Bakar inuwa book 1 - Chapter 20
Bakar inuwa book 1 Chapter 20: Bakar inuwa book 1 Chapter 20. Ta faɗa kamar zatai kuka idanunta har lokacin a rumtse suke ji take kamar ta saki gudawa. Jin…
4,395 words
Ta faɗa kamar zatai kuka idanunta har lokacin a rumtse suke ji take kamar ta saki gudawa. Jin shiru ya sata ɗan buɗe ido ɗaya kaɗan. Wayam baya a wajen, gaba ɗaya ta buɗe tana haɗiye yawun da ya kasa wuce mata a maƙoshi da ɗan dafe ƙirji ta sauke numfashi. sai kuma tai saurin ɗago hanun ta kalla tare da kai masa duka da ɗayan hanunta tana cije baki kamar maiyi da wani (😂ba man kai ... Lol)
“Malama ki rufen ƙofa inba shigowa zakiyi ba”.
Ta tsinkayi muryarsa da ke nuna tabbacin mura yake. Dan baima kai ƙarshen maganar ba ya saki atishawa a cikin tissue ɗin dayay saurin ɗorawa kan bankinsa.
(Masifaffe). Ta ayyana a ranta tana ɗaukar tray ɗin data ajiye a drawer glass da akai ado da shi gab da ƙofan ɗakin nasa. Koda wasa batai gigin kallonsa ba, dan shi ya fuske abinsa duk da kuwa daga shi sai towel. A ɗan table ɗin gaban sofa's ɗin ɗakin ta ɗora, kanta a ƙasa tace, “Ina yini? an dawo lafiya?”.
Sarai ya jita, amma yay banza yana cigaba da shafa mansa lokaci-lokaci yana atishawa, yabi ya tara uban tissue a ƙasa da yake tarewa da shi. Raudha na ƙoƙarin barin ɗakin cikin takaicinsa dan ta tsani wulaƙanci duk da bata da yawan hayaniya ya katse hanzarinta da faɗin, “Bani dustbin”.
(Yadai fi). Ta faɗa a ranta tunawa da wahalar da tasha wajen gyaran ɗakin nasa lungu da saƙo. Shi kansa lokacin daya shigo yaga ɗakin sai da yaji a ransa ba gyaran Tahir bane. Yanda bai tanka ba data gaishesa itama hauka ta manna masa taki tankawar ta fice. Kallo ya bita da shi cikin jin haushin bata amsa maganar da yay mata ba (ƙarfin hali😜 lallai wanzami baya son jarfa).
Guntun tsaki yaja da cirar tissue ɗin ya sake atishawa a ciki. Idanunsa sun kara kaɗawa da ja har suna tara ruwa a ciki. Jijiyoyin goshinsa kam duk a miƙe suke alamar ciwon kai.
Yana ƙoƙarin saka shirt mai ɗan kauri ta shigo, bata yarda ta kallesa ba, cikin ɗan yamutsa fuska da bata san tanai ba tasa yatsu biyu tana a yanayin ƙyanƙyami ta dinga ɗauke tissues ɗin daya tara a ƙasa tana jefawa a dustbin ɗin. Cak ya dakata da abinda yake yana kallonta, a ransa ya ce, (Da gaske yarinyar nan ta bala'in rainani, wai ni take ƙyanƙyami?) a fili kam sai ya taɓe baki ya ɗauke kansa. Ƙarasa shirinsa yay ya ɗauka misk zai ɗan shafa dan baya buƙatar saka wani spray turare saboda mura, dai-dai Raudha ta gama kwashe tissues ɗin sai wani kwaɓe fuska take hanunta a buɗe tabbacin ƙyanƙyami. Dariya yaji tazo masa tsabar muguntar daya shirya mata. Amma sai ya gimtse kayarsa bama zaka taɓa fahimtar hakan a fuskarsa ba. Raudha na ƙoƙarin gyara mayafinta kawai taji saukar atishawa a fuskarta har biyu a jere.
“Innalillahi.....” ta faɗa cikin subutar baki tana sakin dustbin ɗin ƙasa. Misk ɗin daya gama shafawa ya ajiye saman mirror yabar wajen tamkar baima san abinda yayi ba. Yaje saman sofa ya zauna ƙafa daya kan ɗaya. Cikin bada umarni da isar daya gada ga Gimbiya Su'adah ya ɗauka jaridar dake ajiye saman stool ɗin gefen kujerar yana faɗin, “Sai kiyi ƙyanƙyamin da hujja yanzu ai ko? Ina bukatar shayi kuma”.
Wani irin yamutse fuska Raudha tai, kai kace amai ne zai kufce mata. Sai kuma ta fashe da kuka ta ɗauki dustbin ɗin ta fice.
Da kallo ya bita ta saman jaridar, sai kuma ya saki guntun murmushi da taɓe baki lokaci ɗaya yana ɗage kafaɗa irin ko'a kwalar rigarsa ɗin nan.
Cikin sa'a Raudha ta samu bilkisu bata falon, kitchen ɗin dake falon ta shiga, kuka tayi sosai dan har cikin rai taji zafin abinda yay mata, yayinda wani gefe na zuciyarta ke ƙoƙarin nusar da ita abinda yayi ɗin ba komai bane, sai dai taƙi saurarensa. Sai da ta fidda duk wani takaicinta sannan ta wanke fuskar tas har kwalliyar tana faɗin “Anma fasa kwalliyar ALLAH bazaka sake gani ba”. Shayin da yace ta haɗa masa ta haɗa cikin flask mai ƙyau bayan taje ƙasa ta ɗibo kayan data san ana dafa masa shayi da su da yawa.
Maimakon a ɗaki data barsa sai ta iskesa a falo zaune yanzun. Bilkisu na daga zaune ƙasan carpet itama kusa da ƙafafunsa da alama haƙuri take bashi. Dan yanda tai kalar tausayi ya isa tabbatar da haka. Shiko yayi wani kicin-kicin da fuska har yanayin nasa yasa Raudha sake shiga hankalinta. Bayan ta ajiye a gabansa ta zuba shayin tare da saka masa sugar ɗinsu na masu diabetis da yake amfani da shi. Komai baice ba ya ɗauka abinsa ya fara sha.
Kanta a ƙasa tana ɗan wasa da yatsun hanunta tace, “A kawo abincin nan?”.
Cikin mamaki da al'ajab ɗinsa taga ya wani zuba mata idanunsa da mura ta gama firgatawa. Dan harsun kumburo fatarsu tai jaa ga ƙyallin ruwan a ciki, tsaf ya fahimci kuka tayi, sai kuma ya ɗanji babu daɗi. Amma a fuskarsa bazaka taɓa fahimtar hakanba. Dan wani yamutse fuskar yayi ma ya ɗauke kansa bayan ya zuba mata nunanniyar harara.
“Zan sha wannan, idan da buƙatar hakan daga baya na ci”. Ya faɗa bayan yaja wasu sakanni.
Baki ta taɓe zata bar wajen Bilkisu ta ƙyafta mata ido alamar karta tafi. Ta marairaice fuska kalar tausayi da alamar roƙo wa Bilkisun. Da ido Bilkisun tai mata nuni da Ramadhan da ya maida hankalinsa ga jarida... Sai kuma ta ɗauke kanta da faɗin, “Yaya dan ALLAH fa nace, i promise hakan bazai sake faruwa ba. Wannan ma kuskure ne wlhy kuma nice nayi banda Aunty Raudha dan batama san na ɗaura ba”.
Shiru kamar bazai tanka ba sai kuma ya ajiye jaridar yana furzar da huci kaɗan. A takaice ya ce, “Tashi kije”.
Ta san ya haƙura kenan, dan haka cikin jin matuƙar daɗi ta miƙe fuskarta washe da murmushi tana faɗin, “Thanks you Yaya. ALLAH yasa aunty Raudha ta haifa mana ƴan biyu”.
Hannu ya ɗaga kamar zai kai mata ranƙwashi ta kwasa da gudu tana dariya. Shima dai murmushi ne ya subuce masa a bazata. Yana matuƙar son Bilkisu a duk cikin ƙanensa. dan tanada hankali da nutsuwa. Gata da addini, wani lokacin akance halinsu na kamanceceniya da juna. Hakama a fuska suna matuƙar kama. Har lokacin da ɗan murmushi a fuskar tasa ya maida dubansa ga Raudha da mamakin dama yana wasa haka ya narkar da ita. Haɗa idon da sukai ya sata janye nata tai gefe da shi tana tura baki, dan har yanzu a fushi take. Sai kuma tai saurin yunƙurin barin wajen itama......
