Barrister ibrahim khalil complete - Chapter 2
Barrister ibrahim khalil complete Chapter 2: Barrister ibrahim khalil complete Chapter 2. Cire black Combat ɗin dake ƙafan sa yayi yasamu waje yazauna yana…
4,493 words
Cire black Combat ɗin dake ƙafan sa yayi yasamu waje yazauna yana faɗin
"Ina yini Baaba?"
"Lafiya lau Ibarahima, yagida ya aiki? Da fatan kowa dai yana lafiya ko?"
"Alhamdulillah Baaba".
"Ai jiya naji ka shiru bakazo ba, ince dai lafiya?"
Ɗan gajeren murmushi yasaki yace
"Lafiya lau Baaba, ban samu daman zuwa bane shiyasa, da fatan babu wata matsala baku nemi wani abu ba?"
"A'a wlh Alhamdulillah, Nazeefa ce dai ma tafarka ajiyan take neman ka, kuma daga baya sai barci yaɗauke ta, koda tafarka kuma yau bata tambaye ka ba ko magana ma batayi ba".
Ajiyan zuciya yaɗan saki kana yace
"Ina ga yau zan tafi da ita, Nagode sosai da taimakon ki Allah yasaka, ga wanna babu yawa".
"Ikon Allah bawan Allah baka gajiya? To Nagode Allah yasaka, ai babu komi yiwa kai ne, ita kuma Allah yabata lafiya".
"Ameen". Ya'amsa ataƙaice yana miƙewa
Itama tashi tayi tana faɗin
"Shiga tana ciki ai".
Be ce komi ba yashiga, yarinya ce da bazata gaza 16yrs ba a kwance akan katifa, fara ce sol sai dai shatin kwarmin idanunta yaɗan yi baƙi-baƙi kaɗan, barci take yi hankalinta kwance, ahankali yamatsa kusa da ita yasanya hannayen sa yaɗauke ta cak ajikinsa yafito, har waje Baaba Talatu tarako shi tana ta saka mishi albarka tare da godiya ga ɗawainiyan da yayi mata
A back sit yakwantar da ita kana yashiga yaja motan ahankali kamar yanda yasaba, shiru yayi yana nazarin abinda yakamata yayi, ta cikin mirror yake kallon ta duk da baya hango ta sosai, but jefi-jefi yakan kai idanun sa kanta.
A bakin Gate yadakata yayi hon, ba daɗewa aka wangale mishi gate ɗin yatura hancin motan ciki, a packing space yatsai da motan, sai da yaɗan yi minti 3 kafin yabuɗe motan yafito da ƙafan sa, wayoyin sa yaɗauka yashigar dashi cikin aljihu kana yafito yabuɗe bayan mota yana ƙoƙarin fito da ita, ahankali tabuɗe idanuwanta tasauke kan kyakkyawan face ɗin sa, hakan yasaka taɗan saki murmushi ahankali tace
"Yayana".
Shima murmushin yasakar mata yaɗan ja jikin sa daga ɗaukan ta da yayi ninya yace
"Nazeefa.. kin tashi?".
Gyaɗa masa kai tayi still tana murmushi
"Ok fito ahankali muje ciki, yau na dawo dake gida na, anan zamu ci gaba da zama kinji?"
Nan ma gyaɗa masa kai tayi kafin tayunƙuro tatashi tafito daga cikin motan, ahankali take kallon cikin gidan kafin tamai da idanuwanta kan sa, murmushi yasakar mata kana yariƙo hannun ta suka taka ahankali suka nufi cikin gidan, a main palow suka tsaya yanuna mata kujera yace
"Zauna anan".
Ba musu tasami waje tazauna tana ci gaba da kallon Palon don ba ƙaramin burge ta yayi ba, sosai yatafi da imanin ta, tsarin Palon da kayan cikin kan shi abun burgewa ne da sha'awa, fridge yanufa yaɗauko faro water yadawo yazauna gefen ta, miƙa mata yayi ta'amsa tana sakar masa murmushi, shi kuma wayan sa yazaro cikin aljihu yaɗan latsa yakara a kunne
"Ina kike?"
"Ok kizo palow Ina jiran ki".
3minute tafito cikin ɗakin ta, har gaban sa taƙarisa taduƙa tace
"gani Sir".
"Kikai ta ɗakin ki daga yau zakici gaba da kula da ita, zuwa anjima kiyi ma drever magana yakai ki super makert duk wani abun da take buƙata kisiyo mata".
Ita sai lokacin ne ma takalli wajen da Nazeefa take zaune, a ranta tana tunanin "to wacece ita awajen shi?"
Batakai ga ƙarisa zancen zucin nata ba taji muryan sa yana ma Nazeefa magana
"Tashi kibi ta ciki".
Babu musu tatashi, itama Lubna miƙewa tayi takama hanyan ɗakin ta Nazeefa na biye da ita abaya, da ido yabi su da kallo har suka shige kafin yasauke ajiyan zuciya, tashi yayi yanufi cikin ɗakin sa, wanka yayi yasauya kaya cikin ƙaraman t.shirt fara da yellow ɗin Three qweater, yafito palow yanufi saman dainnig yasami waje yazauna, tea cup yahaɗa yafara sipping yana latsa wayan sa, tsawon mintuna ashirin yaɗauka awajen kafin yamiƙe yanufi cikin ɗakinsa, be fito ba sai da aka kira sallan magriba kafin yaɗauro alwala yasanya jallabiya fara sol yafito yanufi masjid, sai da aka yi isha'i kafin yadawo, yana shigowa yatarda Nazeefa zaune saman kujera ta ƙudundune jikinta tana kallo, shigowan sa yasaka taɗago kai tana kallon shi, kujeran dake gefen ta yasamu yazauna yana kallon ta
"Sannu da zuwa yaya".
Tace dashi tana gyara zaman ta dakyau
"Yauwa.. kinci abinci?"
"Eh Yaya".
"Ok."
Shiru yagibta a tsakanin su na ɗan wani lokaci kafin yaɗago da kansa daga duba wayan sa yana kallon ta yace
"Kije kikwanta dare yayi, ki kira min Lubna".
tace "to".
Tamiƙe tawuce ciki, Lubna ce tafito taƙariso kusa dashi
"Kihaɗa min Coffee".
Amsa mishi tayi kawai tawuce cikin kichen, shima tashi yayi yanufi ɗakin sa, ko 2mint be yi ba yafito riƙe da briafcase ɗin sa, yana zama itama tafito tamiƙa mishi takoma ciki, ahankali yasoma aikin sa cikin Computer yana yi yana sipping ɗin Coffee ɗin, har wajen ƙarfe 11:00pm yana nan zaune cikin Palon be gama abinda yake ba, can yaji ihu cikin ɗakin su Lubna, ɗan tsakaitawa yayi daga latsa Computern da yake yi yana kasa kunne. [8/31/2020, 8:26 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📚* ```{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*⚜{{F.W.A📚}}*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
_wannan shafin naku ne masoya Littafina, ina jin daɗin yanda kuke nuna ma Book ɗina ƙauna, thank you._ ❤️
.
*CHAPTER 5*
Tashi yayi yanufi ɗakin yabuɗe yashiga, duhu ne ako ina hakan yasaka yalaluba makunnin wutan ɗakin yakunna ko ina yagame da haske, akan ta yasauke idanun sa tana zaune saman gadon babu inda jikinta baya rawa, gefen ta yakalla yaga Nazeefa na kwance sai sharan barcin ta take yi ko motsi batayi ba, maida kyawawan idanun sa yayi akanta da itama tazuba nata cikin nashi sai ɓari take yi, ahankali kamar baya son magana yace
"Menene kike ihu cikin dare? Lafiyan ki ƙalau kuwa?"
Cikin rawan murya tace
"Mafarki nayi".
Tsare ta da idanu yayi yana nazarin ta, gaba ɗaya tsoro da firgici ne yabayyana a fuskarta, ɗan numfashi yaja sannan yace
"Wani irin mafarki ne haka da yabaki tsoro?".
Sharto gumin fuskanta tayi still cikin rawan baki tace
"Am uhm Mafarki nayi ak..akan Mamana".
"Kina son kije gida kenan?"
Yaje ho mata tambayan tare da ci gaba da faɗin
"Sai in saka drever yakai ki yanzu in kinaso".
Dasauri tagirgiza mishi kai tana faɗin
"A'a".
"Ok koma kikwanta, kitabbatar kinyi addu'a tukun".
Daga haka yajuya yafita bayan yakashe wutan ɗakin, ahankali tasulale takoma takwanta tana jin hawaye na sulalo mata a fuska, cikin raunin murya tace
"Dan Allah karku kashe min su, zan yi duk abinda kukeso".
Sai kuma tasaka hannu tashare hawayen fuskanta tana tuno fuskar sa a yanzu da yashigo, take wasu hawayen suka shiga sintiri saman fuskanta ahankali tafurta
"Ina matuƙar ƙaunar ka".
....... ....... ......... ...... Shi kuwa koda yakoma cikin Palon aikin sa yaci gaba da yi, be fi 20minutes ba yatashi yashige ɗakin sa, sai da yayi wanka yashirya cikin kayan barci farare sol yafeshe jikinsa da turare sai zuba ƙamshi yake yi kamar wanda yayi wanka dashi, kwanciya yayi yayinda fuskar sa ke kallon cilling ɗin ɗakin, yaɗaura kan sa saman dantsen hannun sa yayi matashi tare da lumshe idanun sa, ahankali yabuɗe idanunsa yana ƙure cilling ɗin ɗakin da ido, tunani yake yi cikin ransa, ya daɗe ahaka batare da yaji barci yazo mishi ba, ganin haka yasaka shi tashi yanufi Toilet yaɗauro alwala yazo yatada sallah yafara jero nafiloli, sai da yadaɗe yana Sallah kafin yasoma jin barci yatashi yahau gado yayi addu'a yarufe idanunsa, ba jimawa kuwa barci yasure sa.
.
****** ****** ******
Tsaye take a bakin titi tana jiran keke napep, tana sanye da uniform ɗin makaranta, riga da wando farare, sai ɗan ƙaramin Hijab kalan ruwan goro, sosai kayan suka yi mata kyau kuma suka ƙara fito da zallan yarintan ta da kyawun surar ta, school bag ɗin ta dake rataye a kafaɗan ta tazamo shi cike da gajiyawa, sosai ranan wajen yake dukan ta, tun ɗazu tana tsaye amma har yanzu bata sami abin hawa ba, gashi har abokan tafiyanta sun watse ita tana nan tsaye ba yau ba gobe, yatsina fuskarta tayi taɗan ɗaga face ɗin ta tana kallon ƙwallelen ranan da yasake fantsamo wa, bata kai ga sauke kanta ba taji hon ɗin mota a gefen ta, dasauri tasauke kanta taɗaura idanunta saman motan dake tsaye ɗan nesa da ita, cikin socond ɗin da be wuce 3 ba takalli motan taɗauke kanta, wanda ke cikin motan ne yafito ɗan kyakkyawan sauri ne yatunkaro inda take
"Assalamu alaikum". Yayi mata sallama yana kallon fuskarta da yake a yatsine
Bata kalle sa ba taɗan yamutsa fuska tana motsa ƙaramin bakin ta, hakan yasaka yaɗan saki murmushi yace
"Baiwar Allah da fatan dai ba laifi nayi ba da ban samu an amsa min sallama ba? Duk da nasan be dace natare ki anan ba, amma kuma babu yanda na iya ne tunda bazan iya bari kisuɓuce min ba".
Kallon sa tayi fuskanta a yatsine ga duk kan alamu hakan ya zame mata jiki ne, batace komi ba sai gyara zaman jakan ta da tayi tana kallon hanya
"Baiwar Allah ko dai ke kurma ce?" Yasake tambayan ta still yana kallon ta
Ahankali tagyaɗa masa kai tana ɗan kwaɓe fuska kamar zata yi kuka
"Ayya sorry rashin sani akace yafi dare duhu, kiyi haƙuri but ina son insan sunan ki gashi kuma ina son narage miki hanya, to ya za'ayi yanzu?"
Cikin sanyi da muryanta me daɗi tace
"Ce maka akayi ina buƙata?"
Sai kuma tayi saurin kallon sa tana ɗaura hannu abaki tare da zaro idanu waje tace
"Na manta".
Don ko kaɗan tamanta da yanzu tayi masa ƙaryan ita kurma ce, shi kuwa da yasaki baki yana kallon ta be san sanda yatuntsire da dariya ba yace
"Kai Allah Nagode maka, kinga lokaci ɗaya Allah ya kamaki, sai yasaka ki kika manta kika yi magana, Uhm babu rabon ki wahalar dani kenan, kuma banda abinki ai ƙarya be kamace ki ba, ko kadan bakiyi zubi da masu faɗan magana wanda ba dai-dai ba shiyasa na'amince dake nan take".
Murmushi kawai tayi tana jin kunya na kama ta, ba haka taso ba, taso in yagane ita kurma ce yatafi yabata waje amma kuma sai gashi asirinta ya tonu
"To yanzu dan Allah kitaimaka kifaɗamin sunan ki, kuma dan Allah karki ƙi tayina muje nasauke ki gida kinga akwai rana kar yayi miki illa, kamar ki kyakkyawa be kamata kina tsaye rana na gasa ki ba, ko ba haka ba?"
Ɗan taɓe baki tayi tace
"Ni fa bansan meyasaka kake faɗamin waɗannan kalaman ba, kuma bansan meyasaka kakeson taimako na ba, meyasa zaka damu idan rana tagasa ni? Baka tunanin nafison hakan ne shiyasaka nazaɓi tsayuwa anan ɗin?"
Murmusawa yayi yace
"Ai banga aibu ba idan har nataimake ki, kuma kinsan da cewa duk namiji idan har yaga mace ahanya yanemi yataimake ta to akwai abinda yake so wajenta ne, kuma kema kinsan da haka sai dai in bazaki faɗa ba".
"Zai fi kyau dai kasanar dani da bakinka, tunda nasan da cewa Maza kala da iri ne kuma ko wannen su da abinda ke kawo su wajen yarinya, to kai kuma bansan menene yakawo ka ba".
Ɗan numfashi yaja yana kallon ta cike da burgewa yace
"Tunda kinfi son sai nafaɗa miki dalla-dalla to shikenan, Ni sunana Yazeed tunda Ni kinyi min ruwan sunan ki, kuma abinda yatsai dani wajen ki so da ƙauna ne, tun sanda naƙyalla idanu na naganki naji zuciyata ta kamu da matsananciyan ƙaunarki, kuma wlh ba da wasa nake miki ba, ina son kibani dama Dan Allah na nuna miki irin yanda kika shiga zuciyata kika mamaye min ita acikin mintuna ƙalilan kinji dan Allah".
Ɗan gajeren murmushi tayi kana tace
"Ayya Malam Yazeed Nagode da ƙaunarka gare ni, sai dai ina tunanin ka makaro domin Ni ɗin nan da kake gani tuni na zama mallakin wanin ka, ina faɗa maka wannan maganan ne don kar nawahal da kai".
Murmushi yasaki cike da rashin yarda yace
"To shikenan amma dai kizo muje nasauke ki mana, dan Allah karkice a'a plz ƴar kyakykyawa".
Batasan sanda tasaki murmushi ba takalle sa tace
"Uhm kana son kayi min daɗin baki ko?".
"Ai gaskiya nafaɗa ƴan mata, ko makaho yashafa yasan akwai kyau anan".
Taɓe bakinta tayi tace "to muje".
Gaba yayi yabuɗe mata gaban motan tashige, shima yazaga yashiga yaja motan, sai da yadaidaita motar tasa asaman kwalta ɗin kafin yace
"Har yanzu dai anƙi sanar dani sunan Gimbiyan, sai faman rowa ake min" .
Murmushi kawai tayi ataƙaice tace
"HALWA".
"Wow nice name, Gaskiya sunan yadace dake sosai, Masha Allah suna me daɗi".
"Ko?"
Yace "eh mana, ko bakisan da haka bane?"
Batayi magana ba sai murmushi da tasaki me sauti, daga haka yayi ta jan ta da surutu ita kuma tana amsa mishi wasu kuma iyakan tayi murmushi kawai, har bakin layin gidan su yakaita tace "ya aje ta nan".
Bayan yayi packing ɗin motan yajuyo yana kallonta yace
"To bakiso nakai ki har ƙofar gida ne?"
Ɗan kallon sa tayi tagyaɗa masa kai
"Meyasa to?"
"Babu komi". Ta'amsa mishi ataƙaice
"Uhmmm ko dai bakiso nahaɗu da saurayin ki ne?"
Turo bakin ta gaba tayi sai kuma tataɓe shi tace
"Ba laifi bane hakan ai tunda na sanar da kai dama".
Murmushi yayi yace
"Gaskiya ne, to yanzu bani Numbanki mana tunda kinga ban sauke ki har gida ba, kar kuma yanzu in kin tafi shikenan na rasa ki".
"Hmm tunda har kakawo ni nan ai kamar kakawo Ni gida ne, babu wanda zaka tambaya anan wajen be kai ka gidan mu ba idan har kafaɗa masa suna na, kuma gidan mu ai ba ɓoyayye bane, kana cewa gidan Malam Ayuba za'a kawo ka".
Yazeed yace "to NUMBAN kuma fa bazan samu ba kenan? Please". Yaƙarike maganar yana ɗan marairaice fuska
Cike da ƙosawa tace "bani da waya, sai anjima nagode sosai".
Tabuɗe motan tafito, shi kuma yana ɗaga mata hannu tare da faɗin
"Sai kin ganni kenan ko?"
Kawai gyaɗa masa kai tayi tawuce abin ta, shi kuma yaja motan sa yatafi fuskarsa cike da nishaɗi.
Da sallama tashiga gidan, matar dake zaune tana tatan koko ta'amsa mata tana faɗin
"ƴan makaranta an dawo?"
Cike da gajiyawa taƙarisa kusa da ita tazauna saman turmi tace
"Eh wlh Umma, kin ganni sai yanzu".
Umma tace "gaskiya ne kinsha hanya, ga uban rana da ake ƙwalla wa ai yau ko da gani kin gaji".
"Uhmmm Umma bari ke dai, wlh yau nasha wahala ga wuyan abun hawa da ban samu da wuri ba". Cewar Halwan tana tashi ta'aje jakan ta saman turmin tanufi wajen randan ruwa tabuɗe tana ninyan ɗiba
Umma tace "karki sha wannan ruwan, je ɗakina kiɗauko fure water yanzu na'aiki yara suka siyo min".
"To Umma".
Ɗakin tashige sai gata tafito riƙe da fure water'n ahannu tana faɗin
"Umma ya jikin Zainab ɗin?"
"Alhamdulillah dasauƙi sosai, zazzaɓin ya saukar mata ai, tana nan kwance cikin ɗaki inaga ko barci take yi ne?"
"Ok bari in shiga in ganta".
Ɗaukan jakan ta tayi tashige ɗakin Zainab ɗin, kamar yanda Umma tace kuwa tana kwance tana sharɓan barci duk tayi ɗai-ɗai saman katifan ta sai baza hanci take" bakin gadon tasamu waje tazauna tatsiyaya ruwan ahannun ta tazuba mata a fuska, jin sanyi ya ratsa mata fuska atake tabuɗe idanunta da suka ƙanƙance suka yi ja tana maida su tana rufewa
"To kasa tashi haka barcin ya isa, don nasan ba tun yanzu kike yi ba".
Ɗan yamutsa fuska Zainab tayi taƙara ware idanunta tana kallon HALWA kana tatashi zaune tana sakin hamma, cike da kasala tace
"Har kin dawo?"
Halwa tace "eh na dawo, ya jikin naki? Umma tace "kin samu sauƙi ko?"
"Eh dasauƙi sosai, dama wlh don kaina ya matsa min ne da babu abinda zai sa naƙi zuwa makaranta". Zainab ɗin tafaɗi hakan tana zamewa takoma takwanta
"Gaskiya gwara da kika zauna ɗin don yau babu abunda akayi, Monday ma za'a fara test, amma fa ina faɗamiki show ya wuce ki".
"Dan Allah fa? Ke da mutumin naki?"
Harara Halwa tasakar mata tana yatsina tace
"Banson iskanci fa Zainab, wlh yanzu sai mu ɓata idan kika sake kiran min ɗan iskan nan, mtwww".
Taja tsaki tana ɗaure fuska tare da huro hanci
Ita kam Zainab dariya tayi tace
"Sorry ƙawalliya roman jaɓa wasa nake miki fa, kinsan ni dake bamu haka, bani labari to me yafaru?"
"Ai kuma baki isa ba wlh tunda kika taɓo ni nafasa baki labarin, kinga Ni tafiya ma zanyi dama na biyo ne don naduba jikin naki, tunda yanzu na ganki garas to kinga tafiyata".
Tashi tayi tasaɓa jakan ta a kafaɗa tafice, Zainab na kiran ta amma ko waige batayi ba, tana fita taga Umma har yanzu bata gama tatan ba tace
"Umma na tafi".
"To har zaki tafi? Ina jiran in sauke Dambu nasawo muku kuma?" Umma tace hakan tana kallon Halwa
"A'a Umma kibar sa kawai yau banjin tsayawa ne".
"To shikenan kigaida gida, kigaishe min da Maman naku".
"To zataji".
Daga haka tafice [8/31/2020, 8:29 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📚* ```{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*⚜{{F.W.A📚}}*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 6*
Shiga tayi cikin gidan nasu da sallama a bakin ta, Mama da fitowar ta kenan daga ɗaki riƙe da kwano ahannu ta'amsa mata tana kallon ta, ƙarisowa Halwa tayi tana kallon Maman nata da tasami waje saman tabarma tazauna tace
"Mamana sannu da gida".
"Yauwa ƴata takaina, kin dawo?".
"Washh.. nagaji wlh Mama".
Halwa tafaɗa tana zama gefen Maman
"Ai daga ganin yanayin ki nasan da haka, da fatan dai ba wahalan mota ce tatsai dake ba?"
"Shine wlh Mama, kuma sai nabiya gidan su Zainab na je duba jikinta".
Mama kallonta tayi tace
"To ya ya jikin nata? Ta samu sauƙi dai ko?"
"Alhamdulillah Mama jikin nata ya warware ai sosai, Umma ma na gaishe ki".
"Tom Ina amsawa, naso ma in shiga in gaishe ta Allah be yiba, sai ki tashi kije kiɗau abincin ki yana ɗakin ki, don nasan tunda kika langaɓe anan sai kizauna kiyi ta zuba bazaki ci ba, kuma nasan da yunwa atattare dake".
Dariya Halwa tayi tace
"Wlh Mamana shiyasa nake ƙara son ki sabida ƙaunar da kike nuna min, uhm ai yau bazan iya wasa da abinci ba sabida yanda naji hanjin cikina suna kaɗawa, bari dai inje in ɗauko".
Tamiƙe tsaye tana kwaɓe hijabinta, Mama kuma taɓe baki tayi tace
"Da dai bansan halinki bane, yanzu sai ki jagula kibar shi nan".
Halwa shigewa ɗaki tayi tana ɗaga murya tace
"Mama banda yanzu dai, kibari kigani har ƙari ma sai kinyi min".
"To bansan surutu kimaza kiɗauko kizo nan kizauna kici".
Fitowa tayi riƙe da coolar ahannun ta da wayanta, zama tayi tana tanƙwashe ƙafafunta tasoma danna wayan tana faɗin
"Mama har yanzu Yaya be dawo ba?"
"Ni ban ganshi ba, sai ki neme sa ta waya kiji inda yatsaya". Cewar Mama tana ci gaba da ɓare maggi
Wayan takara akunni tasoma buɗe coolar'n, hannu tasaka tasoma kai loman abincin dai-dai lokacin da aka ɗaga wayan nata tace
"Wai yaya ina kaje ne har yanzu shiru baka dawo ba?"
"Sorry my Dear, Ina nan kusa naje wajen abokina ne, amma yanzu zaki ganni".
Ɗan shagwaɓe murya tayi tace
"To kayi sauri kaji?"
"Ok karki damu my dear, Yayanki yakusa dawowa".
Daga haka sukayi sallama ta'aje wayan gefe, taci gaba da cin abincin tana yi tana zuba ma Mama surutu, ita kam sai Umm take ce mata, Mama da tagama ɓare maggin miƙewa tayi tashige kichen, lokacin ne Nura yayi sallama yashigo, ɗago kanta tayi dai-dai lokacin da ta'afa shinkafan cikin baki tana kuma amsa mishi sallaman
"A'a yi ahankali mana karki ƙware, wannan loma haka sai kace abincin zai gudu".
Nura yafaɗa hakan yana dariya bayan da yaƙaraso kusa da ita yasami wuri yazauna, ɗan yatsina fuska tayi sai kuma tasakar masa harara tana faɗin
"To aina kaga na zuba loma yaya? Ko bakaga yanda naɗibo bane?"
Ɗan sakin murmushi yayi yana ƙare mata kallo yace
"Na gani mana, ba gashi kin ciko hannu ba kamar wanda take gudun shigowan wasu don halin rowa, nasan fa halin ki Sarkin rowa ce".
Ture abincin tayi tana ɓata fuska, cikin shagwaɓa tace
"Mama kin gansa ko?"
Daga kichen ɗin Mama ta'amsa mata da faɗin
"Ni kin ganni babu ruwana kunfi kusa, karki sako ni cikin zancen ku".
Nura dariya yasaki yana mata gwalo, ai ko kawai tasakar masa kuka
"Kai wai me tayi maka ne Nura daga zuwanka zaka sa ta kuka? Bansan haka fa tam". Cewar Mama kenan tana leƙo kai waje
"Wlh Mama Ni ban mata komai ba kinsan halinta ai bata raina abun kuka, to kiyi shiru mana beuaty daga wasa? kinga nakama kunni na ma".
Dena kukan tayi tana turo baki gaba tace
"Ai kuma mun ɓata tunda Ni kace ma me rowa".
Haba ƴar ƙanwata abar ƙauna ta, kiyi haƙuri kiyafe ma yayanki, ban sakewa wlh kinji? Matso da kunnin ki ma kiji wata magana?"
"Me zaka faɗamin?" Tafaɗa tana kallon sa
Murmushi yayi mata yana kashe mata ido ɗaya yace
"Kalaman da kikafi so mana" ko in aje kayana baƙya buƙata?"
"Ina so mana yaya". Tafaɗi hakan dasauri tana matso da kunnen ta kusa dashi
Magana yaraɗa mata tasaki dariya tana janye kunnen ta, ɗage mata giran sa yayi yace
"To muje mana".
"To bari in sauya kaya, kaje kajira ni a zaure sai ka'aiko yaro ko?".
"Eh haka zamuyi". Nura yafaɗi hakan yana miƙewa dasauri
Itama tashi tayi tashige ɗaki, Mama da tafito daga kichen tabi Halwa da tashige ɗaki da kallo, kana tamaida idanunta kan Nura da yasaka takalmin shi yana shirin ficewa waje tace
"To yanzu kuma me kuka shirya ne na ji kuna ƙus-ƙus?"
Dariya Nura yayi yace
"Zance zamuyi mana Mama, amma yau a zaure zamuyi, zan aiko yaro yakira min ƴar taki, dan Allah karki hanata fita".
Kama haɓa Mama tayi tabi shi da kallo don takasa cewa komai, shi kuma fita yayi yana faɗin
"Sweety kiyi sauri fa, karki shanya Ni kuma don nasan shegen nawan ki".
Babu jimawa kuwa Halwa tafito riƙe da ɗankwali da Hijab ahannu, tsayawa tayi tana ƙoƙarin ɗaura ɗankwalin
Mama tace "eh haƙiƙa yaran nan dagaske kuke yi, yau kuma gaba ɗayan ku kenan haukan taku tamotsa?"
Halwa dake shirin magana sai ganin yaro tayi ya shigo yana faɗin
"Wai Halwa tazo inji Nura".
Ƙarisa saka Hijabin ta tayi tana faɗin
"Kai kace gata nan zuwa".
Sai takalli Mama tace
"To Mama Ni nafita".
Bata jira jin ta bakin Maman ba tafice dasauri, girgiza kanta kawai Mama tayi tana murmushi tace
"Allah yashirya ku, yaran zamani baku da kunya wlh, ai bari Baban naku yadawo sai ya ji komi".
.
****** ****** *****
Shigowan ta kenan ɗakin taji wayan ta na ringing dasauri taƙarisa taɗauka tana karawa a kunni
"LUBNA kenan". Cewar Mutumin da yakira ta yana sakin dariya
Shiru tayi tana sauraron shi, sai dai babu inda jikinta baya rawa, har zuciyanta na wani irin tsalle kamar zai faso ƙirjinta
"Har yanzu dai kin ƙi aikata abinda muka sakaki ko? Da alamun kina son kirasa kowa naki ne".
Kallon inda Nazeefa take akwance tayi wanda sai sharɓan barcin ta take yi ta ƙudundine jikinta cikin bargo, cikin ƙasa da murya tace
"Dan Allah kuyi haƙuri har yanzu Ban samu nasara bane, wlh kullum sai nashiga nayi muku bincike amma baya barin komi".
"Kina dai wasa da rayuwan Mahaifiyarki da ta ƙannin ki, domin muddin bakiyi abinda mukasa ki ba zaki rasa su, tun yaushe muka baki aikin nan amma kullum magana ɗaya kike faɗa? To ki saurare ni da kyau, akwai wata yarinya da yakawo ta gidan nan kitabbatar da kin fito da ita cikin gidan nan, zan aiko yarana su ɗauke ta".
Cikin rawan murya Lubna tace
"Meee? Nazeefa?"
"Yess ita, ita nake so naɗauka, kijira umarni na".
Ƙitt yakashe wayan, yayinda ita kuma taciro wayan daga kunnen ta tana kallon Nazeefa
"Menene alaƙan su da wannan yarinyan? Me tayi musu? Me suke so da ita?"
Dasauri tamatsa bakin gadon tazauna tana ƙare mata kallo, sai kuma taji kawai hawaye na zubo mata, kifa kanta tayi saman gadon tasoma rera kuka mara sauti
"Meyasaka waɗannan mutanen suka shigo rayuwanta? Me tayi musu ne? Meyasaka sai ita ne zasu zaɓa? Meyasa basuyi tunanin bazata iya aikata duk wannan aikin ba musamman ma akan shi? Tabbas tana da rauni bazata taɓa iyawa ba".
"Waye zai fitar dani cikin wannan ƙangin?"
Tafaɗi hakan lokacin da taɗago kanta idanuwanta sharkab da hawaye
"Allah gani gare ka kataimake ni".
Kallon Nazeefa tasake yi kafin tamiƙe ahankali tashige toilet.
.
.
_shin su waye waɗannan mutanen ne?_
_Meyasaka suke takura ma Lubna?_
_meye alaƙan su da Nazeefa?_
🤷🏻♀️ 💃💃💃💃💃💃 [8/31/2020, 8:31 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖️ *FEENAH WRITER'S ASSO📚* ```{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*⚜{{F.W.A📚}}*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 7*
Ahankali yake taka motan kamar koda yaushe, wayan sa dake ajiye ne tasoma ringing, hannu ɗaya yamiƙa yaɗau wayan bayan da yaduba yaga me kira, picking call ɗin yayi tare da saka ta a speaker 🔊 yamaida ya'ajiye
"Hello Bro".
Daga can Sameer yace
"Kana ina da Allah?"
"Yanzu gani na taso wajen aiki zan koma gida".
Sameer yace "yauwa kazo kaɗauke ni Please, motata ce tasami matsala an tafi da ita, ina office Ina jiran ka".
"Ok ganinan".
Juya kambun motan yayi yasauya hanya, minti 15 yakawo shi babban asibitin da Sameer yake aiki, bayan yayi packing fitowa yayi yashiga cikin asibitin, direct office ɗin Sameer yazarce, yana shiga yaganshi zaune yana cike wasu takardu, hannu yabasa suka gaisa sannan yasami waje yazauna