Kenza eBookz

Barrister ibrahim khalil complete - Chapter 17

Barrister ibrahim khalil complete - Chapter 17

Barrister ibrahim khalil complete Chapter 17: Barrister ibrahim khalil complete Chapter 17. Girgiza kanta Saleema tayi itama idanun ta akanta, sai kuma…

4,482 words

Girgiza kanta Saleema tayi itama idanun ta akanta, sai kuma tace "amma dagaske zaki zo ɗin gobe?"

Cike da son riƙe dariyan ta dake son kufce wa tace "sosai ma sister gobe zan dawo shiyasa zan tafi yau da wuri".

Gyaɗa kanta tayi sannan tamiƙe tana cire Hijabin ta tace "to shikenan na yarda ki tafi amma goben ki zo da wuri".

Halwa bata iya bata amsa ba saboda dariya da yacika cikin ta sosai ƙiris yarage tasaki dariyan, ɗaga mata kai tayi tana sauke kanta ƙasa tasoma dariyan ta yanda baza ta ganta ba

Saleema kuwa kan gado tanufa batare da ta kula da ita ba, sai zayyano mata saƙon gaisuwa da zata kai ma su Ummi da Abba take yi

Ɗago da kanta Halwa tayi tajuyo gaba ɗaya tana kallon Saleema cike da murmushin da yabayyana haƙoran ta tace "amma fa na kira drever wayan sa be shiga ba kuma gashi ban fito da kuɗi ba".

Saleema tace "to nima ai bani da kuɗi gaskiya, amma bari in duba ko Yaya Barrister ya dawo sai ince yayi ma Drever magana yakai ki".

Gyaɗa kanta kawai Halwa tayi

Ita kuma tatashi tafita tashiga ɗakin Khalil

Yana tsaye ne agaban mirror ya sauya kayan jikin sa zuwa ƙananan kaya, yana fece suman sa da Cumb tashigo

Takowa tayi tazo inda yake tana kallon sa cike da ƙauna, sosai yayi mata mugun kyau har ta manta abinda yashigo da ita ta shagala wajen kallon sa

Ajiye cumb ɗin yayi yajuyo yana kallon ta, tayi saurin duƙar da kanta cike da kunyan kamata da yayi tana kallon sa

Be ce komi ba yamatsa gaban gadon sa yaɗau Wrest watch ɗin sa yana ɗaurawa a tsintsiyan hannun sa

"Uhm dama Halwa ce zata tafi gida shine nace ko zakayi ma drever magana yakai ta?". Tayi maganar a hankali tana kallon sa

Tsayar da abinda yake yi yayi yana juyowa yakalle ta, ganin sun haɗa idanu sai yagyaɗa mata kansa tare da ci gaba da ɗaure Wrest watch ɗin

Murmushi tayi tajuya zata fice, har ta kai bakin ƙofa tajiyo muryan sa

"Tafito sai in sauke ta".

Kallon sa tayi shi kuma yaɗauke kai yana takawa yanufi wajen takalman sa

Cikin sanyin murya ta'amsa mishi sannan tafice. [11/11/2020, 7:49 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

*\F.W.A📚/*

```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*BOOK TWO*

.

_______________________________

*CHAPTER Two*

________🎓Da murmushi a face ɗin ta tashigo cikin ɗakin, tana kallon Halwa wacce itama tazuba mata nata idanun tace

"Sis ki shirya Yaya Barrister zai kai ki".

Halwa wani kallo tayi mata sai dai batace komi ba tamiƙe taɗauki Veil ɗin ta tayi Rolling ɗin sa akanta, sai taɗau HangBag ɗinta tarataya, wayan ta a hannun ta suka fito tare da Saleeman, waje suka fice a tunanin su zasu ganshi sai dai babu shi be fito ba, a compound ɗin gidan suka tsaya suna taɓa hira har sanda sassanyan turaren sa yakawo ma hancin su cafka

Saleema kallon kyakykyawar Mijin nata tayi cike da tsananin ƙaunar sa

Ita kuwa Halwa tunda tayi masa kallo ɗaya taɗauke kanta

Zuwa yayi yawuce su yanufi wajen Farar motan sa yabuɗe yashiga

Su ma takowa sukayi har wajen motan, Saleema tabuɗe mata ƙofan tashiga tarufe mata

Tana nan tsaye har suka fice a gidan kafin taja numfashi ahankali takoma cikin gidan

Shiru cikin motan babu me motsin kirki ahaka sukai ta tafiya

Halwa ma duƙar da kanta tayi ƙasa tana faman juya wayan ta

Yayinda Khalil yake tuƙi amma hankalin sa gaba ɗaya yana kanta, so yake yi yacire duk wani abu dake cikin ransa a game da ita tunda yasan ita ɗin mallakin wani ne

Tafiya suke yi sosai babu me magana cikin su

"Ina ne gidan naki?"

Tatsinkayi sassanyan muryan sa me tsananin daɗi a kunnen me sauraro, ɗago kai tayi takalle sa kamar me tunani sai kuma taɗauke kanta tana faman maimaita maganar nasa aranta har sanda tafahimta sannan tabashi amsa

"Sabon layi".

Kallon ta yayi kamar zai yi magana sai kuma yafasa, ya san cewa Sabon Layi ne gidan su Saleema, to amma taya ita zatace masa anan take? Sai kuma yayi tunanin maybe itama a anguwan take aure

Be sake magana ba har sanda yashigo cikin anguwan, yana jiran yaji ta nuna masa hanya ko wani gidan but shiru hakan yasaka yaci gaba da tafiya batare da ya sake tambayan ta ba

Sai da aka kawo dai-dai gidan su Saleema taga yana shirin wuce wa, takalle sa tace "Nan ne fa".

Tsai da motan yayi kafin yayi Rivers yakoma baya yadanna horn me gadi yaleƙo sannan yabuɗe musu, tura hancin motan yayi cikin gidan sannan yayi parcking

Tana ganin ya tsaya tabuɗe motan sannan taɗan juyo takalle sa suka haɗa idanu tayi saurin janye nata cike da tsananin faɗuwar gaba

"Na gode". Tafaɗa ahankali kafin tafice dasauri tarufe masa ƙofan tatafi

Har tashige yana kallon ta cike da mamaki aransa, yana da tarin tambayayo aran sa sai dai be san wanene zai amsa masa ba

Yasan da cewa Saleema ita kaɗai iyayen ta suka haifa bare yayi tunanin ƴar uwanta ce, sannan ma basu kama ko kaɗan, sai dai yana tunanin ko dangin ta ne

Motan sa yaja yabar gidan yanufi inda zai je.

*____________________*

Sallama tayi tashigo gidan agajiye

Umma ta'amsa mata tana kallon ta

Zuwa tayi tazauna akan tabarman da Umman take zaune

"Kin dawo?"

Gyaɗa mata kanta tayi tana me zame jakan ta kafin tace "sannu da gida Umma".

"Yauwa Zainab da alamun dai yau kinsha wahala tunda naga kina langaɓewar nan?"

Zainab tace "uhm umma ai ba'a magana, wahala kam akwai ta, ko abinci yau ban iya ci ba tun safen nan wlh lectures yayi zafi".

Sake kallon ta dakyau Umma tayi tace "sai kika zauna haka babu abinda kika ci? To ai dama Dole kisha wahala, ki tashi kije ɗakina ki ɗauko abincin ki".

Miƙewa Zainab tayi don dama sosai cikin nata yake ƙwaƙulan ta, shiga ɗakin tayi taɗauko abincin tafito tazauna inda tatashi

Tana ci suna hira kuma duk na hiran makarantan ne

"Ni wlh dama zaki haƙura da karatun nan haka nan abu yaƙi ci yaƙi cinye wa, memakon ki samu miji kiyi aure sai ƙara karatun ma kike yi shi kuma ba me ƙare wa ba".

Kumburo fuska Zainab tayi tace "Umma kema kinsan karatu nake so a yanzu, ban tashi yin aure ba shiyasa ma bana kula kowa a yanzu ɗin".

"To wa yace miki karatu na hana aure ne? Tunda gashi kin soma ai abu me sauƙi ne Mijin naki yabar ki kici gaba, shiyasa wlh nake miki sha'awar auren Nura tunda shi yayi karatun kuma bana da haufi akan zai barki kiyi karatun ki".

Tashi Zainab tayi tsam bayan da Umman nata tagama zayyano maganan, batace komi ba tashige ɗakin ta tafaɗa kan gado

Umma kuwa da tabi ta da kallo baki sake tayi ƙwafa tana faɗin "wawiya kawai wacce batasan me yake mata ciwo ba".

Lumshe idanun ta Zainab tayi wasu hawaye masu zafi suka sauko mata a kunci

Ta rasa meyasaka Umman ta take magana akan Nura, meyasa Ummanta take son auren ta da Nura, taƙi tagane cewa ita baza ta iya auren sa ba, baza ta taɓa auren saurayin da Halwa take mutuwar son sa ba koda kuwa ita tana son shi".

Hannu tasaka tana share hawayen ta tare da yin matashi da duk ka hannayen ta

Tana jin sanda Abban ta yashigo Umma take ta rattabo masa bayani, har da faɗin "wlh Malam tun wuri ayi wa tufkan hanci idan har ba so kake yi Zainab ta tsofe agida babu mashinshini ba, ga yaro son kowa ya fito yana son ta amma ita ƙiri-ƙiri ta shafe wa idanun ta toka taƙi shi akan dalilin ta na banza dana hofi, to Ni gaskiya bazan iya zuba idanu har sai sanda tagama wannan ƙaddararren makarantan ba, kawai kace ma Nura yaturo idan yaso sai taƙarisa can agidan sa yafi".

Murmushi Abba yayi yace "Jummai Ni wannan cece kucen da kike yi banga amfanin sa ba, tunda yarinyan nan ta nuna bata son yaron nan menene na son sai ta aure shi? Duk a ƴaƴana babu wacce nayi mata auren dole bare kuma kan Autana, kibari idan har sun dai-dai ta kansu falillahil hamdu amma Ni bazan mata auren dole ba".

Shiru Umma tayi tana gyaɗa kanta cike da takaici, ba wai don tarasa abun faɗa bane sai dai don haushin Abban da yake goya wa Zainab baya, idan da ya amince ita ana ta da tuni anyi an gama, in taje can sai su daidai ta.

Miƙe wa Abba yayi be sake cewa komi ba yaɗau buta yashiga bayi don taɗauro alwalan magariba da har an soma kira

Ita kuwa Zainab sanyi taji cikin ranta ko banza tasan Abba bazai bari ayi mata aure ba sai da yardan ta, kuma idan har itace zata amince da Nura kafin ayi musu aure to baza ta taɓa amincewa ba har abada..

*______________________*

Turo ƙofan tayi tashigo da sallama a bakin ta

Khalil dake zaune gefen gadon sa yana faman aiki acikin Lapton yaɗago yayi mata kallo ɗaya sannan yamayar da kansa yana amsa mata sallaman

Takowa tayi zuwa wajen gadon tashimfiɗa Husna akai sannan itama tazauna tana kallon sa

Shima alokacin yasake ɗago kansa yakalle ta sannan yamaida idanun sa kan Husna, tsawon sokonni biyar yana faman kallon ta kafin yace

"Wai ina Mahaifin yarinyan nan?". Yaƙarike maganar yana aza idanun sa kan Saleema

Shiru tayi tana sad da kanta ƙasa, ba ta jin zata iya sanar masa haƙiƙanin gaskiya kuma bata san me zata ce masa ba a yanzu

Ci gaba da danna Lapton ɗin sa yayi be sake ce mata komi ba, sai can kamar mintuna biyar yasake jeho mata tambayan

"Ina Mahaifin yarinyan nan nace?"

Yanda yayi maganar ne a kausashe yasa hantan cikin ta ya yamutse, batasan sanda bakin ta yafurta "sun rabu ba".

Cakk yatsaya da abinda yake yi yajuyo yana kallon ta

Itama ɗin shi take kallo cike da tunanin meyasaka yake son sanin Mahaifin Husnan bayan ada be taɓa tambayan ta ba?

Kau da kansa yayi yaci gaba da aikin sa

Ita kuma ajiyan zuciya tasauke sannan tagyara takwanta tana tunani aranta

"Shin meyasa nake son kawo zargi ne acikin auren mu? Meyasa zuciyata take son kawo min abinda zai hargitsa min rayuwa? Shin menene abun zargi anan?"

Kwanciyar ta tagyara tana kallon sa, ahankali kuma tafurta "Allah na tuba Allah ka cire min zargi araina".

Aikin yake yi amma maganar Saleema ke kai kawo cikin ransa, duk da yaji sanyi ta wani gefe nasa amma kuma yasan cewa mafarkin sa bazai taɓa zama gaske ba

A haƙiƙanin gaskiya zuciyar sa ta kamu da ƙaunar Halwa tun ranan farko da yaganta, amma taya zai iya mallakan ta bayan ita ɗin ƴar uwa ce ga matar sa?

Har Saleema tayi barci yana nan zaune yana latsa Lapton ɗin sa duk da kuwa tunani ne cinkushe aran sa wanda yahana sa jindaɗin aikin

Daga ƙarshe ma tashi yayi yashige toilet yaɗauro alwala, fitowa yayi yazauna a bakin gadon yana kallon Saleema dake maƙale da Husna, sosai yake mamakin yanda take ƙaunar yarinyan

Ya jima a zaune awajen yana kallon su, amma azahiri tunani ne aransa wanda har yasoma haddasa masa ciwon kai

Kwanciya yayi yaci gaba da tunanin, yafi mintuna 20 kafin yamiƙe yatashi yasoma jero nafilfilu ganin hakan shine kaɗai mafita a gare shi, domin ko kaɗan ayau ɗin baya jin barci zai iya ɗaukar sa.

.

*Plz Share and Vote*

_More Comments more typing._ [11/13/2020, 11:10 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎓 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

*\F.W.A📚/*

```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*BOOK TWO*

.

_______________________________

*CHAPTER Three*

________🎓Washe gari ƙarfe 07:30am. *BRR. IBRAHIM KHALIL* yagama Shirin sa na zuwa office

Yau yayi shiga na Red colour suit, sai na cikin kuma whiter ne, necktie ɗin sa da Belt ɗin wandon sa baƙi ne, yayi kyau sosai sai tashin ƙamshi yake yi, sosai kwarjinin sa da cikan halittansa suka sake fitowa ainun

Be tsaya yayi breakfast ba duk da kuwa Saleema tuni tatashi tayi masa, haka yafice sabida yana sauri

Aiki sosai yake dashi a office, gashi kuma zasu je wani waje shi da Brr. Tahir

Sai wajen 12:00pm. Yagama sannan suka tafi.

Ƙarfe :2:30pm. Suka gama yanufi gidan su

Yana yin horn me gadi yazo yabuɗe masa, shiga yayi da motar ciki yayi parcking yafito yarufe murfin motan yashiga gidan

Mom na zaune a parlour tana cin Fruits tana kallon tashan African t.v ana wa'azi tajiyo sallaman sa

Fara'a tasaki tana amsa masa sallaman kafin taɗau Remote tarage t.v n

Ahankali yatako cike da gajiya yazauna gefen ta sannan yagaishe ta

Murmushi tayi tana shafa kansa ta'amsa masa tana tambayan Saleema

Sai da yayi releasing akan kujeran kafin yabata amsa da "lafiyan ta ƙalau Mom".

"Masha Allah haka ake so".

Sai da tagutsira 🍌 Bananan hannun ta kafin takalle sa tace "ko asawo maka abinci?".

Gyaɗa kansa kawai yayi yana jan numfashi

Mom har ta buɗe baki da ninyan kiran ƴar aikin ta sai ga Nazeefa ta fito daga ɗakin ta riƙe da plate a hannun ta

"Yauwa Nazeefa sawo ma Yayan ki abinci".

Nazeefa da idanun ta ke kan Khalil ta'amsa mata da "Toh". Sannan tagaishe da Khalil ɗin

Idanun sa shima akanta ya'amsa mata

Kichen ɗin tanufa zuciyarta cike da ƙaunar sa, sosai yau ɗin yasake mata kyau fiye da ko yaushe, domin ta ɗan jima rabon da tagan shi, ko da yazo gidan ita tana makaranta a lokacin

Fitowa tayi riƙe da plate da spoon aciki, taƙariso ta'ajiye masa kan Centre table bayan ta ɗan matso masa dashi, zuwa tayi tazauna can kujeran dake Facing nashi taduƙar da kanta tana satar kallon sa

Shi kuwa abincin sa yaɗauka yana ci yana sauraron hiran Mom da take yi masa akan Yayan nasa Sameer

Ko kaɗan bata gajiya da kallon sa, da ace zata kwana tana kallon sa to baza ta taɓa gajiya ba, a kullum ƙaunar sa sake wanzuwa yake yi a zuciyar ta, ta rasa yanda zatayi tacire sa aranta, bata da damuwa a ko yaushe sai nasa, burin ta kullum tasami hanyar da zata mallake sa duk da tana ganin abu ne me wahala ta same sa, amma baza ta cire rai ba da ikon Allah sai Allah ya mallaka mata shi, koda kuwa zata kasance matar sa ta huɗu ne to zata zauna dashi in dai zai aure ta..

"Nazeefa lafiyan ki ƙalau kuwa tunanin me kike yi?"

Maganar Mom yadawo da ita hayyacin ta, dasauri taɗago kanta tana kallon su

Mom ce kaɗai idanun ta ke kanta, yayinda shi kuma yake cin abincin sa hankalin sa kwance

Cikin daburce wa tace "Mom ban ji bane".

"Yayan ki ne ke magana".

Nazeefa sauke idanun ta kansa tayi tace "Yaya me kace?"

Sai alokacin yaɗago fararen idanun sa yana kallon ta, hararan ta yayi yace "ban sani ba".

Bata san sanda tayi murmushi ba sabida yanda yayi maganar har hararan sai kace wani mace

Mom ma sai da tamurmusa don itama taga sanda yayi hararan, cikin murmushin tace "ayi mata afuwa mana Auta wannan harara haka?".

Ajiye abincin yayi yana kallon Nazeefan da tasauke nata idanun ƙasa yace "meyasa baki taɓa zuwa gidana ba?"

Hannun ta tamatse waje ɗaya cike da fargaba taɗago kanta tana kallon sa tace "Yaya makaranta ne yahana Ni zuwa".

Hararan yasake aika mata dashi cikin ɗaure fuska yace "makarantan ne zai hana ki zuwa gidana?"

Mom tace "ai nima nayi godo da ita taje amma taƙi zuwa wlh, Ni bansan meke damun Nazeefa ba yanzu, ko ranan Saturday ɗin nan sai da nasake yin mata magana".

Nazeefa sad da kanta ƙasa tayi kamar zatayi kuka, ko kaɗan bata son zuwa gidan Yayan nata ba don komi ba sai don kishi, baza ta iya juran ganin sa da wata ba idan har ba ita ba

"Je ki shirya kizo mu tafi, ki haɗo da kayan makarantan ki don kwana zakiyi, idan kin wuce makaranta kya dawo nan".

Tashi tayi batare da tace uffan ba tanufi ɗakin ta, tana shiga tacire riga da skert ɗin jikin ta tasaka dogowar riga baƙi da yasha stone masu ƙyalƙyali, sosai take son dogoyen riguna shiyasa ma Mom Ko da ɗinki zata bada ayi mata, dogayen riguna take saka wa ayi mata, tunda ko anyi mata sauran ɗinkunan bata saka wa sai taga dama

Ɗan ƙaramin jaka taɗauka tasaka kayan makarantan ta sannan taɗau school bag ɗin ta tafito

Ko kaɗan bata murna da zuwa gidan Yayan nata, sai dai sauƙin ta ɗaya zata riƙa ganin sa yanzu

Tana fitowa Khalil miƙe wa yayi sukai sallama da Mom sannan yayi gaba Nazeefa tabiyo bayan sa bayan itama tayi ma Mom ɗin sallaman.

*_____________________*

A mota babu me magana cikin su, tun sanda yatambaye ta karatun ta be sake magana ba, hankalin sa na ga titi har suka iso gidan

Bayan yayi horn me gadi yabuɗe masa yasaka motan ciki, yana parcking suka fito atare, yana gaba tana bin sa a baya sai bin gidan take yi da kallo, komi an sauya ba kamar sanda tataɓa zuwa ba

Suna shiga babu kowa sai Husna dake wasa a ƙasa

Wajen ta Khalil yawuce yaɗauke ta yana saɓa ta sama yana mata wasa

Sai Nazeefa tasaki baki kawai tana kallon su

Sai shine da yajuyo yaganta har yanzu a tsaye yace "tsayuwar me kike yi kuma?"

Sai alokacin tadawo duniyar tunanin ta tasamu wuri tazauna

Shi kuma yawuce ɗakin Saleema da Husna a saɓe a wuyan sa

Yana tura ƙofan da sallama yahange ta zaune kan stool tana shafa Lipstick a bakin ta, tayi shiga cikin riga da skert na ɗan kanti, farar riga me gajeren hannu sai jan skert me ɗan faɗi tare da tsagi ta baya, kayan sun yi mata kyau gashi kuma sun ɗauki white skin ɗin ta, kanta da ɗan siririn ɗan kwali da taɗaura be gama rufe mata tsakiyar kai ba

Amsa sallaman tayi tana juyowa takalle su

Sosai tayi masa kyau yatako wajen yana kallon ta batare da yace komi ba

Sannu da zuwa tayi masa tana murmusawa

Ya'amsa mata still yana kallon ta kafin yace "kin yi kyau matata".

Rufe fuskarta da tafin hannayen ta tayi tana ɗan sakin dariya me sauti kafin tace "Nagode Mijina".

Shima sai yayi dariyan yana sauko Husna yariƙe ta sosai a hannun sa sannan yace "ga ƙanwata nan nazo da ita zata kwana gobe zata tafi".

Miƙe wa tayi ta'amsa mishi da "Toh". Tanufi ƙofa, shima yabi bayan ta

Suna fitowa idanun ta yahaɗe dana Nazeefa, har yanzu dai bata san wacece ita agare su ba duk da kuwa tasan ba ƙanwar Khalil ɗin bane, amma ta danganta hakan da ƙila ƴar uwansa ce

Zuwa tayi da fara'an ta tazauna

Ita kuma Nazeefa ganin Khalil shima yazo ya zauna ne tasaki fuskarta itama sannan tagaishe ta

Saleema ta'amsa mata tana murmusawa sannan tatambaye ta Mom? Ita kuma tabata amsa "tana nan lafiya tace agaishe ki".

"Yaya ko in kawo maka abincin nan ne?" Saleema tayi maganar tana kallon Khalil da yatasa Husna gaba yana faman mata wasa

Girgiza mata kai yayi batare da ya kalle ta ba yace "no sai nayi wanka zuwa anjima zanci".

Sannan yamiƙe tare da Husnan yanufi ɗakin sa

"Ƙanwata taso muje kici abinci". Saleema tafaɗa tana kallon Nazeefa da tabi bayan Khalil da kallo

Murmushi taƙirƙiro tana kallon Saleeman tace "a'a Aunty Alhmadulillah sai da naci abinci kafin na taho".

"Haba dai ko ɗan ruwa ne ai kya sha, bari in kawo miki".

Tashi tayi tanufi wajen Fridge

Nazeefa taraka ta da kallo, sosai take mamakin yarinyan da tagani don bata da masaniyar zaman ta agidan, har Mom ma itama sai daga baya tasani, sai kuma tataɓe baki aranta tace "to Ni ina ruwana".

Saleeman tadawo riƙe da Drinks da taɗauro saman plate ta'ajiye Mata a gaban ta kan Centre table sannan takoma tazauna tana faɗin "bismillah".

Babu musu Nazeefa taɗauka Robbern Fanta tabuɗe tazuba cikin glass cup ɗin da tahaɗo mata dashi, tana sha suna kallo batare da ɗayan su ya sake magana ba tunda babu sabo ko kaɗan a tsakanin su

Suna nan zaune har Khalil yafito, da alamun yayi wanka ne don ya sauya kayan sa cikin shiga na ƙananan kaya wanda sukai ma jikin sa kyau sosai

Duk kansu kallon sa suke yi cike da tsantsan ƙauna

Shima dai kallon su yayi sai ya'aza idanun sa kan Saleema yaɗan ɗage mata gira ɗaya yace "My dear na wuce masallaci, ga ƴar ki can tana barci".

Murmushi Saleema tayi tace "to adawo lafiya".

Gyaɗa kansa yayi yanufi ƙofa yafice

"Ƙanwata muje in Kai ki ɗaki".

Maganar Saleema yakatse mata tunani, cikin son kawar da abunda yatokare mata maƙoshi tamiƙe da jakanta tabi bayan ta

Ɗakin ta takai ta sannan tafito tanufi ɗakin Khalil, anan ita tayi sallan ta kafin tadawo parlour

Alokacin shima Khalil ya dawo har ya zauna saman dainnig yana latsa wayan sa

Wajen tanufa tasoma saving ɗin sa sannan tajuya zata tafi

"Ke kinci abincin ne?"

Juyowa tayi tana kallon sa sannan tagyaɗa masa kanta tana murmusawa

Be ce komi ba yaɗau spoon ɗin yasoma cin abincin sa

Nazeefa tunda tagama Sallah tazauna nan kan sallayan taƙi tashi, sai ma zuba tagumi da tayi ta'af ka tunani

Bata sake fitowa ba har dare

Koda Saleema tashigo tayi mata maganar tafito Parlour ko zata fi jindaɗi, sai tace "a'a nan yayi mata".

Juyawa tayi kawai tabarta takoma parlour taci gaba da kallon ta don shi tuni Khalil ya shige ɗakin sa yana faman aiki a Library ɗin sa

Daga karshe da tagaji da zaman sai tanufi kichen tayi musu girki me sauƙi, taliya tadafa da raguwar miyan ta na jiya

Sai da tagama komi taje tajera a dainning table, lokacin har an kira sallan magriba

Ɗakin Khalil ɗin tanufa tashiga ciki, alokacin ya fito daga Toilet bayan ya ɗauro alwala, kallon ta kawai yayi yafice dasauri

Ita kuma tanufi kan gadon inda Husna ke kwance tarigada ta farka tana ƙananun kukan ta, ɗaukan ta tayi tanufi ɗakin ta da ita

Shiga tayi da sallama a bakin ta, kallon Nazeefa dake sallah tayi tawuce cikin Toilet

Kayan Husna tacire tawanke mata kashin da tayi sannan tayi mata wanka tafito taɗaura ta kan gado, sai takoma taɗauro alwala tadawo tagabatar da Sallah

Nazeefa na zaune akan kujera tana faman kallon Husna dake ta mutsil-mutsil cikin towel da aka nannaɗe ta dashi tana son cire wa tasauko

Har Saleema ta'idar da sallan ta tamiƙe tasoma shirya Husnan, ta kula Nazeefa ba me son yin magana bane shiyasa itama taƙyale ta batare da ta kula ta ba, amma abinda yadace tana tambayan ta

Har tagama abinda zatayi tafito Parlour tazauna tana ma Husna wasa tana kallo

Sai bayan isha'i sannan Khalil yadawo gidan

Suna zaune kan dainning shi ya ɗaura Husna ajikin sa yana cin abinci yakalli Saleema da itama take saving nata yace

"Ina Nazeefa ne?"

"Tana ɗaki tana sallah nayi mata magana yanzu zata fito.."

Bata rufe baki ba nazeefan tafito taƙariso wajen tana gaishe da Yayan nata

Amsa wa kawai yayi yaci gaba da cin abincin sa

Itama zama tayi tayi saving kanta tasoma ci, can kuma taɗago kanta tana kallon sa yanda duk yabada hankalin sa kan Husna ko abincin ma baya ci sosai

"Yaya wai wannan yarinyan wacece?" Tayi tambayar tana ci gaba da kallon sa

Daga shi har Saleema suka ɗago kansu suna kallon ta

Sai da yakau da kansa gare ta kafin yace "Ƴata ce".

Bata sake cewa komi ba taci gaba da cin abincin ta sai dai zuciyarta haushin amsar da yabata take ji

Ita kuwa Saleema murmushi kawai tayi tana kallon Khalil ɗin cike da ƙaunar sa, sannan taci gaba da cin abincin ta

Shi yasoma tashi yanufi ɗaki

Kamar ana tsikarar Nazeefa tana ganin ya shige itama tamiƙe tanufi parlour

Saleema dai bata ce mata komai ba illa kallo ɗaya da tayi mata taɗauke kanta, sai da tagama tattara komi takai kichen sannan tanufi ɗakin ta

Wanka tayi tasanya kayan barci sannan taɗau abubuwan da zata buƙata tare dana Husna tafito tana kallon Nazeefa dake zaune tana kallo

"Ƙanwata koda akwai abinda kike buƙata ne?"

Sai alokacin Nazeefa taganta ma, kallon ta kawai take yi cike da tsananin kishi, tasan tunda tagan ta da shiri ɗakin Khalil zata tafi

"Kenan ko hiran daren ma basuyi sai su shige ɗaki?" Tatambayi kanta tana ci gaba da kallon Saleeman cike da tsantsan haushin ta

Ita kuma Saleema ganin tayi shiru sai tabuɗe ɗakin Khalil kawai tashige abunta aranta tana jinjina wulaƙacin yarinyan, ko ba komi ai ita Matar YaYanta ne bare ma ta girme mata sosai don aƙalla zata bata shekaru uku ƙwarara

Tana ganin ta shige itama tatashi tanufi ɗakin Saleeman zuciyarta kamar zata tarwatse, har wani ɗaci-ɗaci take ji a maƙoshin ta.

Sai Khalil ne daga baya yafito yakashe t.v n yakulle ƙofan Parlourn yakoma ɗaki.

Washe gari ƙarfe 07:20am. Ya riga ya gama shirin sa har breakfast yayi sannan yafita

Lokacin itama Nazeefa tafito da shirin ta na makaranta tana rataye da school Bag ɗin ta tare da jakan da tasaka kayan da tacire, fuskarta duk babu walwala idanunta sunyi luhu-luhu kamar wacce bata samu ishashshen barci ba

Saleema dake kakkaɓe parlour'n taɗago tana kallon ta da murmushi a face ɗin ta tace "Ƙanwata har kin fito?"

Itama Nazeefan murmushin tayafa ma fuskarta sannan tace "eh Aunty Ina kwana?"

"Lafiya lau kin tashi lafiya? Ya baƙunta?" Saleema tasake yin maganar da fara'a

"Alhmadulillah".

"Ok ga breakfast ɗin ki kizo kici".

Nazeefa tace "a'a bazan iya cin komi ba, zan tafi Aunty sai kuma wataran in na sake dawowa ki gaida yaya".

Saleema kallon ta kawai take yi cike da mamakin ta, sai kuma dai batace komi ba ta'amsa mata sannan tabata saƙon gaisuwa wajen Mom

Tana kallo Nazeefan har tafice sannan taci gaba da aikin ta

Drever yaɗauki Nazeefa yanufi da ita school ɗin su. [11/16/2020, 6:56 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

*\F.W.A📚/*

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull