Kenza eBookz

Baƙin ruhi complete by mrs sadauki - Chapter 18

Baƙin ruhi complete by mrs sadauki - Chapter 18

Baƙin ruhi complete by mrs sadauki Chapter 18: Baƙin ruhi complete by mrs sadauki Chapter 18. Ta yi wani murmushi kafin ta ce "Annabin Allah ne ya zo mana…

4,463 words

Ta yi wani murmushi kafin ta ce "Annabin Allah ne ya zo mana da shi fa kin ga ba za a ce bai da amfani ba,sosai ake yin ruƙiya da shi a ƙasashen kiristoci"

"Amma ai musulunci ne addinin gaskiya"

"Shi ma wanda aka bai wa littafin Bible ai musulmi ne,sai dai kuskuren da aka samu shine yadda mabiyan Bible suka bin son zuciya na ci gaba da amfani da shi alhalin hatta Bible ɗin ya faɗa musu cewa akwai Manzo na ƙarshe da zai zo shi za su bi,sannan littafin da ya zo shine za su ci gaba da karantawa su kuma yi aiki da shi"

Na ce "Kaka duk kin san wannan amma kike ci gaba da rayuwa a haka? Kawai ki musulunta hakan shine daidai"

Ta ce "gani na yi na tsufa sosai"

"Shi addini ai babu ruwansa da tsufa kawai ki tuba ki koma turbar gaskiya"

Ta jinjina kai tare da yi min alƙawarin za ta musulunta sai kuma ta tambaye ni,"ina ne gidanku?"

Shiru na yi kafin na ce "gidan malam mijin Agwe "

"To tashi mu je na yi miki rakiya" ta faɗa sai duk muka fito,ashe babu ma wani nisa .A ƙofar gida muka ga malam,shi ne kuma ya baiwa Kaka kalmar shahada ta biya ta a gabana kafin na shiga ciki.

Wanki na tarar anty Agwe na yi,muna haɗa ido ta kawar da kai bayan ta yi min kallon banza .Jikina ne yayi sanyi ganin canjin da aka samu, ina shirin gaishe ta idona ya sauka ga Jafet wanda ke wasa da ruwan da aka yi masa wanka .Muna haɗa ido ya sakar min murmushi irin na nasarar nan ,wato abin da na fahimta zuwa yanzu ya tabbatar wa kansa ina ganin ɓoyayyar siffarsa.

"Kar ki sake kallon yarona,kuma yau sai kin bar gidan nan bari malam ya shigo " Agwe ta faɗa tana zuwa ta ɗauke shi ta goye a baya shi kuwa munafiki har da yi min gwalo yana wani lafewa a bayan wacce in bai yi jika da ita ba to ya haifi sa'anta.

Sallamar malam ce tasa na juya,tare suka shigo da Kaka wacce na bari yana biya mata karatu.Cikin ikon Allah kuwa idonta ya sauka kan Jafet wanda shi ma na lura har sai da ya firgita .

"Ke kam lafiya kika goya shi a baya kina aiki? Kawo shi nan na riƙe miki " Kaka ta faɗa tana matsawa kusa da Agwe,Jafet ya fashe da kuka saboda bai so a sauko shi Kaka ta riƙe shi amma duk da haka munafikin sai da aka sauko shi.

Kaka ta samu wuri a tabarma ta zauna tare da rungume shi tana mai cewa "malam yi ruwan addu'a ka miƙo na basa ka ga yadda maɗagarsa ke motsi alamun ciwon kai ne"

Malam kuwa abin nema ya samu ya kuwa cika kofi da ruwa yana ta zuba addu'o'i, murmushi kawai nake yi ina kallon Jafet da ya soma yin maganar ido.

"Ya za ku yi min haka? Ai ita Agwe ɗin ce ta damu Fasto kan sai yayi mata addu'a ta samu haihuwa yanzu kuma don ta haife ni shine kuke baƙin ciki?"

"Dukkan ku munafukai ne kai da shi,da ta ce tana son haihuwa ta ce muku tsoho take so irinka? Kuma ma mene ne amfanin cutar da Haule?"

"Ita ɗin tamu ce ,ina so ki sani duk inda za ta shiga daga ƙarshe dai dole ta dawo tsagenmu saboda ita jika ce da Nalado " shine abin da ya faɗa ,da sauri na ga Kaka ta juyo tana kallona kafin ta jefo min tambayar "dama ke tsatson Nalado ce?"

Jikina ne yayi sanyi dakyar na iya motsa idona na bata amsa da " eh shi ɗin Kakana ne"

Ba ta ƙara cewa komai ba,ta jira sai da malam ya miƙo kofi sannan ta dinga taɓe bakin Jafet tana ɗura masa ruwan wanɗanda suke ƙona baƙin ruhinsa mai cike da mugunta.Cikin nishin azaba ya buɗe baki ya ce "ku bar ni zan fita"

Malam da Agwe duk suka maido hankalinsu wurinmu ƙila jin muryar tsoho a bakin ɗansu. Kaka ta yi murmushi ta ce "zan tara mutane ka faɗa musu mugun ayyukan da kuke yi a Coci sannan ya zama dole a rufe ta ma"

Haka Jafet ya dinga kuka saboda babu abin da Mayu da matsafa suka tsana irin tonon asiri,amma kafin ka ce me tuni an tara jama'a a ƙofar gidan malam kafin dugunzuma gidan mai gari.A can ne Jafet yayi bayanin cewa shi ne Jatau wani tsoho da yayi zamani kusan ma akwai jikokinsa har yanzu cikin garin.Tsohon maroƙi ne shi,sannan kuma maye ya jima yana cinye jariran mutane sannan kuma suna haddasa husuma a cikin gari tare da ingiza mutane cikin ɓata suna yaɗa da'awar ƙarya tare da yin tsafin da zai sa mutane su yarda Cocinsu tana da wani ƙarfin iko wanda littafin Bible ya basu.A ranar ya shaida mafarin da ke sa wasu daga cikin mutane ke faɗuwa in Fasto na huɗuba,masu ragowar imanin gaskiya ne ko kuma waɗanda tsafin bai kama ba sai idonsu ya ga abin da bai kamata a ce sun gani ba wannan yasa suke ɗauke su domin shayar da jininsu ga abin bautarsu. Sai da Jafet ya sha azabar ayoyin Alkur'ani sannan ya buɗe bakinsa wani baƙin abu yayi ta fita can kuma Jafet ya tsanyara kuka saboda zuwa yanzu iya shi ɗaya ne ke da iko da gangar jikinsa. A wannan ranar aka rufe Coci,yayin da kuma malam ya ɗauki darasin amfanin yi wa ƴaƴa addu'a a kowacce safiya.

Bayan komai ya lafa Kaka ta ja ni gefe tana mai cewa "rayuwarki na cikin haɗari ya zama dole ki bar garin nan tun yanzu ba wai sai gobe ba,mu je na yi miki rakiya" ta faɗa tare da jana muka je gidanta,ko sallama ban yi wa su malam ba Kaka ta busa min irin hodar nan wacce Innarmu ta yi amfani da ita.

A wannan karon ji na yi kamar numfashina ya tsaya na wuccin gadi kafin kuma na bayyana daidai ƙofar wani kamfani. Shiru na yi ina nazari,' to yanzu kuma wace masifar zan haɗu da ita ni Haule ?' na tambayi kaina a zuci,kafin na samo amsa na ji muryar wani babban mutum a kaina .

"Me kike buƙata baiwar Allah?" Da sauri na ɗago na kalle shi tare da ce masa aiki nake nema yalaɓai,ban san me ya gani a tattare da ni ba da har yayi saurin bani aiki a kamfanin.Ciki muka shiga sai ya fara gabatar da ni ga sauran ma'aikata kafin ya kai ni wani wajen,"aikinki shi ne kula da Camera tsaro ki lura ki ajiye hankali ki dinga duba masu zirga-zirga a duk wani sashe"

Godiya na yi masa,tun a lokacin kuma na soma yin aikin nawa wanda kuma ba ni ɗaya ba ce har da wani matashi .Bayan fitar shugaba,sai ya dube ni da kyau ya wani taɓe baki kafin yayi mini wata magana mai kamar hannunka mai sanda ya ce "ki kiyaye aikinki kar ki yi abin da ba a saka ki ba,komai yana da ƙa'ida ki karanta wannan kundin domin sanin lokutan da ake kashe wasu camerori,sannan duk ƙarshen mako za ki fitar da report "

Duk da na ga kamar bai da kirki haka na karɓi kundin na soma karantawa, jefi-jefi kuma ina tambayarsa ya na bani amsa a haka muka yi aikin .Da lokacin tashi yayi sai na fita kamar kowa sai dai banda wurin zuwa ,sai kawai na yi kwanciyata nan bakin ƙofa cikin rumfa.Tsabar yadda na gaji sosai yasa na yi bacci sosai amma duk da haka sai na dinga jin motsi daga can cikin alhalin babu kowa hatta mai gadi iya waje ne kawai yake zagayawa.Washegari tun kiran sallar asuba na yi wanka a banɗakin da ke nan kusan kamfanin,haka na yi sallah sannan na zauna har lokacin aiki yayi na shiga daga ciki .

A cikin Camera sai na lura an kashe ɗaya,ban yi nauyin baki ba na tambayi abokin aikina "me yasa ita wannan take a kashe?"

"Sanoda haka mai kamfanin ya ce,a dinga kashe ta kullum in an sauka daga aiki " ya bani amsa,haka kawai na ji hankalina bai kwanta ba amma dole na yi shiru ya bani ƙosai na ci na sha ruwa.Muna dab da sauka aka kira shi an kai matarsa asibiti,da zai fita sai da ya jadadda min na kashe camerar nan kafin na fita na kuwa amsa da toh duk da cewa a ƙasan zuciyata ƙarya nake yi.

Yau ma da muka tashi bakin kamfani na kwanta,wuraren ƙarfe ukun dare kuma na tashi na yi wanka na wanke kayan jikina.Tsaye na yi don su bushe,sai dai irin yadda na ji ana motsi daga ciki yasa na je bakin ƙofar na kara kunnena.Sautin kiɗa na ji alhalin babu kowa ciki,gari na yin haske mai gadi ya buɗe ko ina lokacin fara aikin ma bai yi ba iya masu shara da guga ne suka soma amma don san sani abin da ake ɓoyo a kamfanin na yi sauri na shige.

Ɓangaren da nake aiki na shiga na yi tsaye gaban Camera wacce ake cewa a kashe,haka na yi ta kallon abubuwan da ke gudana har dare yayi sai komai yayi tsit har zan gusa sai kuma na soma ganin mutane na shigowa ta wata ƙofa da ban san da ita ba.A cikin mutanen wasu na san su ma'aikatan nan ne,shugaban kamfanin shi da kansa ya shigo ya zauna yana kallon wasu ƴan mata biyu da suke a ɗaure.A gabana yasa wuƙa ya yanka su jininsu kuma ya tara wani ƙaton kofi na zinare ya shiga ciki sai kuma suka fara yin shagali shi da sauran mutane suna shan jinin mutane.Hannuna na rawa na soma ƙoƙarin kashe Camera amma ta ƙi mutuwa haka ta ci gaba da nuno min abubuwan tashin hankali yadda ,daga bayana na ji motsi kafin na juya na ga an ziro hannu an kashe Camera sai a lokacin kuma ta mutu.Jikina ne ya ɗau rawa nan take kuma na soma bai wa shugaba haƙuri,bai ce komai ba ya fice.Ganin haka sai ni ma na fito domin guduwa,sai dai da na fito sai rasa wacce ƙofa ce zan bi na fice saboda ƙofofin da ke gabana sun fi ɗari a jere ras.

Kukan doki na soma ji tare da ƙarar takun sawunsa,can kuma na ji saniya da jaki su ma sun ɗauki nasu kafin na farga na tsinci kaina a wannan ɗakin dai da na ga Camera ta naɗo bayanansa sai yanzu kuma na lura ashe gidan ƙasa ne.

Kamar yadda na ga ƴan matan nan biyu a ɗaure,to ni ma haka na tsinci kaina.Ina nan cikin zullumi sai ga gangar jikin shugaba ta fara shigowa amma babu kai a samanta,ina shirin rumtse ido sai na ga ƙaton kan nasa a tsaye a gabana jini na ta zuba na buɗe baki da niyyar ƙurma ihu sai na ji wani abu mai kamar ƙodago ya cika bakina sai kuma na koma zarar ido.

"Kallo ɗaya na yi miki na san da aiko ki aka yi ki leƙi asirina,sai dai ki sani kamar yadda sauran ke zuwa amma ba za su koma ba ke ma haka" shugaban ya faɗa yana mai haɗe kansa da gangar jikinsa wuri guda kafin ya kama rigata da niyyar cire ta sai kuma ya ja da mugun sauri yana zaro ido,"tambarin BAƘIN RUHI? wace ce ke?" yayi min tambayar tare da cire min abin da yasa a bakina.

Ganin yadda ya firgita kawai sai na basa amsa kai tsaye da "jikar Nalado ce" ina furta haka ya soma bani haƙuri,amma ban san inda ƙarfin halin cewa "dole sai an hukunta ka a bisa azabtar da ni da ka yi" ya zo min ba.

Ina gama furta haka sai na ga hoton Kakana wato mahaifin iyayenmu maza ya bayyana a bangon ɗakin yana mai yin wani murmushi ya ce "wannan shi ne ainahin jinina Haule madala da kika amince za ki yi wa baƙin ruhi hidima,barin gida ba zai canza komai ba sai ma sake ɗaga martabarmu da za ki yi .Ki je ina alfahari da ke Hahaha !" yayi wata dariya bakinsa na fitar da wani feshin wutar da ya dabaibaye ni haɗi da cillo ni kuma a wata MAKARANTAR MATSAFA (MRS SADAUKI) .Hum ! A wannan makarantar ne na ga mutane iri-iri,kuma abin mamaki sun san da zuwana kamar yadda suka san wace ce ni.

Tarba ta musamman na samu,yayin da kuma suka dinga bani tarihin yadda Kakana Nalado ke da matuƙar jajircewa akan duk abin da yasa a gaba,da kuma faɗi tashin da yayi wurin ganin BAƘIN RUHI ya bazama a ko ina na duniya.

Cike da mamaki na ce "kenan Kakana ne baƙin ruhi?" na yi tambayar ne ga headmaster amma sai bai ban amsa ba sai cewa yayi "zo na nuna miki ɗakin baccinki,ki kwanta da wuri saboda zuwa ƙarfe biyun dare akwai darasi" Ban ce masa komai ba ya kai ni bakin ƙofar ɗakina sannan yayi tafiyarsa,na bi bayansa da kallo kafin na tura ƙofar na shiga sai na tarar da wata budurwa a zaune ta huda maƙoshin ɓera tana matse masa ciki yayin da jininsa kuma ke zuba cikin wani ɗan ƙaramin madubi mai kamar plate.

"Me kike yi haka?" na tambaye ta,ba ta ɗago ba ballantana ta bani amsa har sai da ta gama tatse dukkan jininsa sannan ta ɗauka ta shanye tare da lashe madubin sai a lokacin kuma ta ɗago ta dube ni.Ta washe bakinta wanda yake kamar na zombie kafin ta ce "ina son kai wa Kakana ziyara ne a can duniyar Ruhaniya ko za ki yi min rakiya?"

"Haule? Haule?" muryar Hajiya ta katse labarin da nake bai wa su Aliya ,na amsa da sauri tare da fita.A falo na tarar da ita a zaune tana duba wasu tsadadun kaya,ta ɗan washe baki ta ce "zo ki duba min a cikin waɗannan less ɗin wanne ya fi kyau"

Na matsa tare da soma dubawa can na ɗauki wani launin ja na ce "hajiya wannan zai fi yi miki kyau"

Ta ɗan ɓata rai kafin ta ce "ba fa ni zan saka ba,Ikilima ce nake son ɗinka ma shi saboda hotunan nan da ake yi na ango da amarya tun da na ga alamu shi Maheer ɗin bai ma fara shiri ba sai ka ce bai san wannan juma'ar za a ɗaura auren ba"

Ji na yi tamkar ta buga min guduma a kai,murya na ɗan rawa na ce "wai Alhaji ne zai yi aure amma ba mu sani ba?"

"To auren ne ya zo ta wata siga ,in ba haka aka yi ba ina ganin haka Maheer zai zauna a tuzurunsa bai aura ba,amma dai yanzu alhamdullah in sha Allah wannan juma'ar za a ɗaura masa aure shi da Ikilima"

Ban san lokacin da na saki less ɗin hannuna ba,na juya da niyyar tafiya na ji jiri ya ɗibe ni na yi baya zan faɗi amma na ji an tallabo ni tare kuma da cewa "Mama aure kuma?" muryarsa tasa na fahimci shi ne,sannan ƙamshinsa duk ya rufe min hanci. "Ita kuma wannan meke damunta ko cutar jinnun ita ma gare ta?" Hajiya ta tambaya,Maheer ya bata amsa yana mai cewa "ban sani ba dai sai na duba ta yanzu" yayi furicin ne yana mai riƙe kafaɗata da kuma ƙafafuna ya tallabe tare da soma tafiya da ni ya fara taka step ɗin sashensa,ina jin muryar Hajiya na cewa "mene ne kuma abin sai ka kai ta can sashenka ba za ka duba ta ba a nan?" bai kula ta ba,haka ni kuma ban buɗe idona ba don har yanzu maganar Hajiya ta ƙi barin jaririya ƙwaƙwalwata sukuni ga zuciyata sai lugude take yi da ƙunci.

Ban san lokacin da ya shigar da mu ɗakinsa ba sai da na ji taushin katifarsa,na ware ido sai na ga yayi min rumfa yana kallona kamar zai cinye ni.'Aurensa da Ikilima wannan juma'ar' zuciyata ta raya min nan take na ƙara jin haushinsa ban san lokacin da na fashe da kuka ba tare da sa dukkan hannuwana na ture ƙirjinsa amma ko gezau bai yi ba,kawai sai na soma dukansa.

"Keee!" ya daka min tsawa,na tsaya cak da abin da nake ina mai ƙanƙame jikina."Ki nutsu na duba ki in kuma kukan za ki yi ai sai ki je ki yi" yayi maganar yana mai jan rigata sama da sauri na mayar da kayata yadda take ina hararensa tare da yunƙurin tashi .

"Sahut!" ya furta da wani mugun sauri na koma na lafe tare da rumtse ido don ban ƙaunar ganin shegen macijin nan nasa,ina jin lokacin da ya ɗage rigata sama ya fara shafar marata yana wani furici cikin sauti ƙasa-ƙasa,nan take na soma jin wani feeling na bijiro min ban shirya ba na kai hannuna na ɗora kan nasa ina mai kuma buɗe idona sai kuma suka sauka cikin nasa,a hankali ya soma yin sama har ya iso daidai fuskata "kishina kike?" yayi mini tambayar ba tare da kuma ya bani damar amsawa ba ya dire bakinsa cikin nawa yana sumbatata yana kuma shafar cikina da sauri na ƙanƙame shi ina jin wani yanayi.....

🌻🌟🌻🌟🌻⭐🌻⭐🌻⭐🌻🌟🌻🌟

*_GYARA SHINE MACE_*

*_shahararriyar Mai Saida kayan Matan nan maman Yusuf likitar mata sokoto kuma CEO ta SOKOTO TOP 3 KAYAN MATA SOKOTO mai gyaran mata ciki da waje ta sake zo maku da zafafan Kayan masu kyau da inganci don farincinku a kullum shine burinmu* 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

*Ina uwargida da Amarya ina masu shirin yin aure budare da zawarawa , ina masu son su zama taurari ✨🌟ababen alfaharin mazajensu , ina mata masu kishiyoyi da ake ci masu zarafi ake wulakantasu akan kishiyoyin su ina wacce keshan wulakancin namiji , ina matan da sukeson burge mazajensu da zallan ni'ima da dandano ??? Ina matan fake fama da rashin ni'ima , budewar gaba wadan da suka faru sanadin ciyon sanyi kokuma haihuwa , ko wadda Ke fama da k'arancin ni'ima da karancin sha'awa , ?? To saurara kiji*✋🏻✋🏻✋🏻

*Ko kinsan Maman Yusuf Dr mata kuwa ?? Hmmm akace in bakasan gari ba to ka saurari daka*,💃🏻💃🏻 *Namu na dabanne kamar yadda salonmu yake daban ingantattun kaya ne da basuda wata illa ajiki sannan ba boka ba malam zaki mallaki mijinki da dandanonki sai yadda kikayi dashi*

Duk abunda kk so a bangaren kayan mata zaki samu hajiyata daga gyaran ciki harma Dana waje

Munada ingantaccen maganin sanyi na maza Dana mata hakama maganin Basir

Maganin nono Dana hips Maganin kiba dakuma maganin rage tumbi da kibar, Maganin gashi

Sabulun wanka na gyaran jiki Sabulun dilka na amare Dilkar amare

Kwallin mallaka (daga ni sai kai) Maltinar mata Bobintan mata Set na lalata gindin kiahiya Set na ukku bala'i Set na rantse bakida kishiya,

Kalolin gumba Kalolin gari Kalolin matsi Kalolin sabulan tsarki Zumar mata Zumar ridi Zumar goron tula Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin sabon budurci Tsumin kankana Tsumin tabaje Tsumin makalemata Shayin mata Sirrikan mallaka Dan goshi da mahadinshi Dan goshi na Mara Kyallen al'ajabu Rakumi da akala Bita zai zai Dahuwar kalolin kaza zabo zakara Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar zuciya Dambun nama Dahuwar yan shila Yajin mata Yajin maza domin Karin karfi

*Hmmmmmm in nace sai na lissafamuku zafafan kayan nan sai in wuni ina typing shawara daya zan baki uwargida in har baki jaraba kayan mmn Yusuf ba to ki garzaya ki saya da kanki zakizo kina godiya , 😉😉😉😉😉😍 wadan da suka San ya kayan suke kuwa. Basa bukatar wani Karin bayani , Domin Neman Karin bayani kokuma ganin kayan da nake dasu Ku tuntubeni ta wannan number 07069711327 call or WhatsApp mmn Yusuf mai kayan mata🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰

Ina bada sari ina sokoto ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah , Don Allah in baki shirya siyaba to kibari sai kin shirya sai muyi magana🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 My book is only 500 via

2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank

DM +22795045822.

🔞In kin san ba ki biya ba kar ki karanta min book,yin haka babban kuskure ne don cin haƙin da ba naki ba ne.Kuma Allah ba yafe haƙin wani akan na wani,don haka kar ki raina girman haƙi komai ƙanƙantarsa.

__________________________________________________ *PAID PAGE*

*Wannan page naki ne Maman Ayman uwar ɗakin Masheer 😂* 28

Tamkar yadda ake shayar da yaro haka Maheer ke shayar da ni yawunsa,ya sa tsinin hancinsa ya toshe nawa numfashi ma dakyar nake jansa ina sauke shi cikin bakinsa.Wasu irin abubuwa ne nake ji da ko kaɗan ban taɓa tunanin akwai wanzuwarsu a wannan duniyar ba.Banda hawaye babu abin da nake iya yi da kaina,sosai duk illahirin jikina ya saki sai shafar cikina yake yi wanda ban san dalilinsa na yin haka ba da na ji ya wuce a inda bai kamata ba sai a lokacin na dawo hayyacina na tuna a inda nake,da kuma wane ne nake tare da shi.

Sosai hankalina ya tashi,duk wata sauran nutsuwata kuma ta tarwatse.Kaina soma jujuyawa ina son cire bakina daga nasa ga kuma hannuna da ke rawa yana son janye nasa sai dai ko ɗaya babu wanda na ci nasarar yi saboda a wannan matakin Maheer ya saka ƙarfinsa yana yin wasa da sassan jikina yadda ya so,duk abin da yake yi kuma cikin ficewar hayyaci ne yake yinsa don ya rasa controling kwanyarsa.

Daga can ƙofa kuwa muryar Hajiya ce ke tashi haɗi da jijiga ƙofar tana ikirarin ya buɗe ƙofar uwar mece ce yake yi min,wane irin bada magani ne da har yanzu bai bani na fito ba.

Furicin Hajiya shi ke ƙara ƙaimin farashin tsorona da tashin hankali da ke cikin tunkarata. Cikin son nemawa kaina mafita na kafa haƙorana a kan ƙirjinsa na kantsara masa cizo da haƙorana masu kaifi,sai a lokacin Maheer yayi baya ya koma gefe yana mai dafe wurin,na yunƙura zan tashi ya wani fizgo ni na faɗo ƙirjinsa .Ƙafafuwansa yasa yayi min zobe da su tare da yin wani furucin da ya saɓule duk suturun jikinmu ina ganin haka casbin hankalina da kuma na numfashina ya katse .

Maheer kuwa duk da ya lura Haule ta bar wannan duniyar na wuccin gadi bai hana shi sarrafa gangar jikinta ba.Haɗuwar jikinsu a haka shi ya ƙara dagula masa lissafi,ba don ya san cewa dole sai in Haule na cikin ganiyar hankalinta zai yi sex da ita ba to da babu shakka babu abin da zai hana shi ya kusance ta duk da abubuwan da yayi mata a yanzun ma kusan kamar sun yi mu'amalar ne.

Surutun Hajiya da hargowarta sam ba su dame shi ba,don ya san ko Sarkin matsafa ya zo nan babu wanda zai iya buɗe ƙofar in ba shi ba.Wata irin wawuyar runguma ya yi wa Haule kamar zai mayar da ita ciki,yayin da yake jin hadarin sonta na ƙara gangamuwa a birnin zuciyarsa suna yi masa yayyafin ƙaunarta.

Wani irin tausayinta ne ya ji bayan ya gama bidirinsa,duk ya ɓata mata jiki da kuma shimfiɗar da suke a kai.Kamar wata baby haka ya ɗauke ta ya kai su toilet ya tsarkake musu jikinsu sannan ya canza zanen gado.Maimakon ya mayar mata da kayanta kawai sai ya zaɓo wasu kayansa Adidas ya saka mata,hatta bra ɗinta bai mayar mata ba,sai da ya busar da gashin kanta sannan ya soma ƙoƙarin dawo da ita a duniya sai da ya ci wuya sannan ya fizgo ruhinta sai dai kuma saboda shock ɗin da ta shiga ya taɓa lafiyarta a likitance.

Sosai hankalinsa ya tashi,sai ya kimtsa cikin wasu suit ya ɗora farar rigarsa sannan ya ɗauko wata rigar sanyi mai kamar jikin Zaki ya saka mata ya ɓalla maɓallanta sannan ya gyara mata zaman hullar a kanta.

Ɗaukarta yayi ya ɗora a kafaɗa sannan ya je ya buɗe ƙofa,a hankali ya soma saukowa daga kan step fuskar nan kicin-cikin yake kallon su Lubna da suka yi cirko-cirko suna yi wa Hajiya fifita duk da kuwa akwai ac a ɗakin.

Hajiya na ganinsa ta tashi tana kiran sunansa,ya ce "zan kai ta asibitinmu can sai su ƙara dubata" yana maganar ne yana juya idonsa tuni kuwa yayi nasarar canza tunanin Hajiya wacce ta ma manta da ainahin abin da ya faru.

"To ka tabbatar an kula da ita sosai ka ga ina son mu fara shirin gasar da za mu shiga tuni na sayo duk abubuwan da za mu buƙata.Ku kuma tsayuwar me kuke yi a nan?" ta ƙarashe tana tambayar su Lubna waɗanda suka cika da mamaki,ita kuwa Aliya cewa ta yi" Alhaji zan bi bayanku don na kula da ita"

Bai ce komai ba yayi gaba ita kuma ganin haka ta take masa baya har ta kai ƙofa Hajiya ta ce "in kika tafi wa zai kula da baturiya? Kin san fa nan duk taron kofi da faranti ne babu wanda zai tsinana komai in aljanun yarinyar can sun motsa"

"Ga Lubna nan Hajiya sai ta kula da ita" cewar Aliyar tana mai ɗan fita a guje don tuni Maheer ya shiga mota.A gidan gaba ya ɗora Haule kan kujera ya saka mata belt sai kuma yayi ɗan baya kaɗan da kujerar sannan ya zagaya ya zauna mazaunin direba,yayin da Aliya kuma ta shiga baya yana driving yana kallonta har suka isa asibitin.Yanzu ma kan kafaɗa ya ɗora ta ya shiga ciki,can VIP room ya kaita ya saita ac bayan ya kwantar da ita kafin ya jawo kayan aiki ya soma jona mata.

Ya ɗauki sama da minti goma kafin ya samu komai ya daidaita,gefe ya zauna yana shafar goshinta da ke fitar da gumi.Ya saki ɗan murmushi yana tuna baiwar surar da Allah ya yi mata sai kuma ya turɓune fuska tuna cewa har da laifin Hajiya da ta sanar da ita banzan auren da za ta yi masa.

Da kuma ya tuna halin kishin Haule sai ya ji wani sanyi,kamar wanda ke tsoro haka ya matsa fuskarsa ya kamo haɓarta da ke da ɗan tudu ya tsotsa haɗi dantsa haƙoransa sai ya ga ta ɗan zabura haɗi da yamutsa fuska.Yana shirin janye wa sai ya ji hannunta kan ƙeyarsa ta tallabe amma idonta a rufe suke tana bacci,haka ya ƙura mata ido yana kallo tsawon lokaci suna a haka kafin nurse Fatee ta shigo wacce tun ɗazu a gaban idonta Maheer ɗin suka shigo tana son shigowa tana tsoron yayi mata irin bala'in da yayi mata kwana bayan.

Bakin ƙofa ta yi tsaye tana kallon yadda Maheer ya mayar da dukkan hankalinsa kan ƴar aikinsu.Idonta ne suka ciko da hawaye kafin ta taka a hankali ta ce "meke damunta?" bai juyo ba haka bai bata amsa ba saboda a duniya bai so ya ga mace na kuka saboda shi kuma ya ji alamun kukan cikin muryarta.

Aka sake turo ƙofa, wannan karon Aliya ce tare kuma da Dr Muhamud shi ma cikin zafin rai ya ƙarasa yana kallon yadda Haule ta riƙe hannun Maheer shi kuma ya wani ƙure ta da ido.

Readers Also Read