Kenza eBookz

Bakin ruhi complt by mrs sadauki - Chapter 30

Bakin ruhi complt by mrs sadauki - Chapter 30

Bakin ruhi complt by mrs sadauki Chapter 30: Bakin ruhi complt by mrs sadauki Chapter 30. Aliya ta matso ta buɗe idon Dr Muhamud kafin ta ce "Oga Maheer ka…

4,489 words

Aliya ta matso ta buɗe idon Dr Muhamud kafin ta ce "Oga Maheer ka yi zama da power na maciji zo ka duba mana cikin ƙwayar idon nan hoton wa ka gani?"

Maheer ya yi kamar yadda ta ce kafin ya soma magana "yana gun Mr Sahil mijin Bahijja yanzu haka suna can gidansa har da su Yasmine ɗin wacce yake ƙoƙarin kaddamar da ita a cikin sabuwar ƙungiyar da suke shirye-shiryen kafawa a karo na biyu"

Na yi wani murmushi kafin na ce " har abada hakan ba zai kasance ba,don duk wata hanya da zan bi sai na binciko ta na hana kafuwar wannan ƙungiyar.Ruhinsa kuma yanzu za a maido masa shi ku dai nutsu ku riƙe mini shi" ina gama faɗar abin da ni kaina ban san ya ake ina furta hakan ba sai na kai hannuna na kama wuyan Dr Muhamud na soma yin magana cikin wani yare na mutanen farko,ɗakin ne ya yi ɗif duka hasken ya ɗauke babu jimawa kuma wata baƙar inuwa ta faso bango ta shigo.

"Lafiya kika aika kirana?'" ruhin Boss ya furta.

"Abin da ke hannunka nake son ka bani ta lafiya kafin na saka ƙarfi" na basa amsa ina juya idona suna fitar da wani irin haske. Yayi wata dariya yana shirin yin magana amma na riƙe masa maƙogoro ta hanyar juya idon nawa masu cike da ƙarfin iko,ya soma kakarin mutuwa amma don taurin kai ya ƙi miƙo mini sai da ya ga ina shirin kawo ruhin Yasmine yana damƙa mini ruhin Dr Muhamud ni kuma ina tsinka nasa tare da jefa shi ɓoyayyar duniya inda su ma can ne suke da niyyar kai Dr Muhamud don ba mutuwar gaske ce yayi ba.

Aliya da MAHEER suna tsaye duk suna kallona,sai a lokacin kuma na ƙara basu wani umarnin na su riƙe ƙafafuwan Dr Muhamud ɗin.

Ido na rufe ina mai yin ɗalasiman da suka kamata,nan take gangar jikinsa ta soma yin rawa kafin kuma bakinsa ya buɗe ruhinsa ya shige.Kamar ƙyaftawar ido haka ya miƙe yana jan numfashi,Aliya ta rungume shi cike da murna yayin da mu kuma muka shiga yin murmushin nasara.Haka muka fito muka wuce gida har da shi Dr Muhamud ɗin,can ɓangaren MAHEER ya tafi yayin da ni kuma na dawo ɗakinmu ni da Aliya,sai a lokacin ne ta bani tarihinta wanda na ji kamar almara don ban ma san iya adadin ɗaruruwan shekarun da da ta kwashe ba a duniya.

"Kina son Dr Muhamud ?" na tambaye ta ina mai kafe ta da ido .Ta saki ɗan murmushi kafin ta jinjina kai,na ce "ya kamata ki musulunta,ki yi addinin Musulunci da niyyar kanki a kuma hukunce kamar yadda ya zo"

"Na sani! Yanzu me kika yanke game da BAƘIN RUHI?"

"Zai koma inda ya fito,zan yaƙe shi" na bata amsa.

Yanayin fuskarta wani iri kafin ta ce "yaƙarsa abu ne da ba zai kawar da shi ba na har abada,ko ya koma wani zai iya ƙara kawo shi amma kashe shi shine daidai"

"Ta ya kenan?" na tambaye ta.

Ta yi ɗan jim kafin ta ce "dole wani rai ya salwanta" "Ni ban gane abin da kike son cewa ba" "Za ki gane in lokaci yayi,yanzu dai sai da safe ni zan kwanta" tana gama faɗar haka sai ta juya mini baya ta yi kwanciyarta,babu jimawa kuma bacci ya ɗauke ta.Ni ma wuri na samu na kwanta sai dai fa ba baccin na yi ba,a'a balaguron ruhi ne na lula a can garinmu.

Dare yayi duk kowa bacci yake,gidan ba baƙona ba ne wannan yasa na soma ratsa ko ina har na isa ɗakin anty Mardiyya tana kwance tana sharara bacci,idonta sun yi suntum da alamun na kukan mahaifinta ne da ta yi wanda na aika barzahu. Fitilun idona ne suka hasko mini yadda ta bangaji Innarmu,cike da zafin rai na soma kallon duk wani bango na ɗakin ina jefa wata ƙwayar cuta nan take shaƙar iskan ɗakin ta canza hayaƙi ya turniƙe wurin ga wani irin yanayi na shi ba duhu ba kuma ba haske ba,sai kuma uban zafi kamar tukunyar sabuwar burodi .

Zufa ce ta soma yi mata tsiyaya,amma ba ta farka ba ƙila ta gaji ne sosai.Wuyanta na shaƙe da furicin bakina,nan ta buɗe ido tana shure-shure amma ba ta ganina sai da na ga tana shirin mutuwa sannan na ƙyale ta.Zaune ta yi tsakiyar shimfiɗa tana maida numfashi kafin ta jawo butalin ruwa ta buɗe tare da kafa bakinta,sai dai na hana ruwan motsi ballantana mu su fita su shiga maƙoshinta.A ɗan tsorace take jijiga gorar ga dai ruwan amma ta rasa dalilin da yasa ba su fita,a dole ta ajiye shi amma na cira shi sama ya tsaya cikin iska tare kuma da buɗe murfinsa ruwan suka soma tsiyaya a gaban idon anty Mardiyya.A guje ta nufi ƙofa sai dai kafin ma ta ƙarasa na murza key wanda tana ji tana ganin kuma yadda ake murza shi amma ba ta ganina.

Cak ta tsaya tana kuka tare da soma waige-waige,so take ta yi magana amma ta kasa.Daidai nan na saka bulala na soma tsula mata tana ta ihu da kururuwa amma a banza tun da babu mai jin ta ballantana ya kawo mata agaji,sai da na yi mata lilis kafin na bar ta a nan kwance cikin fitar hayyaci.

Ina fitowa sai na yi tsinke ɗakin Kawu Laminu wanda tun da jimawa na fahimci ya tsane ni wanda kuma ƙiyayyar mahaifina ce ta shafe ni. Yana zaune yana ƙirga kuɗi,wuri na samu na zaunar da ruhina ina kallonsa.Shi ɗin ya kasance mugu wannan yasa ya ji a jikinsa ba shi ɗaya ba ne a ɗakin duk da kuwa bai ganina,na saki murmushin mugunta ina juya ido a nan take kuɗin ba suka dinga yaga kansu irin ƙanana sosai.

Kawu Laminu ya soma ɗan ƙaramin hauka don duka kuɗinsa ne da ya mallaka har da ma na cuta wanda ya kwashe na Kawu Hamza.

Almakashi na ɗauko daga ɓoyayyar duniya na soma aiki da shi kamar mai yanka atamfa na soma yawo da shi kaf cikin ɗakin hakan ya hana duban Kawu Laminu saƙar don duk inda almakashi ya gifta shi ma sai ya duba har ta kai na matsa shi kusan fuskarsa tuni ya soma fitsari cikin wando amma a haka na soma aske masa kai ina yi masa askin ɓarayi kafin kuma na mayar da almakashin mai siffar ƴar tsanar roba na fitar masa da kai da hanci da baki,ya shiga yi wa Kawu Laminu dariya daidai nan ya faɗi a some.Raina fari ƙal na baro gidan, binciken Yaya Aliyu na soma yi amma ban gansa ba a haka na wuce inda na bar gangar jikina na koma cikinsa.

Washegari kiran sallah ne ya tashe ni daga bacci,dakyar na tashi na yi wanka na gabatar da sallah.Aliya ba ta cikin ɗaki hakan yasa ina gamawa na wuce kitchen,a can na tarar da ita kuwa tana aiki sai na kama mata muna yi muna hira har ta kawo mini zancen Lubna.

"A tunaninki mene ne yasa ita ɗaya kawai suka ci galaba a kanta?" Aliya ta tambaye ni.

"Saboda ita ce mai rauni" na bata amsa.

Ta taɓe baki kafin ta ce "ko kuma ita ce munafuka ba,ita kuma Nadia fa wane wuri kika ajiye ta a yanzu?"

Na saki ɗan murmushi don na fahimci cewa har zuwa yanzu Aliya na kishinta ne.Na ce "ni yanzu wani tunani ne yake ratsa kwanyata,me zai hana mu nemo tsohuwa Yabobo ta bamu wata hanyar da ba sai wani rai ya salwanta ba?"

Ta ce "ba za ta iya zuwa duniyar nan ba,don tana can tana kula da su Anty don dab suke da dawowa gida"

Na sauke numfashi kafin na ce "ni dai ban so rayuwar kowa ta salwanta"

Cikin ɗacin rai Aliya ta ce "abin da ya zama kuma dole ne,don tuni ma an fitar da mutane biyu waɗanda ake sa ran ɗaya daga ciki ne zai mutu tare da BAƘIN RUHI "

Gabana ya faɗi daram! Murya na ɗan rawa na ce "su wane ne kenan?"

Shiru ta yi kamar ba za ta ce komai ba kafin can ta ce "ɗayan dai Yaya Aliyu ne"

"Na biyu kuma fa?"

Tsakiyar ido ta dube ni kafin ta kawar da kai,"don Allah faɗa mini wane ne na biyun ?"

Ƙin bani amsa ta yi kawai sai ta ɗauki flask ta zuba dafafen kayan tea ta miƙo mini tana mai cewa "ki kai wa mijinki" Na ƙi karɓa ina mai cewa "Aliya ki faɗa mini"

"Ba yanzu ba,ungo ki je ki dawo"

Na karɓa na ɗora kan tray ɗin da ta shirya komai nasa,kafin na fita sai dai ina daf da hawa matakalar benen trayn ya faɗi komai ya zube daidai nan Hajiya ta fito tana jan salati.A yadda na ga tsoro ƙarara kan fuskarta na fahimci ba wai na asarar kofunan da suka fashe ba ne,Aliya ma fitowa ta yi jikinta na kyarma .

"Ina sauri ne sai suka zube" na faɗa cikin sanyin murya,Aliya ta haɗiye wasu yawu kafin ta ce "Haule mu je ɗaki ki kwanta ki huta" sai ta ja hannuna muka wuce can ɗaki,gefena ta zauna cike da damuwa lokaci zuwa lokaci kuma tana satar kallona yayin da ni kuma nake jin zuciyata na yi mini wata irin rawa.

"Ban san mene ne kuke ɓoye mini ba ke da Hajiya ,amma fuskokinku sun nuna" na faɗa kamar zan yi kuka.

Cikin sanyi Aliya ta ce " Haule in dai zan sake dawowa a duniyar nan a wani zamani,to ke ce za ki sake haifata"

Sam ban fahimci abin da take nufi ba,sai na ɗauki maganar ta shirme.Na ce "na haife ki kuma?"

"Eh ina nufin ki yi mini takwara" ta faɗi haka tare da shafa cikina tana wani irin murmushi,wani irin sanyi ne ya ratsa ni sai na ji kuma tamkar an ɗaure jijiyoyina.A hankali kuma idona suka soma lumshewa,babu jimawa bacci ya ɗauke ni wanda sam babu wani abun alkhairi a ciki sai mutuwar waɗanda nake ji a cikin ɓargon ruhina da aka nuna mini.

Ina farkawa na ga MAHEER gefena,yana shafar fuskata sai na fahimci hawaye ne yake share mini. "Kina kuka Queen me yasa?" ya tambaye ni.

"Ina Aliya ?" ita ce tambayar da na yi masa. "Sun tafi restaurant " ya bani amsa.

"Mu je ka kai ni" na faɗa cikin sauri tare da yunƙurin tashi amma ya hana ni ta hanyar riƙe ni gam,ido cikin ido muke kallon juna kafin ya ce "ina so ki ƙaryata abin da aka nuna miki cikin mafarki wannan shi ne maslahar ruhinki" na girgiza masa kai na ce "tun da ka ga haka to tabbas zai faru ɗin"

"Haule?" ya kira ni wanda kuma yau shi ne karon farko da ya taɓa kirana da wannan sunan,na dube shi cikin ido sannan ya ci gaba da cewa "a jiya na yi balaguron ruhi,na je gidansu nurse Fatee kuma na yi nasarar rogaza sauran sihirin da ya rage a yanzu ta san wace ce mahaifiyarta,ita ma Hajiya Bintar ta dawo hayyacinta yayin da ita kuma Momy ta zauce ta fara yin rashin lafiya mai kamar hauka.Oga kuma na tsinka igiyar da ke saita maganarsa don ya fi kowa sanin dabarun kafa ƙungiya a halin yanzu kuma ba zai iya yi musu komai ba.Boss kuma ya mutu,a yau aka rufe shi tun bakwai na safe duk fatar jikinsa ta yi duhu ta rine,Bahijja kuma ta tafi can wurin danginta ita da ƴarta.Mutum ɗaya ne kawai ya rage a ahalin family shi ne Yaya Aliyu,shi kuma bai da gogewa da yadda ake gudanar da komai duk wanda za su taimaka masa babu su sai mahaifinki kawai wanda shi kuma rashin Inna a kusa da shi ya raunata ruhinsa.Faɗa mini ina BAƘIN RUHI yake a yanzu?"

Shiru na yi ba tare da na basa amsa ba,don a iya bincikena na daren jiya ko sawunsa ban gani ba. "Ban sani ba" na basa amsa. Maheer ya miƙe tsaye tare da juya mini baya,a hankali kuma ya shiga cire rigarsa har ya fitar da ita duka.A mugun razane na tashi tsaye ina waro ido saboda ganin ƙaton tambarin baƙin ruhi a allon ƙashin bayansa na hagu.

A hankali MAHEER ya juyo yana kallona da idonsa da suka canza kala suka koma baƙi ƙirin dukkansu babu ɗigo fari ko ɗaya.Tsoro ne ya kama ni wanda ban taɓa ji ya ziyarce ni ba,in dai na fahimta MAHEER shi ne BAƘIN RUHI a yanzu,shi ne wanda ya ɗauki alhakin dakonsa a gangar jikinsa.Tako ɗaya kawai yayi na gansa dab da ni,a hankali kuma ya soma yin wani abu mai kamar na zautatu haɗi da wangale bakinsa na ƙurma ihu ina shirin bazawa a guje sai aka banko ƙofa Aliya ce ta shigo tana mai yin wani furicin da yasa idonta suka ɗau haske tana mai cewa "A yau ƙarshen komai zai zo,ruhika biyu za su narke su zama babu.Queen Haulat wakiliyar FARIN RUHI tare da King Maheer wakilin BAƘIN RUHI ku zo zuwa ga duniyar Ruhaniya"

Tana gama wannan furici sai sarƙar wuyana ta faɗi ƙasa,dutsen tsakiya ya soma kawo haske yana mai fitar da wani kamar shatin zuciya amma an rabata gida biyu.Uwa Yabobo ce ta bayyana ita da Innarmu wacce ke miƙo mini wuƙa,na karɓa ina mai tsaga yatsana manuniya sai na miƙawa MAHEER shi ma yayi haka sai muka tara yatsun namu kan sarƙar jininmu ya dinga ɗiga a ciki yana haɗewa cikin juna.

Innarmu ta cire sarƙar wuyanta sai na ta zama tamkar murfin tawa sarƙar,haka ta haɗe su wuri guda ta miƙawa uwa Yabobo ita tana mai cewa "mun cika alƙawarin Baba Maitama"

Yayin da ita kuma uwa Yabobo ta ce "daga yau kowa zai karɓi hukuncin abin da ya aikata,adalci zai wanzu a duniyar Ruhaniya yayin da farin ciki da zaman lafiya zai yi wa duniyar ado" tana gama faɗar haka sai kuma ta soma yin wani furici ,farin abin nan da na ga ya ratsa jikina ya shiga lokacin da muka je dajin sirri,shi ne yanzu ya fita ya shiga sarƙa wacce take tamkar mayen ƙarfe zuƙo ruhi ne a aikinta.Haka ma wani abu baƙi ƙirin ya fita daga jikin MAHEER ya shiga sarƙar,uwa Yabobo ta yi sama kamar wata leda ta bi ta rufin ɗaki ta fita yayin da kuma MAHEER ya faɗi ƙasa babu numfashi,wanda yayi daidai da fara kukan Aliya...... My book is only 500 via

2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank

DM +22795045822.

🔞In kin san ba ki biya ba kar ki karanta min book,yin haka babban kuskure ne don cin haƙin da ba naki ba ne.Kuma Allah ba yafe haƙin wani akan na wani,don haka kar ki raina girman haƙi komai ƙanƙantarsa.

__________________________________________________ *PAID PAGE*

*The End*

Kukan Aliya shi ya tabbatar mini da abin da nake dai gudu ya zama gaskiya.Duk da ƙwaƙwalwata ta kasa ɗaukar lamarin amma gaske dai ne MAHEER ya mutu kamar yadda na gani a mafarkina,Innarmu ce ta shafa masa ido ita ma tana hawaye kafin ta zo ta rungume ni wanda yayi daidai da jin wani abu na rufe mini fitilun idanu ban sake sanin abin da ya faru ba sai tsintar kaina na yi a ɓoyayyar duniya wacce take cike da ɗumbin al'umma maza da mata,nagari da kuma mugaye.

Sun kasu kashi biyu,ɓangaren dama sanye suke da fararen kaya yayin da masu ɗaya ɓangaren ke sanye da baƙaƙe.Kaka Nalado na gani a gaban maƙarabansa tamkar shi ne dai ke wakiltar BAƘIN RUHI har zuwa yanzu,yayin da kuma Maitama ke sanye da fararen kayansa shi ma yana tsaye kan ƙafafunsa hannunsa riƙe da furen floris wanda aka rubuta saƙon maraba da zuwan ruhin MAHEER wanda ke dab da shigowa.

Kamar zararriya haka na tafi a guje ina kuka tare da zubewa kusan ƙafafunsa ina kallonsa da idon tausayi na ce "ta ya za ka yi mini haka duk da uwar wuyar da muka sha don ganin burinka ya tabbata? Me yasa sai MAHEER? Akwai wani aiki da ya kamata a ce yayi wanda bai cika ba? Ko da akwai inda ya yi kuskure? "

Kaka Maitama ya duƙa tare da kamo ni amma na zille na ƙi yarda ya ciro ni,a dole ya soma yi mini magana cikin taushin murya "jikata Haulat haka alƙalamin ƙaddara ya nuna,domin kawar da BAƘIN RUHI ana buƙatar hadiyar wani ruhin,kuma MAHEER shi ne jinina na kusa wanda ya kamata na bayar in kuma ba shi ba to ke ce ko kuma Aliyu sai dai kuma ruhin Aliyu ɗin ya gurɓata da duhun zunubi ba a buƙatarsa"

Wani kukan na sake fashewa da shi kafin na ce "na yarda na mutu domin MAHEER ya rayu"

Maitama ya ce "ruhi biyu ne da ke sai dai ki zaɓa cikin biyun wanne za a ɗauka sabo ko tsoho?"

Ba tare da na fahimci abin da yake nufi ba na ce "tsohon!"

Sai ya miƙo mini wata munduwa wacce aka ƙera da ƙarfen yin kuɗi ya ce "ki ɗora wannan a saman goshin MAHEER" na karɓa daidai nan na farka na samu kaina kan gadon asibiti.

Babu kowa ɗakin wannan yasa na yunƙura na tashi zaune da kaina.Wani abu na ji cikin tafin hannuna,ko da na duba sai na ga ƙarfen nan ne da Maitama ya bani sai yanzu ne kuma duk abubuwan da suka faru suka dawo mini a kai.Da sauri na dire daga gadon na buɗe ƙofa na fito,direct hanyar da za ta kai ni mutuware na nufa don na fi kyautata zaton can dai za a ajiye gawarsa .

A bakin ƙofar na hango Dr Muhamud sai rarrashin Aliya yake,shi ne ya fara ganina ya sanar da ita.Sai ta juyo,muna haɗa ido da ita sai na ga ta saki murmushi kuma kamar ta san abin da zai faru.Da sauri ta nufo ni tare da rungume ni"kin samo mafita? Wa kika bayar matsayin sacrifice?"

"Tsohon ruhina" na bata amsa,da wani mugun sauri ta sake ni tare da ja baya ta soma girgiza kai tana furta "a'a! A'a! Don me?"

Ban tsaya bata amsa ba na wuce ciki,ban wani sha wahalar ganin MAHEER ɗin ba.Na yaye zanen da aka rufa masa na ƙure kyakkyawar fuskarsa da ido kafin kuma hannu na rawa na ɗora munduwar kan goshinsa,nan take ta soma fitar da wani haske kafin sannu a hankali ta dinga nitsewa cikin koshin nasa har na bar ganinta sai hasken kawai shi ma zuwa wani lokaci sai na bar ganinsa.

Sama da minti biyu ina tsaye amma ko alamun numfashi babu a tattare da shi,tuni na sare kawai sai na faɗa jikinsa ina mai fashewa da kuka.Tsawon lokaci ina a haka kafin na ji hannunsa kan gadon bayana tare da amon muryarsa "H.lat!" ji na yi kamar an narkar da ni tsabar shock da kuma farin ciki.Na ɗago kai da sauri muna kallon juna kafin na kafa bakina kan nasa na shi yi masa sumbar fitar hankali.

"Haule?" na ji muryar da har abada ba zan taɓa mancewa ba, da sauri na saki MAHEER na juya na je da mugun sauri na ƙanƙame anty Aliya ina wani kukan.Ita ce ta jawo ni muka fito waje,yayin da kuma Dr Muhamud ya taimakawa MAHEER ya kimtsa suka fito.

Direct gidan Hajiya muka yi tsinke wacce ba ta san komai da ya faru ba sai yanzu da Innarmu ta bata labari.Babu jimawa aka haɗa family meeting ,an yi kuka sosai an zubda hawaye yadda Innarmu ta dinga zayyano irin matsalolin da muka fuskanta a gidanmu.

Dangi tamkar za su haɗiye ni haka suka dinga ririta ni,muna a tare sallah kawai ke sa mu tashi.Wuraren ƙarfe takwas na dare na haura can sama inda Aliya ta haɗa mini ruwan wanka masu ɗumi,yau wani sabon salo da ta ɗauko wai ita za ta yi mini wanka.

Haka na shiga bahon wanka,gashin kaina ta soma wankewa kafin ta soma yi mini maganar da sam ban fahimci abin da take son faɗa ba.

"Haule duniyar Ruhaniya da kike ganinta ta wuce duk yadda kike tsammani,yanzu ne za a baki sharuɗa sai kuma kin bi su amma kuma in kin tafi gaba sai ki ga ba ki tsira ba.Na so a ce kin yi haƙuri kin yi juriya ba ki yi saurin ɗaukar zaɓin da aka yi miki ba,don tuni na tsara nawa plan ɗin" sai kuma ta yi shiru.

Na ja numfashi kafin na ce "Aliya me kike son faɗa haka?"

"Babu komai! Bari na tsane miki gashin da kyau sai ki yi wanka" ta faɗa tare da soma yi mini wasu manyan kitso guda biyu tana gamawa ta fice,ina kallonta yadda take sharar ƙwalla .

Shiru na yi ina tunanin wane ne tsohon ruhina? Ban sani ba,don in ba don Maitama ya shaida mini ba sam ban san ma ruhi biyu ne da ni ba.Sai da na yi wanka mai kyau kafin na fito,na tsane jikina na saka wata rigar bacci mai santsi sai na yi zaune kan kujera.Babu jimawa Aliya ta sake shigowa ta kawo mini Apple da madara ,ta tsiyayaini a kofi kafin kuma ta zuba wani magani fuskarta dai cike da takaicin nan da ban san na mine ne ba kamar dai na wacce aka sanarwa da ranar mutuwarta.

"Aliya wai meke damunki?" na tambaye ta. "Gobe ne ake yin gasar abinci zagayen ƙarshe,ki kwanta ki huta don ina so mu yi komai a tare" ta faɗa maimakon ta bani amsa. Ina shirin yin magana kuma sai MAHEER ya shigo,da sauri ta fice bayan sun gaisa shi kuma ya zo ya zauna kusa da ni.

"Mene ne nan?" ya faɗa yana kallon madarar da Aliya ta zuba mini ,na ce "madara ce mana" kawai sai ya ɗauka ya soma sha.

Ni kuma na yi shiru na tsura masa ido kawai ina tunanin da ace babu shi da ban san abin da zai faru da ni ba."Ba ki tambaye ni ta ya aka yi na zaɓi na mutu da BAƘIN RUHI ba" MAHEER ya faɗa. Ban ce komai ba sai hannuna da na sarkaye a nasa ina shafar sajensa da ya kwanta luf gwanin sha'awa,ya ci gaba da cewa "a yayin da kika kashe Kawu Hamza sai baƙin ruhi yayi tsalle ya diro nan gidan da niyyar ya shige ki kamar yadda alƙalamin ƙaddarar da suka yi rubu da shi ya bayyana cewa ke ce za ki gaji Kaka Nalado,amma sai na tari aradu ba gammo na ce ya shige ni zan yi masa hidima.A daidai lokacin da yake ratsa gangar jikina a wannan sa'ilin ne Aliya ta fito daga cikin ɗaki ta gani,ban san mene ne ta yi ba amma tabbas ta sarrafa wani magic nata sai ya zamana ni ne zan fi ƙarfin baƙin ruhi na sarrafa shi ba wai shi ne zai sarrafa ni ba .A cikin wannan dare mun yi lissafi iri-iri dangane da wanda zai haƙura ya tafi ɓoyayyar duniya domin kawar da baƙin ruhi .Tashin farko ta ce ita za ta ɗauki wannan kasadar don ba za ta iya jurar ta zauna a duniyar nan alhalin babu ke,gara ta yi tafiyar mai mafari ta mutu madadinki.Sai dai duk yadda muka ɗora tsaunin cimma nasara ya ƙi daidaita,sai kuma ta kawo shawarar mu jingina wa Aliyu shi tun da ba mutumin kirki ne ba.A nan mafita biyu muka samu muddin Yaya Aliyu yayi dakonsa to ke ce da hannunki za ki caka masa wuƙa a zuciya su mutu su duka biyun,mafita ta biyu mai rauni ce in mun yi nasara saka ruhin a gangar jikin yaya Aliyu zai iya yiyuwa ya boɗare ya fi ƙarfinmu kuma,kuma dai ba zai yiyu ma ya iya mutuwa ba.Dole na ɗauki kasadar dai ta na mutu tare da shi,kamar yadda ki ga komai ya faru"

"Amma lokacin da numfashinka ya fita gangar jikinka me ka ji?" na tambaye shi wannan karon ina mai ɗale cinyarsa.

Sama yayi da rigar jikina yana shafar fatata kamar mai yi mini susa,kafin ya ce "wata duniya ce na tsinci kaina mai abubuwan ban mamaki,a cikinta na hango duk wasu mutane waɗanda tun ina yaro ake zarginsu da maita,haka ma matsafa daga cikinsu.Sannan abin da zai baki mamaki bayan tawagar Kaka Maitama da Nalado akwai wasu keɓaɓun jarumai da suka zo tarbena suna murna tare kuma da bani labarinsu.Daga ciki dai akwai wani Mahadi ya ce shi ne jarumin nan wanda ake yi wa laƙabi da KABEWAR KAN KABARI,sai wata sarauniya wacce ta kasance shugabar masu MAITAR IDO ita muna da alaƙa da ita ta jini " na ɗan turo baki na ce "kenan kallon mata ka yi?"

Yayi dariya tare da kamo leɓena na ƙasa ya ɗan ciza kafin ya ce "dayawan jaruman fa mata sun fi yawa,a can ɗin ma sai da wasu ɗaliban MAKARANTAR MATSAFA suka so kawo mini caffa amma gimbiya Ayodele ta yi saurin taimakawa esprit ɗina ya koma can cikin MUTUWARE sai numfashina ya dawo"

Na ja ajiyar zuciya na ce "ko ka san da ina sonka sosai?"

Tamkar ya suma haka ya tsaya cak da numfashi,kafin ya lumshe ido yana wani ajiyar zuciya.Fuskarsa na tallabe da dukkan tafukan hannuwana na ci gaba da cewa "ina sonka sosai MAHEER! Tun ranar farko da na soma ɗora idona a kanka na ji a raina kaina makullin sirrina"

"H.lat kar fa ki haukata ni da daɗin kalamanki" MAHEER ya faɗa yana jan numfashi tare da ida cire mini rigar duka ya yar.Da sauri na manna ƙirjina da nasa don ko bra ban saka ba,karon farko da tun da muka zama abu ɗaya na ji mahaukaciyar kunyarsa.So yake ya ciro ni amma na ƙi yarda na laƙanƙame masa kamar cingam,murya na ɗan rawa ya ce "please H.lat!"

Kaina na soma jujuyawa a ƙirjinsa ,kafin cike da dubara na cire maɓallan rigarsa.Cike da tsokana na mayar da muryata ta yara na ce "a yi feeding ɗina" sai na ɗora bakina a ƙirjinsa ina wawura kamar yadda yara ke yi.

Kusan suma MAHEER yayi,ya zame mini kamar mahaukaci ya soma yi mini wasu salon da suka sa sai da muka zube kan capet. Sai da ya gajiyar da ni sosai kafin ya yi mana wanka,tsabar iya yi irin nasa kuma ya hana mu saka kaya wai a haka za mu kwanta luluɓa kawai muka yi.

Shiru kawai na yi ina tunanin abubuwa dayawa da suka shuɗe,ina son sanin halin da Hassana take ciki a yanzu da kuma ahalin gidan namu .Ina lumshe ido kuwa na hango ruhin Hussaina tana sakar mini murmushi kafin ta ɓace ,cike da nutsuwa na yi bacci.

Duk yadda na gaji ɗin kuma bai hana ni yin sallah kan lokaci ba har ma na shiga kitchen na yi abubuwan da zan yi,duk da dai yanayin Aliya duk yasa na ji wani iri. Sai da na koma sama na yi wanka sannan na sauko a karo na biyu,Hajiya na je na gaida ta amsa cikin sakin fuska kafin ta ce "ina Maheer?"

"Ya fita tun da safe" na bata amsa. "Ƙila yana can wurin Innarki kin san jiya can babban gida suka wuce da ita,ke ma ki shirya zuwa maraice sai mu je lokacin Aliya ta dawo "

Readers Also Read