Kenza eBookz

Auren huce haushi complete - Chapter 32

Auren huce haushi complete - Chapter 32

Auren huce haushi complete Chapter 32: Auren huce haushi complete Chapter 32. Sallama ta yiwa Iya Rahane suka fito tare da Zilan, Saida sukayi nisa sannan…

4,380 words

Sallama ta yiwa Iya Rahane suka fito tare da Zilan, Saida sukayi nisa sannan zahra ta tsaya itama Zilan tsayawa tayi. "Aunty zilai me Kika fashimta daga lokacin da mukazo zuwa yanzu?" Zahra ta jefa Mata tambaya. "To abin ne da yawa gaskiya, Dan ni lissafina ya kwance gaba daya wallahi na rasa tudun dafawa Amma dai komai rintsin mijinki shine ke Jan ragamar gidan nan Dan dazu lokacin da oga Sameer ya kawo Hajiya naji suna magana da wasu ma'aikatan gidan Nan akan oga yayi zuwan bazata, sai Kuma lokacin Daya fito a can gurin Naga ya Tara su yana magana dasu oga Sameer Yana gefe harya gama oga Sameer ya rarraba musu kudi muma har ya aiki wani Wanda Naga ya shigo da waccen babbar motar ya kawo Mana dubu ashirin ashirin nida iya Rahane". Ajiyar zuciya zahra tayi tana duban bangaren motocin hango motarta tayi a cikin parking lot din, kenan a Nan ya ajeta ko kuma jiyan yazo da ita Nan Dan kamar Bata ganta ba jiya, rausayar da Kai tayi tana wani tunani kafin tace. "Muje kawai Aunty zilai mu zuba idanu a hankali gaskiya zatayi halinta, nifa duk hankalina ya koma gida Amma naji yana fadin zasuje Azare jibi za'a dawo min da Aunty Rukayya, Kinga ba zancen komawar mu kenan, ni Kuma abinda bazan yarda ba kenan ya ajeni a wannan gjdan da bansan asalinsa ba gashi Nan Kashi-kashi kamar gidan marasa gaskiya". "A'a kada kiyi haka ki Bari kiga iya gudun ruwansa Mana nasan dai baze cutar dake ba, to kiyi Masa biyayya a duk abina ze umarceki matukar Bai sabawa shari'a ba,kiyi hakuri wata rana ma garinsu ze koma sai kice bazaki bishi ba? ai shi aure ba inda baya Kai mace, ki duba Maman Akwanga kin taba cewa tayi rayuwar Azare". Haka zilai ta dunga tausar zahra har suka shiga part din da suka zauna Zahra ta dauki luggage dinta Zilan ta karba suka shiga ta ciki suka fito barandar nan zilai sai mamakin abin take Bata taba tunanin da wani ginin a bayan wannan ba, Bata Gama sarewa da lamarin ba Saida suka shiga ciki, a parlourn farko suka tarar da Hajiya ta rabsa uban tagumi ta zubawa kofa idon suna shigowa ta sauke ajiyar zuciya tana fadin "Haba 'yar Nan daga Bari na dawo Kika nemi gurin Zama Kika manta Dani saboda Allah kin kyauta min kenan? duk sanyi ya game min jiki har attishawa na Fara nasan mura Kuma sai abinda hali yayi kawai". Da sauri zahra ta karasa kusa da Hajiyar tana fadin "Ayya wallahi nayi tunanin ko zakiyi nafilfili ne fa shi yasa na fita dauko wayata da kayana Dana Bari a wancen dakin, taso muje kici abinci kinji Hajiyarmu insha Allah bazakiyi mura ba, Aunty zilai Naga da kaji a can bangaren inda muka fito kiyi Mata irin pepper soup din da Naga kin yiwa Inna maimuna lokacin tana mura, ko a soya Mata ta tafi gida dashi". "To in Sha Allah Bari naje ai kayan dazu wani mutum ya debesu ya mayar kitchen din part din da muka koma harma an karo wasu kayan masu yawa mun shafa'a mu nuna Miki su". Ta fada tana mik'ewa ta nufi kofa ita Kuma zahra ta nufi dining ta daukowa Hajiyar abinci.

*** *** ***

Tunda garin Allah ya waye Mama ke faman Kai kawo a cikin Daki ta Kai gwaro ta Kai mari, tun bayan wayar da sukayi da Aunty larai hankalinta Bai kwanta ba sai yarfe gumi takeyi baji ba gani, ta Kira wayar Asabe yafi Shurin masaki amsar Daya ce switch off. Wannan wane irin Abu ne Kullum tana tubkar gaba baya na warwarewa, Wai ita wannan Matar meta taka ne, duk abinda takeyi ya tashi a banza Kenan? Tun bayan kaiwa Mai gadi sakon Nan Basu Kara samun damar shiga gidan Nan ba ko kofar ma tafi karfin zuwansu gashi yanzu Kuma aunty larai tazo Mata da wani Abun d'aga hankalin ga sako Amma isar dashi shine aiki ga wayar Asabe Bata shiga da sai ta Kai ko ta bayan gidan ne ta jefa abin bukatar dai ya shiga gidan ga sakon ya taho daga Jos din Kuma ance ba'a son ya kwana ba'a aiwatar dashi ba, akwai matsala Dan ze iya warware duk ayyukan baya, kuma wani aikin ze iya yin kome a Kanta ko 'ya'yan ta shine ta tada hankalin ta, tunda tasan idan tayi sake kwabarta ce zatayi ruwa, tayi tunanin ko sahura zata aika Tasha ta karbo sakon idan yaso sai tayi Mata bayanin yanda zatayi da sakon idan ta Kai can gidan zahrar, tayi tunanin ko zilai zata Kira tace Mata ta fadawa Zahra sahura zata je tayi musu share-share kafin su dawo, Nan ma taga abun ba lallai ya yuwu ba. Kara Kiran Asaben ta gwada still dai a rufe, dangwarar da wayar tayi duk abin duniya ya taru yayi Mata yawa. Duk iya tunanin ta ya Kare ta rasa Ina ne mafita dole ta tashi ta fice daga dakin tana tunanin dole ta tura sahura taje ta Kirawo Mata Asaben in ba haka ba tasan watan Jin kunya ne yake neman Kama Mata. Wannan kenan.

Tunda Ammah ta fita daga bangaren Abban take kokarin neman zahra Amma Shiru har bayan Azzahar inda taji Dadi da zilai tace Mata zahrar a gidan ta kwana Kuma Mai gidan ma yazo, tasan kome ne ne zezo da sauki. Banda kada yaron Nan Sameer yaga Kamar ta raina abinda yakeyi da yanzu ta tsufa a Kano, sakon text ta turawa zahrar ta tashi ya nufi bedroom dinta.

**** **** ****

Tun bayan fitar zilai zahra ta wuce bedroom tabar Hajiya nacin abincin ta, a gurguje ta sake wanka ta gyara jikinta Bata wani Bata lokaci ba ta shirya cikin wata doguwar Rigar lace cotton Mai kalar blue black, anyi touching dinsa da silver ash yayi Mata kyau sosai.Bata daura dankwalin ba rolling tayi da ash din gyalen ta feshe jikinta da turenta ita abin har mamaki yake bata, ta rasa yanda akayi duk inda take sai taga turaren da take amfani dashi a gurin. Dan watsa hannu tayi irin baka gane Abu ba din nan. Parlourn ta koma gurin Hajiya dai dai lokacin da su Sameer da Mahmud suka shigo. "Bakin Hajiya ne yaki rufuwa data hango zahra ta nufo ta Fadi take "Masha Allah! Haka ake so wwnnan 'ya naga alama bazakiyi saken da za'a karbe miki miji ba, ki Kama abinki ki rike wallahi sonsa akeyi kamar goron hannun sarki ki matse kayanki tunda Allah kadai yasan gwagwarmayar da yasha kafin ki shigo hannunsa..." Sameer ne ta katse Mata hanzarin zancen data dauko ya Fara fadin "ki tashi na mayar dake gida garin Zan Bari yanzu Banda kina Nan da nayi nisa a Hanya". Shi kuwa Mahmud Banda kallon zahra ba abinda yakeyi gani yayi ta Kare Masa wani sanyin kyau a idanunsa, Kuma fir Taki yarda su hada Ido dasu duk kowa da kalar kunyar da takeji tasa.

"Hajiyarmu ya zaman guri Daya nasan kin gaji sosai ko". "Mahmud din ta kalla Wanda ya nufo ta. "A'a ban gaji ba ai wannan yarinyar da Abun gari take, jiya ma dai an Bata Mata Rai ne yasa na ganta Kamar marar wayo Amma yau ai ka gani sai Ina taka saka Dani takeyi". "Dan Allah ki taso bana son nayi dare a hanya ke Kuma kin tsaya sai maimaita zance kikeyi, abinda ya wuce ai ya wuce". Da sauri Zahra ta juya ta koma ciki ta barsu Sameer nata yiwa Hajiyar Dan zance, turarika da sabulai ta daukowa Hajiyar ta fito, lokacin Hajiyar na gyara lullubin gyalenta tana fadin "ai Zan dawo ne tunda ban karbo Mata dawa'in Dana saka ayi Mata ba a sanka, Kasan duk wannan jidaliyar ta jiya Bata Hana da almuru Saida Tofeek ya kaini Sanka naje na fadawa Malam karami ya taimawa jikata da maganin tsarin jiki Dana Baki, yo anyi sake Baki ya Kamata dubi fa yanda take tubarkalla, yo tunda ya fito da ita Nan ai magana kuma ta gare haka ze dunga reto da ita,to kasan wani idon da bakin ba masu kyau bane, shi yasa gara a dafata daga Nan" shi dai mahmud ban kunshe dariya ba abinda yakeyi yasan kadan da aikin Hajjaju ne hakan, shi Kuwa Sameer ya cika yayi fam shi yayi Dana sanin kawota gidan nan Dan Allah kadai yasan abinda ta fada Mata tunda kanwa Bata jiqa a bakinta. "Wallahi Zan tafi na barki a gidan nan haba saboda Allah kin kama zance kamar an saka Miki batir". Dakuwa tayi Masa ungo Nan. Dan nema kake wani zaro min Ido to tsoron ka zanji kome? wato gaskiyar ce baza'a fada ba". Juyawa yayi ya nufi kofa da hanzari Hajiyar tabi bayansa itama zahrar da sauri tabi bayan Hajiyar, ji tayi an riko ledar da hannunta gaba daya ya dawo da ita jikinsa. "Precious ba irin huge din Nan na welcome saiki wani shareni" Ya fada Yana Dan goga Mata sajensa a gefen kumatunta cikin wani irin low voice. Wani yar taji a jikinta. Cikin shagwaba tace "Dan Allah ya Bari na rakata kada su tafi ban Bata komai ba, Kuma na saka Aunty zilai ta dafa Mata nama". Juyota yayi suna facing din juna. "Baze tafi ba kawai ya gaji da surutun Hajiya ne itafa Bata gajiya da magana, kawo na gani dame-dame za'a bawa kakar tamu?" Ya fada Yana duba cikin ledar. "Inye ashe dai da wayonki irin wannan Abu haka? jazakumullahu khairan. Bari na Kara gyara Miki kudi ya Ciro daga aljihun wandonsa ya saka a ledar Yana fadin sai kice ta sayi man shafawa ko kice ta sayi goro, bari mu dawo ki bani abida ya samu, Kuma idan anjima Zaki rakani gidan su Sameer na gaishe da mommy sannan muje muga Mai sunana" . Bai saki hannun nata ba, a haka suka nufi kofar fita. Taso ta zame hannunsa daga cikin nata tasan ba Karamin aikinsa bane su fita harabar a haka, kuma taga alama gidan da mutane da yawa ga kuma Hqjiya da Sameer. Ganin kada ya Bata kunya yasa ya saki hannun ya rike ledar kawai kafin taje gurin motar ta shiga gurin su Aunty zilai ta gani ko angama. Cikin ikon Allah ta samu an Gama soya Mata cikin roba, Ashe Daman tun safe suka dafa aka saka a fridge yanzu soyawa kawai sukayi, a ciki babban warmer aka zuba zilai ce ta dauko suka fito suka nufi gurin da suke tsaye suna jiran zuwansu. Saida Motar tabar harabar gidan sannan suka juya suka koma, Saida suka wuce idanun jama'a ya janyota jikinsa Yana shagar kamshin jikinta, a haka suka shige ciki zame jikinta tayi tana Dan dubansa. "ga abinci Nan na kawo maka nan ko can table Amuje". Dan bakinta ya shafa kadan ka Yana kwaikwayon maganarta.. "Bari nayi wanka sai muzo muci abincin nasan kema bakici ba ko?". "Kai ta gyada masa. Gurin da Hajiyar taci abincin ta gyara sannan ta dauko wata table mat da shimfida a kasa ta jera abincin, gurin kayan kallo taje da gani ko hadasu ba'ayi ba, ta tsuguna tana hadawa ya shigo, yayi wanka ya saka Riga armless da wando three quarter blue black na kamfanin Adidas sai fitar da wannan kanshin nashi yakeyi wanda har ya Zama constant a jikinsa, direct inda take ya nufa dago ta yayi "oya taso kibar wannan ba aikin ki bane akwai Wanda zaya hadasu". Kai ta gyada masa ta bishi suka koma, abincin ta zuba musu sukaci Saida suka koshi, sannan ta tattara gurin ta dauke komai ta dawo ta zauna a gefensa. Jikinta ya Dan kwanto Yana Dan matsa kafadar ta. "Precious". Ya Kira sunan sunanta. "Na'am". "Fada min me Haseenar ta fada Miki Kika yi yaji Zaki Kira min Ruwa? Banda Allah yasa Ammah tana yina da kin tayar min da zaune tsaye, ni na taho Ina mararin ki ke kuma kina gudun Zama dani ko?". Sakin kafadar yayi ya kwantar da ita a cinyarsa suna facing na juna. "Nifa na fada maka ba guduwa nayi ba to a cikinsu ai ba Wanda yayi min laifin da zanyi yaji? Kuma Dan lalacewa na tsaya Ina yiwa wannan Mai saffar mazan yaji,kawai dai Naga bazan iya tolerating na nonsense dinta ba,wato zatayi amfani da damarta tayi min illah tunda Nina hanata cikar muradinta ki? Ai naji ance tare kukayi karatu ba a UK? Dan Allah ka fada min waye Kai wallahi zuciyarta taki samun nutsuwa, abubuwan da nake gani a Nan sun girmewa tunanina, pls tell me, Me amor". Tsuru yayi da Ido Yana kallonta Dan kalmar ta bashi mamaki data fito daga bakinta. "A ina Kika iya yaren Portuguese?". Ai Yana fadar haka ta bude Baki alamar mamaki da sauri ta yunkura zata fece ya mayar da ita jikinsa. "Ya haka Zaki gudu daga tambaya". "Nima bansan ko wane yare bane na fada sunan ne naji yayi min Dadi shi yasa na fada maka Ni ko ma'anarsa ban sani ba". Ta fada tana Kara sunne Kai a kirjinsa. "A'a idan ba Rami meya kawo zancen Rami? Meye na Jin kunya tinda kince Baki San ma'nar sunan ba duk da haka yau ranar Nan special ce a gurina badan da dutse tsakanin mu ba da Saina bada special gift Nima".

.✨✨✨

AUREN HUCE HAUSHI.

✨✨✨

MAMAN FATEEMAH.

Page. 47

📖🖋️

________Duk yanda Mahmud yaso zahra ta bashi amsa abun yaci tura da gaske take kunyarsa Bata taba zaton Yana Jin yaren ba, shima kyaleta yayi dan bashi da amsar tambayarta a yanzu dai sai hakan yayi Masa dadi, wata hirar ya dauko Mata ta tafiyar da yayi da ire-iren cigaban da yake ganin makarantun mu zasu samu, har aka Kira sallar la'asar suna gurin tashi yayi suka shiga ciki yayi Shirin masallaci. Misalin karfe takwas da kwata suka fito zuwa unguwar da zata raka shi, sunyi wata irin dacewa dole idan ka kallesu ka Kara, Dan kallonsa tayi "Zan leka na yiwa su Aunty zilai sallama". Daka ya amsa Mata saboda Yana amsa waya. A parlour ta iskesu suna Hira, a gurguje suka gaisa ta fada musu zasu fita, a dawo lafiya sukayi Mata ta juya ta nufi kofa har ta kusa fita ta ji maganar Aunty zilai bayanta. "Uwar dakina Ammah tace a fada Miki ki bude wayarki tana son magana dake, yanzu ba dadewa ta kirani tace na Kai Miki tawa, na fada Mata Mai gidan Yana Nan shine tace to idan kin fito na fada Miki lallai ki bude zakuyi magana". Dan rausayar da Kai zahra tayi da alamun damuwa a fuskarta. "Ni wallahi na kasa bude wayar ne laifi nayi Mata fa". "Laifi Kuma kina Nan tana can akayi laifin?" Kai ta gyada Mata alamar Eh. "Dan Allah ki bude wayar kuyi magana ko hankalinta ya kwanta,Allah a cikin damuwa take". "To shikenan sai mun dawo din". Ta fice tana amsa a dawo lafiyar Aunty zilan. Motarta daya kawo ta gani, Wanda ya Kira da safwan dazu ya fito daga ciki da alamar shiya kawota nan seat din kusa da driver Mahmud ya budewa Zahra Yana fadin "Bismillah" Saida ta zauna sannan ya nufo gurin safwan din yayi Masa magana sannan ya shigo ya tayar da motar suka nufi gate din fita, a dawo lafiya masu gadin sakayi musu Dan ba mutum Daya zahra ta gani ba. Sunyi tafiya Mai Dan nisa kafin ya riko hannunta Bai kalleta ba gabansa yake kallo yace. "Kina tambaya ta wannan gidan na wanene ko?" Ya Dan juyo Yana kallonta. "Eh" ta fada a takaice.

"Gidan a hannuna yake, kusan Kuma ni aka wakilta a Kan ma'aikatan cikinsa to Yana yin rayuwa ne yasa nayi nesa dashi Amma yanzu bani da sabgogi da yawa Ina ga ma anan zamu Dan Zauna na wani lokacin kafin muga yanda za'ayi akan matsalarki ta fibroid din nan dan tunda aka fada min hankalina kasa kwanciya yayi Saida na Kira likitan dana fada Miki, shine yace ya kamata muje suyi nasu binciken su tabbar da abinda Nan din suka fada". Dan marairaice Masa tayi. "Nifa wallahi na warke na fada maka ba wani ciwo fa yanzu Dan Allah ka hakura, kaga su Ammah Basu San zamu Dade ba, kaga harda Mai aikinta ta bani aro fa Kuma kusan itace ma'aminciyarta a fannin abincin bangaren ta".

"Kin warke kamar Yaya? Ai abinda ze Hana a duba min lafiyarki sai ikon Allah kinaji fa Yana Hana Mata haihuwa Ni Kuma da nake son duk shekara ki aje Mana baby koma babies, idan Allah yasa nafi ki karfin jini ki dinga bamu twins, kawai lokaci kadan ki ciki gidan da 'ya'yan mu". Ya fada Yana Kai hannunsa akan cikinta Yana kashe Mata Ido daya. "Oya talk Mana kinyi shiru". "To me kakeso nace ai ka Gama Yanke hukunci". Saita share maganarsa ta biyu. Gidan Sameer suka Fara nufa Sam Sameer din besan da zuwansu ba Saida ya kusa da shiga kuntau din sannan ya kirashi ya fada Masa gasu Nan zuwa. "Masha Allah gida ne shima Babba Mai kyau sosai Amma baiko Kama kafar inda sukayi masauki ba, da fara'a sosai Fateeha ta tarbi zahra wannan shine haduwarsu ta farko face to face ba karamin mamaki Fateeha tayi ba, duk da Sameer ya nuna Mata wani hoton zahra amma sai taga hoton Wasa ne akan zahirin gaskiya ba karya oga Mahmud yayi mace dai dai da level dinsa Dole 'yan bani na iya su dauki na wuta Dana gashi da ita, me wannan mezeci da irinsu Haseena. Da sauri ta garasa gurin zahrar tana fadin "maraba da babbar bakuwa irin wannan zuwan bazata? Ta mika Mata yaron da yake hannunta tana murmushi, itama zahrar murmushin ta mayar Mata. Cikin parlourn suka shiga gaba daya, gaishe da Muhmud din Fateeha tayi, yayi Mata barka, sannan zahrar ma suka Kara gaisawa da oga Sameer, taje ta Mikawa Mahmud Babyn. "Ki rikeshi a haka na ganshi, wallahi bana iya daukar Yara a haka tausayi suke bani, Sai naga kamar Zan karya su ne idan na dauke su".Ya fada Yana jifanta da wani kallo. Itama kallon nasa Zahra tayi da yi Masa alamar zakayi bayani da hausar garinku, tana Dan kada Masa sexy eyes dinta. A haka yayi masa addu'a ya shafa kansa, cheque ya Dora Masa a jikinsa abinda ta gani jikin cheque din ba Karamin mamaki ya Bata ba, shi Kuma Dan gogan Saiya fuske yayi kamar baiga kallon tuhumar data bishi dashi ba. Godiya sosai Fateeha tayiwa Mahmud ta dauki cheque din ta kaiwa Sameer, ba karamin mamaki yayi ba yana Kara duba cheque din Yana kallon Mahmud. Kai ya girgiza Masa "don't say anything pls shi yasa ban baka ba na madam ne wadda tayi nakudar haifar min takwara" Shiru yayi kawai Dan wata kyautar tafi gaban godiyar fatar Baki, a haka Fateeha ta wuce ta barsu tana kakabin abun a zuciyarta Wai shi wane irin kudi wannan bawan Allah ya mallaka Wanda baya Jin ciwon kashe da kyautar su irin haka?. Abubuwa motsa Baki Fateehar ta kawowa Mahmud, sannan taja zahra suka shige bedroom dinta. Kan sofa zahra tayi masauki tana rike da Ayyan sunan da ake fadawa yaron kenan, Fateeha na fadin " Masha Allah, Amarya kin Sha kamshi sai yau Allah yayi haduwarmu?". "Wallahi kuwa Aunty, barka Allah ya Raya Mana". "Amin ya Rabbi, nifa na dauka da Rana zakizo mu yini muna hira Amma sai naji sweetheart Yana fadar Wai gaku Nan a harya". Da gyarawa Ayyan riko tayi tana zame rolling din kanta. "nima bansan da fitar ba sai dazu da yamma yace zamuzo nifa naso ya barni nazo suna lokacin Amma yace a'a saiya dawo zamuzo". Har Fateeha ta bude Baki zatayi magana ta tuna gargadin Sameer akan sakin bakin magana yace ta iya bakinta akan abida Zata fadawa zahrar. "Kinsan komai nufin Allah ne sai yau ne ya kaddari mu hadu,munga sako Allah ya saka da Alkhairi yabar zumunci, Kaya irin haka kamar za'a bude Masa Boutique dasu, wasu ai har ya shekara biyar sannan yayi amfani dasu, Kinga wannan material din da Kika sako min me kalar peach wata sister dina da za'a yiwa biki ta kwallafa rai a kansa tana son tasa ranar dinner da taje kasuwa kasa sayensa tayi 350k 4yrd, saita gano na sayar Mata da nawa tunda suna gidan safwan ya kawo kayan". Ita dai Zahra Shiru tayi Dan ji tayi wani bambarakwai tunda ita dai bataga wasu Kaya ba, amma saita wayance da fadar "lah ba komai ai dan "komai nayiwa d'ana ban fad'i ba, Allah dai ya Raya Mana yayi musu Albarka". "Allahumma Amin". Knocking akayi daga waje, umarni Fateeha ta bayar wata yarinya 'yar matashiya ta shigo da babban tray da kayayyakin motsa Baki a Kai ta aje ta gaishe da zahra ta juya ta fice. Suna cikin hira Sameer ya Kira yace zahra ta fito zasu wuce. Har gurin mota suka rakosu suna ta godiya, jikin window din da zahra take ta Dan leka tana "Fadin zamu mu shigo in Sha Allah mu yini a gurinki tunda ni bakizo Mana da rana ba".

"To ai ba laifina bane Kinga niba sanin garin naku nayi sosai ba sai a yanda akayi Dani". Dariya Fateeha tayi "to ai kin Zama 'yar kanon kema tunda gaki a cikinta Baki San ranar barinta ba". Sameer ne ya yiwa Fateeha magana ta yiwa zahra sallama, ta bude back seat ta saka ledar dake hannunta. Direct gandun Albasa suka nufa gidan mommy, zahra Bata tashi Jin abinda tayi da Bata kyauta ba Saida suka shigo harabar gidan mommy din. Dan marairaice Masa tayi da fuska a Karon farko ta riko hannunsa. "Please me amor ka shiga Kai kadai wallahi kunyar mommy nakeji bazan iya shiga ba". Ta fada a shagwabe kamar zatayi Masa kuka. Saida ya gyara parking sannan ya maido hankalinsa gaba Daya gurinta. Meya hadaki da mommy Kuma da kike Jin kunyar haduwa da ita?". "Jiya fa harda ita a gidan Hajiyar oga Sameer". Mai gadi ne ya karaso Yana gaishe da Mahmud tare da jera masa godiya wadda zahra Bata Dan isalinta ba, fitowa Mahmud yayi suka gaisa da Mai gadin,abinda ya tilastawa Zahra fitowa, gaishe da Mai gadin tayi ta Dan Fara tafiya duk da Batasan inda kofar shigar take ba. Gurin wasu kujeru data gani ta nufa ta zauna da alamar Kamar Baki ne suka tashi daga gurin. A Nan ya sameta ya Mika Mata hannunsa ta kama ya mikar da ita tsaye, "zo muje ciki dare Yana karayi kin zaunar damu a gurin Fateeha kome kuje fada ma oho Allah yasa dai ba gulma kujeyi ba". Kafin tayi yunkurin bashi amsa daga bayansu sukaji maganar Rukayya "lah wa nake gani kamar Ya Mahmud da Auntyn mu?" Da sauri zahra ta zame hannunta ta juya baya tana Fadin "wallahi Aunty Rukayya nayi fushi saboda Allah saiki taho bako sallama". "Ayya sorry wallahi Nima karfina akafi dole tasa na taho kinsan Ya Sameer ba sauki shine ya tattaroni ko wanka fa sai a gidan Nan nayi". Ta juya ya Mahmud Ina yini an dawo lafiya?".

"Lafiya kalau Ruky ya kikaji da 'yar rigima Ashe Kuma yaji tayi muku ta gudu". "Wallahi kuwa ya Mahmud ai jiya nayi kuka kamar ba gobe tashin hankalina Daya idan ta B'ata me za'a fada maka idan ka dawo Ashe kana hanya". Baki zahra ta zubura tana kiftawa Rukayya Ido. Kafin yayi magana sukaji magana daga bayansu. "Waye nake gani kamar DANGEN SHUNI!?" Da sauri Mahmud ya juya itama zahra juyawar tayi Jin kamar muryar data sani ce take Fadin hakan. "Lah! Lah! Lah! Wa nake gani haka? Zakariyya Daman ana ganinku, rabon da mu hadu tun zuwana na karshen kontagora". Zahra ce ta Matso tana Fadin Lah Ya Abba, Kaine ina yini?" "Lafiya kalau ya kukaje gida? ai da safe na Kira Rukayya take fada min bakwa tare ta dawo gida". "Eh wallahi, yasu Umma?" "Suna lafiya daga Ina haka?" Dan kallon Mahmud tayi kafin tace Masa "daga gida muke Mommy mukazo gaishewa". Kusa da Mahmud ya matso Yana Fadin "DANGEN SHUNI! Allah ya taimaki manyan kasa. Daman ana ganinku haka available? Gaskiya na zama lucky. Daman wallahi neman number ka nakeyi nayi interview da kamfanin ku na Nan Kano last two weeks Amma har yau ban samu number ba, kasan lamarin kasar Saida wakasani,to ya akaji da jama'a?" . "Lafiya kalau Alhamdulillahi, Rukayya ki bashi number ta zamuyi maganar later, ko kana Shirin Zama sirikina ne?". 'yar dariya yayi "Hakan nake fata ai zuwan zahra jiya Ni Alkhairi ya zamar min". Dan Jim Mahmud yayi, me kenan zakariyya kenan brother din sajida ne? "Anyway we'll talk later in Sha Allah, madam let's go". Sukayi sallama da Ya Abba suka nufi ciki zuciyar zahra fal murna wato duk abinda Allah yayi akwai hikima a cikinsa, wannan dalilin ne yasa ta tattara ta nufi Janbulo Ashe ita zata Zama dalilin haduwarsu.

Saida suka gulewa ganinsu sannan Ya Abba ya kalli Rukayya, "Daman Kuna da relation da DANGE?". "Eh aminin Ya Sameer ne tun suna secondary School, yanzu haka shine P.A dinsa ai jiya zahra da muka dauko daga can wife dinsa ce an samu wani incidence ne tayi tafiyar ta can Janbulo din". Baki sake yake kallon Rukayya abin jinsa yake kamar Almara badan ya gansu tare ba baze taba gaskata zance Rukayya ba, gaskiya he's surprised to ai shi ba haka maganar tazo Masa ba daga bakin sajida.

"Wai kina nufin DANGE ne mijin zahra?"

"Eh Mana shine, Wai Daman Kasan Ya Mahmud din ne?" "So sai kuwa farin sani, muna haduwa da a kwantagora a unguwa Daya ma kuwa, ai kakarsa ta wurin Babansa 'yar can ce Nima kakata 'yar can ce Ummar mu kadai ta Haifa a Rimin sumaila Aurenta ya mutu ta koma gida, duk 'yan uwan Umma suna can kwantagoran na Niger state da Abuja, kinsa meya daure min Kai kuwa?" Girgiza Masa Kai tayi alamar A'a. "Cewa fa akayi ita zahrar an aura Mata Almajirin wani malami da yake a unguwarsu saboda duk Wanda yazo ze aureta sai an fasa Auren"

"Nima naji kadan daga labarinta gurin ya Sameer to ga dai mijinta Nan sauran bayanin Kuma ban San yanda akayi ya faru ba, tunda ya Sameer ba fada mana zeyi ba".

A parlour suka Sami mommy da kannan Rukayya Mata Bilkisu da Husna sai karamar yarinya 'yar Auntyn su Sameer Afra.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull