Bakin ruhi complt by mrs sadauki - Chapter 11
Bakin ruhi complt by mrs sadauki Chapter 11: Bakin ruhi complt by mrs sadauki Chapter 11. Lubna ta haɗiye wasu yawu kafin ta ce ,"ni ban je ba ƙarya ya yi…
4,462 words
Lubna ta haɗiye wasu yawu kafin ta ce ,"ni ban je ba ƙarya ya yi miki "
"Hahaha! Ogan ne zai yi miki ƙarya? To ka ji.Oh na manta anty Bahijja ina wuni? Oga ne ya ce na zo na duba lafiyar Yasmine " Sai a sannan ne muka san sunan matar gidan Bahijja,adadin farashin tsoronta ne ya hau kafin ta ce "tana can sama"
Zuly ta kama hannun Lubna tana mai cewa "mu mana ƙawata ki yi min rakiya" ba ta ida rufe bakinta ba na kai hannu na zare hannun Lubna daga cikin nata kafin na ce "ba ki ta nuna miki ba ta son hulɗa da ke ba? Ko ana ƙawance dole ne? Mu tarkacen dai mu take ra'ayi,ke kuma da kike ƴar gayun ba ta yinki"
Wani irin juya ido Zuly ta yi da niyyar cutar da ni,sai dai tuni ta makaro don ni ma ina da tawa power ta hana abu motsi ko kuma saka shi abin da bai yi niyya ba tuni na gusar da ganinta ta koma tamkar makauniya sai kuma na saka ƙafa na shure ta nan ta faɗi jikin kujera kanta ya bugu har ya soma zubar da jini.
"Ku zo mu je mu fitar da Yasmine kafin su rige mu ɗaukarta,ke Bahijja ki tsaya nan yanzu mun fito" na faɗa cikin sauri.
Aliya ta ce "Lubna ta zauna tare da ita mu kuma sai mu haura can sama"
"Hakan ma yayi" na faɗa tare da kama hannun Aliya muka je da sauri muka haura can sama,tun kafin mu isa muke jin wani irin yanayi marar daɗin ji mai kuma tattare da tashin hankali. Aliya ce ta yi amfani da ƙarfin ikonta muka ɓalla ƙofar muka shiga,cak muka ja muka tsaya muna kallon Yasmine a kwance kan bed babu sutura a jikinta.Dukkan wasu alamu a bayyane suke,ana tarayya da ita ne kamar yadda ake mu'amalar aure banbancin kawai ita ba da mutum ba ne take yi ba ko dai ruhi ko kuma aljani.
Wani irin kuka ne ta fashe da shi kafin kuma ta tashi zaune tana ƙanƙame jikinta,zuciyata ce na ji ta yi rauni sai Aliya ce ta ƙarasa ta je ta ɗauki doguwar rigarta ta mayar mata sai kuma ta jawo ta suka zo gabana.
Yasmine ta faɗa jikina tare da ƙanƙame ni gam tana kuka,ba tare da na tambaye ta ba ta soma bani labarinta "ƙalubalen nan ya riske ni tun ina ƴar ƙaramata, lokacin da na cika shekara uku na san za ki yi mamakin jin ta yadda aka yi har na yi wayon riƙe abu a ƙanananun shekaru irin haka,to hakan nada nasaba da rainon da jinnu suka yi min tun ina cikin mahaifiyata.Tun daga wannan shekarar na soma fuskantar wani abu da ban san mene ne ba,sai ina tsaka wasa da yara sai na ji wani abu ya zo ya kwantar da ni yana wasa da sassan jikina haka za a yi ta ganin ina juye-juye kwance a ƙasa babu wanda ya san taƙamaimai abin da ke faruwa da ni hatta kuwa mahaifiyata.A lokacin da kuma na kai gaɓar shekaruna biyar sai na ɗauki tabi'ar auren hannu na yaɓa,haka zan dinga taɓa jikina ba tare ni kaina na san dalili ba ,ba zan manta ba Mama ta taɓa ganina ina wasa da jikina ta yi mini duka tare da yi min hani da hakan sai dai abin da ba ta sani ba haka nake shiga ɗaki ina yi ko kuma in ta yi bacci.Kar ki tuhume ni domin ba yin kaina ne ba,wata murya ce nake jin tana yi min suwa a dodon kunne tare kuma da bani umarnin yin haka.Lokacin da na kai shekara takwas tuni an saka ni makaranta,a daidai wannan gaɓar za ki ga yara suna sha'awar yin karatu amma ni ta baibaye lamarin ya zo min sam na tsani makaranta in ma na je to kallon yara mata ƴan ajinmu nake tsayawa yi ina jin wani abu na fizgta ,da farko ban gane me hakan ke nufi ba sai daga baya na fahimci sha'awarsu ce nake ji.Haka in mun fita shan iska zan dinga yin wasa da ƴan ajinmu ina taɓa jikinsu,su suna ɗaukar haka matsayin normal wasa ba tare sun san ni daɗin haka nake ji ba ko kuma na ce BAƘIN RUHIn da ke jikina ke jin daɗin haka ba.Sosai nake son mata ƴan uwana amma na tsani mazan ajinmu da duk mazan duniya in kika cire Daddyna.Har zuwa lokacin da na shekara sha biyu a duniya ina yin auren hannu ni da ƙawayena na makaranta wanda tuni muka jone muka zama tantiran kanmu,mu uku ne muke wannan mummunar ɗabi'ar,ni,Firdo sai Malika.Mafi yawan lokutan da muke biya juna buƙata shi ne lokacin shan iska,haka za mu je cikin banɗaki makaranta mu yi duk abin da muke so mu fito.Ko kuma a gidansu Firdo kasancewar iyayenta masu aikin gwamnati ne ba zama suke yi a gida ba,mun sha guduwa daga makaranta mu je can kawai don mu yi baɗala.Ina shiga shekara ta sha uku sai na fara period daga nan ne ƙalubalen ya ƙara ta'azzara kullum cikin baccina haka zan dinga ganin muna yin sex ni da wata halitta,da na shaidawa ƙawayena sai suka ce ai su ma suna yin irinsa kuma sosai suke jin daɗin haka.Wannan mafarkin da muke yi shi ya yi sanadin kuma barin lesbian ɗin da muke yi sai dai inda matsalar ta ƙara yawa shi ne ko a ina nake haka zan ji wani irin yanayi kafin kuma bacci ya ɗauke ni shikenan sai dodon nan ya zo min yana mu'amala da ni.Watannin da suka gabata na taɓa yin bacci cikin aji ,da na farka sai malamarmu ta kira Mamana ta shaida mata shikenan sai aka hana ni zuwa makaranta .Ashe wannan duk shirin ruhin da ke cikin jikina ne,saboda yana son yin mu'amala da ni duk bayan kowacce awa tun yana zuwar min a mafarki har na fara ganinsa a zahiri shi ne da na buɗe baki da niyyar yin ihu ya damƙe min murya Please ki taimaka min ki fitar da ni daga cikin gidan nan,a ranar nan da na gan ki sai na ji kamar ke ce fitilar da za ta haska rayuwata wannan yasa na faki idonsa a lokacin da ba ya nan na fita na je nemanki sai kuma aka yi rashin sa'a macijin da ya bani don kula da ni ya so cutar da ke" tana gama faɗa min labarin sai ta fita daga jikina tana wani waige-waige cike da tsoro, wannan karon da ido ta yi min magana don alamu sun nuna muryartata ta ƙara maƙalewa,"ga alamun zuwansa nan Please ku yi sauri ku fitar da ni"
"Aliya mu je" na faɗa tare da kama hannun Yasmine ɗin muka fito a guje sai dai muna fitowa falo muka yi tsaye cak sakamakon ganin mutumin nan na ɗazu wanda ya ja hannun Yasmine a asibiti sannan Zuly na tsaye kan ƙafafunta ga Lubna da anty Bahijja suna kuka.
Yasmine ta ɓuya a bayana tana riƙe ni gam,sai yanzu na fahimci wannan mutumin shi ne Oga. Kana kallonsa ka ga mugu,takowa ya soma yi yana tunkaro mu yayin da ni kuma na riƙe hannun Yasmine gam na soma ja da baya haka ma Aliya,har sai da muka dangane da bango.
"Su wane ne ku? Da izinin wa kuka shigo nan?" su ne tambayoyin da ya jero mana,ban iya cewa komai ba sai aukin kallonsa.
" Yasmine ɗin Daddy zo nan ,zo na kai ki wurin Daddynki " yayi furicin cikin taushin murya,ƙin tafiya ta yi ya zo da ƙarfi zai fizgo ta amma na yi saurin dakatar da shi ta hanyar amfani da ƙarfin ikona sai ya daskare wuri guda.
Da gudu muka barsa nan muka je can wajensu Lubna,Zuly ta kamo hannun Yasmine amma na buge ta a dole ta sake shi tare da daskarewa ita ma .Aliya da Lubna suka kama Yasmine ɗin tare da nufar ƙofa da ita,yayin da ni kuma na kamo hannun anty Bahijja sai dai fa fita da ita daga cikin gidan ya cuttura don da dukkan alamu an yi mata mugun kafi wanda ba zai bar ta iya fita ba.
Cikin kuka ta ce "ku tafi ku bar ni,ba zan iya ƙetare iyakar ƙofar nan ba"
"Ba zan bar ki ba wallahi,Aliya kawai ku tafi zan same ku a gida " na faɗa tare da soma duba ko ina na gidan ko Allah yasa na hango wani abu da ya shafi guru ko laya,su kuwa tuni sun bar wurin.
Sama da minti talatin ina bincikar gidan amma ban ga komai ba,can dubara ta faɗo min sai na riƙe hannun anty Bahijja sai na lumshe ido da niyyar karanto wasu formula masu taimakawa mutum ya tashi sama kamar leda.Azababen zafin da na ji ya caki hannuna shi yasa ni saurin buɗe ido nan na yi arba da Oga wato ya kwance ƙullin da na yi masa,ko kafin kuma na yi wani yunƙuri ya soma karanto ɗalasiman tsafi nan take gidan ya soma juyawa yana rangaji,guguwar da ƙura tuni sun turniƙe ko ina.A yadda na ji yana ambatar ƙasar Japan na fahimci so yake ya kai mu can ta hanyar tsafi,da sauri na lumshe ido na soma karanto abubuwan da Aliya ta faɗa min in ina son haɗa tunanina da na kuma Maheer.Cikin ikon Allah kuwa na samu nasarar damƙo tunanin nasa,yana tsaye cikin wani ɗako yana aikin tiyata idonsa sanye da wani gilashi ga fitilar tsakiyar goshinsa,yayin da fuskarsa ke rufe da facemask.
Hasken fitilarsa ne ya ƙara yawaita,wanda nake jinsa har cikin ɓargon raina ina dab da shiga komar Oga Maheer ya samu nasarar jefo ni wajen gidan.
Tari na soma yi ina kallon yadda hayaƙi yake tashi sama,iya ni ɗaya kawai na fito banda anty Bahijja.Ba don na so ba haka na tafi na bar ta saboda yadda jini ke yi min zuba a hannu,ko kafin na kai bakin titi jiri ya soma ɗibata saboda babbar jijiyar magudanar jini ce Oga ya tsinka min ba.
Da na tsayar da taxi na faɗa masa sunan asibitinsu Maheer,ko kafin a isa na fita hayyacina wai ma don mai taxi ya taimaka ya ɗaure min hannu.
Dr Muhamud ne kuwa kan aiki,shi ya bani taimako yana tsaka da rufe ciwon Maheer ya shigo da alamu sai yanzu ya gama aikin.Saurin sunne kai na yi don na san ko makawa babu sai ya aiko min mugun kallon nan nasa, Dr Muhamud na gama naɗe min hannun ya fita ya bar mu nan mu biyu.Duk da ina jin idonsa a kaina amma na ƙi ɗagowa,na yi shiru ina sauraren bugun zuciyata da ya ƙi daidaituwa ta ƙasan ido na ga lokacin da ya ja ƙafafunsa ya fice sai a sannan na ɗaga kaina ina mai jan wani numfashi.
★A can ɓangaren su Oga kuwa cike da baƙin ciki ya tsayar da manufarsa .Komai ya tsaya cak tare da dawowa normal,ya dubi Bahijja wacce ta kasance matar Boss ɗinsu cike da takaici sai dai babu damar yi mata masifa ko zaginta.Zuly ta fito ita ma a tsakiyar gidan fuskartar na bayyanar da tsantsar tashin hankali,"oga ina Yasmine?" ita ce tambayar da ta yi.
"Sun tafi da ita! Amma yaushe har Luby ta samu ƙarfin iko haka? Sannan wace ce wannan ta tare da ita mai ɗauke da wani abu na musamman mai bata kariya?"
"In akwai wacce za ta baka amsa ai anty Bahijja ce,don a tare na tarar da su" Zuly ta faɗi haka duk kuma sai suka tsurawa Bahijja ido wacce ke kukan farin cikin. Suna cikin halin ƙaƙanikayi kiran Boss ya shigo wayar Oga,babu damar ƙin ɗauka wannan dalilin yasa Oga yin shahada ya ɗaga kiran.
"Mene ne ke faruwa a can? " ita ce tambayar da Boss yayi.
Murya na ɗan rawa Oga ya ce "babu komai Boss".
"Ina Yasmine?"
"Tana bacci sai mahaifiyarta kawai ke farke"
"In ta tashi ka tabbatar ka bata maganinta,sannan ina buƙatar Leena nan da wani ɗan lokaci tun da ta dawo aiki tare da family wannan karon ya zama dole ta bani haɗin kai"
Oga ya ce "wannan ai dolenta ne,kuma kamar ta zo a shimfiɗarka ne ta gama don ba za mu ɗaga mata ƙafa ba" nan dai suka gama waya suka yi sallama,goshin Oga sai tsatsafo da zufar tsoro yake.
Ko inda Bahijja take bai kalla ba ya ja hannun Zuly suka bar gidan.Can kamfani suka wuce,bayan sun shiga ofishinsa ne ya dube ta da kyau kafin ya ce "ki san duk yadda za ki yi ki nemo Leena domin ta hanyarta ne kawai za mu samu Yasmine ,na baki nan da 24h ki nemo ta"
Zuly ta ce "Oga me zai hana mu yi amfani da ƙarfin tsafi wurin binciko su?"
"Matsalata da ke Zuly kwanyar kifi ce da ke,kina tunanin madubin tsafi na iya binciko mana inda suke? Kafin su je can dama sun yi dogon shiri ta yadda babu wani madubin sharri da zai iya nuno su.Ke dai ki zage dantse ki yi aiki tuƙuru kafin Boss ya farga ƴarsa ba ta gida,sannan in son samu ne har da waɗannan ƴan matan biyu duk ina buƙatar su "
"Na fi tunanin cewa ƙarfin ikonsu ya samo asali ne daga Uwa Yabobo,don kamar ira take aiki da power canza tunani da ta kuma daskarar da mutum"
"Kina tunanin in mun je ita Uwa Yabobo za ta faɗa mana wani abu dangane da su ne?"
"Eh ! Duk da na san sai ta nemi abu mai matuƙar muhimmanci a gare mu"
Suna tsaka da tattaunawar nan ne Boss ya bayyana a ofis ɗin,sanye yake cikin wasu baƙaƙen kaya ya ɗora hullarsa ta gado mai kamar ta sheɗan.Fuskar nan kicin-cikin,bai wani ɓata lokaci ba ya ce "ku faɗa min duk abin da ke faruwa kawai"
Zuly ta haɗiye wasu yawun tsoro kafin ta soma koro masa bayani daki-daki,bayan ya gama saurare sai cewa yayi "a halin yanzu yarinyar da ta fitar da Yasmine ta fi yi min muhimmanci,don haka ita nake so.Duk ku ture tunanin ceton ƴata don ina da tabbacin ba cutar da ita ne za su yi ba "
Oga da Zuly wani irin sanyi suka ji zuciyarsu ta yi,jin Haule kawai yake so ba Yasmine ba.
★Asibiti Sai da na ci zama sosai kafin na fito,Dr Muhamud na gani a tsaye sam ban san cewa waya ce yake yi ba na matsa cikin sigar rarrashi na ce "Please Hamud ka yi haƙuri" wata irin zabura yayi yana mai ciro wayarsa daga aljihu ya kashe kiran sannan ya cire ɗan ƙaramin bluetooth ɗin da ke maƙale a kunnensa.
"Haulatu?" ya kira ni cikin wani sauti,ban kai ga amsawa ba wayarsa ta ɗau ringing sai ya ce "ina zuwa" sai kuma yayi gaba kaɗan kafin ya ɗauki kiran,yana magana yana kallona hakan yasa na ƙure bakinsa da ido har ta kai ina iya jin abin da yake cewa.
"Hearty wallahi gaskiya nake faɗa miki babu wata mace da ta zo kusa da ni,to wai me zan yi da wata ni da nake da kyakkyawa irinki? Ai a wurina duk sauran mata kwadon shara ne ..." ban tsaya ida jin abin da yake cewa ba na yi gaba na fita,tafiyar ƙasa na soma yi na ɗan yi nisa sosai kafin na ga mota ta parker a gabana.
Na yi tsaye ina kallonsa ina tuna ƙaryar da ya gama shararawa yanzu. "Zo ki shiga na sauke ki a gida" ya furta lokacin da ya fito yana mai buɗe min gidan gaba,saboda na ga da mutane a wurin sai na shiga na zauna ina shirin rufe murfin muka yi ido huɗu ni da Maheer yana tsaye gaban wani tsoho suna magana .Dr Muhamud ya ce "ya dai me kike kallo?"
Na ɗan yi murmushin yaƙe na ce "kamar Dr Maheer nake gani a can" na faɗi haka ne don sake gaskata shin wai da gaske shi ɗin ne ko yaya.Amma da mamakina sai ji na yi Dr Muhamud ya ce "ko dai idonki sun fara samun matsala ai babu kowa a can"
Na ce "a'a naka idon suka samu matsala ga Dr Maheer can shi da wani tsoho"
Dr Muhamud ya tuntsire da dariya kafin kuma ya soma tuƙa motar,har sai da ya kawo inda nake nuna Maheer na tsaye sannan ya ɗan tsaya ya ce "suna ina?" ban basa amsa ba saboda numfashina da ke barazanar tsinkewa,na farko irin kallon da Maheer ɗin ke yi min,na biyun da ya fi dukan zuciyata shi ne ganin mutumin nan da suke a tare sam fuskarsa babu wani alamun siffar mutum,babu ido ,babu hanci,haka ma baki babu fuskar a shafe take lis.Ko da Dr Muhamud ya ji ban ce komai ba sai ya ci gaba da driving har muka isa,ban ma tsaya mun yi wata sallama ba na wuce ciki sai na taras da Yasmine tana hauka yayin da Aliya ke ta ƙoƙarin ganin ta lalaɓe ta,Hajiya da Lubna suna a ɓoye bayan kujeru sai ido suke zarowa..... My book is only 500 via
2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank
DM +22795045822.
*Ina masu sha'awar karanta horror Books ɗina? To ga dama ta samu na yi muku bonanza ku zo ku zaɓi waɗanda kuke so a farashi mai sauki wacce ta shirya ta tuntuɓe Ni a waccan lambar tawa ta sama* __________________________________________________ *PAID PAGE* BONUS
19
"Yasmine???" na kira sunanta da ƙarfi sai ta tsaya cak tana juya manyan idonta da suka canza kala,tare kuma da maida harshenta da ya zazzalo har yana shirin jan ƙasa.A hankali na soma takawa har na tsaya kusa da ita sai na jawo ta na rungume ,wata irin ajiyar zuciya ta soma saukewa akai-akai daga nan bacci ya ɗauke ta,dakyar na iya janta na kwantar da ita kan kujera sai a lokacin Hajiya da Lubna suka fito daga maɓuyarsu.
Cikin balabalin bala'i Hajiya ta ce "wallahi wannan aljanar ba za ta zauna min a nan ba,ina dalili ni da gidana a hana ni shaƙat ana tsoratar da ni bari Maheer ɗin ya dawo wallahi sai dai ya kai ta can ɗakinsa tun da shi ya jajiɓo ta"
Ina jin abin da Hajiya ta ce sai na fahimci wato ƙarya su Aliya suka yi mata suka ce Maheer ne ya ce a kawo ta nan gidan.Da ido kawai na kalle su kafin na nufi hanyar bangarenmu, toilet na shiga na yi wanka na fito na zauna ina tsaka da shafa mai daga ni sai ɗaurin ƙirji aka banko ƙofa.Maheer ne,cikin halin nasa wanda in bai yi ba to ba zai ji daɗi ba ya ce "yaushe na yi da ke na ce ki dinga kawo min patient ɗinki a gida ? Sannan ban hana ki shishigewa Dr Muhamud na ba? Shine yau kika shiga gaban motarsa ke ga isasshiya wacce ta cika ta tumbatsa kin fi ƙarfin ki ɗauki maganar da aka yi miki"
Ban ce masa komai ba in banda ƙoƙarin nemo hijabin da zan saka da nake yi,ya ja uban tsuki ya ce "me ne za ki rufe wanda ban sani ba? Ƴan tsiri-tsirin abin kamar ƙwan budurwar kaza ko kuwa baƙin tambon da ke cinyarki?"
Cak na tsaya tare da tsure shi da ido,hankalina kuma sai na ji ya tashi.Murya na rawa na ce "ya aka yi ka san ina da tabo ga cinya?"
Wani banzan kallon yayi min kafin ya fice yana mai cewa "ki tabbatar kin samowa baturiyarki wurin da za ta zauna"
Sam kasa nutsuwa na yi haka na yi ta tunanin ta yadda aka yi har ya san ina da tabo a cinya,sannan shaf na manta da cewa ya taɓa kai ni ɗakinsa.Kamar kazar da ta fashewa a ciki haka na samu na kimtsa,da zan saka bra sai da maganarsa ta dawo min .Wato ƙirjina ne ke kamar ƙwan budurwar kaza tsabar ya raina ni,ina tsaka da fesa turare Aliya ta shigo tana mai cewa "ina son zan fita"
"Ina za ki je?" na tambaye ta,ba ta kai ga bani amsa ba kuma muka jiyo kururuwa can falo da sauri muka fita sai muka taras da wata baƙar ybudurwa ce ke wannan aiki,a cikin abin da bai fi minti biyu ba na hango tsantsar kamanninta da Hajiya .
Maheer na kalla wanda ke tsaye fuskar nan tasa ta yi kicin-cikin kamar zai fasa kuka,da na dubi ɓangaren da Hajiya take ita kuma sai na ga tana sharar ƙwalla kafin ta ce "ina Ummarki take ? Tun yaushe kuka shigo garin nan? "
Cikin kuka budurwar ke cewa "Umma tana can sun ɓoye ta ni ma guduwa na yi"
"Ya isa haka! Ta je ta yi wanka ta ci abinci ina zuwa" Maheer ya faɗa tare da tafiya ya soma taka matakalar benen da zai kai shi sashensa,na bi bayansa da kallo har ya ɓacewa ganina.
"Haule kai ta can ɗakinku,ki nuna mata yadda za ta yi wanka sai ki bata kaya ta canza" Hajiya ta faɗa .
Cike da ladabi na ce "to hajiya" sai kuma na je na kamo hannun yarinyar,wani irin shock ne ya ziyarce ni tamkar na riƙe wayar lantarki haka na ji har sai da na rumtse idona nan kuma na hango wasu abubuwa masu kamar mala'iku duk sun tsaya kan ƙafafunsu suna gaishe ni,da sauri na buɗe idona na zube su kan budurwar sai na ga ta yi min ƙuri tana kallo.
Na ɗan saki murmushin yaƙe kafin na ja ta zuwa sashenmu,kamar yadda Hajiya ta ce ɗin haka na yi mata wannan gatan ko kafin ta fito daga wanka kuma na fitar mata da kayan da za ta saka yayin da Aliya kuma ta kawo abinci ta fice.
Bayan ta fito daga wankan ta saka kayan,ta zauna za ta ci abinci kenan na ce "wace ce ke?"
Ta ɗago da mamaki kafin ta ce "kamar ya?"
Na ɗan gyara zama kafin na ce "ina nufin ya kuke da Hajiya ?"
"Da Ummana da Hajiya uwarsu ɗaya,muna zaune ne a can ƙauyen Kagota can ne tushenmu " ta bani amsa . Na ce "ya aka yi kika zo nan? Ko dama kin taɓa zuwa ne?"
"A'a yau ne farko kuma ni ma ban san ya aka yi na zo ba,kawai na tsinci kaina a ƙofar gidan ne sai kuma na ga Hajiya "
"Bani saƙon da kika zo kawo mini " na faɗa ba tare da ni kaina na san takamaiman abin da yasa na ce haka ba.
"Wane saƙo?" ta tambaye ni kamar ba ta san abin da nake nufi ba,cikin ƙwaƙwalwata na ji an faɗa min abin da zan ce sai kuma ni ma na furta "wanda aka baki"
Ta saki ɗan murmushi kafin ta ce "amma ai matar Maheer aka ce na bai wa ba ke ba,kuma alamu sun nuna ke ƴar aiki ce sam babu alamun siffar wacce aka ce na bai wa saƙon"tana gama faɗar haka sai na saka idona cikin nata tare da juya su na soma yi mata maganar ido,"ki bani labarinki to"
"Sunana Habiba,kamar yadda na faɗa miki daga ƙauyen Kagota nake.Ni marainiya ce,banda kowa in banda Ummana wacce dangin mahaifina da kuma danginta suka juya mata baya ba tare da na san dalilin haka ba.Haka mutanen ƙauyenmu suna tsangwamar mu sam ba su yin duba da irin halin talaucin da muke ciki wanda shi ne yayi sanadiyar soma yin bararmu ni da Ummana.Ta hanyar mara muke samun abin da za mu ci muka tufatar da jikinmu,muna samun kuɗi sosai don zan iya faɗa miki duk wanda Umma ta neme ya bata sadaka to sai fa ya bayar.Ina mamakin haka don na sha yi mata tambayar ko dai asirin yin bara take da amma ba ta bani amsa,a ranar da Allah ya so ya nuna min ɓoyayyar fuskar Ummana ta aike ni bakin hanya sai na manta abubuwan da ta lissafa min hakan yasa na dawo sai dai cak na tsaya a bakin ƙofa.
Dukkan illahirin jikina rawa yake ,amma hakan bai sa na motsa daga inda nake ba sai ma ci gaba da kallon yadda Ummana ke wani rufe ido tana tsotse jinin wata ƴar jaririyar mage wacce tun tana shure-shure har ta kai ta bar motsi. Ummana na wurgi da gangar jikin magen na yi saurin dafe saitin zuciyata da take ta ƙoƙarin faso allon ƙirjina ta faɗo ƙasa.Ji nake kamar a ce mafarki ne nake ba gaskiya ba ce,sai dai ruhina yayi amanna cewa abin da idona ya gani zahiriya ne.
"Habiba?" na ji shaƙaƙar muryar Ummana na kiran sunana,sai a lokacin na fita jikin ƙofar ina mai shigowa cikin tsakiyar gidan namu wanda yake kamar juji tsabar datti.
"Anna ga ni " na faɗa kasancewar shine sunan da nake kiranta da shi,ina ta ƙoƙarin danne fargaba da kuma tsorona,sai dai haƙata ba ta cimma ruwa ba saboda tambayar da Anna ta watso min.
"Me kika ga na yi yanzu?" ta yi tambayar tana mai kafe ni da jajayen idonta waɗanda na lura da canjinsu daga jiya zuwa yau ne suka fara yi mata haka.
Na ɗan ƙaƙalo murmushi na ce "kina hutawa abinki" "Ɗauki mushen magen nan ki jefa cikin shara" ta faɗa tana mai ci gaba da tsare ni da ido.
Ko motsawa ban yi ba daga inda nake saboda ina da mugun tsoron mage sai da ta daka min tsawa na yi saurin ɗaukar wani busashen icce na ja magen har can cikin wani rame da muka haƙa don zuba shara.Na ja ajiyar zuciya ina mai juyo wa sai wani luguden tashin hankalin ne na kuma cin karo da shi yadda Anna ta soma rikiɗa kamar wata hawainiya.Ƙafafunta sun koma na mage har ma sun gota don guda takwas ne suka fito ras, sannu a hankali kuma ta ida rikiɗewa ta koma komai nata na mage in aka cire kanta da ke na mutum a daidai wannan gaɓar ne igiyar da ke saita hankalina da kuma ganina ta katse.
"Habiba?" na ji muryar Anna kamar a mafarki tana dadaɓa ni, a hankali na ware idona sai na ga tuni gari yayi haske alamun safiya ta yi. Anna na duba wacce ke gyara zaman wata cakuɗaɗiyar jaka ta fata akan kafaɗarta,"ki tashi kar mu makkara kin san an fi samun kuɗi lokacin wucewar ƴan kasuwa"
Ba tare da na maida hankali da tunanin abin da ya faru jiya ba na miƙe,ko ido ban wanke ba ƙafata dai ta yi sa'ar samun koɗaɗin takalmi wanda tsabar yadda suka siɗe ko kalarsu ba za a iya ganewa ba.
Fita na yi daga cikin ƴar bukar tamu na samu Anna a tsakar gida tana daidaita ƙusumbin ƙarya da take yi a kullum in za mu fita yawon bara.Bayan ta gama sai ta ɗauki sanda ta ɗan duƙe ta soma tafiya kamar wacce ke da ƙusumbin gasken.Ni kuwa tsohon kwanonmu da muke fita da shi na ɗauka kafin mu fice,manyan titunan da muka san motoci na bi muka fara bi muna amsar sadaka har muka isa cikin tasha.