Bakin ruhi complt by mrs sadauki - Chapter 28
Bakin ruhi complt by mrs sadauki Chapter 28: Bakin ruhi complt by mrs sadauki Chapter 28. A duniya tun can ya tsani wanda zai salwantar da rayuwar wasu…
4,444 words
A duniya tun can ya tsani wanda zai salwantar da rayuwar wasu domin shi ya gyara tasa rayuwar,tabbas gwara da Yabobo ta karɓe muƙamin nan don muddin yayi bincike mutum ya basa labarinsa in ya ga yayi mugunta sosai kawai kashe shi zai yi,amma yanzu da bai da wannan ikon na tambaya dole ya ja bakinsa yayi shiru .Direct daga nan asibiti ya nufa ,yana ƙoƙarin bin wata hanya sai ya ga an jawo gadon gawa za a wuce da ita MUTUWARE(MRS SADAUKI) amma abin mamaki gawar magana ce take yi masa..... My book is only 500 via
2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank
DM +22795045822.
🔞In kin san ba ki biya ba kar ki karanta min book,yin haka babban kuskure ne don cin haƙin da ba naki ba ne.Kuma Allah ba yafe haƙin wani akan na wani,don haka kar ki raina girman haƙi komai ƙanƙantarsa.
__________________________________________________ *PAID PAGE*
42
"Ka ga ƴan baiwa masu muƙami bibbiyu,ga na ifiritan ruwa ga kuma na cikin iska,zo ka taimaka mini na sake dawo da ruhina a duniyar bil'adama ko da na daƙiƙa biyar ne burina na sha sigari da giya" shi ne abin da gawar ta cewa Maheer,cike da mamaki yayi tsaye yana kallon gadon da ake ɗauke da gawar har aka shige da ita cikin mutuware.
Direct ciki Maheer ya wuce,shugabansu shi ne mutum na farko da ya soma yin tozali da shi.Wannan karon suna haɗa ido ya gaishe da Maheer cikin girmamawa kafin ya ce "ina neman yafiyarka ashe kai ma cikinmu kake kuma kana ma gaba da ni,na yi tunanin cewa kawai ka taka dokar ne don ganin ƙwaƙwaf" Maheer bai ce masa komai ba,sai dai ya fahimci cewa a tsakanin miyagu akwai wani haɗin kai mai girma,da wannan ne yayi amfani ya shiga gari ya dinga binciken duk wani abu da ya shafi ɓoyayyar duniya a haka ne kuma ya samu tasirin furen floris har yake nunawa abokansa su Dr Muhamud da kuma yadda yake juya siddabaru,sai dai bai taɓa sanin ruhin Bairama na cikin gangar jikinsa ba sai a yanzu da ya rikiɗe ya zama maciji.
Shi ke ɗauke da zuciyarsa amma Bairama ce ke juyata,wani irin tunani take saka masa na tsanar mata ciki kuwa har ita Haulen ji yake da a ce zai ganta a yanzu da tabbas zai kashe ta ne. Tsawon lokaci Maheer na cikin siffar maciji kafin ya rikiɗe ya dawo mutum,sai a lokacin ya farga irin muguntar da ya yi wa Ikilima.Shi ne ya ciciɓe ta zuwa asibiti,an ci nasarar ceto ta sai dai fa bakinta ya samu matsala ya jirkice kuma ba zai dawo daidai ba.Tana dawowa hayyacinta ta dinga ƙara da ihun ba za ta zauna da Maheer ba,tuni danginta sun zo su ne masu rarrashinta.
A ɓangaren MAHEER kuwa bayan ya kai Ikilima asibiti sai ya wuce can wajen rijiyar nan,sai dai sama da minti talatin Yabobo ba ta fito ba nan ne ya ida yarda cewa yanzu fa bai da wani ƙarfin iko.Wani takaici ya luluɓe shi har sai da ya ji idonsa sun cika da ƙwalla,babu jimawa kuwa suka ɗiga cikin rijiyar nan take wani haske ya cika wurin kafin kuma fuskar Bairama ta bayyana,ta yi kicin-kicin da rai tana kallonsa shi ma ɗin ita yake kallo kafin ƙyaftawar ido kuma ta ɓace,ya ja tsuki tare da komawa a cikin motarsa yayi mata key sai gida.
Hajiya ta tarbe shi don jin lafiya,ya katse ta da "a kawo mini tea mai zafi" yana gama faɗar haka ya haye sama,ita kuwa Hajiya Lubna ta kira ta ce ta haɗa ta kai masa.Wannan lamari ba ƙaramin daɗi ya yi wa Lubna ba kawai ta shiga kitchen ta haɗa masa,sai da ta kai bakin ƙofarsa kafin ta jefa wani magani a ciki ruwan flask ɗin.Bayan ta nemi izini sai ta shiga sannan ta ajiye trayn tare da cika masa kofi ta basa,Maheer wanda ransa ke ɓace kawai karɓa yayi ya soma sha har sai da ya sha kofi biyu a na uku ne ya soma jin wani yanayi na buƙatar mace. Hannunsa na ɗan rawa ya ajiye kofin tare da lumshe ido yana tunanin Haule,bai taɓa jin kewarta ba irin na yanzu.
Lubna wacce ta fahimci cewa tarkonta ya yi nasara kawai sai ta miƙe ta shige bedroom ɗinsa,don samun wuri har da shiga toilet ta kunna pampo ta cire kayanta ta soma yin wanka tana wani irin murmushi tana jin yau dai burinta zai cika za ta ɗanɗana zumar Maheer sai ta ji abin da Haule ta ji.
Murya ta maƙe tana kwaikwayon irin ta Haulen,an kuwa yi katari Maheer ya shigo bedroom ɗin.Yadda ya ji tana kiran nasa duk sai ragowar hankalinsa ya watse bai san lokacin da ya cire kayansa ba ya shiga toilet ɗin.A tattare da Lubna Haule yake gani wannan yasa ya isa gare ta tare da rungume ta suka ci gaba da yin wankan tare yana romance ɗinta .
Hankalin Lubna yayi ƙololuwar tashi,burinta guda shi ne kawai ya kusance ta .Ido ta lumshe tana tuna ranar da ta soma yin sex ita da Dr David wanda guguwar sonsa ce ta ɗaga ta sama ta kai ta har wurin da yake ta yarda suka mu'amulanci juna.Yanzu kuma ga Maheer namijin da take jarabarsa tun ranar da ta ƙyallara ido ta gansa.
Wani irin abu ne ya ziyarce ta jin abin da rabon da ta ji shi tun shekarun baya da suka wuce,wani irin daɗi ne yake ratsa ta cikin shauƙin da ke fizgarga ne ta kai hannunta a ƙirjin MAHEER da niyyar mayar masa da martani,amma abin da hannuwanta suka taɓo mata ne ya watsar da duk shauƙin da take ciki.
Idonta ne ta soma buɗewa,da zaton ko ƙila hannuwanta ne suka jiye mata ba daidai ba don in ba kuskure ta yi ba ƙirjin mace ne ta ji ta dafa har sun fi nata girma.Tana ware idonta ta yi tozali da fuskar Maheer kuma,ƙirjin nasa ta ƙara taɓawa har yanzun dai ba ta canza zane ba.Tana shirin maida dubanta a can sai kuma idonta ya sauka cikin madubin da ke manne da bango,wata tsaleliyar buduwar ta hango rungume da ita tana yin sex da ita daidai nan igiyar numfashin Lubna ta soma katsewa tana shirin yin ihu Bairama ta danna ta ƙasa tare da rikiɗa ta koma maciji tana shirin shiga bakinta ta ji wani abu mai ƙarfi ya riƙe ta wanda ba komai ba ne sai addu'ar Ummah wacce ke can a gidan tana yi wa ƴarta Lubna addu'ar neman tsari.
Ba don rai ya so ba Bairama ta dawo da ruhinta a nan bedroom inda ta shemar da Maheer kan bed yana bacci.Babu jimawa kuma ya dawo hayyacinsa,sai ya tuna kuma duk abin da ya faru da shi.Daga inda yake yana jin kukan Lubna wacce ke can tana kukan nadamar da ba ta da amfani don kuwa tuni Bairama ta sakar mata ƙwayoyin cuta a al'aurarta.
Ransa ne yayi mugun ɓaci,cikin tsawa ya ce "wallahi ko ki fito ko kuma ni na shiga ɓalla ki" Babu shiri ta mayar da kayanta tare da fitowa a kunyace ta fita,ya bi bayanta da harara kafin ya soma tunanin ta ina zai ga Haule?
Wanka yayi ya kimtsa cikin wasu kayan Adidas masu dogon wando, kasancewar kayan baƙaƙe sai suka fitar da haskensa.Ƙasa ya sauko wanda yayi daidai da soma zubar ruwan sama,Aliya ya gani tana yi wa Hajiya bayanin yadda gasar girkin da suka yi a ranar farko ta kasance yayin da ita kuma take ta jimamin yadda Haule ba ta nan aka soma ita kuma tana kwantar mata da hankali.
A tare duk suka ɗaga kai suka dube shi,kana ganinsa ka san yana cikin damuwa.Aliya kuwa yau dai ta cire shakkarsa da take yi ta kafe shi da ido tana kallonsa tsakiyar idonsa,wanda shi kansa Maheer yayi mamaki sannan kuma ya soma jin kallon nata har tsakiyar ruhinsa.
Ta ɗan taɓe baki kafin ta juya ta kalli Hajiya ta ce "zan tafi can restaurant na gani"
Maheer ya ce "mu je na sauke ki" ta saki wani murmushi daga ɓoye don dama keɓewa take so su yi don tattauna matsalar da ta gani kuma ta tunkaro su.
Lema ta ɗauko suka fito har zuwa motarsa,yau dai a gaba ta zauna bayan yayi nisa sosai a tuƙi sai Aliya ta ce "me ya haɗa ka da Bairama?"
Ya ɗan juyo ya dube ta kafin ya ce "ke komai kin sani"
"Eh ko ka manta cewa ni ba jinsin mutum ce ba?"
"Ta ya zan manta alhalin ƙabilarku ɗaya da abokina Dr Muhamud "
"Duk dai ba wannan ba ka bani amsar tambayata"
"Tun shekarun baya ne lokacin ina tsakiyar karatu"
"Amma me yasa ka kira ta alhalin ba ka shirya son ta ba?"
"Ni ban kira ta ba"
"A'a fa! Kai ne ka kira ta don ruhikan cikin ruwa ba su cika fitowa ba sai in an kira su" nan ne fa MAHEER ya ba Aliya labarin abin da ya faru ita kuma ta jinjina kai kafin ta ce "da buƙatar ka koma can garin ka mayar da ita cikin ahalinta sannan ka bata haƙuri"
"Ni dai duk ba wannan ba,ta wace hanya zan haɗu da H.lat?"
"Hanya ce mai sauƙin bi amma mai cike da ƙalubale,don a dole sai in ta haɗe tunaninku wuri guda kamar yadda ka yi mata a farko to a yanzu ita ce ke da wannan ƙarfin ikon"
"Bayan haka fa?"
"Za mu je farautar BAƘIN RUHI da kanmu ba tare da mun bari ya sake dawowa cikin doron duniyar bil'adama ba,don maganar da nake yi maka tuni masu niyyar maido shi suna kan hanyar zuwa Japan inda a can ne dajin sirri yake"
"Ke yanzu ba za ki iya duba mana inda Queen take ba?"
"Ba ta cikin gidansu dai,sannan tun da ta rogaza baƙin ruhi wasu ƙarfin ikona suka gudu kamar sauran masu riƙe da shi,amma a ƙiyasina Dr Muhamud ne kawai za mu iya samu da nasa tun da bai taɓa yin aiki da shi ba"
"Na fahimta! Ita kuma wannan da ruhinta ke cikin gangar jikina?"
Aliya ta ce "ita tana bayyana ne a duk lokacin da wata mace ke ƙoƙarin zuwa gare ka da niyyar soyayya kenan ka ga yana da kyau ka sanar da ƴan matanka su nisance ka in ba so suke su rasa rayuwarsu ba,yau saura ƙiris ta sake sace gangar jiki ta dawo cikin wannan duniyar,don da a ce ta yi nasarar shiga bakin Lubna da tabbas ita ce BAƘIN RUHI ta biyu don za ta yi ɓarna sosai fiye da ma shi"
A cikin wannan ruwan saman da ke zuba kamar da bakin ƙwarya Maheer ya tattara abokansa waɗanda suka taɓa fuskantar barazanar da kuma shiga komar BAƘIN RUHI.
Aliya ce ta yi musu bayanin komai,Lubna wacce ita shaida ce ta fi nurse Fatee fahimtar gargaɗin da Aliyar ke yi na su cire MAHEER daga ransu sannan za su yi aiki ne domin ceton al'umma. Bayan sun gama tsara yadda komai zai tafi ne Aliya ta matsa kusa da Dr Muhamud ta shafi tafin hannunsa nan take wani haske ya bayyana duk sai suka matso suna kallon dunƙulallen hasken wanda ya fitar da shap ɗin lula.
Hankalin kowa na kan hasken in aka cire shi mamallakin ƙarfin ikon da ya tsurawa Aliya ido yana kallo.A hankali ta ɗaga kai ta dube shi,sai ya sakar mata murmushi yayin da shi kuma MAHEER yayi gyaran murya sai duk suka nutsu suka mayar da hankalinsu sai a lokacin kuma Aliya ta soma yin wani abu tana bincike har ta samu wata alama mai nuni da inda Haule take.
"Tana cikin wata makaranta mai bayar da horo na musamman akan matsafi da tsafi,an shimfiɗa matakan tsaro sosai sai dai duk da haka shigarta ba zai yi mana wuya ba duba da duk muna da tabo ƙarfin iko,wanda zai kasa shiga a cikinmu shi ne Dr Umar don bai da komai a ruhinsa "
Dr Umar wanda ya kafe kan cewa sai ya yi wa nurse Fatee rakiya kallon Aliya ya yi kafin ya ce"ki yi wata dubarar dai don ba zan bar wacce nake so ta yi tafiyar nan ita ɗaya ba"
Shiru ta yi na ɗan wani lokaci kafin ta ce "ok babu damuwa! Oga MAHEER ka fitar da rana da kuma lokacin da za mu tafi"
Maheer wanda yake a matse ya ga sanyin idaniyarsa sai cewa yayi "wannan lokaci shi ne daidai da mu tafi kin ga zubar ruwan sama alama ce ta nasara"
Aliya ta jinjina kai kafin ta ce "yanzu yadda za mu yi kowanne daga cikinmu zai ɗora yatsansa manuniya kan hasken nan sai ya lumshe ido yayin da Dr Muhamud zai yi mana jagora" ta ƙarashe faɗa tana ɗaga kai ta kalle shi,wani irin kallo suke jefowa junansu kafin kuma dukkansu su yi yadda ta ce Dr Muhamud yayi wani furuci sai ga su a zube bakin wata mahaukaciyar makaranta wacce aka gina da ƙasusuwan namun daji.
★HAULE Mentor na kiranmu sai yayi mana jagora can ajin darasi,a can ne na samu wani ƙarin haske dangane da baƙin ruhi da kuma duk abin da ya shafi duniyar Ruhaniya. Muna cikin yin darasin ne danjoji masu kula da matakan tsaro suka fara fitar da alamar jini,kusan duk a tare muka fita zuwa waje ina jin ana cewa shirya karnukan farauta a isa bakin ƙofa.
Babu jimawa kuwa aka fito da karnukan baƙaƙe ne ƙirin waɗanda kana gani ka san jinnu ne a siffar kare. Nadia ta yi tsaye kusa da ni tana mai cewa "ko wane mai ganganci ne ya hauro makarantar nan ba tare da neman izini ba?"
"Kenan kashe shi za a yi?" na yi tambayar sai dai kafin ta bani amsar ƙofar makarantar ta buɗe,idona bai sauka ko ina ba sai cikin na MAHEER wanda shi ne a gaba tawagarsa na bayansa. Wani irin burki karnukan suka ja a daidai lokacin da suka kwasa a guje suka tunkari Maheer ɗin .Mentor da sauran malaman makaranta su ne kuma suka dinga kwantar wa da ɗalibai hankali suna cewa kowa ya koma ɗakinsa baƙi ne na gida matsalar dai ba su sanar za su zo ba. Nadia ta kama hannuna ta ce "mu je" ban musa ba na take mata baya ina waiwayen Maheer wanda tuni ya soma shigowa maƙarabansa na take masa baya,har zan tsaya sai kuma idona ya sauka kan aminiyata.Da ido kuma Aliyar ta yi mini alama da kar na nuna na san su kawai na bi Nadia mu tafi ɗin,ba don na so ba haka na bi bayanta muka muka koma can ɗakinmu yayin da kuma zuciya da ruhina ke tsumayen abin ƙauna....
🌻🌟🌻🌟🌻⭐🌻⭐🌻⭐🌻🌟🌻🌟
*_GYARA SHINE MACE_*
*_shahararriyar Mai Saida kayan Matan nan maman Yusuf likitar mata sokoto kuma CEO ta SOKOTO TOP 3 KAYAN MATA SOKOTO mai gyaran mata ciki da waje ta sake zo maku da zafafan Kayan masu kyau da inganci don farincinku a kullum shine burinmu* 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
*Ina uwargida da Amarya ina masu shirin yin aure budare da zawarawa , ina masu son su zama taurari ✨🌟ababen alfaharin mazajensu , ina mata masu kishiyoyi da ake ci masu zarafi ake wulakantasu akan kishiyoyin su ina wacce keshan wulakancin namiji , ina matan da sukeson burge mazajensu da zallan ni'ima da dandano ??? Ina matan fake fama da rashin ni'ima , budewar gaba wadan da suka faru sanadin ciyon sanyi kokuma haihuwa , ko wadda Ke fama da k'arancin ni'ima da karancin sha'awa , ?? To saurara kiji*✋🏻✋🏻✋🏻
*Ko kinsan Maman Yusuf Dr mata kuwa ?? Hmmm akace in bakasan gari ba to ka saurari daka*,💃🏻💃🏻 *Namu na dabanne kamar yadda salonmu yake daban ingantattun kaya ne da basuda wata illa ajiki sannan ba boka ba malam zaki mallaki mijinki da dandanonki sai yadda kikayi dashi*
Duk abunda kk so a bangaren kayan mata zaki samu hajiyata daga gyaran ciki harma Dana waje
Munada ingantaccen maganin sanyi na maza Dana mata hakama maganin Basir
Maganin nono Dana hips Maganin kiba dakuma maganin rage tumbi da kibar, Maganin gashi
Sabulun wanka na gyaran jiki Sabulun dilka na amare Dilkar amare
Kwallin mallaka (daga ni sai kai) Maltinar mata Bobintan mata Set na lalata gindin kiahiya Set na ukku bala'i Set na rantse bakida kishiya,
Kalolin gumba Kalolin gari Kalolin matsi Kalolin sabulan tsarki Zumar mata Zumar ridi Zumar goron tula Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin sabon budurci Tsumin kankana Tsumin tabaje Tsumin makalemata Shayin mata Sirrikan mallaka Dan goshi da mahadinshi Dan goshi na Mara Kyallen al'ajabu Rakumi da akala Bita zai zai Dahuwar kalolin kaza zabo zakara Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar zuciya Dambun nama Dahuwar yan shila Yajin mata Yajin maza domin Karin karfi
*Hmmmmmm in nace sai na lissafamuku zafafan kayan nan sai in wuni ina typing shawara daya zan baki uwargida in har baki jaraba kayan mmn Yusuf ba to ki garzaya ki saya da kanki zakizo kina godiya , 😉😉😉😉😉😍 wadan da suka San ya kayan suke kuwa. Basa bukatar wani Karin bayani , Domin Neman Karin bayani kokuma ganin kayan da nake dasu Ku tuntubeni ta wannan number 07069711327 call or WhatsApp mmn Yusuf mai kayan mata🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰My book is only 500 via
2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank
DM +22795045822.
🔞In kin san ba ki biya ba kar ki karanta min book,yin haka babban kuskure ne don cin haƙin da ba naki ba ne.Kuma Allah ba yafe haƙin wani akan na wani,don haka kar ki raina girman haƙi komai ƙanƙantarsa.
__________________________________________________ *PAID PAGE*
43
A yayin da kowa ya samu damar shigowa cikin makarantar shi Dr Umar kasa shiga yayi saboda babu ɗigon komai a cikin jininsa kamar yadda Aliya ya faɗa tun farko . Mentor ya dube su ya ce "shi kuma wannan?"
"Abokinmu ne,yana son zama kamar mu amma ba mu da lokaci isasshe ballantana mu ƙaddamar da shi amma please ka basa izinin shigowa na san da sannu za ka yi alfahari da shi" Maheer ne yayi maganar wanda idonsa suka soma sauya kala zuwa na Siren sakamakon tururin son Haule da ya yo masa sama ita ma ta dinga jefo masa kallon so.
Shi Mentor bai san taƙamaimai abin da ke faruwa ga MAHEER ba,yayi tunanin ma aiki ne yake yi da ruhikan ruwa wannan yasa bai wani damu da bincike ba ya kwance matakan tsaron da suka hana Dr Umar shigowa ɗin.
Shi ne yayi musu jagora zuwa wani ɓangare na cikin makarantar kafin ya sa a kawo musu cofee sai ƙamshi yake ,babu wanda ya damu da shi don hankalinsu ba kwance yake ba. Aliya ce wannan karon ta ɗau magana tana mai cewa "sunana Evaliya ina ɗaya daga cikin waɗanda suka rayu a tsawon ƙarni uku da suka wuce,na yi zamani da manya kuma shararrun matsana na duniya.Na san sirrikan ruhaniya da kuma yadda lamurran can ke gudana,amma har zuwa yanzu kana da ilimin da ni ban da shi ya mai girman Mentor da son samu ne ina son a koyar da ni yadda ake yin baƙin tsafi da kuma wargaza shi " yadda ta yi magana cikin taushin murya haɗi da sadda kai ƙasa yasa ta saye zuciyar Mentor,sai dai duk da haka bai sa shi yayi saurin bada kai bori ya hau ba sai da yayi mata tambayoyi ita kuma ta dinga basa amsa sannan ya yarda da zancenta.
Can kuma ya dubi Dr Muhamud ya ce "da alamu kuma wannan ɗin jinsinku ɗaya kuma kamar kuna son junanku ba?"
Duk shiru suka yi , Mentor ya ce "me zai hana a ɗaura muku aure ne kamar tafiyar taku za ta fi tafiya daidai" ya ida maganar cikin salon barkwanci yayin da kuma su Maheer suka soma ƴar kallon-kallon.
Mentor ya saki wani murmushi kafin ya je ya buɗe wani wuri ya ciro wata ƙatuwar kalanda ya buɗe ta tare da ɗora ta kan wani table.Zanen doddani ne iri-iri tun na ƙarnin farko zuwa yanzu,ba tare da sun tambaye shi ba ya ci gaba da cewa "tun kafin ku zo nan na san da akwai ranar da za ku zo,na yi karatu mai zurfi da bincike akan abin da kuka sa gaba sai dai har zuwa yanzu ban dace ba ban cika burina na yin gamdakatar da BAƘIN RUHI ba.Ban damu ya kashe ni ba,burina dai na gansa a fili ba wai iya hoto ba"
"Meke haɗinmu da baƙin ruhi kuma Mentor?" Lubna ta faɗa don a tunaninta rame ne yake son yi musu . Ya dube ta kafin ya ce "wannan ɗakin da muke ciki ya kasance keɓaɓen wuri mai bayyanar mini da gaskiyar duk wani baƙo da za mu yi don haka bari wani zancen ɓoye gaskiya"
Kusan lokaci guda suka ja numfashi kafin MAHEER ya ce " a binciken da ka yi me ka samu matsayin result dangane da fafatawar da tawagar bil'adama da kuma baƙin ruhi ta kasance?"
"Babu gamsashiyar amsa,don wani binciken ya nuna baƙin ruhi zai ƙara wanzuwa a doron duniya a karo na biyu a kuma cikin gangar jikin wanda ya fara cakarsa da wuƙar sirri..." MAHEER yayi saurin katse da "kana nufin a jikin Queen ?"
Aliya ta ce "ka barsa mana yayi mana bayani"
Mentor ya ci gaba da cewa "wani binciken kuma ya nuna zai dawo a duniya amma zai dinga shawagi cikin iska saboda rashin wanda zai yi dakonsa,yayin da kuma wani binciken ya fitar cewa ba zai samu damar shigowa ba saboda hanyar da jaruman mutane za su toshe kwata-kwata " a daidai wannan gaɓar ma sai da suka sake kallon juna kowanne na fatan Allah sa result ɗin ƙarshen ita ce wacce za su samu ɗin.
A nan ya bar su ya kama gabansa bayan ya basu wasu littattafai masu magana akan doddani har da ma mutanen farko kafin zuwan canjin yanayi.
★HAULE
Da na je can ɗaki sam kasa nutsuwa na yi,burina bai wuce na ji ni a ƙirjin MAHEER ba.Kasa jura na yi ta yadda hatta Nadia sai da ta gane ina cikin damuwa.
"Ya dai? Ya na ga duk kin tashi hankalinki daga zuwan baƙin nan,ko dai akwai wanda kika sani?" ta tambaye ni.
Na girgiza kai na ce "a'a kawai ban jin daɗin jikina ne amma ban san kowa ba"
"Hahaha! Wai me kike ɓoye mini ne? Ko dai akwai mijinki a cikinsu?"
Ido na tsura mata na kasa bata amsar tambayarta,sai da ta sake cewa "ki faɗa mini mana kika sani da akwai taimakon da zan yi miki?"
Na ja numfashi kafin na ce "eh wannan na daga gaba shi ne mijina"
"Awooo! Handsome ɗin nan? Yana da kyau sosai gaskiya kin yi dacen miji.Amma me yasa ba ki je wurinsa ba?"
"Ina tsoron Mentor ne,kina ga ba zai iya yi masa illa ba in ya gano cewa ya zo ya tafi da ni ne?"
"A'a babu abin da zai yi masa ai na ga yana da ƙarfin iko da kuma izza "
"A'a bai da wata power a yanzu ni na sani"
Nadia ta ce "ki bari har dare yayi sosai zan kai ki har ɗakin da ake sauke baƙi sai ku gana da mijinki"
Na saki wani murmushin jin daɗi kafin na ce "na gode sosai Nadia bayan Aliya ke ce wacce kika nuna mini ƙauna da kulawa"
Ta mayar mini da martanin murmushin kafin ta ce "ina fatan ke ma za ki mayar mini da alkhairi " Na kamo hannunta kafin na ce "kar ki damu zan kasance mai kirki fiye da yadda kike tunani " haka muka yi ta zaman jiran dare har lokaci yayi da za mu tafi.
Kamar wasu ɓarayi haka muka fito,Nadia na gaba ina take mata baya.Da powerta ta yi amfani har ta gano wane ne ɗakin Maheer a cikin jerin ɗakunan baccin,tana shirin buɗe mini ƙofa muryar Aliya ta katse mana hanzari.
"Me kike shirin aikatawa? Wace ce ke da za ki yi mata jagora?" ta yi furicin tare da cire hannuna da ke cikin na Nadia. Cike da masifa ita kuma Nadiar ta ce "ke kuma a su wa ɗan wake a hotel? To ita ɗin ƙawata ce" ta ida furucin ita kuma tana mai kamo hannuna nan ɗin ma Aliya ƙara fizge shi ta yi tana kallona.
Ni kuma banda murmushi babu abin da nake yi,wato Aliya na kishin ƙawance ne ganin na samu wata bayan ita.Ban ce komai ba sai da na ga suna shirin yin faɗa,"Aliya don Allah ki yi haƙuri zan yi miki bayanin wace ce ita ke kuma Nadia ki yi shiru Please "
Cike da jin haushi ta ce "ni ban damu da sanin wace ce ita ba,kawai ta rabu da ke ta je ta kama gabanta ina ce dai ni ce ke baki shawara akan komai da ya dace to ban yarda ki je wurin Oga Maheer ba ko za ku haɗu ba yau ba"
Nadia ta yi wata irin dariya kafin ta ce "to Mama yadda kika ce ai haka za a yi? Kina tunanin har kina da wani ƙarfin iko da ban mallake shi ba?" sai kawai ta furzo da wata wuta don ƙona Aliya amma na yi saurin tarewa sai dai kafin ni ma ta sauka jikina Maheer ya fito yana dakatar da wutar ta hanyar furzo ruwa nasa ɓangaren.
Aliya ta saki murmushi kafin ta ce "hakan shi ne daidai,Oga MAHEER ya zo gare ki ba wai ke ki je ba ga shi sannu a hankali zai kuma samun wani ƙarfin ikon ya kuma juya ruhin Bairama"
Haka-haka nake jin kalaman Aliya sakamakon jirgin so da ya zo ya sure ni,kallon juna muke ni da Maheer kamar yau ne muka saba ganin juna.Nadia ta ja tsuki ta yi tafiyarta,Aliya ta ce "a je dai can a ƙarata ba mu da buƙatar ƙawancenki"
Na saki murmushi mai sauti ina ɗan satar kallon Aliya ita kuma da sauri ta kawar da kai bayan ta yi mini alama da ido. Na sunne kai ina wasa da yatsun hannuna,ya zo dab da ni tare da jawo ni ya rungume ƙam a ƙirjinsa.A tare muka ja ajiyar zuciya yayin da Aliya kuma ta yi wani siddabaru wani abu mai kamar ginin ƙanƙara ya zagaye mu har da fitar da ɗaki .Kamar mai jira haka Maheer ya lalubo bakina ya soma yi mini wata irin sumba,bayansa na zagaye da dukkan hannuwana ina jan numfashi mun kwashi sama da minti goma yana abu ɗaya kafin ya janye bakinsa ya tsure ni da idonsa masu fallasa sirrin zuciyarsa.Duk yadda na so na tsere daga wannan kallon mai kashe jiki da saukar da kasala kasawa na yi,murya can ƙasan maƙoshi ya furta "shi ne kika tafi kika bar ni ?"
Ban ce komai ba sai ƙirjinsa da nake ɗan dannawa,ya ja ajiyar zuciya kafin ya ci gaba da cewa "saura ƙiris na mutu fa"
Na ce "ai tare za mu mutu"