Kenza eBookz

Baƙin ruhi complete by mrs sadauki - Chapter 1

Baƙin ruhi complete by mrs sadauki - Chapter 1

Baƙin ruhi complete by mrs sadauki Chapter 1: Baƙin ruhi complete by mrs sadauki Chapter 1. *BAƘIN RUHI*🧌🐲

4,489 words

*BAƘIN RUHI*🧌🐲

```LoVe aNd HoRrOr story```👽

By Chamsiya Laouali Rabo {MRS SADAUKI💫✍️}

*SADAUKARWA :* Ga dukkan iyayenmu MATA da suka tsaya tsayin daka don bamu kariya a kan dukkan wani da ke son cutar da mu.

*FCWA*☀️

________________________

Happy sallah my dear fans, Allah karɓi ibadunmu Amen !!!

*Wannan labari da da kaso saba'in ya faru da gaske,don haka don Allah kar wacce ta ji haushina yayin ganin abin da ya saɓawa ra'ayi*

01

"Kowanne ahali da nasa sirrin,haka kowanne ahali da nasu tabo ko ƙaddara ko kuma dai wani al'amari wanda suke ɓoye wa.Motar tsautsayi ce ta ja ni na bankaɗe mayafin da ya luluɓe baƙin sirrin gidanmu wanda silar haka yasa na baro ahalina domin tseratar da da gajiyayen ruhina,wanda aka raunata shi ta sigogi da dama" na yi shuru saboda hawayen da suka cika min ido.Ita kuwa Lubna banda aukin kallona babu abin da take yi,da dukkan alamu ta ƙagu ta ji ainahin labarin nawa.

Na ɗan yi murmushi mai ciwo wanda ya bai wa ƙwallar da ta taru a idona sa'ar zubowa kan kumatuna,na ci gaba da cewa " Gidanmu irin family house ne wanda za ki kaf yayyu da ƙannai a ciki,mu biyar ne mahaifiyarmu ta haifa,mu biyu ne mata ukun maza.Anty Aliya ce babba,sai Aliyu,sannan Fahad,sai ni sannan autanmu Haidar.Sannan akwai ƴaƴan kawunana su ma duk da matansu da ƴaƴansu,duk yawanmu a tukunya guda ake yi mana girki haka muka taso muka ga iyayenmu na yi.Sannan in za a ci abinci ma su iyayenmu maza a tare suke ci haka ma matan,mu kuma ana banbanta wa ƴan sa'inni ɗaya ake zuba mana a cikin faranti guda da wannan ne na yi sabo da cousin/cousine ɗita Hassana wacce ƴan biyu ne su ɗaya ta rasu a wani dare bayan mun gama cin abinci.Ni da Hassana akwai wani abu da ke faruwa cikin ahalinmu da yake mugun ɗaure mana kai yake kuma ci mamu tuwo a ƙwarya.Ba zan manta wata rana mun je ɗebo ruwa a ƙatuwar rijiyar da ke can bayan ɗakunanmu Hassana ta dube ni da kyau ta ce "Haule har yanzu mutuwar Husseina ta ƙi fita raina , kowane dare sai na yi mafarkinta tana kuka tana ce min na cece ta,amma jiya sai take ban shawara wai na gudu na bar gida ban san dalili ba"

"Kawai don kin san abin a rai ne shi yasa, sannan duba da cewa ku ƴan biyu ne ƙila shi yasa kika kasa fidda abin a kanki amma kusan shekara fa yanzu da ta rasu" shi ne abin da na faɗa mata a wancan lokacin amma sai ta girgiza kai ta ce "a'a na fi tunanin dai wani abun ne yasa take zuwar min a mafarki, sannan kar ki manta ko sau ɗaya ba ta take rana sai ta kawo min ziyara tana maimaita abu guda na cece ta,amma na jiya ya banbanta kawai ta ce na gudu" ban kai ga ce mata komai ba goggo Lami wacce ta kasance mahaifiyar Hassana ta iso bakin rijiyar,sam ba mu yi tunanin ta ji abin da muke cewa ba don ba ta nuna alamu ba kawai dai ta ɗauki bokitin da muka cika da ruwa ta tafi.To mu ma sai muka watsar da zancen muka ci gaba da aikinmu,bayan mun gama sai muka koma can cikin gida.

Wani irin kallo na ga Innarmu na bi na da shi,tun ban damu ba har na soma tsarguwa sai kawai na bar inda take don kaucewa kallon.Da dare bayan duk mun yi sallar isha'i muka fito cin abinci,tamkar wasu ƴan biki haka duk muka yi kashi-kashi muka kewaya kowa da faratinsu muna ci muna santin girkin iyayen namu har muka gama sai aka soma yin gatana har sai da dare ya tsala sannan duk muka rabu.

Ina shiga ɗakinmu har na kwanta na ji muryar Innarmu ta kira sunana cikin wani sauti "Haule?" sai da gabana ya faɗi amma na daure na ce "na'am Innarmu"

"Zo nan" ta faɗa ,sai na tashi na je kusa da gadon ƙarfenta mai rumfa na yi tsaye tare da sunne kai saboda har zuwa yanzu irin kallon nan ne na ga tana yi min. "Kar na sake jin kin yi zancen nan ke da Hassana ,kin ji ko ba ki ji ba?"

"Wane zance Innarmu?" na tambaye ta don ni har ga Allah na manta. "Na mutuwar Husseina,ki je ki kwanta" shi ne abin da ta ce,na je na kwanta ɗin sai dai fa sam ba baccin na yi ba kamar yadda na so yi tun farko.

Ido kawai na lumshe,ina jin lokacin da anty Aliya ta zo ta kwanta gefena bayan kuma Innarmu ta ce ta kashe ƙwan lantarki.Duhu na game ɗakin na buɗe idona,tunanin na shiga yi iri-iri yadda ake yawan yin mutuwa gidanmu kusan kuma duk date iri ɗaya ne.Na jima sosai cikin wannan tunanin,don gari yayi tsit kafin kuma na soma jin motsi a can babban falon ahali.Kamar munafuka haka na miƙe na fita,amma ban fita zuwa ƙaramin falo sai na laɓe,iyayenmu maza na gani kaf illahirinsu suna magana akan zancen da ban san ina ya dosa ba.

"Ibrahim yanzu ta ɓangarenka ya kamata mu fitar da alƙawari" Kawu Hamza ya faɗa wanda shi ne babba kaf cikinsu.

Kawu Laminu ya karɓe da cewa "hakan shi ne daidai,kuma dai kyautar namiji don ni ai mace na bayar wancan lokacin " wato mahaifin Hassana .

Ibrahim wanda ya kasance mahaifina yanayin fuskarsa ce ta ɗan canza kafin ya ce "zan yi shawara" sai kuma suka miƙe suka shiga wani ɗaki ƙwaya ɗaya tal wanda tun da na yi wayo ban taɓa ganin an buɗe shi ba sai yanzu.

Ba tare da na san mene ne meeting ɗin nasu ya ƙumsa ba sai na koma kan shimfiɗata na kwanta.Ina shirin rufe ido haske ya game ɗakin nan muka haɗa ido da Innarmu,"daga ina kike?" ta jefo min tambayar da kafin na bata amsa Haidar ya fashe da wani masifafen kuka wanda yasa Innarmu nufarsa da sauri.

Haidar ƙaramin yaro ne duka ba a yi wata biyu da yaye shi ba,ruwa Innarmu ta basa amma yadda take ɗura masa su to kamar haka ya maido su ta baki da hanci kafin kuma daga ƙarshe jini ya zubo masa ta hanci shi kenan bai ƙara motsi ba" ina kawowa nan na miƙe na bar Lubna zaune sake da baki da hanci.

"Haule ina kuma za ki je?" ta tambaye ni,ba tare da na juyo ba na ce "zan wanke kwanuka kafin Hajiya ta dawo".

Wurin da aka tanada don yin wanke-wanke na nufa na soma wanke plate ɗin da customa suka ci abinci.Ina tsaka da yi Lubna ta zo tana yi min ɗauraya,mun yi kamar minti biyar muna aikin kafin ta ce "fatan dai ba mutuwa Haidar ɗin yayi ba?"

Na san halin Lubna da mugun son jin labari,in ba ta gamsu ba to ƙila har gida tana iya bina don ta ji ƙarashe hakan yasa na ɗora daga inda na tsaya.

"Ina tsaye a gaban idona Innarmu ta soma yin hawaye tare da furici guda "don me sai Haidar?" wannan kalmar ta daɗe tana yi min yawo cikin kwanya don nemo ma'anarta amma tsawon lokaci ban samu ba.Na durƙushe kan gwiwaina tare da tambayarta "Innarmu me ya samu Haidar ɗin?"

"Ya mutu Haule! Haidar ya mutu!" ta bani amsa tana ƙanƙame gawar Haidar,ban san lokacin da na yi kururuwa ba wacce kusan ita ta tashi kowa na gidan ciki kuwa har da anty Aliya.

Kan ki ce wani abu ɗakinmu ya cika da mutane,ana ta kuka goggo Lami ce ta je ta rungume Innarmu tana bata haƙuri.Yayin da Hassana ta yi tsaye kusa da ni ta ce "duba ki ga irin yadda Husseina ta yi ne yayin mutuwarta" cak hawayen da suke yi min zuba suka ɗauke,yayin da idona ya soma tariyo min gawar Husseina wacce har bayan an yi mata wanka jinin da ya fita ta hancinta yana nan bai goge na sai ma ƙari da aka samu wanda kafin safe har da idonta suke shatatar da kukan jini.Ban iya cewa Hassana komai ba a wannan lokacin sai dai mun ci gaba da kukan mutuwar Haidar,wanda har asubah babu uba namiji ko ɗaya da ya leƙo ɗakinmu sai da gari yayi haske shi ma ɗin karɓar gawar suka zo.

Bayan an yi wa Haidar wanka aka bai wa Innarmu damar yi masa ganin ƙarshe,haka don ƙwaƙuwa na mara mata baya har sai da ta buɗe likafanin nan na yi arba da idonsa su ma suna shatatar da jini.Kuka ne ya kubcewa Innarmu,kawai aka rufe gawar tare da fita shi nan gidan namu ya ƙara kancamewa da koke-koke ganin an fita da shi.

Ana cikin zaman makoki ne Hassana ta zo ta ja ni gefe,na ce "ke lafiya?" Sai da ta waiwaiga sannan ta ce "jiya bayan mun kwanta na yi mafarkin Husseina ta ce na baki kayanta waɗannan wanda ta mutu da su ki saka a jikinki"

"Saboda me?" na tambaye ta ,ta ce "ke dai don Allah ki saka" nan na yi da ita zan saka ɗin kamar yadda ta buƙata" sai kuma na sake yin shuru na kalli Lubna wacce ta tsaya cak da yin aikin,na sakar mata murmushi na ce "ya dai kin tsorata ne? Ai ba ki ji komai ba nan duk shimfiɗa ce ke dai ki yi haƙuri da sannu duk za ki ji dukkan labarina"

Lubna ta ce "ai duk jikina yayi sanyi duk da dai ni ma da nawa labarin mai matuƙar firgici "

Masifar Hajiya ce ta katse hirar tamu,da sauri na fita ina bata haƙuri ita kuwa kamar ƙara zuga ta nake sai ƙaimi take ƙarawa wurin faɗan.

"In ba ku canza ba wallahi sai duk na kore ku na kawo sabbin ma'aikata,dubi yadda har yanzu ba ku goge table ba".

"Yi haƙuri Hajiya amma don Allah kar ki kore ni ba ni da kowa" na faɗa murya na ɗan rawa ,amma da yake Hajiya ƙarshe ce wurin rashin mutumci sai ta tsiro da wani zancen "yau ba za ki ci abincina ba sai da ki saya da kuɗinki,saboda kin ga ina tausayinki ne kike yi min iya shege" tana gama faɗar haka ta yi ƙuuu ta fice,ni kuma na yi baya na zauna kan kujera saboda kaina da ke mugun sara min..... *BAƘIN RUHI*🧌🐲

```LoVe aNd HoRrOr story```👽

By Chamsiya Laouali Rabo {MRS SADAUKI💫✍️}

*SADAUKARWA :* Ga dukkan iyayenmu MATA da suka tsaya tsayin daka don bamu kariya a kan dukkan wani da ke son cutar da mu.

*FCWA*☀️

________________________

02

In akwai abin da ya fi ɗaga min hankali shine zancen kora ta da Hajiya ta ce tana iya yi,wanda kuma ya ɓata min rai shi ne yadda a kullum take wulaƙanta ni kawai don ina ƙarƙashinta.

Lubna ta fito wacce ita tun tuni ta gama aikinta,dama ita iya girki ne take yi.Ni kuma tarben baƙi da kawo musu abin da suka buƙata,sai kuma wanke kwanuka da share restaurant ɗin.

"Ki je ki yi wanke-wanken ni sai na goge wurin" ta faɗa cikin sanyin murya,ban ce mata komai ba na miƙe dakyar na je na ida aikin nawa.Sannan na dawo nan muka ƙarasa gugar,bayan mun gama na rufe ko ina kafin mu kama hanyar gidan Hajiya .Da ɗan nisa wannan yasa sai da muka yi sauri kafin mu isa,a falo muka tarar da ita ta ƙure ƙarshen ac amma duk da haka sai gumi take fitarwa. Kallo ɗaya na yi mata na ɗauke kai,saɓanin Lubna da ta je tana cewa "hajiya ko jikin ne ya motsa?"

Cikin murya wacce kana ji ka san babu lafiya ta ce "olser ce ta yi min wuf sai ɗan kanoma,ki bani maganin nan na sha wanda kike bani"

Lubna ta ɗan dube ni kafin ta ce "ai Haule ce ke da shi dama ba ni ba"

"To ki karɓo min" Ina jin haka na yi saurin wucewa can ɗakinmu da aka ware na ƴan aiki.Ina tsaka da rage kayan jikina Lubna ta shigo hannunta riƙe da kofi ta ce "ki zuba na kai mata"

Cikin ƙunar rai na ce "na ƙi na zuba ina ce dai yawuna ne"

Lubna ta tuntsire da dariya tare ɗan matsowa kusa da ni ta ce "ke ba abin alfaharinki ba ne a ce kamar Hajiya tana shan yawun ƴar aiki ? Kin san da ace ta san mene ne ainahin maganin da ba za ta sha ba Alkur'an yadda ta tsani talaka"

Wani ɗan murmushi na yi kafin na tofa yawuna cikin kofin ruwan,nan take suka soma tafasa suna motsi tare da canza kala. Lubna ta ɗaga gira ta ce "ai ke ce Hajiyar,sannan don Allah ki yi haƙuri ki bar saka mana hajiyarmu cikin wancan halin kar ta je ta mutu mu shiga tara"

"Tafi dai ki kai mata kika tsaya surutu" na faɗa tare da shiga toilet na yi wanka,ko da na fito sai na tarar da Lubna ta kawo mana abinci.Nan ɗin ma wani murmushi na yi kafin na ce "cewa ta yi fa ba za ta ban abincinta ba"

"Tun da dai ta zuba miki sai ki yi haƙuri ki zo mu ci" cewar Lubna.

Sai da na canza kaya sannan na zauna muka ci shinkafa da miya muka hauda ruwa masu sanyi.Sai kuma muka hau yin hira kafin kuma ta miƙe ta ce "bari na je na gyara kayan miya na gobe,ki shirya don da na dawo za ki ɗora min labarinki" na yi murmushi kawai ba tare da na ce komai ba.

Ina shirin kwanciya Lubna ta shigo kamar an jefo ta,na ce "ke lafiya?"

Ta ce "uban ƴan tsamin rai ne ga shi can a falo tare da Hajiya yana juya kofin da na bata ruwa wai yana son ganin wane irin magani ne wannan da ta sha ta samu lafiya lokaci guda"

Na ce "to mene ne na ga duk kin tayar da hankali?"

Ta waro ido ta ce "hajiya ce ta basa amsa wai ke ce kike da maganin,kuma walla..."sauran maganar ce ta maƙale mata ganin an banko ƙofa da mugun ƙarfi har ni ma sai da na zabura yayin da haɗuwar idonmu ya saukar min da matsanancin faɗuwar gaba amma na aro mayafin jarumta na gaishe shi cike da ladabi kamar yadda uwarsa ta ce mu dinga yi.

"Ina wuni Alhaji ?" na furta cikin sanyin murya ina mai sauke idona ƙasa.

"Bani maganin da kika jiƙawa Mama " shi ne abin da ya ce.

Na ce "ya ida ai dama guda ne ya rage"

"Bani kwalinsa " "Bai da kwali " "Ina aka taɓa sayar da magani babu kwali?" "Wannan ɗin ba sayar da shi ake yi ba ai,na gargajiya ne"

"Ina son ganin ledar da aka ƙulla shi to" ya faɗa cikin son sai ya ƙure ni,na ɗago kai na kalle shi kafin na juyar da idona gefe na ce "na share ledar"

Bai ƙara cewa komai ba ya fice ƙuuu tare da banko ƙofa.

"Ina ga gida zan je zuwa an jima sai na dawo, wannan masifar ba ta ida ba wallahi sai ya sake dawowa kin san shi da zafin kai.Kuma ni ban son ganinsa cikin wannan halin duk sai na ji babu daɗi kuma gwiwaina su yi sanyi" Lubna ta faɗa tana yin wani kalar tausayi.

Na taɓe baki na ce "ni ban ga abin da kika gani a jikinsa ba da har kike wani sonsa haka,mutum a bushe kamar mai cutar HIV sai shegun manyan ido kamar ƙuliƙuli dama-dama dai lips ɗin nasa su ne kawai masu kyau"

Lubna ta yi min dundun wasa ta ce "ke ban fa son rainin hankali,alhajin ne kike shammata haka? Haba dai! Kuma ni ba sonsa nake yi ba kawai dai yana burge ni" ta ƙarashe zancen tana wani murmushi mai tona asirin zuciyarta.

Canza zancen na yi na kamo wani," sai yaushe za ki dawowa nan da kwana? Allah na gaji da zama ni ɗaya cikin ɗaki kamar mayya"

Lubna ta ce "ke na manta ban faɗa miki ba,ɗazu bayan kin tafi restaurant an kawo wata ƴar aiki da alamu nan za ta zauna ita ma tun da ba ta da kowa kamar ke take"

"Ni babu ruwana da wata,ke nake magana yaushe za ki dawo nan? Na ga dai san ba za a hana ki ba duba da Umma ƙawar Hajiya ce "

"In na je yau zan tambaye ta in ji in za ta bar ni,amma da wuya kam zan dai gwada.Na tafi sai zuwa yamma zan zo kamar kullum" cewar Lubna .Sai na saka hijabi domin yi mata rakiya duk da ba wani nisa ne ke da kwai da gidan Hajiya zuwa nasu .

Muna ratso falon muryarsa ta tarbe mu sai masifa yake duk a kan maganin da na bai wa uwarsa ta sha ta warke. Muna haɗa ido da shi ya ce "nan gaba duk ƴar iskar da ta sake bai wa Mamana maganin ƴan bori sai na kulle ta ,kar a sake shigo mana da kayan tsibo cikin gidan.Ke ma Mama ki rasa maganin da za ki sha sai na gargajiya? To mene ne amfanin karatun likitacin nawa?"

Ban kula shi ba don na fahimci tun ranar da na zo nan gidan ya tsane ni,wannan dalilin yasa ni ma yake ban haushi.Muna fitowa daga gidan Lubna ta ja wata ajiyar zuciya a bayyane kafin ta ce,"matar Maheee nada jan aiki,a yi mutum sai masifa kuma sam bai ma gajiya "

Na ce "shi yasa yake ramewa ita ce duk ta cinye shi masifafe Allah ma ya raba ki da aurensa,don wannan ina ga har dukan mace sai yayi"

Lubna ta ƙyalƙyace da dariya ta ce "mutumniyata inda fa kike burge ni ke ɗin kamar yayen aljanu kike,to in faɗa miki jiya-jiyan nan ya ɗirka wa buduwarsa shegen duka saboda ya tarar da ita tana hira da wani ɗan ajinsu.Ina jin Hajiya na bai wa uwar budurwa haƙuri wai shegiyar zuciya ce da shi wannan yasa bai controling kansa"

Ban san me yasa na ji zuciyata ta yi min wani iri ba duk sai na ji babu daɗi,na ce "budurwa? Dama yana da budurwa ne?"

"Kin ji ki da wani zancen kuma,kamar Maheee ɗin ne zai rasa budurwa? Hum! To in faɗa miki shegen son mata ne da shi a yadda na ji Ummah na faɗa ƴan matan da yayi ba su da iyaka,in kin gansa da wannan yau to da an kwana biyu ya canza wata"

Cike da ɗacin rai na ce "amma kuma bai yi kama da mai son mata ba,duba da ko kallon su bai yi.In fa kin ga ya kalle ki to fitinarsa ce ta motsa kawai don ya tsorata ka da shegun idonsa kamar na jinjirin jinnu"

Lubna ta ce "ki shirya wata rana mu je asibitin da yake aiki ki ga yadda mata ke ɗaukar wanka saboda shi,kuma wallahi har da matan aure"

Ban ƙara ce mata komai ba na yi gaba don dama can tsaye muka yi muna ta zuba,sam ban ji wuyar tafiyar ba saboda yadda zuciyata ke azalzala tana wani irin zafi .Ban taɓa jin haushinsa sosai kamar irin na yau ba,kamar wasu kurame haka muka ci gaba da tafiya har muka isa gidansu Lubna.

A tsakar gida muka tarar da Ummah tana gyara wake,bayan mun gaishe ta sai muka shiga daga ciki.Kan katifar da ke shimfiɗe na yi wa kaina masauki na kwanta tare da yin lamo,maganganu Lubna ta kai wa junansu karo a cikin kwanyata.

"Bari na yi wanka,kin ga kunun tsamiya nan ki zuba ki sha" ta faɗa kafin ta fice,sai dai a yadda ta bar ni haka ta same ni.Cike da mamaki take cewa "wai ba ki sha kunun ba?"

Na ɗan yamutsa fuska na ce "ban ra'ayi ne"

Ta taɓe baki kafin ta ce "ke ma ai jujun ce kamar Maheer ba a gane kanki wani sa'in ni dai ci gaba da bani labarin naki "

Na ja ajiyar zuciya kafin na ce "zan baki har mu koma can gidan Hajiya "

"Ni dai ki fara bani yanzu"

Na ce "a daren ranar muka faki idon Goggo Lami muka je ni da Hassana muka binciko kayan Husseina waɗanda suke ajiye ko tsinke ba a taɓa ba.Kayan da ta mutu da su wata doguwar rigar atamfa ce,tana mugun sonta wanda kusan tana yawan saka su wannan yasa har zuwa lokacin ba mu manta ta ba.A nan cikin ɗakinsu Hassana na saka rigar sannan na hauda tawa a sama,sai na mayar da hijabina.Waje muka fita kamar babu komai muka zauna cikin ƴan uwanmu muka ci abinci kafin duk a watse saboda yau babu wata hira mai daɗi da za mu yi in banda ta jajen mutuwar Haidar . Ko da na je ɗakinmu sam ban cire hijabi ba da shi na kwanta,babu jimawa kuwa bacci ya ɗauke ni.A cikin baccin na ji ana buga ƙofa tare da kiran sunana,na buɗe ido sai na yi tozali da Husseina sanye cikin kayan matattu wato likafani.Idonta na zubar da hawayen jini take kallona,kafin ta ɓace ba tare da ta ce min komai ba..." Lubna ta yi saurin katse ni "wai a zahiri kika gan ta?"

Na ɗan harare ta na ce "ke fa ba ki iya cin ƙwan makauniya ba,ki bari na baki labarin mana"

"To na bari" ta faɗa tana gyara zama.

Ni kuma na ci gaba da cewa "daidai nan na farka daga bacci sai na fahimci mafarkinta ne na yi,wanda kuma hakan ba ta taɓa faruwa da ni ba in ba yau da na saka kayanta ba.A lokacin wani irin tsoro ne ya kama ni sai na kasa yin bacci,don da zarar na rufe ido Husseina nake gani tsaye kusan ƙafafuna da fararen kayanta .Ƙwan lantarki na kunna saboda tsoro,ɗakin ya kawo haske sai na ga Innarmu zaune a tsakiyar gado ta yi tagumi da dukkan hannuwanta yayin da kuma hawaye ke yi mata shatata kamar an kunna pampo.Na matsa kusa da ita na ce "Innarmu kuka kike? Ki yi haƙuri don Allah ki bar kuka in kina yi hankalina tashi yake" ban san me ya ja ra'ayin Innarmu a wannan lokacin kawai dai na ji ta jawo ni tare da rungume ni tana mai cewa "Haule ina son nesanta ki daga gidan nan amma banda ƙarfi ko izzar yin haka,na sani ke ce ta gaba"

"Ta gaba kamar yaya? Innarmu wai mene ne kike son faɗa min?" na tambaye ta duk da a lokacin ba zan wuce shekara goma sha biyu ba amma na fahimci kamar da akwai wani sirri da Innarmu ke ɓoye min" ina kawowa nan sai na yi shuru ina goge ƙwallar da ke yi min zuba saboda wata irin kewar mahaifiyata da ta tsirga min,na miƙe na ce "zan tafi sai kin iso"

"Jira na saka kaya mu koma tare" ta faɗa ita ma duk idonta sun yi ja,bayan ta kimtsa muka yi wa Ummah sallama muka dawo gidan Hajiya sai kuma muka tarar da wani sabon tashin hankali Maheer ne a kwance duk ya sandare kamar gawa ga kuma likita biyu kai gare shi.Ni da Lubna muka kalli juna don kuwa tuni muka san mene ne matsalar,da kuma maganin da zai warkar da shi..... *BAƘIN RUHI*🧌🐲

```LoVe aNd HoRrOr story```👽

By Chamsiya Laouali Rabo {MRS SADAUKI💫✍️}

*SADAUKARWA :* Ga dukkan iyayenmu MATA da suka tsaya tsayin daka don bamu kariya a kan dukkan wani da ke son cutar da mu.

*FCWA*☀️

________________________

03

Daga inda nake tsaye muke ƴar kallon-kallon ni da Maheer,kallo ne yake yi min wanda ke nuni da cewa eh ya san komai a kaina.A yadda yake juya idonsa tuni na fahimci abin da ke zuciyarsa,magana yake yi min ta ido wacce kuma sarai nake jin abin da yake cewa tamkar da bakinsa ne yake magana.

"Ki zo ki cire min ƙwayar kambun maitarki da kika jefa min ,in kuma mutuwata ce farin cikinki shi kenan sai ki ci gaba da riƙon inuwata da kika damƙe"

Ido na lumshe bayan na gama sauraran abin da ke fito wa daga idonsa,maimakon na basa amsa ko yi masa zancen abin da ya shafi maganin cutarsa sai tambaya da na jefo masa ni ma ta ido kamar yadda yayi min ,"wane ne kai ? " ƙin bani amsa yayi sai ya juyar da kansa gefe.

"Kar dai ki ce min zargina gaskiya ne ke ce kika jefa shi cikin wannan halin?" Lubna ta tambaye ni tana mai matso bakinta kusan kunnena."Ki ɗauko kofin ruwa ki same ni a ɗaki" shi ne abin da na ce mata kafin na yi gaba abina,babu jimawa kuwa ta shigo kofin hannunta na karɓa na yi ta kallon ruwan na ƴan sakanni kafin na tofa yawuna a ciki suka fara tafasa suna canza kala a sannu-sannu,sai kuma na ƙara tofa wasu sannan na miƙa mata kofin ta fita.

Na ja wata ajiyar zuciya ina jin duk babu daɗi yadda ya wahala domin ni,duk da cewa ni kaina ban son hakan nake yi ba na cutar da mutanen da suka ɓata min rai. Na saki ɗan murmushi a fili na ce "ko wane ne shi? Ta ya aka yi yake magana da ido?" ban kai ga samo amsa ba Lubna ta shigo tana yi min wani kallo kafin ta ce "sai ki je suna son yin magana da ke"

Na ce "su wa?" "Likitocin da suka kasa yi masa magani mana,a gabansu na basa ruwan ya sha ya kuma tashi daram ya zauna kan ƙafafunsa shine suke son sanin sunan itaciyar maganin da kika yi amfani da ita"

Banda kallonta babu abin da nake yi,kafin ma na ce wani abu Hajiya ta shigo ɗakin tana washe baki tare da kamo hannuna ta ce "zo mu je yarinya kin zama cele ai ,manyan likitoci sun kasa maganin cutar Maheer amma maganinki na gargajiya ya warkar da shi garas.Kar ki so ki ga yadda na fita a guje neman taxi ni na manta ma da akwai mota a gidan,ina dawowa kuma aka ce ke ce kika basa maganin" tana maganar ne tana jan hannuna har muka iso falon.

Wani irin faɗuwa gabana yake yi,ga manyan likitocin da duniya ta san da su don har a tv ana nuno su.Duk sun gyara zama suna jiran amsa daga gare ni,shi kuma gogan ya wani haɗe rai kamar ba shi ne ya gama shan yawuna ba yanzu.

"Ga ta nan ita ce mai maganin" Hajiya ta faɗa tana wani murmushi kafin ta ɗan bangaje ni ta ce "ki gaishe su"

A ɗan rikice na ce "ina wuninku?" kusan duk a tare suka amsa kafin ɗayan ya ce "hajiya dama wannan ce ai kamar na sha ganinta restaurant " yayi furucin yana wani sanyayyen murmushi yana ɗan ƙare min kallo.

"Eh ita ce, tana ɗaya daga cikin masu kula da restaurant ɗin ai" Hajiya ta faɗa .

"To likitar gargajiya muna son ganin maganin naki " ya ƙara faɗa wannan karon cikin raha. Da sauri na kalli Hajiya kafin kuma na maida dubana ga Maheer wanda nake jin idonsa a kaina tun ɗazu.

"Eh muna son gani Please " shi ma ɗayan likitan ya faɗa.

Readers Also Read