Boyayyen mutun complete - Chapter 37
Boyayyen mutun complete Chapter 37: Boyayyen mutun complete Chapter 37. Da sauri su kwamissiona suka shigo kitchen ganin jini ga Abba kwance awajen, wani…
3,321 words
Da sauri su kwamissiona suka shigo kitchen ganin jini ga Abba kwance awajen, wani irin finciko shi kwamissiona yayi awulakance yana jijjiga shi yace "how dare you? How dare you? Ka sace yarshi, kai kidnapping dinshi, ka aure yarshi, yanzu kuma kabiyoshi har gida ka kashe shi? Me wanan family suka maka ne? Meya maka daka kasheshi?" da sauri Nadeera ta mike tsaye tana neman faduwa tafashe da kuka tama manta da ciwonta ta matso wajen tana girgiza kai tana kallon kwamissiona tana nuna kanta da yatsar hanunta tace "ni..." anatse Marwan yana kallonta ganin tana shirin fadin gaskiya yace "shut up" kallonshi tayi kaman wacce tasami matsalan tabin hankali shima kallonta yake calmly, da hannu kwamissiona ya nuna musu Abba yana kokarin zaro ankwa ya sama Marwan da sauri wani daga cikin police din ya zare fork din ahankali yana danne wajen da clean rag gudun kar jini yacigaba da zuba yamikama na kanshi wukan dake rike da zipper bag ya wurga fork din ciki akai sealing ya sanya yatsunshi biyu a wuyan Abba kafin da sauri ya janye hannun ya shiga daddane kirjinshi kafin ya janye hannun ya kalli kwamissiona dake kallonshi yace "he's not responding let's take him to the hospital first" daukanshi sukayi kaman matattce suka fita dashi daga kitchen din while kwamissiona yawani irin fizgo hanun Marwan ya sakamai handcuff, fashewa Nadeera tayi da kuka sosai tana kallon handcuff din da aka samai, kwamissiona ya kalleta yace "ya isa Nadeera dena kuka, Allah ya riga ya kubutar dake daga hanunshi muje yanzu we are all going to the station kibada statement dinki, karki damu he will pay for his crime justice will surely be served" kallonshi Marwan yayi ido cikin ido yace "akawo mata hijabin ta, my wife is not going out like this" wani wulakantattcen kallo kwamissiona yamai kafin yaja tsaki ya kalli Nadeera dake kuka still looking at the handcuff yace "ina hijabin ki y'ata?" kaman wata zararra tahau shafa kanta danko kadan bata gane mema yake tambayan ta ba, ahankali yasa hannunshi dake cikin ankwa ya riketa da guda daya da sauri ta kalleshi da idanunta dake tsiyaya da hawaye, lumshe ido yayi yabude ya saukesu akanta wani irin tausayin ta na ratsa shi kaman yamata kuka, ahankali calmly yace "where's your hijab?" da sauri tace "hijab?" gyada mata kai yayi yace "yes where is your hijab?" fashewa tayi da kuka sosai tana kara rikeshi tanaso ta rungumeshi tace "daki?" tamai tambayan tana shigewa jikinshi duka not minding hanunshi dake cikin ankwa tadaura kanta kan kirjinshi gently tana sauke ajiyan zuciya tadaura hannayenta akan kafadarshi takama gam gam tafashe da kuka sosai ajikinshi, fizgota Kwamissiona yayi yace "ke lafiyan ki kike wani rikeshi kina shigemai? Bazaki godema Allah kin kubuta daga hanunshi ba? Yanzu sai batun raba auren ku a kotu kuma which zaizo mana da sauki sosai" ya kalli daya daga cikin polisawan dake tsaye a wurin yace "kawomata hijabin ta, duba daki kugani" da sauri daya daga cikin police din yafita daga kitchen din yana kallon Marwan dayaga ya kafe kwamissiona daya rike Nadeera dawani irin jajayen ido kaman zai kasheshi, sakin hannun Nadeera kwamissiona yayi yawani irin sharara mai mari yace "kallon rainin nan dakake min fa?" wani irin fashewa Nadeera tayi da kuka zatazo wajen tana wani irin nishi kaman zata sume kwamissiona yatare ta da hanunshi yana huci yana kallon Marwan daya kafe Nadeera dayaga kaman zata suma da ido kirjinshi namai zafi dan ko kadan batada lafiya she need care, hijabin aka kawo aka mika mata, alamu yamata da akai akan ta karba ta karba ta saka tana kallonshi, ahankali ya mika mata hanunshi daya alamun ta rikeshi da sauri ta rikeshi gam kwamissiona yay gaba yanacema sauran polisawan su fito dashi, Janshi sukayi ahankali yake tafiya sabida ita yana kallon yanda take runtse idonun idan zatai tafiya jiyayi kaman yay kuka har suka kai wurin mota aka sashi sanan ta shiga gefenshi aka tada motar sai police station ana kaiwa aka wani irin jashi aka fita dashi sosai take kuka tafito ahankali tana biyosu abaya tana kuka sosai aka jefar dashi abayan kanta ita kuma kwamissiona yace tabishi zuwa office dinshi, make mai kafada tayi taje da sauri ta zauna kusa da inda aka jefa Marwan ta kankame shoulder dinshi tana kuka kaman ranta zai fita, binta da kallo kwamissiona yayi irin lafiyan yarinyan nan lau kuwa kodai yamata magani ne kokuma wani asirin, amma mutumin dayay kidnapping dinta take makalewa haka, juyawa yayi zai wuce tsabagen takaicin ta Marwan yace "abani waya inaso nayi kira" juyowa kwamissiona yayi ya kalleshi yana mamakin boldness din yaron, he can't say no dan yasan yanada right na a bashi waya yay contacting family shi kokuma lawyer dazai kareshi, kallon wani officer dake gefe yana rubuce rubuce yayi yace "bashi waya yana 2min ka krbe" Sara mai officer yayi yace "okay sir" kwamissiona ya wurgamai mugun kallo sanan yawuce office dinshi, waya officer ya dauko ya mikamai ya tsaya akanshi ahankali Marwan ya karba da dayan hanunshi wanda Nadeera bata rikeba, officer ya juya yabar wajen yace "2min aka bama aidai kaji me ogana yace"
Number Omari yasaka yay dailing ringing kusan na hudu Omari ya dauka, magana yafara mai a natse yadanyi briefing dinshi akan wat happen, kafin ahankali yace "come to the station kazo da files din, inaso you guys kutafi da ita gida she's not doing well hurry" kaman Omari zaiyi kuka daga ta dayan bangaren yace "wat about you Ya Marwan" dan murmushi yayi yace "don't worry about me, but let's just hope bai mutu ba, idan yamutu things will damn hard and complicated but am willing to face anything for Rahma, just come as for me am fine" ya katse wayan kafin Omari yasake wani maganan.
Omari da Abdallah ne suka shigo police station din dadan saurin su rike da file har biyu suna kallon Marwan dake bayan kanta daya kafesu da jajayen idanunshi ga Nadeera data daura kanta akan kafadarshi tana gyangyadin wahala dan bacci sosai ke fizgarta, bayan sun gabatarda dalilin daya kawosu office yaje yafadin ma kwamissiona yabasu izinin aka taho dasu, kujera ya nuna musu yana kallon fuskan kyawawan yaran barinma kyan dan uwansu da har yanzu ya tsayamai arai kana ganin su kasan bayan Nigeria bane ba su kujera ya nuna musu yace "ku suwaye agareshi?" zama sukayi sanan Omari ya mikamai files din yace "mu kanenshi ne, And Nadeera kanwar muce, and ba kidnapping dinta yayiba he tried to save her from her wicked father saisa ma ya aureta dan yarabata dashi dat was his intention badan wani abuba" dago kai kwamissiona dake kokarin fara bude files din dasuka bashi yayi yakalli Omari kafin ya maida file din yarufe yace "kaman ya mekake nufi da taimakon ta yayi from her wicked fathet? Alhaji Naseer din my childhood friend ne wicked? Am not getting you" nan Omari da Abdallah suka fadanmai komi na tundaga ranan daya fara kawo ta gidansu kayan ta abarbarke fuskanta a kumbure har zuwa komi da komi yakara da. "inhar baka yarda da komiba I don't know bansan ko kannada number matan shi ba you can call her tafada ma komi" shiru CP yayi yana kallonsu saikuma ya nisa yafara bude file din yanabin komi daki daki yana karantawa saida yagama sanan yafita daga dakin yana mamaki duk yanda yake da Alhaji bai taba fadanmai cewa Nadeera ba yarshi bace to ya haka? Maisa yay hakan? Cemai yayi dasuna eygpt suka haifeta achan, Number mum ya shiga nema dayake dashi da kyar ya iya samin number tana dauka yace "Hajiya kwamissiona ne, dan Allah inaso ki fitar dani daga duhu dan ban yarda da maganan yaran chan ba, Hajiya please ku kuka haifi Nadeera koba yarku bace? Dan wanda yay kidnapping yarku Nadeera ya chakama Alhaji fork akan hallitar sa, yanzu haka rai a hannun Allah, mun kaishi asibiti mun kama yaron...." nan ya sanar da Mum komi har abinda su Omari suka fada yace "Hajiya da gaske ne maganan yaran nan?" dan murmushi Mum tayi tana kallon Muhsin da Ahmad ta window dakinta yanda suke buga basket ball a compound looking very happy abinsu, murmushi tadanyi ahankali tace "are you sure ba Nadeera ce tachaka mai fork ba? Kako bincika al amarin da kyau, Alhaji fa has been trying to rape dat girl batun yauba, ta wahala ta wahala a hanunshi, yaki hakura, ya nace, kaman sabon maye hala saisa tamai haka wanan karan" dan shiru tayi saikuma tace "banason maganan Alhaji yanzu dan am fine nariga na manta da chapter shi, abinda yaran nan suka fadama ko karya daya babu aciki, Nadeera ba yarmu bace, Nadeera kanwar suce, please ka gaggauta sakin yaran nan dan ko mesukayi nasan kokarin kare kansu ne daga shirin Alhaji, na barka lafiya" ta katse wayan tana share dan guntun hawayen daya zubo mata har ga Allah, ko Allah yasan tana mugun son Alhaji bana wasaba kuwa amma yanzu da tasan babu aure kuma tsakanin su saisa take jajircewa tanason ta yakiceshi aranta, ahankali tace "Allah bashi lafiya" kafin ta zauna ahankali akan lumtsatsen bed dinta tareda rike remote tafara chanza channel.
Kwamissiona was shocked dajin wanan sabon labarin dashi kanshi Alhaji bai taba fadanmai ba, bai taba sanin cewa Nadeera ba asalin yarshi bace, Alhaji bai taba fadanmai ba, dan zufa ya share kafin ya koma office din ya shiga ya zauna yana kallon su Omari dake kallonshi, anatse yace "nai magana da hajiya and tafadamin gaskiyan lamarin, abinda tafadamin shi kuka fadamin kuma but!" yay dan shiru yana bubbuga byro akan table yace "for now everything zai sama on hold ne, zamu jinginar da komi zamu jinginar da shari'an, yaron nan will remain in our custody har sai randa Alhaji yaji sauki ya warke, let's just hope yaji saukin inba hakaba dan uwanku yariga ya shiga matsala inhar Alhaji ya mutu, as for yarinyar zan iya baku ita kutafi da ita gida dan naga bamatajin dadi in yaso kwa kaita asibiti, duk randa muka bukaci ganinta zamu nemeku but shidai zamu saka shi a cell harsai Alhaji yaji sauki dat is the least I can do for you" shiru duk sukayi suna kallonshi sun kasa magana hakan yasa ya mike tsaye yace "let's go" fita yayi daga office din suna biye dashi suka fita har zuwa bayan kanta inda suke zaune tana bacci a shoulder shi, kafe su Omari dayaga idanunsu sunyi ja yayi kafin ya sakin musu murmushin karfin hali da sauri Abdallah ya share hawayen daya zubomai ya tsani yaga yayanshi a matsala, kwamissiona ya kallesu yace "zaku iya tafiya da ita" ya kalli officer dake wurin yace "take him to cell shikuma" "yes sir" ya saramai, ahankali ya kalli Omari ya nunamai ita yace "zoka dauketa" ahankali Omari ya mikama Abdallah files din yakaraso wajen ya tsugunna yana kallon Marwan da shima kallonshi yake ahankali yace "take care of her" gyadamai kai Omari yayi yana dukanta idanunshi sunyi jajir jiyake kaman ya kurma ihu, bude ido tayi ta kalli Omari da sauri tajuya ta kalli Marwan ta koma jikinshi, ahankali yay tapping bayanta yanajin yanda jikinta kaman wuta yay murmushi chan kasa yace "go with them kinji Sugarlips, I love you" pink lips dinshi takafe da ido tana kallonshi tana kuka tana girgiza mai kai kafin yama Omari alama daya dauketa ya dauketa ahankali suka fita daga wajen tana kallonshi tana kuka tana mikamai hannu shikuma officer yawani irin dagashi kaman wanda yay sata su Omari na kallon yanda yay dragging dinshi aka bi dashi. tawani lungu dan kaishi cell da sauri suka fita sabida yanda kukanta ya karu suka shiga mota sai gida. [10/17, 6:01 PM] Aishat Muhammad: *masu tura min novel waje su da Allah*
*idan baki biyaba karki karanta*
*3107021073 first bank aisha Muhammad Zaki tura 300 access fee saiki turo evidence to my watsapp no 07012181461 sai nai adding dinki a group din danake posting, you can also send MTN card to my watsapp no*
*A15*
Kafin su kai gida tasha kuka harta gaji, ahaka barcin wahala yayi gaba da ita. Ko dasuka isa gida she was deep assleep, bata ma san sun isa ba. Omari ne ya zagaya ya bude back door ya dauketa ya shigar da ita ciki, yanata tunanin yanda zaiyi dan jikinta yay mugun zafi, ahankali ya kwantar da ita akan gadonta da Marwan ya riga ya chanza ma zanin gado tun safe, bude ido tayi tana kallon ko ina cikin tsananin zazzabi kafin ta fashe da kuka sosai jikinta na rawa tace "Ya Omari wlh nine ba Ya Marwan ba, I killed Abba na, nine wlh, na shiga uku please kace sukamani" kallonta yayi cike da tausayi dawani irin kaunar kanwar tashi, murya chan kasa yace "Rahma stop crying okey? Brother will be fine I promise, and you will be fine also" yafada yana zama gefan gadon, daga kai yayi ya kalli kofan da aka bude Abdullah ne ya shigo dauke da tray mai dauke da kayan tea yana kallonta, tashi tayi zaune da kyar ta daura kanta akan sholder ya Omari still tana shasshekan kuka tana kallon Abdallah tana goge fuskarta da bayan hannu. Sosai Omari yaji yanda jikinta keda zafi kallon Abdallah daya jawo stool yadaura tray din kan stool yayi yace "Abdullah, Rahma is running tempreture and she needs medical attention seriously, so you stay with her while i go to a nearby clinic to get a nurse or doctor on a home service deal, please don't let her cry, keep her company" gyada mishi kai Abdallah yayi duk jikinshi a sanyayye yana kallonta, tashi omari yayi tare da mata peck a goshi ya amshi car key yafita daga dakin da dan sauri gabaki daya ya shiga damuwa daurewa kawai yake yanzu shine babba dole shizai kula dasu.
Ahankali Abdallah ya zauna abakin gadon bayan yadau tray daga kan stool ya ajiye tray din agabanta tare da kai hannunshi ya daura a forehead dinta yay feeling tempreture dinta wani irin tausayinta yaji yake ji kaman zai mata kuka, ahankali bakinshi nadan rawa yace "My shagwabatu sis" kallonshi tayi tana wani irin sauke ajiyan zuciyan kuka, ahankali yace "zakici abinci yanzu?" girgiza mai kai tayi, dan saita kanshi yayi dan bayaso yafashe mata da kuka, ahankali yace "tashi kaje kiyi alwala kiyi sallah to, shower as well ko kyaji dadin jikinki, i..will be back in the next 20mints okey..oya clean those tears and cheer up, ya marwan will be fine ok..ey?" yay maganan muryanshi na breaking sosai, gyada mishi kai tayi tare dasa hannu tashare hawayen daya zubo mata murmushi yayi yana hadiye kukan dake zuwan mai yahau mata tafi yace "that's my lil sis, my shagwababbiya" murmushi yasake mata yatashi da sauri ya fita daga dakin yana waigenta, rufo mata kofan yayi ya tsaya a wurin yana kuka mara kara yana share hawaye da bayan hannu, bayason anything yasami Ya Marwan, he can give his life for Ya Marwan, Ya Marwan shine gatansu, ya kasance uwa agaresu, uba agaresu, yaya agaresu, kani agaresu, Ya Marwan has been everything to me, ahankali yace "Ya Allah please don't let dat man die kodan Ya Marwan ya kubuta please Ya Allah" yay maganan yana goge kwalla.
Yana fita daga dakin takara fashewa da sabon kuka, ta rasa meke mata dadi, tarasa ina zata sa kanta taji dadi, kawai shes not just her self and so many thought are running over her head, she's regretting, dana sani take sosai na chakama Abban ta fork, gashi yanzu tasa Ya Marwan in trouble, gashi yanzu an kamashi, takai kusan 10min tana kuka dakyar ta mike tana takawa ahankali dakyar ta shiga bathroom, cire kayanta tayi tasa a washing machine tasakin ma kanta shower bayan tagama tashiga cikin warm water kamar yanda tagan ya marwan na mata, da kyar ta daure ta zauna sanan tafito, ba karamin dadi ruwan ya mata ba, dauro Alwala tayi tadaura towel tafito daga toilet tana tafiya kaman zata fadi dan tsananin jiri ga yunwa, cikinta sai kuka yake da kyar taja mai tashafa tasaka gown kafin ta dauko hijab da praying mat tahau kai ta tayar da sallah.
Zama tayi akan dadduma tana ma ya Marwan addua na Allah ya kubutar dashi, kuma Allah yasa kar Abbanta ya mutu, bataso chakamai fork ba, sosai take kuka ba kakkautawa data tuna abinda daya faru some hours ago. Tana danasanin abinda yasa tadauki fork harta chaka ma Abbanta,haka tacigaba da kuka har Abdullah yayi knocking kofa ya shigo jin sautin kukanta.
Da sauri yakaraso cikin dakin ya dagota daga kan dadduma tare da hugging dinta yana patting bayanta murya chan kasa yace "its okey, stop crying kinji, ya Marwan nothing will happen to him, kinsan mesa? Because ya Marwan is strong and bold ga juriya, he will be fine I promise" gyada mishi kai tayi ahankali wani irin bakin ciki ne yatokare mata zuciya sosai, hannunta yarike yace "Oya zoki sha tea" girgiza mai kai tayi bakinta na rawa sosai tace "am not hungry" bai sauraretaba yaja hannunanta yazaunar da a edge din gado ya hada mata tea a mug mai kauri sosai ya mika mata, ahankali ta mika hannu ta karba, kadan tasha ta ijiye tana girgiza mai kai hawaye na fitowa daga idanunta tace "ni banaso, please Ya Abdallah I don't feel like eating" tafashe da kuka sosai, kafeta yay da ido danji yake kaman shima yataya ta kukan, ahankali yasa hannu ya dauki ragowar tea da tray ya mike tsaye yana kallonta yace "i will be right back, stop crying pls" gyadamai kai tayi tana share fuskanta da bayan hannu.
Agaban tap ya tsaya a kitchen yana dauraye cup din tea yaji alamun bude kofa, da sauri ya ajiye cup din yafita daga kitchen din dan ganin ko waye ya shigo gidan su, Ya Omari yagani da wata nurse biye dashi that will be in her late 30's. Bismillah yama matar sukai sama suka shigar da ita cikin dakin da Nadeera dake kwance ta lumshe ido, ahankali ta bude ido hoping aranta taga Ya Marwan, ganin su Abdallah ne da Omari ne yasa ta mayar da idanunta ta lumshe tana sakin ajiyan zuciya, Ya Omari ne yakaraso jikin gadon yace "Lil she's here to check u, feel free kifada mata abunda ke damunki, okay?" gyada mai kai tayi yajuya suka bar dakin shida Abdallah tareda rufo musu kofa. Kafeta da ido nurse din tayi kafin ta karaso tazauna gefen ta abakin gadon takai hannu ta taba goshinta da wuyanta zafin dataji saita taji tsoro da sauri tace "meke miki ciwo haka?" shiru tayi tana kallonta sai kuma tai mata bayani abinda ke damunta alokacin ne ma ta tuna she's a nurse itama fa, gyada mata kai nurse din tayi tace "kina zama ai cikin ruwan dumi?" ahankali tace "eh" "good kidage da zama cikin ruwan zafin zai warke, yanzu kawai pain relief zan miki prescribing da kuma pcm sabida wanan temperature dakike running" gyada mata kai tayi ta juya ta fita daga dakin ta sauka kasa, da sauri Omari da Abdallah dake zaune a palour suka mike suna kallonta, karasowa tayi ta mika musu prescription na magani tace "kusiyan mata maganin nan in shaa Allah she will be fine, and idan akwai anyproblem dont hesitate to call me, will come back nanda 3days to check on her, na barku lafiya". Godiya suka mata sosai Abdullah ya amshi key daga hannun Omari to drop her and from there yayi branching pharmacy ya siyan ma rahma drug nata, suka fice.
Shigowa gidan Abdallah yayi dauke da ledar magani, direct dakin Nadeera yayi daddan sauri, sallama ya tsaya yayi jin shiru yasa yatura kofan ahankali bacci tanata sauke ajiyar zuciya irin na wanda tasha kuka tagaji dinnan. Tashinta yayi ya bata magani da kyar tayarda tashanya ta koma barci, juyawa yayi yafice bayan yaja mata kofa yay dakin palo duk hankalin shi yaki kwanciya da halin da ya Marwan ke ciki.
Bayan kwana biyu.