Kenza eBookz

Auren huce haushi complete - Chapter 21

Auren huce haushi complete - Chapter 21

Auren huce haushi complete Chapter 21: Auren huce haushi complete Chapter 21. Saida Zahra tayi barci Mai isarta sannan ta farka lokacin biyu har da minti…

4,482 words

Saida Zahra tayi barci Mai isarta sannan ta farka lokacin biyu har da minti ashirin da hudu, da sauri ta Mike tana addu'ar tashi daga barci tayi mamaki ita fa gani tayi kamar barcin minti goma Sha biyar tayi Ashe lokacin ya ja haka, alwala tayi tazo ta Fara sallah bayan ta idar wayar ta da dauko Ummee ta Kira cikin shauki tun dazu ta nemeta network din na garin ba kyau sai hakura tayi, Bata jima ba tana ringing aka daga ba Ummeen bace wata ce ta daga tana ta yi Mata larabcin gargal ita kuwa zahrar na language yafi kwarewa a Dan daburce tayi Mata bayini ta gane Ummeen ta fita masallacin Annabi sallah tunda har lokacin suna Madina basu tafi ba Kuma a yanda sukayi daga Saudi Arabia Nigeria zasuyo gurinta, sallama tayi wa matar ta kashe. Number sajida ta lalubo ta syprus tasan zata Sha mita tun ranar da sukayi ways da wayar Amatu tayi Mata buyagi ta kashe Basu Kara waya ba, har tayi ringing ta katse Bata dauka ba, Bata hakura ba wani Kiran ta karayi shima Yana daf da ze katse aka daga. "Haba bestie Ina ta kira kin shareni ko har yanzu fishin ne?" Mai makon taji bestien sai muryar Fatima taji tana kwallawa Sajidar kira tana fadin "ku taho ga Amarya Zahra! Zahra" ta kirata da karfi tana murna kamar zata tsaga wayar, daya bayan daya suka dunga gaisawa suna ta korafin amarci Dadi ta Kama waya ta rufe wato Bata so a shigar musu rayuwa ko? Hakuri ta Basu tare da fada musu tayi missing din waccen wayar ne har sim din, sai daga karshe sajida ta karbi wayar. "'yar duniya wato kinji dadin lamarin ko Kika wani shareni, ni yanzu ai yallabai Mahmud ya fiki kirki kinsan ya kirani Kusan sau uku? Daman ko Baki kirani ba Zan kiraki dazu wurin Sha daya ya kirani Wai na kiraki na lallasheki yayi tafiya ya baroki kina kuka?". Ya fada tana kunshe dariyar ta. "Malama ki fito kiyi dariyar ki sosai kada ta kume Miki a ciki,da kike wani kunsheta". Dariyar tayi da gasken sai tayi Mai isarta tace. "Dan Allah bestie mekika bawa wannan guy din Kinga yanda yayi masifar macewa a Kanki? Wlh har tausayi yake bani Ni har mamaki nake idan ya kirani Yana min maganarki ranar Nan fa cewa yayi na bashi labarin zamanki a Nan syprus din wlh nayi zaton da Wasa yaki tunda nasan ba Karamin cajin kudi za'ayi ba. Amma haka na ware na rinka bashi labarin har na Gama ko a jikinsa, yanzu Ina aka tsaya da fatan komai ya dai daita? Dan nafi son dai dai lokacin ganawarmu muyi murna biyu graduation da naming ceremony". "Wlh Zan kashe yaushe Kika zama haka Mai bin kwakwkwafin jama'a? to bazakiji ba an fada Miki kowa ma irinki ne ai wlh ya Abdul Hakeem ya debo ruwan dafa kansa Dan nasan Dan bawan Allah saiya rinqa guduwa daga gidan" Wata irin dariya ta saki tana fadin "billahil Azeem gara wata wainar data wake yarinya gyara zancen ki idan ana cin baure ba'a tona cikinsa Kuma idan ana sallah ba'a magana". "Wlh sharri zakiyi Masa Amma shi dai salihi ne". "A inda salihai sukayi karanci ba". "Mubar zance kawai tunda abun ya Zama haka". Zahra ta fada tana cire hijabinta daga jikinta vest ce Fara Kal sai wando shima fari ai pink din kananun flowers gashin tayi parking a tsakiyar Kan ta kashe da band shima pink, sai fito baby sak. Gyara kwanciya tayi, tayi ringinnine da wayar a kunnenta Hira sukaci gaba da sajida yawanci duk akan auren zahrar ne. Sun dauki lokaci Mai Dan tsawo suna tattaunawa akan bututuwa da dama kafin suyi sallama, ta nufi toilet wanka take son yi kafin ta fita cin abinci.

********

Jirginsu Mahmud a Addis Ababa Bole international airport yayi landing, daki biyu Sameer ya kama musu Nan kusa da airport din tunda a kalla zasuyi Kusan three hours. Saida ya kaiwa Mahmud jakar laptop dinsa sannan ya nufi nasa dakin, bayan fitar Sameer Mahmud wanka yayi sannan yayi sallah maimakon ya kwanta ya Dan huta sai kawai ya bude wayarsa so yake ya ganta duk wani matsi da yayi tana manne da zuciyarsa so yake ya ganta kafin ya kirata. CCTV ya shiga ta wayarsa duk abinda akeyi ya rinka bi Yana gani yasha dariyar karon Zayyan da wannan matar wadda ko sunanta Bai sani ba, shi yasa ya dauko shi yasan shi kadai ne cikin amuntattunsa Wanda ze Masa wanna aikin ba tare da an samu matsala ba. Saida ya gama kallon ko ina na gidan yaga ba wata matsala, sannan yayi zooming din cikin bed room dinta daga ita sai vest purple da wando skintight kanta tayi parking da purple din band sai tayi wani irin kyau na musamman, kura Mata ido yayi Kamar ya warto ta yakeji, turare ta dauko tana fesawa a jikinta. Nan ya shiriri ce Yana kallonta knocking din da akayi Masa ya katse Masa abinda yakeyi, umarni ya bada a shigo Sameer ne sai ma'aikaciyar hotel din dauke da tray na abinci sai karairaya take shi har dariya abin nata ya bashi, me Kamar zahra yaushe irin wadannan zasu burge shi, bayan ta wuce ne ya dago ya dubi Sameer "kada ka qara zuwar min da irin wannan a rinqa bawa maza suna kawo min kawai". "Noted sir" Ledar dake hannunsa ya Mika Masa Mai tambarin wani boutique ne, sannan ya aje Laptop dinsa a kusa dashi Yana nuna masa wasu ayyukan da ya Gama yanzu, sun jima suna aikin kafin sameer ya fita saboda lokacin tashinsu ya kusa cika shi kuma Mahmud ya ciro kayan da nufin sakawa.

Saida Zahra ta Gama feffesa turarenta sannan ta dauko after dress ta zura ta yane kanta da gyalen sannan ta nufo parlour, zalai ta samu tana 'yan goge goge duk da ba wani datti a gurin, gaishe da zilan tayi tana Mata sannu, ajiye mofar tayi "Allah ya taimaki uwar dakina ga abincin can nayi Miki abinda kikeso faten dankalin turawa da pepper soup din kifi" Zama Zahra tayi tana fadin "Kai Amma wlh na gode kwarai da gaske shi yasa nake yinki kinsa favorite Dina wlh". "Ai shi yasa na cewa Ammah kada a wani dauko yarinya tun daga Mubi Nima na isa na zauna dake saina kirawo Kanwata Alawiyya ta cigaba da yiwa Ammar kafin Allah yasa yallaban ya dawo, ai ni har zaman wanka ni zanyi Miki Koda kuwa bakwa garin Nan ne". Dan smile tayi kawai bata ce komai ba saima ta canza akalar zancen. "Ni Kuma Aunty zilai kin mikawa mutumin Nan abinci kuwa?". "Ai tunda na Gama na zuba na hada harda ruwa da lemo na mika Masa. Naga Dan gayu ne beyi kalar masu gadi ba". Dariya zahra tayi tana fadin "Aunty zilai kenan shi Mai gadi har Kama gareshi". Yana da kama Mana Wai Kinga wannan din?" Na ga wani dai dazu ban sani ko shine Wanda aka Kira jiya cikin dare". " Cikin dare Kuma?" Kai ta gyada "Mata kusan Hakan tunda Sha biyu ta wuce ya kirawo wani kawai umarni ya bashi yazo garin Nan da safe kinsan bakwai a Nan tayi mass nifa mutumin Nan wlh tsoro yake bani na kasa gane kansa". Dan murmushi zilan tayi tana kallon Zahra "kiyi hakuri uwar dakina a hankali Zaki San komai a kansa badai Kuna tare ba da sannu Zaki gane shi din waye, kici abincin sai muci gaba da hirar idan kin gwma". Bata k'i Shawarar zilan ba ta tashi ta nufi dining ita Kuma zilan ta nufi dauko Mata ruwa da mutuniyarta farm fresh, sai da ta Gama cin abincin sannan ta dawo parlourn gurin da tabar Aunty zilan sukaci gaba da hirar su, amma Kusan hankalin Zahra yana Kan Mahmud haka Nan sai taji ya fado Mata ta yarda da ake cewa sabo turken Wawa, yanzu da baya Nan sai taji duk kewarsa ta kamata, tun dazu take duba waya ko zataga kiransa Amma shiru tasan tsakanin Nigeria da inda zasu indai da gaske chinan zasu da nisa a kalla jirgin zeyi landing a Ethiopia da India yaci ace ya kirata Amma shiru har Yanzu ko lfy? ta ayyana a cikin zuciyar ta. Ganin tunanin Zahra yayi zurfi yasa zilan ta tashi tana fadin Bari nayi wanke wanke tunda kin Gama da kwanukan" Tayi hanyar kitchen, ita kuma ganin tunanin ze dameta yasa ta kunna tv ta kamo MBC MAX tana son finafinan su sosai,Aunty zilan ma data Gama Zama tayi sukaci gaba da hirar jefi jefi har aka Kira magariba suka shiga sallah. Tana addu'oin yaumiyya na cikin du'aul mustajaba ne kira ya shigo wayarta da sauri ta dauko tana duba Mai Kiran Ummee ta gani da sauri ta daga tana fadin "Ummeena" Amsawa tayi suka gaisa Ummeen ke fadar an fada Mata ta kirane nan tayi Mata fadan rufe layi da tayi,nan Zahra taji kuka yazo Mata, Nan da Nan Ummeen ta rude tana tambayar ta ko tana da damuwa ne ta fada Mata cikin kukan tace "Ummee Shima fa wannan daga kawo ni gidansa ko sati daya ban rufa ba ya tafi ya barni Wai aiki zejeyi uk" shiru Ummee tayi kafin ta shiga rarrashinta da kalamai na kwantar da hankali da nuna Mata ba lallai ne hasashenta ya kasance gaskiya ba, kada ta damu saboda ita har Umara tayi bayan auren tayi mata addu'oin samun nasara akan dukkan lamuranta, sannan ta yi mata fadan ta kiyayi yawan kukan Nan bashi da ma"ana, daga karshe tayi Mata albishir zawan su next week harda Mama Hanifa da Aunty Nawwara duk suna hanya Daman ko Bata sameta a waya ba zata kira Hajiya Asma'u tasa a fada Mata. Murna ta shigayi Kamar tayi me har Ummee na Mata dariya Nan da Nan ta ware ta shiga lissafo abinda takeso Wanda za"a taho Mata dashi. Bayan maga wayarsu da Ummeen Ammah ta Kara kira lokacin tana tare da Abba. Tana zubawa Abba Dan fruit salad wayar ta dauki ringing Abban ne ya dauko ya duba 'yar dariya yayi Yana mikawa Ammar wayar tare da fadin. "Uwata ce ke kira". Ganin Kiran ze yanke yasa Abban karbar fruit salad din yaci gaba da zubawa Yana fadin "A dauki Kiran uwata kada ya yanke". Daukar tayi tana amsa sallamarta da gaisuwar da take mata. "Ammah yanzu Dan Allah bazakizo ba Kuma Aunty Hasana ma fa batazo ba fa Kuma Ni sonake na ganki". "Ikon Allah yanzu ke saboda Allah sai a ganni a gidanki a irin wannan kwanakin ai sai a dauka ba lafiya Auntyn taku dai zatazo Daman jiya take fad'a zata shigo ta ganki tunda mijin naki baya Nan, ai Mahmud din ma ya turowa Abban ku da sako ba dadewa ta whatapp yace sun sauka lafiya, ke dai abinda nakeso ki kwantar da kiyi Masa biyyayya kinji". Ta fad'a tana rarrashinta. "To Ammah, daman kira nayi na fada Miki Ummee tace next week zasu shigo Nigeria nasan zata fada Miki". "To Allah ya kaimu Daman munyi maganar shekaran jiya har take tambayar meya faru da taki wayar? Nace ta Dan samu matsala ne, ga Abbanku yace a gaishe ki" "Lah! Ammah Daman yana Nan amma ba'a fada min ba Bashi na gaishe shi" Sun gaisa da Abban har Yana Dan tsokanar ta, tunda a wani bangaren kakace a gurinsa, Nan yake fada Mata mijinta yace ya tafi da motarta Kano tana airport Dan haka daga nan Zuwa jibi za'a kawo Mata daya motar ta gurin Muttaka, godiya ta yiwa Abban sannan sukayi sallama. Ta jima Bata aje wayar ba, tana juya maganarsu da Ammah Wai ya fadawa Abba sun sauka wato ita da bayaso Bata da matsayin da ze kirata ko sako ya fada Mata sun sauka, kenan Daman duk abinda yake Mata a 'yan kwanakin Nan yaudara ce Dan ya lasa Mata Zuma a baki ya gudu ya barta da kewarsa inda ta godewa Allah be lalata mata rayuwa ta gudu ya barta ba wlh duk rintsi sai ta bar Kasar Nan ta koma Jordan, Dan tasan Allah kadai yasan halin da Ammah zata shiga idan bawan Allahn Nan yaqi dawowa....

✨✨✨ ✨✨✨

AUREN HUCE HAUSHI.

✨✨✨ ✨✨✨

Story & Written by Naman Fateemah.

page 31

______________Har aka Fara Kiran sallar insha'i tana zaune tana faman tunanin makomarta, tashi tayi tayi sallah, nan Kan sallayar ta kwanta tana lazimi a haka har barci yayi awon gaba da ita. Tun zilai na saka ran fitowa Zahra har ta hakura ta shige ciki duk da ba barci take ji ba, tun yamma take ganin zahrar wani sukuku Kamar marar lfy. Zahra ba ita ta farka ba sai Kusan daya da kwata, tashi tayi tana mik'a tare da salatin Annabi, duk jikinta ciwo yake Mata hijabin ta cire tare da after dress din ya Zama daga ita sai vest da wandon toilet ta shiga Bata Dade ba ta fito canja kayan jikinta tayi da rigar barci ta Kashe wutar Mai haske ta kunna bed side camp tayi shiru tana istigifari ga Allah s.w.a da Salati ga fiyayyan halitta Annabin Rahama duk yanda tunani yaso ya bijiro Mata saida ta kawar dashi kawai ta fawwalawa Allah lamarinta tasan duk rintsi Yana tare da ita, a haka har barci yaci karfinta. Da safe har zulai ta Gama share share da mofin Zahra bata fito ba ganin shirun tayi yawa yasa tayi tunanin buga Mata kofa kada ta Zama babbar banza zuwanta ya Zama marar amfani rabonta da yarinyar nan tun magaribar jiya Bata Kara sakata a idonta ba, kofar bedroom din ta nufa tayi knocking taji shiru lokacin Zahra na Wanka, Kara bugawa tayi still dai shiru taji Nan da Nan hankalinta ya tashi kada fa wani abu ya Sami yarinyar Nan ta shiga uku. Tana Nan tana shawarwarin ta bude ta gani ko lafiya? taji alamun motsin tafiya daga ciki da sauri ta Kara knocking din, Zahra da towel a jikinta ta nufo kofar ta bude. "A'a Aunty zilai kece? Ina kwana?" Ta fada tana goge gashinta daya jike gurin wanka. "Lafiya kalau, naji ki shiru ne tun daga shiga sallah jiya harna gaji da zama Baki fito ba, gashi yanzu ma naji shiru har Ina kokarin Kiran Ammah na sani koba lfy ba". Ta fada tana kokarin barin gurin "na gode da kulawar ki Aunty zilai wlh jiya barci ne ya daukeni a nan Kan sallaya bani na farka ba sai Kusan karfe biyu na dare". "Ikon Allah kice kwanan kasa kikayi da sanyin tayis Bai Kama ki ba, tunda Naga gidan naku ko Ina sanyi Kamar gidajen larabawa". Sai Kuma ta rufe bakinta da hannu. "Kin jini ba wlh na manta Ashe gidan nasu ne". Dariya Zahra tayi "Kayya Ina wani balarabiya anan ai da uba ake ado Ni bafulatana ce kalarce dai na dauko tasu Amma idan masu abun suna yarawa wani abun sai kallo Dan ma Allah ya hadani da jarimin uba da yayi tsayin daka gurin ganin na iya yaren saboda na samu saukin mu'amala da dangin Mamana". "Wannan gaskiya ne Allah ya sakawa Alhaji da Alkhairi ya biya Masa bukatunsa na Alkhairi" "Allahumma Amin". Zahra ta fada. "Me za'a dafa miki? Mu dai nayi Mana nida bakon ku". "Wai bakon mu wato dai bazaki ce Mai gadin ba ko?. Dariya tayi. "Wlh baya Kama da masu gadi Kinga kuwa ai bana ce Masa ba". "Haka ne ki dafa min indo mie da cooker oat kawai". "To an gama sai kin fito". Ta fada tana juyawa zuwa main parlour din yayin da Zahra ta koma ciki.

************* DAMAGARAM NIGER REPUBLIC.

Cikin takun ta na nutsatstsiya kuma wayayyar mace 'yar gayu ajin karshe ta shigo parlourn tana sanye da doguwar rigar madam gezber kalar peach sai gyalen kalar light yellow touching din flowers din dake jikin kayan sai takalmi plat Mai azabar kyau shima light yellow din tun kafin ta karaso kamshinta ya hade gurin. A hankali ya dago ya dubeta har ta karaso gurinsa, tattara aikin da yake yayi ya Maida hankali a kanta lokacin da take Zama a kujerar dake gefen da yake. "Sannu da aiki Yaya barka da Asuba". Ta fada tana sadda kanta kasa Bai amsa ba Jin shirun yayi yawa yasa ta dago kanta ta dube shi, ita yake kallo. "Yanzu abinda Kika zaba kenan Zainab da girmanki da hankalinki ki zazzage jiki ki baro dakin mijinki kizo ki nemi guri ki zauna mijinki yayi rarrashin duniyar Nan kinqi ki saurare shi daga karshen ma Kika zabi ki dawo Nan Damagaram saboda a Yamai uncle Yousoufu ya nuna Miki rashin kyautatawar abinda kikayi shine kikayo yajin Nan ko?.Ni tunda tubus ne Bari kizo ki zauna ki Mike kafa gashi nan har an Fara kawo Miki caffar ana son aurenki idan kin Gama idda wannan arzikin ki ne?". Ya fada Yana kureta da ido, da sauri ta cira Kai ta dube shi. "Ni Kuma Yaya ake jawo min zawarci kawai daga ganin mace sai ace zawara ce". "Kada kiga laifinsu sun ganki yau sun ganki gobe Baki da niyyar tafiya,idan Badi'a zata fita ki wanke jiki ku kama tafiya ba dole ace Miki haka ba". Idonta taf da hawaye ta dube shi "to Yaya ya akeso nayi kasan dai yanda abun Nan ya kasance duk yanda naso a saurareni idanuwa suka rufe ba Wanda ya kula da abinda nakeso su gane Saida suka rabani da Dana yabar gida cikin bacin Rai Wanda har gobe ba Wanda yasan inda yake, gaskiya Kuma tayi halinta yanzu za'a matsamin da zarya na fada musu niba yaji nayi ba duk ranar da yarona ya dawo Zan dawo". "Zainab a gabana kike fadar danki, Dan farin ba zakiyi min Kara ba". "Kayi hakuri Yaya na Bari d'anka to" ta fada. 'yar dariya yayi na nawa Kuma sai dai a koki gaba, yanzu Dan Allah Alfarma zakiyi min kiyi hakuri ki koma dakinki Suma sauran yaran suna bukatarki kusa dasu ko badan Babansu ba ki duba girman Hajiya Inna har Yamai Saida tasa aka kaita ko a jirgine dai ai tanayi dake ne amma Kika kasheta da dadin Baki akan kina tafe kikayi zaman ki karshe ma kikayo hijira daga can, duk laifin Hajja ne wlh ita an taba Mata dan 'yar so ba zaman lfy, gobe nace aje Abuja a daukeki tunda ba jirgin sokoto direct, kije kiyi ta yi masa addu'a bakin uwa Mai Albarka ne akan 'ya'yan ta muma muna tayaki nasan fushi yayi idan ya huce ze nemi gida". Har ranta bataso wannan hukuncin ba Amma yata iya da Yaya ishaq uba ne sak tun bayan rasuwar mahaifinsu bai barsu da kukan maraici ba, duk rintsi baya Bari su koka uwa uba yanda ya janyo gudan jininta ya nuna Masa hanyar nema tun a kananun shekaru duk abinda yaronta ya zama shine sila gashi Zuwa yanzu Allah yayi Masa karfin daya fi na Yayan. Hira sukaci gaba har Aunty Badi'a ta fito itama kamar me Zuwa gasar sarauniyar kyau ita Fara ce tas buzuwa kallonta Yaya ishaq din yayi "wato ta wata fuskar naji dadin zuwanki Zainab ko banza mutuniyar ta koyi gayu irin naki da dai sai a hankali". "Kai Yaya wlh bani na koya Mata gayu ba Daman Aunty na me class ce ko Aunty?". "Fada Masa dai,kawai nasan dai na koyi amfani da perfumes designers dani kowa ne ma saye nake Amma yanzu tunda ta bani naji dadinsu nake amfani dasu". Dariya yayin Yana fadin . "Ba cinya ba Wai 'yan magana sukace kafar baya, Wai yanzu Ina da kikace min zakuje? Bana son yawo har an Fara min sallama idan ta Gama idda". Ido Aunty Badi'a ta kwalalo "sallama Kuma?. "Wlh kuwa shi yasa nace ta tattara tayi hakuri zanyi Mata booking ta tafi kawai muci gaba da addu'ar Allah ya bayyana shi duk inda yake". "Gaskiya kam shi yasa kenan ranar da mukaje gidan sarki kingmakers sun fito daga meeting da Mai martaba Naga ana nuna ta har wani dogari Yana kokarin Zuwa gurin mu muka tafi". "Kinsan kuwa sakon daga fada yake". Baki Ammi ta rike "tab gara nasan inda dare yayi min kafin wannan labarin ya Isa kunnen general". Ta fada suna nufar kofar fita daga falon. "Da dai kin yiwa kanki gata" Yaya Ishaq ya fada.

*********

Tun safe su Mahmud suka fita da Sameer su shiga can su fita can duk da Sameer Kusan Dan kallo ne an Kai ruwa Rana kafin a samu ganawa da Wanda alhakin matsalar ke hannunsa Basu suka dawo ba sai dare a gajiye suka dawo Jin dadinsu daya ba a hotel suka sauka ba gida ne. Sameer yayii musu order din abincin Africa. Saida sukayi wanka sannan sukaci abincin inda Allah ya taimaka sunyi sallah a wani masallaci a hanya. Bayan Mahmud ya shiga daki wayarsa ya Ciro ya shiga ciki gurin da akayi Masa connecting da CCTV nan ya lalace gurin kallon Zahra yanda yake more kallonta yasan da ace tasan da CCTV a dakin bazata Bata sakewa haka ba tana sabgoginta. Amma ganin ita kadai a dakin take zuba yanda takeso, amma yanda ya fuskanceta kamar wani Abu Yana damunta ya Raina yanda take walwalarta, ya rasa aikin me suke ita da Mai Taya ta zama Dan gani yayi ita Mai tayata zaman ta fita waje da alama wani Abu ta sawo Dan can baya yaga ta hada wuta da gawayi akan wani Abu ta Dora tukunya Mai Dan girma, so yake yaga wace wainar zasu toya. Dayar wayar ya dauko Yana kokarin kiranta sai kuma Kiran Mr Lee ya shigo akan Yana fada Masa kome yake ya fito bakin da zasuzo daga Thailand sun karaso shi kadai ake jira, tashi yayi Yana Kiran Sameer akan ya zama ready zasu fita.

** ZAHRA.

Tun bayan data gama break Basu zauna ba aiki Zahra ta dauko dambun Nama take son yi yau akwai Naman da yawa sai kuma abinci shima Mai Dan yawa haka Nan taji tana son kaiwa Abban ta da Baba Malam abincin juma'a zilai ce tace a sawo kufat ayi suyar dambun a Kai tunda da yawa za'ayi ta Bata kudin aka sawo ta Dora, Basu suka Gama aikn ba sai bayan azzahar zilai ita ta mikawa zayyan bayan ta wuce ne ya bude abincin yaga irin garar da aka kawo Masa yayi ta mamakin yanda matar oga ta iya girkin hausa haka Mai shegen Dadi gashi ita Kuma ba bahaushiya bace ko Ina ya samo wannan da Kuma dalilinsa na zabar wannan rayuwar shifa ko a mafarki baiyi tunanin ogan nasa ze iya sakewa har ya Mike kafa yayi zamansa a irin wannan muhallin ba da iyalinsa, haka yayi ta sakawa Yana kwancewa. Sai da su Zahra suka Gama Zuba komai a mazuban da suka Dace sannan Zahra ta wuce ta Kira magaji a waya akan yazo tana nemansa sannan ta shige wanka sai bayan la'asar magajin yazo lokacin ita kadaice a falon tana tulawar alqur'ani, Saida ya cika cikinsa Yana zuba Santi sannan ta bashi yace ta fito Masa na Baba Malam Dana gurinsu Ammah har ya Kai kofar fita daga parlour ya juyo Yana fadin "inyeeh su Adda Zahra an girma har an Fara aikin neman ladar tsaffi da fatan dai kin fadawa mijin naki kada garin neman lada a kwaso zunubi". Ya karasa fada Yana dariya. "Allah ya shiryeka magaji Kai Kullum baka girma ko?"

"A'a zancen gaskiya ne Dan bawan Allahn nan baki San yanda yayi ya Nemo kudin sayen kayan nan ba Amma kin tashi kin zuba irin wannan garar Dan kawai Kinga baya gari ko?"

Harararsa tayi "To nayi kayan nan dai nawa ne mijina ya aje min Bai Kuma yi min iyaka ba duk abinda nakeso zanyi dasu idan bazaka Kai ba dawo ka aje min sai Aunty zilai ta Kai ko naje da kaina". Ta taso ta nufo inda yake da sauri yayi gaba Yana fadin. "Allah ya huci zuciyar uwar gidan Mahmud tuba nake". "Dan rainin hankali shi dai gurinsa ya saka mutane magana". Aunty zilai ce ta Bata amsa Sam Bata lura da fitowarta ba. "Kema uwar dakina Kamar kin manta halin Mai sunan Alhaji ai shi burinsa Ke nan yayi jan magana".

"Ai sai yayi tayi tunda halinsa ne" Abincin zilai ta kawowa Zahra Nan cikin parlour some times Bata fiye son zaman dining ba, kitchen zilai tayi niyyar komawa Zahra ta Hana "ki zauna a nan muyi lunch din Ina Zaki kuma koni bafulatana bana irin wannan d'abi'ar". Sun Fara cin abincin kenan door bell din tayi k'ara zilai ce ta tashi taje ta bude Mujiba ce tare da wata yarinya Sa'ada 'yar makotansu. "Kai! Kai!! Kai!!! Tab amma dai batan hanya kikayi Mujiba, yanzu Alkawari da amana sunce haka? Yaushe rabonki da gidan Nan?" Dariya mujibar tayi tana fadar "eh lallai da sauranki irin wannan Baki zai- zai, Kuma shike Nan daga kawoki saina dunga sunturi a gidanki ai Mai gidan saiya saka Mai gadi ya hanani shigowa tinda Zan zamar masa matsala, Wai ke tsaya waye a gate din gidan nan daya tsaremu da dogon turancin daga Ina zuwa Ina me mukazoyi ke tambayoyi dai gasu nan kamar zanga Mrs president". Ta fada Tana Zama a kujerar dake kusa da zahrar Sa'ada ma ta zauna. Spoon din hannunta Zahra ta aje "Bari kawai Muji wlh Nima haka na ganshi haka Nan Rana tsaka ya canzawa Mai gadin gurin aiki ya mayar dashi makarantar gidan Baba Malam ya ringa share share ya kirawo wannan bansan ko daga Ina ba yanda aka wayi gari da Mahmud shima haka aka ganshi nifa lamarin yafi karfin tunani na kawai na saka ido ne Naga karshen film din". Ta fada tana Dan tab'e Baki. "Amman wlh Baki da kirki auren naki kike cewa film dan bawan Allah ya biya sadaki ya daukoki daga gidan ku ya killace ki guri daya ya Baki ci da Sha amma ki Kira Masa aure Shirin film humm zakiyi bayanin film da alama komai normal yake tafiyar Miki ko Aunty zilai?" Dariya tayi "A'a babu ni a cikin wannan maganar kunga tafiya ta". Ta wuce kitchen da plate din abincin ta. " Kinga Sauko kiyi serving din ku, ni ban iya abinda Kika iya ba ku Kenan bakinku ba kintsi ku dunga sakin magana irin haka Ina Dadi Kinga kin Kori Aunty zilai daga wurin". Tasowa tayi ta sauko kusa da zahrar tana fadin "lallai kina Jin Dadi irin wannan garar haka sauko sa'ada Wai Ina Mai gidan na Dan kwana biyu ban ganshi ba?" Plate din ta ture gefe ta dauko tissue tana goge bakinta. "Yayi tafiya jiya baya Nan". Tsayawa mujiba tayi da cin abincin. "Bayanan Kamar ya?" "Kamar yanda na fad'a Miki yaje taron gamayyar Qungiyoyin da suke taimakawa ilimin makarantun government Dana allo a Nigeria da wasu kasashen Africa, to a Nan zone din namu na north east shine aka dauka a Bauchi state, a jigawa da Kano ma duk suna da nasu wakilan tunda state uku suka dauka".

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull