Ina ga a gida ta baro wayar ka ganta Nan sai rigima take zabga min irin tasu ta shagwababbun 'ya'yan larabawan" ya fada yana dan matse dantsen Hannunta kadan. "Wash Allah na da zafi fa". Ta fada tana Masa wani kallo Mai ma'anoni kala kala. "Allah ya bamu Alkhairi" Sameer ya fada Yana kashe wayar Bai jira yaji abinda Mahmud din ze fada ba. "Kinga kinja ya katse Kiran bamu gama bayani ba irin wannan Abu haka ai sai ayi zaton muna hanyar shuga wata nahiyar ne".

Sunne Kai tayi a jikin kirjinsa, "Dan Allah ka Bari ni me nayi,". "Ba komai". "Bayani zakiyi da yaren garinku yarinya". Gurin zamanta ya maida ta sannan ta tada motar suka koma kan titi, tunda zahra ta koma gurin zamanta take Masa kallon tukuma da neman Karin bayani. Amma saiya fuske abunsa kamar be gane ba, Yana ta faman tukinsa ko a jikinsa. Zaranda hotel taga sun shigo, kallon mamaki tayi Masa a kasan zuciyarta tana tunanin me kuma za'ayi a Nan shida yace unguwa zata raka shi to Wai mema ya hada shi da hotel ne? Gurin da aka tanada don parking ya nufa ya kashe motar. Fitowa yayi ya zagayo kofar da tare zaune ya bude ya Mika Mata hannunsa ta Kama ta fito. Kulke motar yayi ya jata suka nufi ciki, a Hanya suka hadu da wani security da gani akwai sabo sosai a tsakaninsu. "Ranka ya Dade an shigo lfy? Ya fad'a Yana kallon Zahra a kaikaice. "Lafiya kalau Ibrahim ya aikin?" "Lafiya kalau yallabai". Ya fada Yana niyyar wucewa yana Kara kallon Hannunsu dake sarke Dana juna. " Ibrahim gafa madam Dina Yau na kawota taga mafakata". Ya fada Yana Dan murmushi. Dawowa yayi Yana fadin. "Masha Allah yallabai Allah ya bada zaman lfy, ai Dani aka daura Auren babban masallacin juma'a, madam sannu da zuwa gurin namu". Ta amsa ta gaishe shi ya amsa yana Mata Allah Sanya Alkhairi sannan sukayi gaba, dakin da yake kusan mallakinsa ya bude musu suka shiga lumshe ido Zahra tayi Dan wani special kamshi da sanyi A/c ne ya bugeta, yanayin ba Karamin Dadi yayi Mata ba, direct kan sofa ya nufa da ita tare suka zauna har lokacin Bai sakar Mata hannu ba. Falon tabi da kallo ba karya komai yaji Dan an kawata shi sosai. "Wai me zakayi a nan?" Ta fada tana masa kallon ido cikin ido. "Me kikeci na baka na Zuba? ai dai muna tare dake ko! zakiga abinda zanyi yanzu ki zauna ki dan tayani aiki kafin naje unguwar ku gurin iyayena sallama".

"Dan Allah kaje Dani " "Kai ! Naje dake Ina? Lallai kina so na amsa tambayoyi kenan kwanan ki nawa rabonki da gidan? Kawai na kawoki Nan ne kisan dakin yana cikin abubuwan da suka zamar min abin tunawa a zamana na garin Nan kinsan saboda ke na kama shi ya Zama permanent dakina tsawon shekara kusan biyu da nayi a garin nan?". Galala take kallonsa. "Saboda Ni kamar Yaya?". Wani kallo yayi Mata Yana Dan taune gefen lips dinsa na kasa. "Naki Wasa ne yarinya,Wai kin zata daga cewa an bani Mata saina karba kawai? Niga sarkin tausayi ko to Daman Nima Ina son kayana kawai dai kinfi karfina ne na mikawa Allah kukana Ina zaune Kuma ya juya lamarin gareni tunda shiya hadani dake a inda ban zata ba ya cusa min soyayarki lokaci daya nasan baze Bari na shiga gararin rayuwa ba, duk rintsi ze kawo min mafita sai gashi ya kawo min lokacin da har nayi given up Ina kokarin barin garin idan na shaida dauri Aurenku, amma fa da Allah kadai yasan meya faru yanzu to Sai ya taqaita cikin shikimarsa". Agogon hannunsa ya duba, Zahra tana kokarin magana ya katseta. "Adana tambayar saina dawo Kinga idan na biye Miki ba inda zan fita, a 'yan kwanakin nan kin mayar Dani wani parrot sai magana nakeyi ba comma ba full stop, wlh kin canzani kwata-kwata da Hajiya Inna zata ganni Ina zuba haka hum..". Ya fada Yana daukar luggage din daya shigo da ita da dayan hannun dayan Kuma ya mikar da ita tsaye. "Zo muje ki tayani shiryawa". Nokewa tayi tana Dan ware idanunta. Shiryawa kuma? Kaje kawai Ni ina nan". Gaba yayi yaga alama da gasken ze iya shashancewa a gurinta. Komawa tayi ta zauna tana jujjuya lamarin bawan Allahn nan sai wasu maganganu yake fada Mata ba tare da fashin baqinsu ba. Kamshinsa shiya fada Mata wanzuwarsa a falon, a hankali ta dago Kai ta kalleshi "Masha Allah" ta fada a hankali Dan ba lallai yaji ba. Gurin da take zaune ya Dan tsuguna a gabanta ya Dora Mata laptop din dake hannunsa da wasu takardu da list na sunan mutane kusan dari da ashirin da biyar daga local government hudu Alkakeri, Jama'are, Zaki da Dass, karkashin makarantun Allo zasuyi step down training a Nan Azaren schedule ne na aikin da payment dinsu. Ta dago zatayi magana ya Dora Mata yatsa a biki "kiyi kawai idan na dawo kin tambayeni duk abinda kike bukatar sani bana son nabar garin Nan aikin Nan Bai kammala ba". Ya Mike fuskarsa ya kawo dad da tata ya Bata light kiss a gefen kumatunta, saina dawo take care". Ya nufi kofar da sauri da key din motar a hannunsa.

Harya rufe kofar Bata dauke idonta daga gurin ba, ita fa mutumin Nan ya Fara Bata tsoro mutane suna daukarsa wani Abu daban ita Kuma tana ganinsa wani Abu daban. Ta Dan jima Tana sakawa da kwancewa daga karshe ta watsar da komai ta dauki laptop din ta shige cikinki bedroom din ta Haye lafiyayyan gadon ta bude ta shiga aikin inda Allah ya taimaketa yaci karfin aikin karasa Masa zatayi.

******* Lokacin da Mahmud ya fito Ibrahim da wani sulaiman ya Kira ya Basu aikin kula da dakin da Zahra ke ciki duk da yasan suna da matakan tsaro sosai Amma hankalinsa Bai kwanta ba sai da ya Kara Mata da nasa, gurin motar ya nufa bayan ya zauna ne ya Ciro wayarsa ya bude ta haka Nan ya shiga CCTV da akayi connecting da wayarsa. Hotunan ne suka fito rababa na dakinta yayi zooming qura Mata Ido yayi lokacin data fito daga wanka tana daure da Karamin towel fararen cinyoyinta sunyi wani sambal dasu ta Kai ta kawo Yana kallonta harta gama, tunda ya Fara kallon yake sakin wani Nishi kadan kadan Dan da gaske ta yamutsa Masa tunani ji yake kamar ya zubar da Alkawarin daya daukarwa kansa a kanta, komawa yayi baya na kofar gate ya dauki hankalinsa ganin wata mota mata sun fito sun dauko wani Abu a Leda sun nufi gate din gidan full screen yayi da gurin da suke ya waye da mama amma Asaben çe bai ganeta ba yana kallon duk abinda sukayi har Zuwa lokacin da Asabe tayiwa Mama rad'a a kunne ta Kira Mai gadin ta bashi kudi suka juya da yanda suke kwasar dariya har da tabawa kamar yara sai abin ya bashi mamaki, meya kawo su gidan su kadai ga Kuma motar da gani ta commercial ce, girgaiza Kai kawai yana tunanin abinyi. Da gurin malam ya fara zuwa ya Dan jima tare dashi kafin ya aje Masa Alkhairi yayi Masa sallama, Yana Kara yi Masa addu'ar samun nasara a tafiyar da godiyar Alkhairnin daya bashi, Habib ne ya Dan kalli Mahmud din bayan sun fito Yana tambayarsa.. "Da gaske baka fad'awa Baba malam ba inda zakun kada fa yaji daga baya yayi fada yace ka tsallake kasa baka fada Masa ba. Kafadarsa ya dafa. "Kada ka damu da kaina Zan fada Masa in sha Alllah". Tare sukaje gidansu Zahra inda suka Dace suna kokarin yin knocking sai magaji ya fito, daga gani wani gurin zaya yanda yayi Shar dashi. Gaggaisawa sukayi kafin Magajin yayi musu jagora zuwan gurin Abban nasu. Anan falon ganawa da bak'insa suka sameshi, sun gaisa Sosai a Nan Mahmud ya fada masa tafiyar da zeyi, Abban yasa Albarka soshi.

. ✨✨ ✨✨

AUREN HUCE HAUSHI.

MAMAN FATEEMAH

Page 27

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull