Batuol mamman complete novel - Chapter 60
Batuol mamman complete novel Chapter 60: Batuol mamman complete novel Chapter 60. Kunya Radhiya taji har ta rasa inda zata sa kanta. Awwab kuwa yadda take…
3,364 words
Kunya Radhiya taji har ta rasa inda zata sa kanta. Awwab kuwa yadda take yi ga dimple dinta yana ta shigewa ya burgeshi sai da yasa hannunsa a wurin.
"I love this...." kanta ta sunkuyar yasa hannu ya rike kunnuwansa "sorry baby ina takura miki ko? Lets eat amma kinsan bazan ci na bakinki ba ko" ya kashe mata ido.
Bata fuska tayi "Ewwwww ka zama kazami dai"
"Kinga laifina an aura min ke"
Hannuwa ta nade a kirji tana cika tana batsewa yana mata dariya. Kawu Zakari ta hango ai kuwa ta daga masa hannu tana dariya za ta rama.
"Kawu Zakari tun dazu nake ta nemanka"
Fuskar Awwab ba shiri ta sauya ya bata rai kamar wanda aka yiwa duka. Yau dai ya ga wannan Kawu Zakarin. Dan kyakkyawan bafillatani ya karaso ya mikawa Awwab hannu. Radhiya sai sakin murmushi take sai da ta ga Awwab ya koma abin tausayi ta dena jansa da hira.
"Me yasa baka zo Antyn tamu ba ne?"
"Tayi nauyi bana so ta wahala"
Ba kunya Awwab ya saki fuska "ashe kayi aure"
"Eh muna da yaro daya ma ga na biyu a hanya" Kawu Zakari yayi murmushi.
"Kai Madallah wannan abu yayi kyau Allah Ya bar kowa da masoyinsa" Awwab yayi maganar farinciki ya mamaye fuskarsa abin dariya.
Radhiya tana dariya harda hawaye don yanayin relief din da ta gani akan fuskar Awwab kamar wanda aka yiwa bushara.
Kawu Zakari yayi murmushi "mijinki yana da barwanci Radhiya. Ana kirana bari na baku wuri"
Sai da ya tafi Awwab ya kalleta "to dai kinji yana da aure matarsa tana shirin haihuwa ta biyu"
"Dadin abin nima ina da auren nan and God knows I love my husband"
Wani irin kallo yayi mata sai kuma kunyar abinda yayi ta kama shi ya cire hularsa ya rufe fuska tana jin muryarsa sai ka rantse kuka zaiyi "did I just make a fool of myself a gaban crush dinki Alheran?"
"Eh mana" itama ta yi kamar kukan zata yi.
Hular ya cire ya ajiye a gefe yana murmushi "laifinki ne Schatzi yanzu duk inda na ganshi sai na tuna da wai likita kike so"
"Hamma Awwab" ta kira shi bata so ko kadan ya rinka tunanin akwai wani kafinsa ko bayansa don babu.
Hannuwanta ya kamo ya rike "na'am"
"Kai na fara so kuma kai kadai zan so har abada in sha Allah" tace da wani irin yanayi.
Zuciyar Awwab ta sake yi mata wani babban masaukin "Alheran ki sassautawa zuciyata kada sonki yayi mata illa"
Bata sake magana ba ta nuna masa abincin. Spoon biyu ta sako amma yaki yarda sai dai suci da daya duk da tana kunya ga iyayensu ko ina amma haka ya tilasta mata suka ci babu magana sai kallo mai cike da ma'anoni.
DJ ya soma nasa aikin ana sako wakoki wuri ya kaure sai rawa wurin masu jini a jika. Ana soma wakar Nura M Inuwa ta amarya 'yar amana jikin Radhiya ya fara mazari tana hango 'yan mata musamman na Nijar 'yan uwansu ga Zahra can da Raji ana ta nishadi ta mike tsaye.
"Ina zuwa?" Awwab yace jikinsa na bashi rawa zata yi.
Wurin rawar ta kalla da ka tayi masa alama.
Maltina ya cigaba da sha hankali kwance "zauna Schatzi please"
"Hamma manaa" ta langabe kai.
"Allah bazaki je kiyi rawa a wurin nan ba"
Idanu ta zaro "harda rantsuwa?"
"Kinga ya dace?"
Juyawa tayi ta hango Yousuf yana cewa Arifah wai zaiyi rawa tazo tayi masa video.
Kuka take shirin yi tace "Ka gani fa kowa yana yi"
"Mu ba kowa bane. Sunana Awwab sunki Alheran...don't tell me you expect me to seat here and watch you dance a gaban mutane"
"To...to..." kasa karasawa tayi sai dai ya sani ran ta ya baci. Dauke kai yayi ta gama kunkunin ta yana tunanin ma harda hawaye amma yaki bari ta tashi saboda indai akan tayi rawa gaban mutane ne ya yarda tayi ta fushin ya rarrasheta daga baya.
Tana ji tana gani wakar ta kare aka sako wata Awwab ya tashi dama magrib ta gabato "ki jirani a nan zanje na shigo da mota ciki na kiraki mu tafi"
Shan kunu ta sake yi harda kawar da kai gefe ya sunkuyo da kansa wurin kunnenta "you still look sweet" ya yafi. Murmushi tayi duk da ba wai ta hakura bane.
To filin rawa ma Zayyana na hada ido da Ibrahim yana zaune da robar ruwa a hannunsa ya sha kunu yana mata nuni da ta fita da hannu. Kafada ta noke ya kuma hade girar sama da kasa dole ta fita tazo wucewa ta gefensa ta murguda masa baki.
"Naji dai, rawa ce ban yarda ba" taji yace yana murmushi.
Rahima dama bata shiga ba don bata iya ba tayi zamanta sai jakunkunan su Hibbah da Zayyana da su ka bar mata. Karamar wayarta kirar samsung sabuwa mai torchlight ce a hannunta tana game din snake jikinta ya bata kallonta ake yi ta baya. Juyawa tayi a hankali ta ga Emzee yana murmushi.
Kujera yaja a kusa da ita ya juyata ya ware dogayen kafafunsa ya zauna ta yadda gabansa ne ke fuskantar bayan kujerar ya dora hannuwa a samanta kansa akan hannuwan.
"Kinsan saurin da na rinka yi kuwa da naje raka abokai na?"
"Meya faru?"
"Kawai waka na jiyo nace Allah Yasa kada Rahiman Muhammad tayi rawa if not tear gas zan saki a wurin nan bayan na kai su Daada gida"
"Meye tear gas kuma?"
Yadda tayi tambayar kadai yasa shi shagala da kallonta kafin ya yi mata bayani. Kanta a kasa take dariya da yace shi fa kishi gareshi "samarinki nawa ki kawo numbers dinsu yanzu duk na kirasu na fada musu anyi miki miji"
"Goma ne ba yawa kasan ba wani farin jini gareni ba" Rahima tayi dariya saboda kafin ta kai karshe ya kusa tuntsirewa daga kan kujera.
Gyara zamansa yayi yace yana bata fuska "Kasheni ki huta"
Shiru yaji tayi ya kira sunanta bata amsa ba. Tashi yayi ya dawo gabanta ya tsuguna yana leken fuskarta. Hawaye ya gani suna gudu akan fuskar da yake matukar so yaji hankalinsa ya tashi. Ya san iyakarsa ba don haka ba da ya rungumeta ya rarrasheta.
"Rahiman Muhammad?"
"Uhmm" tace da muryar kuka.
"Na bata miki rai ne?"
Gyada kai tayi "eh"
Zuciyarsa yaji tayi masa nauyi "Ya Salaam me nayi miki?"
"Cewa kayi fa na kasheka" ta fashe da kuka sosai.
"Oh my God...am sorry kinji wasa nake yi"
Soyayyar da suke yiwa juna ba ta wasa bace. Kowa na damuwa da damuwar dan uwansa. Hankalinsa ya tashi da kukanta ita kuma bata kaunar wani abu ya gifta tsakaninsu musamman mutuwa a yanzu da take jin ta samu farinciki irin wanda bata taba tunanin akwai ba.
Irin matar da yake mafarkin samu mai shagwaba ya gani a tattare da Rahima saboda yadda take yi da fuska da muryarta "To ka dena cewa in kasheka"
"Na dena...ban karawa"
Wayar hannunta ya karba ya saka numbarsa yayi dialling layinsa yana cewa "in chanja miki waya?"
"A'a wannan ma sabuwa ce. Sai mun gama WAEC za'a bani wata" tace da murmushi tana tuna abinda Ummi tace mata ranar da ta bata wannan din.
"Ajinki nawa? No shekarunki nawa kada ace ina koyawa yarinya soyayya fa" Emzee yace yana dariya.
"Ajina hudu a primary kuma shekarata 13"
Kallonta yayi yasa yatsansa a baki ya ciza "da gaske? 13 amma kika iya kallon soyayya? Wannan idan kika 20 na zama sorry"
Rahima sai dariya take irin wadda bai taba gani tayi ba hankalinta a kwance "kuma babana yace kada na kula kowa sai nayi 25"
"Ba damuwa nima ba kulaki zanyi ba aurenki kawai zanyi sai ki karasa primary din a gidana" ya amsa mata don ya fuskanci tsokanarsa kuma take yi.
Kalmar aure da ya sako ita ta kashe mata baki. Ya samu ta fada masa ainihin shekarunta wato sha shida da ajinta a makaranta. A take yayi mata alkawarin yana yin POP zai fadawa Daada a nema masa aurenta.
Ko da wasa Rahima bata kawo cewa Emzee bai san ko ita wacece ba. Dadin hira ya saka shi mantawa da yi mata wannan tambayar tunda ta tabbatar masa da cewa tana nan a gidan sai bayan bikin Radhiya.
**********
Wayar ta kalla tana ringing tasan Awwab ne ta kuma tura baki kamar yana wurin sannan ta dauka "fito mu tafi" kawai yace.
Tafiyar kurame suka yi zuwa gidan ashe an fara komawa saboda iyayensu maza sun ce a gida za'ayi magriba babu wanda za'a bari a wurin taron. Yasan Yousuf da Arifah zasu tafi yau ma zaiyi rakiya shiyasa bai neme shi ba. Suna zuwa gida sai nishadinsa yake fushinta kamar baya damunsa ya fito ya zagaya ya bude mata itama ta fito. Hannunta ya kama kai tsaye ya wuce falon da su ka je jiya da ita.
Wayarsa ya dauko ya bude wakar yar amana ta youtube sannan ya kama mayafinta ya cire ya ajiye akan kujera.
"Kinsan wahalar da nasha kafin na sami wakar nan a youtube kuwa? Ni bana gane me suke cewa da kyar naji ance 'yar amana shine na nemo miki" idanunsa ya dora a kanta yana ganin yadda tayi kyau sosai kamar wata 'yar tsana "baby ga 'yar amana ki tashi muyi rawa"
Shan kunun ne ya kare ta soma dariya da Awwab yayi playing wakar.
"Wai da gaske nemo min kayi Chèri?"
"Anything to see your smile Schatzi" ya janyota jikinsa yana shafa gefen fuskarta.
Tsigar jikinta ke tashi ta soma rawar jiki ya rungumeta tsam a jikinsa.
"Calm down ba yau zan baki tsoron ba ai. Rawa zamuyi kuma bazan bari ki fita a falon nan ba sai kinyi"
Sai yanzu take jin kunya sosai "Hammana na tuba kayi hakuri"
"Baby I want to see you dance...ba wai don na hanaki ba dazu wannan bazan taba yarda dashi ba amma between us harda kafi rawa zamu rinka yi a gidanmu"
"To ai dai nan ba gidanmu bane kayi hakuri" tace ido wiki wiki tana nadamar yi masa gardama don ya hanata rawa.
"Tunda ance sai anyi biki zaki tare kowa sai ya rufe ido kawai a barni duk inda kike muna tare"
"Naji amma na fasa banda rawa...kunyarka nake ji"
Fuskar tausayi yayi "Inje gida inyi kuka?"
"A'a"
Kashe wakar yayi ya kunna wata ta cikin wayarsa da yake yawan kunnawa idan yana tunaninta lokacin da suka yi fada mai suna You and I. Kidanta cikin taushi yake tashi babu hayaniya ko kadan sai kalmomi masu tasiri a zuciya. Takalmanta ya fara cire mata matsu tsini shima ya cire nasa sai safa. Wani irin riko Awwab yayi mata ya duko da kansa ya hade goshinsu. Hannuwansa na kugunta nata a kafadarsa sun zagaye wuyansa a hankali yace "hau kan kafafuna"
Runtse idanunta tayi ta dora kafa daya a hankali tana jira taji ko zaice tayi nauyi ko ta cire sai taji yace "dora dayar"
A tsaye take amma akan kafafun mijinta sannu a hankali yake bin kalaman wakar yana fada a saitin kunnenta yayin da yake tafiya a nutse suna takun rawa amma shi yake yin duka motsin. A haka suka kwashe kusan minti hudu bai nuna gajiya ba yana rike da ita suna musayar numfashi har wakar ta kare.
"Duk lokacin da kike son yin rawa baby zan tayaki, a gaban wasu ne kawai ban yarda ba saboda ina kishinki. Da sonki na girma a zuciyata kina tunanin akwai ranar da zanso bata miki rai da gangan?"
Girgiza kai tayi a hankali kalamansa na shigarta sosai kawai ta rungumeshi tana masa kukan da ake kira na kissa batare da tasan ma'anarsa ba. Idan an barta bata san dalilin hawayen nata ba idan ka cire tsantsar soyayyar Captain Muhammad Awwab Mustapha.
Habarta ya dago suna kallon juna ta kasa tsayar da hawayenta.
"Kukan na meye?"
"I. Love. You Chèri"
Kamar jira yake ta fada ya soma kissing dinta sosai. Karatu suka ji alaman an kusa kiran sallah ya dawo dasu duniyar da suke ya shafi gefen fuskarta "Da nasan hanaki rawa ne zai sa naji da kanki kin fada min wadannan kalmomin da na dade da cewa ban yarda da rawa ba"
Duka ta kaiwa kirjinsa ya saketa ta dauki takalminta ta saka sannan ta bude jakarta ta fito da janbaki za ta kara sakawa.
"Ana kiran sallah za ki sake kwalliya?"
Kunya taji tayi saurin mayarwa sai da ya matsa mata tace "Jiya Adda Fauzy cewa tayi wai an shanye min janbaki"
"Mata. Mata sai a barku...an fada min kuna zuwa ma ganin tafiyar amare washegarin da aka kaisu ko" yace yana tsareta da ido.
Ba karamin rikicewa tayi ba kuwa don babu karya ko ita sun gama JS3 da akayi bikin wata 'yar ajinsu kawayensu suka ce wai azo aje gulma. Da ita aka je din amma babu abinda chanjin tafiyar kawar tasu ya sa mata a rai sai tunanin ko duka mijin yayi mata. A lokacin ta yiwa kanta alkawarin idan tayi aure miji ya kawo mata wargi sai dai su daku don ba kyalewa zata yi yaci zalinta ba. Murmushi ne ya subuce mata da ta tuna lokacin da sharrin kuruciya.
Hannuwansa duka ya dora a ka "Na shiga uku kin taba zuwa kenan nima za'a zo mana"
Da sauri ta rinka cewa bata je ba yana cewa sai ta fada masa gaskiya. Nan aka fara kiran sallah ya fita kamar ya tafi da ita. Ciki ta wuce ana ta layin alwala a waje mazan ma suna nasu.
Gidan sai bayan isha ya dan daidaita inda Daada da su Daddy da iyalansu suka zauna a falonsa suna hira. Mama ce tace ita dai sai ta bude gift din DK daga bangaren da matan suke zaune yaran nasu suka soma murna suna jira a bude. Mami ce ta farke abin suka ga takardu ne a ninke. Ta bude ta karanta tana wani irin murmushi ta mikawa Mama. Ita kam hawaye ne ya zubo mata na farinciki Baba Hadir na kallonsu yace "Zainab?" Da alamar tambaya yaji me ya faru.
Ibrahim ta bawa takardun yaje ya mika masa falon yayi shiru sai da ya karanta ya kalli Zayyan.
"Yayi. Yawa" ya daure yace shima muryarsa na nuni da taba masa zuciya da abin yayi.
"Babu ruwanka da kyautar uba da da kuyi mana addu'a Allah Yasa yaci gajiyarsa."
Amin kowa yace ana mamakin Zayyan ya mallakawa Zayyan Hadir gidansa na Kano. Wannan ya biyo bayan dogon nazarinsu shi da Ummi sun san cewa duka sunfi Hadir karfi yanzu kuma Daddy yana da gidan kansa a Katsina.
Mama ta karbi na Zayyana ta bude a take su ka bude baki da mamaki.
"Zayyan meye haka ne?" Daddy yace yana kallon dankareren saitin gwal din da ya mallakawa Zayyana. Dankunne, sarka hade da zube da manyan abin hannu guda biyu iri daya biyu iri daya na kudi har dubu dari biyar.
"Kada ku shiga tsakanina da 'ya'yana ba ku na bawa ba"
Mami ta share kwalla tana jinjinawa zumunci irin na Zayyan da matarsa mai goya masa baya.
Gift na karshe na Emzee mukullin mota ne sabuwa fil. Zayyan yace "waccan sai ta zama ta Ibrahim shi kadai. Allah Yayi muku albarka 'ya'yana"
Saidai ayi ta cewa amin domin babu sauran godiya a tsakanin wadannan iyalin. Kaya Zayyan ya chanja zuwa farare irin na Daddy da Baba Hadir ga matansu kayansu iri daya suka zauna akan 3 sitter mazan a tsaye kowa a bayan matarsa aka dauki hoton tarihi na iyali uku masoyan juna.
[5/22, 11:03 PM] Sis Ruky: Washegari kafin a kira assalatu Emzee ya gama shirinsa. Ana kiran sallah yayi tare da Daada a nan wurin masu gadi sannan yace zai tafi.
"Ba ka ci komai ba Zayyan, Umminka bazata ji dadi ba"
Agogonsa ya kalla "Daada so nake kafin 9 ina cikin NDA in sha Allah"
Addu'a da fatan alkhairi Zayyan ya yiwa dansa suna jiran karasowar Ibrahim ya kaishi tasha saboda ba a gidan ya kwana ba. Kan wasu kujeru masu kyau daga gefen kofa suka zauna suna hira irin ta uba da da gwanin ban sha'awa. Ummi ce ta fito sanye da hijabi akan doguwar rigar baccinta da ta daura zani ta ciki da tray yana ta turiri ta taho inda suke.
"Inata saurin kada ka tafi ba ka ci komai ba. Ungo kuma ban yarda ka rage ba"
Indomie ce guda biyu da daffafen kwai biyu sai kofin orange juice mai sanyi. Tasan halinsa baya shan abu mai zafi da safe sai dare.
"Wayyo Ummi kinsan bana iya cin abinci da sassafe" yace yana kallon Daada yana neman agaji.
Daure fuska tayi "baka isa ba kuwa, ina fitowa kitchen na hadu da Rahima a falo ina jin ma ruwa ta fito sha idonta alamun bacci bai isheta ba amma ta karbi girkin tayi kuma kace na mayar"
Karba yayi da sauri bai gama jin me take cewa ba ya soma ci yana murmushi. Rankwashi ta sakar masa tana zaune akan kujerar da Zayyan ya tashi ya koma bayanta ya tsaya. Kuma ya hana Emzee tashi ya dauko masa wata. Ya kusa cinyewa suna ta masa tsiyar dama da yunwar Ibrahim ya shigo. Kafin yayi parking Zayyan ya duku kansa tsakanin Ummi da Emzee.
"Jama'a wai ni yaushe zaku koya min mota ne? Da kunya fa ace Zayyan Tureta bai iya dan murza sitiyarin nan da kowa keyi ba"
Me kuwa zasu yi banda dariya shi kuwa ya cukule yana cewa a motar Emzee zai koya yadda zaiji dadin bubbugeta kuma bazai ba da kudin gyara ba.
Ibrahim yana karasowa bayan ya gaishesu ya karbe fork din hannun Emzee wai zaici. Emzee ya damke hannun ya hana shi.
"Yanzu ko loma daya bazan samu ba?"
A daidai kunnensa Emzee yace "Idan ka dawo Zayyana ta dafa maka"
Yana jin haka ya gane wace ta dafa ya tasa Emzee a gaba karshe a tsaye ya karasa ci yana ta juya baya Daada da Ummi suna cewa da mai kwadayi da mai rowa. Cikin sauri sauri su ka bar gidan Ibrahim ya ajiye shi ya dawo. A hanya ya turawa Rahima text yana godiya da girkin da tayi masa da rokon kada ta bar gidan sai ya dawo.
A ranar ne kuma Aishatou kawar Tante ta iso za ta fara gyaran amarya Alheran Radhiya. Tante Nasara tace mata ta tabbata ta fito mata da 'yarta ta yadda ko ita kanta Radhiyan idan ta kalli mudubi sai tace bata gane kanta ba. Sai da Ummi taci dariya tace to ayi mata wankan inji mana daga nan.
Ba bata lokaci suna gama baccin gajiyarsu da kwana biyu aka fara gyara ciki da waje. Baki kuma kowa ya kama gabansa su Salame duka sun koma Sumaila na Nijar da Sakkwato suma sun tafi.
**********
Wayar gaggawa Daddy ya samu daga Katsina da daddare Alh Baba yana son ganinsa tare da iyalinsa. An tabbatar masa kowa yana lafiya sai shi Alhajin ne ma da yake ta fama da ciwon suga.
Washegari kuwa ya hada kan iyalinsa su ka tafi. Dama kuma a ranar Bilal yaso tafiya da Fauziyya idan an fara bikin sai ta dawo.
Awwab sallamarsa da Radhiya da ga nesa-nesa akayi. Tun ranar da akayi taron nan da suna waya yace mata akwai sauran rawar da za ta yi masa. Wani mugun kida kamar zai tsaga mata waya ya tura mata yace tun wuri ta koya suna sake haduwa zata yi masa. Shikenan take gudunsa duk da yayi ta magiyar cewa wasa yake yi. Ana fara gyaran jiki Aishatou tace shima mijin sai ana masa rowar ganinta domin a haka ne idan sun hadu zai fi ganin kyaun da tayi. Haka yayi ta korafinsa da mita ya hakura tunda ya fuskanci da gaske maigyaran jikin da Tante Nasara suke. Zamu hadu kawai yake cewa Radhiya don sai ya fanshe wannan punishment din na babu gaira babu dalili an hana shi ganin matarsa.
Mota uku su ka yi ranar da zasu tafi. Daddy da Mami a motarsa dreba na jansu. Sai Awwab da ya dauko Zahra, Raji da Zayyana. Mota ta uku kuwa Fauziyya ce da Bilal ana tuki ana shan soyayya wai kara'i take yi saboda laulayi ya sa ka ta a gaba kwana biyu yanzu kuwa anyi lafiya.