“Ina su Muneera?”.
Tambayar tasa ta sakata tsayawa cak, sai kuma ta juyo kanta a ƙasa. “Inaga suna can gida, Yau kwanansu biyu”.
“Kinaga? Bamaki da tabbas kenan?”.
Yanda yay maganar a dake ya sata ɗagowa ta ɗan kallesa. kasancewar idanunsa a kanta suke saita janye. Duk da zafi da zuciyarta ke mata sai ta danne. Banda ma ya raina mata hankali su Lubnah dake manyanta ne zai nuna kamar laifintane barinsu fita. A fili kam cikin sanyin murya da ɗan fushi-fushi tace, “Nasan can ɗinne kawai zasu je. Kuma ni da zasu wuce basuyi sallama da ni ba ai miye nawa”.
Yanda taɗan tunzura baki ya fahimci haushi taji. Batare da yace mata komai ba ya ɗauke kansa kawai gareta ya maida ga jaridarsa. Itama ganin haka ya sata barin wajen tai wucewarta bedroom.
*BAYAN SALLAR ISHA'I* tana zaune a ɗaki ita kaɗai dan bilkisu na ɗakin da su Lubnah suke tana waya da saurayinta ne. Yunwa takeji sosai shiyyasa tana idar da salla taje falo ta ɗibo abinci....
A hankali ya turo ƙofar waya manne a kunensa, kan agogon ɗakin ya fara sauke idanunsa kafin ya maida kan Raudha da mamakin shigowar tasa ya sakata shagala a kallonsa.
Takawa ya cigaba dayi inda take a hankali, tsabar yanda ta tafi wani tunani daban yasa harya iso gabanta bata sani ba. Firgigit ta dawo hayyacinta jin an hure mata idanu. Yanda ya ɗan ranƙwafo fuskarsa gab da tata har yana busa mata numfashinsa ya sata ƙoƙarin jan jikinta baya amma sai ya saka hannunsa jikin kujerar ya tokare. Koda ta matsar da kan nata sai ya sauka akan hanunsa. Saurin ɗagawa tai hakan kuma sai ya ƙara basu kusancin da take gudu. A haka ya cigaba da wayarsa cikin harshen turanci idanunsa cikin nata, yayinda yatsansa ke shafa girarta.
Fuska Raudha ta ɓata kamar ta fasa ihu da wannan dabaibayi nasa data gagara fassarawa, acan kuwa zuciyarta na liguden daka, sai dai duk yanda taso ɓoye firgicinta ya riga ya gama karantarta, dan duk ta daburce. Hatta cokalin da take shan farfesun gabanta ya suɓuce a hanunta ya faɗi saman table ɗin. Duk yanda ya fahimci takurata yay yaƙi janye jikinsa. Sai ma cigaba da wayarsa yay hankali kwance numfashinsa na sauka saman fuskarta itama yanajin nata a wuyansa, ta rasa yanda zata fassara lamarin nasa.
“Ina yini”.
Ta faɗa kamar zatai kuka dai-dai yana sauke wayar a kunensa alamar ya kammala wayar, dan wannan kusanci nasu ya matuƙar sakata cakwalkwalin ruɗani. Kaɗan ya rage dariya ta suɓuce masa amma ya danne. Janye jikinsa yay da ga gareta ya kai zaune a kujerar gefenta cikin basar da gaisuwar tata.
Da ƙyar ta iya sakin numfashin data riƙe a ƙirji. Fitsari ne kawai ya ragema Raudha ta saki itakam dan al'ajabinsa. Bata gama dawowa hayyacintaba ta tsinkayi muryarsa still da wani furicin.
“Har yanzu kina ƙyanƙyamin nawa?”.
Babu shiri ta kallesa ido a zare. cikin marairaicewa ta ce, “Ni yaushe nace ina ƙyanƙyaminka?”.
Yanda tai maganar ya sashi tsura mata idanunsa da mura ta cika. Sai kuma ya janye yana sake tamke fuska. Kamar yanda itama ta ɗaure tata tamau.
Fuskarsa ya ɗan sake matsarwa gab da tata, still yanzu ma suna shaƙar numfashin juna. “Idan ma baki faɗa da baki ba ai sirrin zuciyarki ya fito, shiyyasa na baki numfashina naga idan kin ɗauka ke kuma yaya zakiyi da kanki?”.
“Ya ALLAHU!”. Ta faɗa cikin subutar baki da waro idanunta waje gaba ɗaya kansa. Yatsun hanunsa biyu ya ɗan kaɗa mata, sai kuma ya duba bowl ɗin gabanta mai ɗauke da farfesun kayan cikin da Bilkisu tai musu. Yunwa ce ta addabeta dan tun safe rabonta da abinci, fargabar dawowarsa da tuna azabar masifar da yay mata a waya ya hanata sake cin wani abu. Dama da safen Bilkisu ce ta takura mata........
“Ammafa wannan cin amana ne, aci nama ina gidan nan babu ni, wannan ƙawancen dake tsakaninmu kuwa na tsoron ALLAH ne Ustazah?”.
A yanda yay maganar ya sata kasa daurewa sai da ta kallesa. Ganin idonsa a kanta ya sata ɗauke nata da sauri tana tura baki. (Na shiga tara ni Raudha, ALLAH yasa dai da gaske ya huce kenan) ta faɗa a ranta, a fili kuwa sai ta ja kwanon namanta gabanta da faɗin, “Naji a kwance, idan na gama ci sai mu shirya”.
“Ko? to andai ji kunya Ustazai da rowan nama, idan kina son kanki da arziki muje ki bani nawa naci kokuma na ɗiba rabona a can”
Yay maganar cikin ɗage mata gira ɗaya yana miƙewa. Batare da ya jira cewarta ba ya fice abinsa. (Uhm, su Ramadhana an fara zama ƴan is...😏🚶🏻)
Filo Raudha ta ɗauka ta balla masa cizo tana matsesa a ƙirjinta. Sai kuma ta tillashi ƙasa tare da dafe kai tana faɗin, “Ni Raudha yama haukatar dani”.
Babu yanda ta iya dole ta miƙe ta ɗau mayafinta na ɗazun dan kayanne a jikinta har yanzun ma ta fita. Tsaye ta samesa a falo hankalinsa gaba ɗaya akan television da ake nuna labarai. Koke-koke da taji anayi a tvn ya sata saurin kallo gabanta na faɗuwa. Jikinta ya kama rawa, domin kuwa rahotone na wani ƙauye a ƙaramar hukumar Gaman dake jihar Kuddo faɗa ya ɓarke a tsakanin ƙabilun dake ƙauyen. Gawarwakine zube na yara da manya harma da dabbobi, wasu jina-jina da raunika abin babu daɗin gani. Ga wasu nata kuka durkushe gaban gawarwakin ƴan uwansu da aka kashe ko aka raunata.
Kuka da Raudha ta fashe da shi ne ya maido Ramadhan da ga ɗaukewar numfashi da ya tafi na tashin hankali. Ya kai zaune jib cikin kujera hajijiya na neman ɗibarsa. Ba yau ne aka fara irin wannan rikicin a ƙauyen ba, sai dai bai taɓa gani ba kamar yau, ga shi yau ɗin daya gani kuma yana amsa sunan shugaban kasar NAYA ne da hakkin kowa ya rataya ne a ƙarƙashin mulkinsa..... Yanda jikin nasa ke rawa ya sakashi riƙo Raudha data kai dirƙushe a gabansa tana kuka ya rungume, itama ƙanƙamesa tayi kawai tana sakin wani sabon kukan.....
Wayarsa ya fara laluba da hannu ɗaya a aljihu, yayinda ɗayan ke tallafe da Raudha. Yana cirota kafin ma ya aiwatar da abinda yake shirin yi kira ya shigo masa. Da ƙyar ya iya controling kansa tsabar ruɗani ya ɗaga, da ga can hankali tashe cos ya ce, “Ranka ya daɗe kaga abinda ake nunawa a tashar Q-TV kuwa? Kodai halin ƴan adawa ne kawai....”
“No Jafar, karka kawo wannan, ka bincika yanzu abun ke faruwa ne ko tun ɗazun?”.
“Okay sir ina zuwa”.
Wayar ya jefa saman kujera, ya kai zaune shima har yanzu Raudha na jikinsa tana sharɓar kuka. Ji yake kamar shima ya fashe da kukan, amma ya daure ya ɗago Raudha, cikin dakiya yake faɗin, “Please Ameenatu relax mana. Kukanki sake tadamin hankali yake, bayan daga gareki ya kamata na samu ƙarfin gwiwa”.
Hannu tasa tana sharar hawayen, “Kayi haƙuri”. Ta faɗa tana ƙoƙarin tashi daga saman cinyarsa da take zaune ɗare-ɗare gudun kar Bilkisu ta fito, kuma a karankanta ma dai da kunya ai.
Komai baice mata ba, sai wayarsa data fara ring ya kai hannu ya ɗauka ganin cos ne.
“Ranka ya daɗe a yanda suka faɗa su dai yanzu ne. Amma dai yanzu I.G ya tabbatar min tun kusan magrib ne abun ya fara faruwa kamar yanda C.P ɗin jihar Kuddo ya sanar masa. Sai dai ka kwantar da hankalinka ya tabbatar min komai ya dai-daita zuwa yanz.......”
A matuƙar tsawace shugaban ƙasa Ramadhan ya katse cos, “Taya zan kwantar da hankalina Jafar? mutane na cikin irin wannan tashin hankalin!! Ka duba fa kaga mata ne da yara kanana a cikin jini saboda rashin imanii!!! Yanzu da akan familyna ya faru zakace na kwantar da hankalina ne? Na shiga uku ni Ramadhan!........”
A yanda yay maganar dole ne ya baka tausayi ya kuma tayar maka da hankali, dan abun al'ajabi sai ga hawaye na sakko masa. Wayar yay jifa da ita tare da dafe kansa yana yamutsa gashinsa da duka hannayensa biyu.
Sosai Raudha ta sake rikicewa itama, dan yanda yake birkita sumarsa yana hawaye da ambaton ya shiga ukun itama sai ta sake fashewa da kukan da zuwa gabansa ta durƙushe hannayenta duka biyu akan gwiwoyinsa............✍
Kubaku gane nima a tsorace nake da dawowar Ramadhan ba, karya haɗa dani😣🤕.
End of book
Leave a comment
Post
Comments
serlmerh2 Oooh Allah....nxt page plz
18 minutes ago
bilki Takwara a karo mana
19 minutes ago
bilki Wayo president abun tausayi
21 minutes ago
104835043420935222197 To Aishikknan munyadda atsorace kike amma yanxu aiya hakura pls kisamana wani Dan Allah 🤗
22 minutes ago
Contact Us Arewa Books Publishers
WhatsApp: 09031774742
Email: arewabookspublishers@gmail.com
Navigation Home About FAQ's Legal Privacy Policy Terms of Service Social Facebook Instagram
Copyright 2021, Arewa Books | ALL RIGHTS RESERVED | Powered by thinkcrypt.io Menu Dashboard My Library Create Story Home About us FAQ's Privacy Policy Terms of service Logout
BAKAR INUWA...!! Chapter: 44
Share:
Report
BAKAR INUWA...!! View: 405
Words: 3.1K
Chapter 44 44
..........Su dukansu fuskokinsu washe suke da fara'a da farin ciki. Gasashshen naman rago ne a banƙare a tsakiyarsu. Sai lemuka masu tsada da daɗi ajiye gaban kowa. Gaba ɗayansu hankulansu nakan tv da ake nuna abinda ke faruwa a ƙauyen Kauci na ƙaramar hukuma Gaman. Cikin ƙyalƙyalewa da dariya Mr MM ya kai tsokar nama daya cako da pork spoon bakinsa yana faɗin, “Wato ranka ya daɗe dabarar nan taka tayi ɗari bisa ɗari, yaje ya dawo yana farin cikin samun na sarori sai yaci karo da ƙyaƙyƙyawar tarba ta musamman”.
Kwashewa sukai da dariya baki ɗayansu, Alhaji Haladu Gwandu dake dariya harda hawaye ya ce, “A to ba gani yake shi yanada dabarar shinfiɗa aiki ba ta hanyar ɗaura ƴan uwansa matasa kan manyan muƙamai, to sai yayi aikin mugani. Basai da zaman lafiya a ƙasar talakan zai ga aikin ba?”.
Wata dariyar suka sake kwashewa da ita. Sai dai banda oga kwata-kwata da yake murmushi kawai yana cin namansa shima. A cikin God fathers ɗin nasu ɗaya ya tsaida dariyarsa ya ajiye wuƙar daya yanko wani ƙaton nama ya ɗauka da hannu yakai baki. “Ai indai mune baima ga komai ba. Sai mutuwar fitinannen tsohon kakan can nasa ta tabbata nan da kwanaki uku, a kuma ranar plan B zai bayyana shima, yanda mutuwar Alhaji Hameed Taura bazatayi tasiri a zukatan mutane ba balle ya samu addu'a da nuna tausayawa”.
Dariyar suka sake tuntsirewa da shi. Forma president ya ce, “Wa yaga gaba kura baya sayaƙi. Bashi gani yake mulkin wasan yara bane ba, zai yabawa aya zaƙinta. Yanzu nan fa ina shirin fitowa ma nakejin wani ƙishin-kishin ɗin gulma, wai da yayi niyyar bincike akan kwangilolin da muka bada, sai dai ya dakatar dalilin wani abu da ba'asan tabbaci ba.........”
Vice president Alhaji Yaro glass ya karɓe zancen forma president da faɗin, “Wannan maganar kam tabbas ce, sai dai nima ina kan bincike miye dalilin hanashi fasa binciken. Dan yanzu haka ma gobe za'a zauna da masu kwangilan meeting tare da J.P.S”.
“What!! Alhaji Haladu Gwandu (Mahaifin Amnah) Ya faɗa aɗan razane. Dan kuwa akwai yaronsa a cikin wanda aka bama kwangilolin, kuma tabbas yau kusan kwanaki uku yana kiransa bai samu damar ɗaga wayar tasa ba saboda busy da yayi.....
“Wlhy da gaske haka zancen yake”.
Alhaji yaro glass ya faɗa a yanayin takaici da jin ɗaci. Waya Alhaji Haladu Gwandu ya lalubo a aljihun babbar rigarsa. Da sauri ya shiga laluben lambar yaron nasa. cikin sa'a kuwa bugu ɗaya ya ɗauka tamkar dama kiran nashi yake jira. Ko sauraren gaisuwar tasa baiyiba ya jeho masa tambaya. Sai dai amsar daya bashi tai matuƙar firgitashi ya saki baki da hanci yana saurare har yaron nasa ya gama bayanin saƙon da suka samu na kira da ga ofishin Minister.
A hargitse ya ajiye wayar bayan sun kammala yana faɗin, “To tunda ya fasa binciken kiran ubanmi yasa Minister ɗin yake musu?”.
“To wa ya sani”.
Cewar Alhaji Yaro glass.
A harzuƙe Forma President ya ce, “Amma ya kamata ace irin waɗan nan abubuwan kana ƙoƙari saninsu Alhaji Yaro. Kasan kuwa wanene Ramadhan da Alhaji Hameed Taura?!!...”
“Haba Alhaji Usama ya zakaga laifina? Bayan kaima kasan yaron nan komai yinsa yake a ƙudundune, daga shi sai matsiyacin cos ɗin nan da nafi tsana fiye da komai yanzu a duniya. Sai ko shegen kakansa ɗin nan da ubansa da nasan sune masu bashi shawara sama da mashawartansa na mulki.....”
Mr MM zaiyo magana Oga kwata-kwata ya dakatar da shi ta hanyar ɗaga masu hannu. “Inaga wannan cece kucen ba shine mafita ba. Amma tabbas Alhaji Yaro akwai sakacinka anan. Sai dai muma munada laifi da bamu ɗoraka bisa hanyar data dace ka dinga sanin komai da komai ba. Amma ka sani matarka tana ɗaya daga ciki, dolene ta cigaba da kawo mana mike gudana a cikin gidan gwamnati ta hanyar matarsa tunda ƴa take a wajenta. Sauran magana kuma zamuyi daga baya idan na kammala nazari, amma a dakatar da kashe Alhaji Hameed Taura ba yanzu ba”.
Cikin gamsuwa duk suka ɗaga masa kawuna, duk da a ransu suna son sanin dalilin dakatar da kashe Bappin, sai dai babu damar yin jayayya........
*______________________________*
A matuƙar ruɗe Raudha ta kai hannu tana riƙo na Ramadhan jikinta na rawa. “Dan ALLAH kayi haƙuri, nasan wanda suka rasa ransu bazasu taɓa dawowa ba. Sai dai akwai mafita da zata taimaka a taimaki wanda sukaji raunika da tsananta tsaro ga wanda ba'a cutarba”.
Duk da bai ɗago ya kalleta ba yanda ya dakata da yamutsa kan ya tabbatar mata yana saurarenta. Sai kuma ya ɗago ɗin ya zuba mata idanunsa. Hawayenta tai saurin sharewa tana miƙo masa wayarsa data ɗakko. Sai kuma takai ɗayan hanunta ta share masa nasa hawayen shima da har yanzu suke sakkowa.
“Kasan yanayin ƙasarmu da ƙarancin kulawar da talaka yake samu akan harkar lafiya da tsaro. Lokuta da dama wasu a cikin jami'ai najin abu na faruwa sai dai tsoro da rashin kayan aiki na daƙilesu akai taimako, wasu kuma son zuciya ke hanasu yin kowane irin yunƙuri. To kamar hakane ga jami'an lafiya suma. Shiyyasa idan sakacin shugabanni ya haɗu da masu raunin taimako a jami'an lafiya ma yana ɗaiɗaita rayuwar talaka. Mafita itace yanzu ba wakili zaka saka ya bincika ba ko ya bama C.P na jihar umarni, kai da kanka ne ya kamata kai magana da I.G da C.P ɗin zasufi jin tsoron tashi suyi abinda ya kamata suma bawai su tura yara ba. Hakama asibitin da kanka ka kira Commissioner lafiya na jihar kai magana da shi dan ALLAH Ya Ramadhan......”
Ɗari bisa ɗari ya gamsu da maganarta, dan haka ya ɗago da sauri, wayar da take miƙa masa ya amsa yay dailing number cos. Kai tsaye yace, “Ka sameni”.
“Ranka ya daɗe yanzu haka ina cikin gidan nan ai”.
Cos ya faɗa da sauri gudun kar shugaban ƙasa Ramadhan ya yanke wayar. Duk da cos baya shigowa har nan yau dai ya bashi umarnin ya samesa. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa sai ga cos ɗin. Saurin janye jiki Raudha tai daga rungumar da Ramadhan ya sake mata bayan yayi magana da cos. Sai dai hanunta ya riƙo cikin nasa dole ta zauna a hanun kujerar da yake a zaune hanun nata rumtse a nasa.
COS ya rissina yana gaishe da Raudha data amsa a kunyace, dan yanda ya gansu da yanda yake bata girma har mamaki takeyi.
Cikin bada umarni Ramadhan yace, “Ina bukatar magana da I.G & commissioner of police na jihar, tare da commissioner lafiya”.
Kai Cos ya jinjina yana mai fara danna wayarsa. A taƙaice Cos yayma I.G bayani ya mikama Shugaban ƙasa Ramadhan wayar. Koda ya amsa bai wani tsaya sauraren gaisuwar ɗin ba da jikinsa keta ɓari da ga can shi zaiyi waya da shugaban ƙasa. Kamar yanda Raudha ta bashi shawara haka yayi, yana gama kora masa bayani cike da ƙasaita kamar bashi ya nema birkicewa ba yanzu ya miƙama COS wayar. Amsa yay da girmamawa ya sake kira masa C.P na jihar Kuddo da Commissioner ɗin lafiya. Daga ƙarshe yasa aka kira Gwamna ɗin jihar shima inda Shugaban ƙasa Ramadhan ya balbalesa da masifa jin tamkar ma shi babu wata damuwa tattare da shi.
★Tabbas umarnin shugaban ƙasa Ramadhan yayi matuƙar tasiri, dan cikin ƙanƙanin lokaci dukkan abinda ya lissafa aka ninkashi ga jama'ar wannan ƙauye. Kafin wayewar gari tako ina garin jami'an tsaro ne har cikin dazukan yankin da sauran ƙauyikan, ga helicopters na sojoji sai yawo suke ta sama. Na asibitima suna samun ƙyaƙyƙyawar kulawa. Waɗan da sukai musabbabin fara haɗa rikicin da CP ya bada umarnin dankosu sai ga gawarwakinsu a cikin waɗanda suka mutu. (Dama haka fitina take, a mafi yawan lokaci wanda ya takalota shi take fara zubarwa a ƙasa. ALLAH ka zaunar da ƙasashenmu lafiya. ya gafarta mana kurakuranmu ka wadatamu da tsarkakakkiyar zuciya😰).
★★★
Da ga Raudha har Ramadhan idan sunyi barcin kirki a wannan dare sai dai ɓarawo. Ga mura ta mugun addabarsa da zazzaɓi mai zafi ma ya kwana. Yayi waya da Bappi yayi da Pa duk akan lamarin. Anne ma ta kwantar masa da hankali ta hanyar nasiha sosai da muhimmincin tashi tsaye akan addu'a .
Basu kaɗai ba hatta Bilkisu da damuwar ta kwana. Duk da dai nata tsananin tashin hankalin nada nasaba da halin da taga Yayansu da Raudha a ciki. Adalilin hakan ma yau a ɗakin Raudha ta kwana. Ita kuma Raudha a ɗakin Ramadhan suka kwana tare.
Da sassafe shugaban ƙasa Ramadhan yabar gidan batare da sanin su Raudha ba, dan ɗakinta ta tafi yin sallar asuba bayan ya fita massalaci shima. Sai da suka fito sukaci karo da shi a tv ana nunasa a cikin ƙauyen Kauci, abinda zai birgeka har da shi cikin tawagar masu zana'ida duk da karancin lokacin dake garesa. Ana kammalawa suka baro garin sai dai yabar jama'arsa suna sake zagaya ciki da bai ɗin ƙauyen. Tare suke da gwamnan jihar Kuddo ɗin. Daga ƙauyen asibiti suka wuce nanma shugaban ƙasa Ramadhan ya duba wanda suka sami raunika. Da ga haka bai ƙara ko minti biyarba a jihar Kuddo suka nufo Bingo dan da ƙyar yay squeezing time ɗinsa dama. Sai dai abinda yayi ɗin ya kara masa kima da daraja a idanun talakawan ƙasar NAYA. Gaba ɗaya a yinin nan babu abinda kakeji sai ruwan albarka da ake jera masa tako'ina.
Yayinda a ɓangaren su Alhaji Yaro glass kuma sukai yinin baƙin ciki da ƙunci dan basuyi zaton shugaban ƙasa Ramadhan zaije har ƙauyen ba domin nuna kulawa. Ba ƙaramin shiri ya wargaza musu ba akan hakan.
A ɓangaren mai gayya mai aiki kam Ramadhan yau ya yini ne cikin damuwa da ɗunbin fargabar wannan mulki mai cike da ƙalubale kala-kala. Tun ba'aje ko inaba fa kenan, inaga nan gaba kuma da shekaru huɗu da watanni kusan bakwai ke jiransa. Kai anya kuwa zaya iya?.
Da wannan tunane-tunanen ya yini a office ga mura da ciwon kai ga zazzaɓi ga kuma aiki. Yini gudan nan kuma bai ci komai ba ƙishi ma sai da yaji maƙoshinsa na neman fara yayyankewa sannan yasha ruwa, dan daya tuno jinin daya gano a Kauci sai tsigar jikinsa ta dinga tashi.
Duk da wannan damuwar hakan bai hana wakilan da yasa minister ya naɗa zaman mitin da masu kwangilar nan ba. Sun kuma gudanar da zaman tamkar yanda ya bada umarni. Yanayin zazzaɓi daya rufesa ya sashi barin office tun 2pm ya shiga gida.
★Koda ya shigo gidan ya iske Raudha bata gidan, shi shaf ma ya manta da batun fara zuwanta school yau. Ɗaki ya shige ya kwanta, duk da abinci ya kamata ya fara ci ya sha magani hakan bai faruba, sai dai yaji ciwon kansa na ƙara tsanani ya ɗauka man zafi ya shafa ya sake lulluɓe jikinsa gaba ɗaya cikin duvet.