Canjin rayuwa Book 4 - Chapter 3
Canjin rayuwa Book 4 Chapter 3: Canjin rayuwa Book 4 Chapter 3. 2⃣1⃣Daga nan fa duk wanda yazo jin meya faru, sai tace, qanin mamansu Ummi ne zaije karatu,…
4,274 words
2⃣1⃣Daga nan fa duk wanda yazo jin meya faru, sai tace, qanin mamansu Ummi ne zaije karatu, ya dawo da matarsa Gida. Dama ita balaraba gun nan duniya ce. Ga duk maison jin wani tsegumi a Unguwar, gurinta yake zuwa don ta shahara. Tunda taga anayin fenti a gidan take shige da fice don jin dalili. Bata samu cikakken bayani ba, sai a bakin Ummi. Saida komai yayi tsaf, sannan suka tafi. Bayan sunyi sallama da Mahmud ya shiga gida, ya zauna. "khadija na barki ke daya ko? Don Allah kiyi haquri. Ta dube shi, sannan ta kwantar da kanta gefe, babu komai, karka damu dani na saba da zama ni kadai. Yace, an gama gyaran dakin naki, na gidan su yaya Amina, yaushe zaki koma? Cikin sauri ta tashi, "ynxun zan koma. Yayi murmushi, meyasa kk gaggawar rabuwa dani? Kin gaji da zama dani ko, bana kula dake yadda ya kamata. Cikin sauri tace, a'a Nayi kewar yaya Amina ne, kuma nan din ina takura maka sosai. Qasa fa kk kwana, amma kana kula dani sosai. Yace nikam inata kewar rabuwa dake, tsawon lokaci muna kwana daki daya, zamu rabu. Ta sunkuyar da kai, "ba zaka rinqa zuwa Gidan ba? Yace, zan dinga zuwa kullum kafin in tafi. Ya kamata in sai miki waya ko? Sai mu dinga gaisawa ko? Tace, ka barni kawai tunda banida wanda zan kira. Yace, ba gani ba? Tace, a'a ka saimin novels na dan dinga karatu. Yace, wadanne iri? Tace, na turanci. Yace zan hada miki dana addini, tarihin Annabawa, da kuma wadanda zasu koyar dake, kisan yadda zaki ibadarki. Suma akwai masu fassarar turanci, akwai na hausa. Tace, to ka saimin. Yace kuma sai gobe zako koma gidan yaya din, sbd yau da dare nida Mahmud mu kwashe kayankin nin, ya nuna akwatunanta da yatsansa. Tace, "to Allah ya kaimu. Ya shiga cikin Gida ya sanar dasu inna cewa, matarsa zata koma gidansu yaya Amina, sbd zasu tafi makaranta. Tace, "sbd nan din ba za'a kula da ita ba? Yayi murmushi, don dama ya zaci zata fadi haka. Yace a'a saboda bata gama samun sauqi ba. Tace, Allah ya taimaka. Yace, Ameen. Haka kuma da dare ya samu 'yan uwansa mazan ya fada masu. Suma sai suka ce, hakan yanada kyau. A daren suka kwashe kayansa da Mahmud tsaf. Sannan washe gari ya kama ta Suka shiga cikin gidan tayi musu sallama, dukda dai ba kulata suke ba, sai wanda yayi biyya yake leqawa dakin yayi musu sannu. Tayi mamakin ganin dakin haka don gsky bata zaci dakin yayi kyau haka ba. Ta kalli Ismail, nagode da kulawa. Sannan tace ma yaya Amina taba ta Ummi su dinga kwana. Yaya tace gatanan. [17/09 1:18 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa
2⃣2⃣Shi kuwa Ismail daya koma ya kwanta a dakinsa kan katifarsa, sai yakejin dakin yayi masa girma. Zuciyarsa ta cika da kewar Mimi. Itama a nata 6angaren haka ce ta kasance, juyi kurum takeyi tana kallon Ummi wadda keta sheqa varci. Gizo Ismail yakeyi mata, sai taga kamar gashi yana sallah. Koda ta tabbata ba wai tanason Ismail bane, amma yana da dabi'un da take matuqar so, suke kuma burge ta. Yanada tausayi, ga gsky da Amana. Shine mutum na farko wanda ya kasance mai addini kuma yake birgeta. A da in taga ustaz kamarsa, sai ta dinga yi musu kallon 'yan kauye wadanda basu waye ba. Haka kuma yana burgeta Kasancewarsa tsayayyen namiji, wanda baya daukar raini, gwarzo mai tsayawa da safafunsa. Don duk lokacin da ta tuno da yadda suka yita takun saqa dashi, tana jinjina masa, domin ko a gabanta bai ta6a shakkarta ko nuna Tsoronta ba, kamar yadda sauran mazaje da yawa sukayi a baya. Ta tuna irin yadda tayi ta wulaqanta samari 'ya'yan manyan mutane, wadanda suka nuna cewa suna sonta. Kai ko khalil dinta ya wulaqantu kafin ta soma sonshi, kuma har zuwa lokacin da ya rasu, bai daina shakkarta da tsoronta ba. Tasan cewa da ya kasance mijinta, babu shakka za suyi zama ne na sai yadda tayi. Domin ba zai iya juya ta ba. Da wadannan tunanukan varci yayi awon gaba da ita. Shikam Ismail bayan ya dawo daga masallaci sallar asubahi, saiya nufi gurin malaman da suke daukar karatu. Daga gurin karatun ne ya nufi gidan yaya Amina. Lokacin abbansBBCu saddam shima zai shiga Gida. Suka gaisa, cikin salon tsokana abban saddam yace, kazo duba ajiyarka ne? Ismail cikin dariya yace, kuma fa kamar hakane. Tashin Mimi kenan daga varci, tana tunanin da suna tare da Ismail da ynxun ya kaita ban daki, sai taji Sallamar sa. Da sauri ta koma ta kwanta don taga me zaiyi. Yaya Amina tana kicin tana dora ma yara ruwan wanka, suka gaisa. Yace, 'yar amanata ta tashi kuwa? Yaya Amina tace, leqawata biyu bata farka ba. Yace, kinsanta sarkin varci ce dama, ko gajiya batayi. Yace, bari in tasheta tayi sallah. Yaya tace, "to" amma tasan cewa mimin tana fashin sallah, domin jiya da dare bayan tafiyar Ismail ta tambayi yaya audugar mata. Yaya kuwa da kanta ta fita zuwa shagon Bello ta siyo mata. [17/09 1:18 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa
2⃣3⃣Ya jima tsaye yana kallonta, sannan ya dauko kujerar gaban madubi, yazo bakin gado ya zauna. Babban yatsan safarta ya kama ya dan ja. Dole tayi motsi, domin taji dan zafin qafar. Yace, ki tashi kin makara, kiyi sallah. Ga Ummi har ta tashi tayi nata. Tace, cikin salonta na shagwa6a "nifa ba zanyi ba yau. Ta sake sunne kanta cikin filo don kunya. Ya gane batunta, cikin sigar tsokana yace, wai, wai, wai, shine baki fadamin ba in sai miki biredinku na mata? Koda yake naga ba kiyi ba muna asibiti, sai na zata baki fara bane. Ta dago, tayi masa wani kallo, meke daukeni ne? Ya kashe ido daya, "Baby mana. Ta tashi zaune, me kace? Kada ka manta fa naje jami'a. Yace, haka fa, kinje jami'a, na manta sam, shekarunki nawa ne ma? Ta gano so yake yaji shekarunta, don haka tace, ba zan fada maka shekaruna ba, sai dai ranar zagayowar haihuwata. Tace daya ga watan daya. Yace tabdi! Gsky ke ta musamman ce, to bari in kalleki in fadi 'yan shekarun naki, don basuda yawa. Tace, fadi muji. Yace sha takwas, sha tara, ashirin, in na cika miki kenan. Ta dan zaro ido, alamun aciki ya fadi daidai, amma sai ta wayance da cewa, sam ba haka bane, baka canka ba. Yaya Amina ta katsesu da sallama suka amsa, tace, khadija ga ruwan wanka can muje in kaiki ko? Ismail ya miqe "to nima bari in tafi dama nazo ne mu gaisa. Yaya Amina tace, kardai ka manta da sandar da za'a sai mata ta tafiya, tunda sunce zai taimaka mata sosai gurin tafiya da sauri. Ismail yace, ai kuwa nagode, shaf na manta. Anjima zamuje asibiti da Mahmud. Haka kuwa sun sai mata sandar. Kwanci tashi, babu wuya har anzo jajibirin tafiyarsu Ismail. Kafin ranar tafiyar dama ya zaga duk 'yan uwansa mata, yayi musu ban kwana, domin shi harga Allah yanason 'yan uwansa mata, yayi musu ban kwana, domin shi harga Allah yanason 'yan uwansa. Kuma yana sha'awar suyi zumunci. Wadanda basuje asibiti duba su ba, sai 'yan kame-kame gami da ban haquri yace, babu damuwa Allah ya bada ladan niyya. Haka nan yaje Daura, yayi bankwana da dangin mahaifiyar sa. Ta kano zasu tashi, don haka tun ranar jajibirin zasu tafi kano din tare da Malam Aminu. Sai yaga tashinsu sannan zai dawo. 2⃣4⃣Sun gama shirinsu tsaf, Ismail ya shiga don yin bankwana da matarsa da kuma yaya Amina. Ya dauko wayarnanda ya ta6a saima Zainabu yazo ya samu tayi aure, ya bawa yaya Amina, yace, ya dinga kira don jin lafiyarsu ba sai ya dami abbansu saddam ba. Mimi tana kwance akan gado Rigingine, ta tasa tulin littafin daya sai mata, sai dai duk na addini ne, bai sai mata novels dinba, waishi baisan ina ake saidawa ba. Yace, ta karanta wadannan don tafi buqatarsu ynxun, kuma kinga duk na turanci ne, tunda kince hausa tana baki wahala. A sanyaye yace khadija! Ta kalleshi, yace munfa shirya zamu wuce. Malam da abokinsa da kuma Mahmud zasu biyo tanan ynxun mu wuce. Ta dubeshi, "tam shikenan sai kun dawo, kamar zuwa yaushe kenan zaku dawo? Yace, sai dai munje muji lokacin da suke samun hutu. Ai zan dinga kiranku muna gaisawa. Tace, am nayi zaton kafin ka wuce zaka sakeni? Gaban Ismail yayi wata muguwar faduwa, har taso ta gane. Amma sai ya wayance tare da yin dan yaqe, "kinada gurin da zakije ne kafin in dawo? Ta kalleshi "a'a" yace to kada kiyi gaggawa, wannan kibar zancen, sai in nazo hutu, sai muga yaya za'ayi ko? Tace shikenan, Allah ya taimaka, ya kaiku lfy. Ta koma ta kwanta. Ya dube ta, "babu rakiya? Tace ka manta banida qafa? Yace, shikenan kiyimin Addu'a sai munyi waya. Su yaya Amina ce da yaranta suka rakashi lokacin da su Mahmud suka iso. Suna tsaye har saida motar ta 6ace, sannan suka koma Gida. Suna idar da sallar asubahi, jirginsu Ismail ya daga, su Malam suka dawo cike da kewarsu. Zainabu ta gama girki ta raba taba kowa, kusan kwano ashirin da uku. Matuqa ta qosa ta fita a madafin sbd hayaqi da kuma zafi. Ta dauki nata da kuma na mai gidan, duk da baci yake ba, amma qa'ida ce kullum sai an zuba masa. Habu da adamu suna jira ace su dauka, tace, ku dauka, sai ku fadama sauran cewa suzo su dauki nasu. Habu ya dauka tare da fadin, ke kullum abincinki baya dahuwa. Adamu yace, eh mana ke baki iya girki ba. Tace, ku bakuda kunya. Ni sa'arku ce? Maman su Habu ta fito, dama kamar tana jira, "karki takura min yara. Ai ba qarya sukayi ba. Duk ranar girkinki, saidai a zubar ko ko aci da haquri. Jikin zainabu ya soma 6ari don tsoron fada gareta. Tace, ni bazan takura musu ba kuyi haquri, ta nufi samansu. [17/09 8:49 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa
2⃣5⃣Daidai lokacin kuma Alhaji ya shigo, yana jiyo hayaniya, yace, Hama lfy kuke min hayaniya da farar magriba? Tace, Zainabu ce zatayi min rashin kunya, don yara sunce ba zasu iya cin abincinta ba. Alhaji yace, sbd me? Tace, to abincin bai ciyo don bata iyaba. Alhaji mutum ne wanda komai qanqantar magana, sai ya ririta ta. Don haka sai yace, yanason duk 'yan gidan su hallara. Ya tara su har zainabun. Yace, su fada masa da gske ne girkin Zainabu babu dadi? Maman bushira tace, injiwa? To kai da zaka tambayemu baka ta6a ci bane? Yace, to iya magana, jikar zance, ban dake, don na kula kinfi son yarinyarnan da iyalina. Ya dinga bin yaran da sauran matan yana tambayarsu ko ta iya? Suka dinga cewa babu dadi. Sai 'ya'yan Maman bushira ne kurum Sukace sudai suna ci. Alhaji yace, ban ta6a cin abincinta ba amma yau zanci, in har baiyi dadi ba, kamar yadda kuka ce, to zan dauki mataki. Don bazan dinga fita da sassafe neman abinci ba, sannan kizo kina girka shi son ranki, a kasa ci ana zubar dashi. Zainabu dai shiru tayi, sbd ba tada ta cewa, amma fatanta shine Allah yasa ya yanke mata hukuncin saki. Shi Alhaji ba mutum bane maicin abincin gidansa, yafi zuwa Gidan abinci shagunan masu indomie koko gurin masu tsire. Dakinsa ya kira Zainabu yace, ta bude abincin ya gani. Jikinta sai 6ari yake, ta bude, qauri ya cika dakin. Yace, eh lallai dole yara su kasa cin abinci, tun kafin in kaishi baka ne wannan qaurin yake tashi? Ta kalleshi cikin tsananin tsoro, yace, uwarki bata koya miki girki bane? Tace, ni ban iya yin girki da babbar tukunya ba, kuma gashi a murhu. Yace, da Allah rufe min baki! Nine zaki fadawa baki iya girki a murhu ba. Ubanki baya iya ci da gidanku. Ni nake riqe da gidanku, da har zakice min baki iya girki da murhu ba. Wa zaki gaya ma kokai dan uban waye. Da dai kince sakaryar uwarki bata koya miki ba, sai yawon talla da nafi yarda. Ran Zainabu yakai maqura gurin 6aci, tace nidai gsky duk abinda za'ayi, ayi, amma a daina zagin iyayena. Kuma ai duk yaushe muka hadu da zaka ce kai ne kake ci da gidanmu? Ashe Zainabu ta tafka kuskure daya fada ta fada. Domin ba'a fadi yana fadi. Nan take ya tashi a fusace, ya hau kilarta. Maman bushira tana zaune Zugum tana jiyo ihun Zainabu, baqin ciki fal a zuciyarta, domin tana tsoron kar wannan halin da mijinta keyi ya juye kan 'ya'yanta, sbd in ka cutar da dan wani, sai an cutar da naka don kaima kaji. Haka yayi ta kilarta har ya gaji, yabarta don ba zuwa ceto. 2⃣6⃣Tun Zainabu tana kuka har ta kasa. Yace, tashi ki fitarmin a daki! Kasa tashi tayi, domin data yunqura, sai ta koma ta zube. Sai kuma ga jini ya soma zuba. Idanu ya zaro yana kallonta. Sai kuma ya soma kiran Maman bushira. Ta shigo ranta 6ace, yace, kamata zuwa daki, naga jini yana zuba, ko dai al'ada takeyi? Maman bushira tace, wace al'ada kuma? Yarinyarnan ciki gareta, saidai inka sake doko cikin. Yace, ni ban doketa a ciki ba. Maman bushira ta dago ta tana kiran sunanta "Zainabu! Zainabu! Cikin tsoro tace, Alhaji yarinyarnan tana da rai kuwa? Da sauri yasa takalmi yace dauke ta zuwa dakinta, bari in kira danladi Mai chemist. Tace, ka dauketa dai, ni ai bazan iyaba. Cikin tsawa yace, kama ta muje mana. Kan gadonta suka dora ta, duk jini ya 6ata hanyar da kuma dakinsa da nata. Ya fita da sauri. Maman bushira tace, maganinka kenan! Allah yasa ya zamar maka ishara. Zainabu dai tanaji, ba suma tayi ba, amma tana cikin mawuyacin hali. Sake yin lamo tayi tare da sakin jiki sbd jin rudewar da Alhaji yayi. Ko da danladi mai chemist yazo, dauke Numfashinta tayi. Dama shi ba wai ilimin gareshi ba, ya ta6a yin shara ne a asibitin Gwamnati, shine yazo ya bude chemist mutane suke ta tururuwa. Danladi yana ta6a ta, sai yace wai, wai, Alhaji! Gsky kuje asibiti, don gsky ba zan iya ba. Dubi jinin fa kamar an yanka qaramar dabba. Alhaji ya zaro ido cikin fargaba, to ni yanxu wane asibiti zamuje? Banason zuwa wannan asibitin Gwamnatin. baba yace bari in kwatanta maka wani na kudi ka kaita bakinka alaikum. Sun kaita, an amsheta, amma yayi kashin kudi masu yawa, sannan kuma cikin yananan bai fita ba. Bayan tafiyarsa Gida, gurin qarfe sha daya Nurse din da ta taya likitan aiki lokacin da ake qoqarin tsaida jinin, ta samu maman bushira a zaune kan kujerar dake kusa da gadon da Zainabu take kai kwance, tace, sannu mama. Maman bushira tace, yauwa 'yan mata sannu da aiki. Mun gode fa. Tace, yauwa dan Allah mama, wannan 'yarki ce? Maman bushira tace, a'a kishiya ta ce. Nurse din ta zaro ido. "Kishiyarki kuma? Kina nufin wancan daya fita mijinku ne?" tace, eh. [17/09 9:56 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa
2⃣7⃣Nurse tayi shiru tana matuqar mamakin lamarin. Can tace, to wai wanene yayi mata dukan jikinta? Tace, shine ya duke ta. Wlh haka yakeyi. Yayita auro 'ya'yan mutane yanacin zalinsu. Nurse din tace, kinga ko Mama da ace Allah zan hadaki da ainihin babbar likitar dake da wannan asibitin. Kiyi mata bayani, wlh zata gyara masa zama. Maman bushira tace, rufamin asiri. In ya sani ai na shiga uku, domin dama inacin darajar manyan 'ya'ya na ne, sai kuma irin wannan ranar in yayi ta'asarsa yazo ya matsamin in tayashi. Nurse tace, inda zaki iya da na hadaki da ita. Allah zatayi muku maganinsa, sai ya daina. Kuma ko daya sunanki ba zai fito ba. Tace, to shikenan ki hadamu don zan mata bayani, amma don Allah kamar yadda kkce, kar sunana ya fito. Tace, ba damuwa. Gobe ai kina nan ko? Tace, eh nizan kwana, amma na san shima zaizo da safe. Alhaji lawal, tunda yaje Gida ya tara sauran matan yasa su suka gyara gurin jinin. Shi dai tunda ya shige dakinsa ya zauna ya zabga Tagumi, ya rasa bakin magana. Da na sani ce cankas a zuciyarsa. Tsoronsa daya kar 'yar mutane ta mutu. Ranar dai bai runtsa ba, sai juyi yake. Washegari tun takwas ya nufi asibitin. Lokacin Zainabu tana varci don ta farka cikin dare har Maman bushira ke bata labarin yadda sukayi da Nurse. Zainabu tayi ta roqon ta akan cewa, ta taimaka mata don Allah don Allah ta fadawa mai asibitin. Ya kalli Maman bushira yace, ya jikin nata? Tace, da sauqi. Yace, ta farka? Cikin son qara tsorata shi, tace eh ta farka, amma bata cikin hayyacinta. Domin bata ganeni ba ma. Alhajin ya sake rudewa. To likitan bai sake dubata bane? Ance asibitin kudi, kuma na bada duk abinda akace, amma ba zasu duba ta yadda ya kamata ba? Zai fara sababinsa tace, Alhaji gara fa kabi ahankali sbd likitan ya fara tambayoyi akan shedar dukan dake jikinta. Sannan zuwan su biyu nemanka. Yace, to ni dai bari ma inzo in tafi kawai. Ya ciro kudi ya qirga dubu goma ya bata, "ga wannan ki riqe a gurinki. In sun tambaye ni kice nayi tafiya. Sannan karki sake aji daga bakinki cewa, ni na duketa." Tace, to shedar dukan fa data fito a jikinta? Yace, kice musu bulala ce ta fito mata. Ba awai ciwon bulala ba? Tamkar Maman bushira ta saki dariya, sbd ganin yadda Alhajin ya birkice. Bayan tafiyarsa tace, ai zaka gane kuranka. Nurse dai tazo kamar yadda tace, kuma ta raka ta har gurin mai Asibitin a cikin ofishinta. Da ma takan zo qarfe goma ta tashi sha biyu. Bayan Maman bushira ta gaisheta ne, sai Nurse din tace, gata nan momy. Doctor din ta kalleta, malama kiyimin bayanin dana samu daga wannan Nurse din. Maman bushira tayi mata bayanin yadda abin ya faru har ya kaiga dukanta. Sannan tace, tashi muje in ganta. Sun samu Zainabu ta farka. Tana ganin likitar ta soma kuka tana cewa, don Allah ta taimake ta. Likitar tace, karki damu, hadin kanki nake buqata. Tayi ma Zainabu tambayoyi, ta amsa. Sannan tace, to babu damuwa qarfe nawa zaizo? Maman bushira tace, ai yazo har ya tafi. Kuma zaiyi wuya ya qara zuwa don a tsorace yake. Likitar tace, qarfe nawa za'a saleshi a Gida? Tace takwas na safe ko tara na dare. Likitar tace, babu komai. 2⃣8⃣Doctor Asma'u Adamu mace ce mai kamar maza. Tana da taimako sosai, musamman akan abinda ya Shafi mata. Duk lokacin data samu matsala makamanciyar wannan, ko ba'a Asibitinta ba ne, takan nemar wa mai haqqi haqqinta. Har ta kai ga kafa qungiya mai qwato wa mata 'yanci. Suna da lauyoyi da mai qwato wa mata 'yanci. Suna da lauyoyi da 'yan sanda da malamai da kuma alqalai a cikin qungiyarsu. Bada 6ata lokaci ba suka rubuta takarda suka aikawa 'yan sanda, inda suka gayyaci Alhaji lawal zuwa ofishinsu. Da yaso yayi gardama, sai suka tura masa 'yan sanda. Dole ya zo suka tasa shi har asibiti. Lokacin Zainabu tana zaune tana shan tea. A cikin kudin daya ba Maman bushira ta fita ta siyo kayan tea din. Sun duba jikinta kuma sunyi mata tambayoyi ta basu bayanin duk avinda kenan tun daga tun daga tursasa mata auren sa da akayi har zuwa yau dinnan. Sun tasashi har Gidansu Zainabu inda aka taso qeyar innar Zainabu. Likita Asma'u ta rufe innarsu Zainabu da fada. Tace, aje a rufesu, sai gobe za'a shiga dasu kotu. Nan fa hankalin Alhaji yayi matuqar tashi. Ya shiga bada baki, tare da roqon don Allah ayi masa afuwa tunda bata sonshi, yaji kuma ya haqura, zai sake ta. Likita tace, ai dama wannan dole ne, sannan kai zaka kula da ita har ta warke, sannan ka dauki nauyin cikinta, har ta haihu ta yaye. Yace, duk na yarda. Ita kuwa inna, saida aka rubuta takarda dasa hannu kan cewa ba zata sake tursasa ta ba. Cikin su duk wanda ya sake, sai yayi zaman jarum. Bayan gargadi mai tsanani aka sallamesu, bayan Alhaji ya rubuta takardar sakin Zainabu, yayin da maman bushira ta shirya yanata-yanata, ta dauki kudin da Alhajin ya bata, taba Zainabu. Zainabu taba ta dubu uku daga ciki. Har taqi kar6a, Zainabu tace, lallai saita kar6a. Ta qara da cewa, taimakon da kk yi min, Allah ne kawai zai biyaki. Murna gurin Zainabu tamkar sallah, wannan sakin da akayi mata, matsalarta daya, wannan cikin dake jikinta. Kwana uku ta qara aka sallameta. Suka je ta kwashe nata-yanata suka nufi Gida. Kafin su wuce, dama likita ta tabbatar ma da Zainabu duk wata, gurinsu zata dinga zuwa ta amshi duk abinda aka yanke dashi. Shi kuma sun tabbatar masa cewa, sun saka ido akansa, in ya sake yiwa 'yar wasu haka, to ba shakka zai qare rayuwarsa a Gidan kaso. [18/09 3:31 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa
2⃣9⃣Rayuwar Na'ima a Gidan minister dai sai a hankali, don in yana gari ne zaka ga suna kula ta, amma da yayi tafiya ko ya fita, banza ma ta fita. Abbas kuwa ko yazo gidan bata isheshi kallo ba. Haka qannensa batajin dadinsu, har gara Aisha ma data dawo hutu, takan dan kulata. Saima ta gwammace zaman gidan Abbas dana iyayensa. Don haka wata safiyar talata ta samu Hajiya Bilkisu, bayan ta gaisheta, ta amsa cikin jin kai. Na'ima tace mata, momy na samu sauqi inaso in koma gidana. Hajiya Bilkisu tace, ai gara kam ki koma don nima kin takuramin. Ta kira Abbas tace masa, "ka kira daddynku ka fada masa cewa, zaku koma gida. Ko da Abbas ya kira shi, saida ya kira Na'ima ya tambayeta cewa, ko itace ta buqaci komawa gidanta? Tace, eh itace. Ya tambayeta ko akwai wani abu da take buqata? Tace, a'a babu komai. Yace to likitan dake dubata yayi mata? Tace eh yayi yace, to zaici gaba da zuwa duba ta a gidanta. Haka ta tattara ta koma Gidanta wanda bata iya bambantashi da gidan yari, ko da dai bata san gidan yarin ba. Shi kam Abbas dalilin cikinnan ya samu abubuwa da dama a gurin mahaifinsa. Sannan, yasha gargadi cewa, ya lura da jikansa, tare da ba uwar duk abinda take so, don jikansa ya fito duniya da girma.kusan duk sati biyu, sai anyi hoton cikin don tabbatar da lafiyar sa. Namiji ne kamar yadda sukeso. Sai dai fa, har ynxun Abbas bai daina kawo mata gidanba, mata kala-kala wataran a ita yake sawa tayi musu girki, kuma dolenta tayishi tana kuka, tana komai ga ciki. Hakanan kuma duk randa yaji cewa, yana ra'ayinta dolenta ta miqa kanta, sannan kuma ya gargadeta cewa, har dai in ta bari dadynsa yaji wata magana daga gareta, to kuwa nata daddyn sai abinda yafi haka. Babu ranar banza da Na'ima ba zatayi kuka ba, gami da dana sani, ga dinbin nadama data cika zuciya da ga6o6inta. Gani take ko mimi ynxun ta fita kwanciyar hankali. Abin takaicin gashi babu dama ta koma gida sbd in daddy yaji allura ce zata tono garma. Ita kanta Momy Nafisa komai ya kwance mata. A ynxun bata qi ace auren Na'ima ya mutu ba, cikin ma ya 6are. Rayuwa kenan mai canji. 3⃣0⃣Kwancitashi har an cinye wata daya da tafiyar su Ismail. A farkon tafiyarsu, Mimi bata da wata matsala domin yaya Amina tana yi mata komai, sannan ko girki zatayi, saita tambayi Mimi me zata ci, a dafa. Mimi bata komai, sai kwanciya sai sallah, sannan takan dan taka da sandarta a tsakar Gida da cikin daki. Zuwa ynxun ma takan dan taka ba sanda, amma ba sosai ba, din Mimi tana da tsoro. Haka nan Ismail kan kira su a waya yana jin lafiyar su a duk lokacin daya samu sukuni. Sai dai kamar yadda hausawa suke cewa, zara bata barin dami haka yake. Domin kudinda Ismail yabar ma yaya Amina sun qare, sannan abincin ma ya qare, sai dai awo sukeyi in abban saddam ya dan samo. Haka ruwan sanyi in sun saka na saidawa a fridge, sai a yini bai fisu yi Naira hamsin ba, ko kuma maqota su amsa bashi. In kuma da kudi zasu saya su tafi shago. Hakan yasa suka shiga halin matsi, musamman ga Mimi wadda bata saba da irin wannan rayuwar ba. Kafin akai wanu lokaci, Mimi ta qara lalacewa, tayi baqi, ta kode. Ga wasu qurarraji da suka fito mata a fuska. Wata safiya Mimi tana zaune akan tabarma a tsakar dakinta, ruwan Lipton ne a gabanta da yankan biredi. Hawaye suka zubo mata da ta tuna abinda takeyin kari dashi a gidansu. Ta kalli fatar jikinta, a fili tace, dubi yadda fata na mai daukar hankali ta dawo. Ta shafa sassan wuyanta, ga rama wadda ta sani yin muni. Ta kalli dakinta, dole jikina ya zama haka, babu cima mai kyau, ba AC, ba makwanci mai kyau, ga hayaniya. Sai dai duk da haka babu abinda zance ma wadannan mutanen. Saboda sunyi matuqar qoqari daidai qarfinsu kenan. Duk abinda takeci a gurinsu bata saba da cinsu ba koma tace, bata ta6a ci ba. Amman batada za6i, dole taci, domin yunwa ba tada hankali, kamar yadda taji wani almajiri yana fadi in yazo bara. Haka nan ta tsantsoma taci ta tashi. Su kuwa mutan madina suna can karatu yana tafiya yadda ya kamata, musamman dayake sun samu wadansu 'yan Nigeria acan suna gabansu a karatu. Don haka basu sama wata matsala ba, domin har abinci sukan samu gurin 'yan uwa mazauna can wadanda suka je da matansu. Hazaqa da nacin karatu, da nacin halattar majalisin da malaman sukeyi sune suka sa Ismail kar6uwaba gurin malamansu da dama. [18/09 10:20 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa