Kenza eBookz

Captain ahmad junaid complete - Chapter 13

Captain ahmad junaid complete - Chapter 13

Captain ahmad junaid complete Chapter 13: Captain ahmad junaid complete Chapter 13. Washegari da safe Junaid ya rasa yanda xai fara ce ma Mumy xai kai…

3,681 words

Washegari da safe Junaid ya rasa yanda xai fara ce ma Mumy xai kai Humainah gidansu El-ameen kamar yanda suka shirya, har ya gama breakfast bai samu courage din gaya mata ba don yasan dole xata zargi abu, Mumy tace "Kana kallon lokaci ma kuwa" da sauri ya mike daga dinning ya dau hularsa da waya yace "Am off Mum" tace "Allah ya tsare, ka shiga gaida Abban ka?" yace "Eh but yana bacci" daga haka ya fice, Hajiya ya gani tsaye da Umma a bangaren Umman suna kallon bakon motar dake ajiye parking lot suna kus kus, duk a tunaninsu sabuwa ce, ko kallonsu bai yi ba ya nufi motarsa ya bude ya shiga, yana warming motar ya hango Khadija a balconynsu tana shara, y'afito ta yayi, ta ajiye broom din hannunta ta taho, su Umma suka bi ta da harara, gaishesa tayi, yace "akwai maganar da zamu yi dake a waya, you make sure you are alone while picking my call kin ji" tace "Alryt big bro" daga haka ya rufe motarsa, ta koma balcony. Karfe sha daya El-ameen na xaune office dinsa rike da wayarsa yana jujjuayawa da ganinsa kasan ransa a bace yake, kwafa yayi ya ajiye wayar yana tunanin walakancin da xai ma Junaid, shi kansa ya rasa gane dalilin da ya sanya ya kasa cire hannunsa a patient din Junaid, kila don ya fara tausayin yarinyar ne, sake daukar wayar yayi ya kira Junaid for the 5th time, yanxun ma har ya gama ring bai daga ba, El-ameen ya fuzar da iska ya ajiye wayar, toh yanxu ina xae samo Wanda xai kai can gidan ta xauna da ita gashi Karfe sha biyu mama jummai xata tafi, tsaki ya ja ya jawo files din gabansa, why is he even bothering his self this much, tayi ta xama ita kadai a gidan after all ba shi ya ajiyeta ba, kwankwasa office dinsa aka yi ya daga kai yace "Come in" wata nurse ta shigo tace "Sir kana da bakuwa a waje" ya sauke kafarsa daga kan table yace "is she a patient?" Ta girgixa kai tace "I don't think so" yace "Ait, let her in" juyawa tayi ta fita ba a dau lkci ba sai ga ta ta dawo tare da bakuwar, da sallama ta karaso tana murmushi tace "ina yini ya El-ameen" ya sauke ajiyar xuciyar relieve yace "Lafiya khadija," ta xauna saman table dinsa tace "Ya Ahmad yace in xo office in same ka" yace "Ya maki bayani ne?" Tace "Eh daga wajensa ma nake yanxu" kallon agogo yayi ya mike ya dau makullin motarsa yace "Amma Hajiya baxa ta neme ki ba?" Tace "Gidan kawata nace mata xa ni" a tare suka sauko reception, ya kalli nurses din yace "If MD shud ask of me tell him I was called for an emergency" suka amsa masa da yes sir, sannan ya fita khadija na biye da shi duk suka bi sa da kallo, front seat khadija ta bude ta shiga, shi ma ya shiga ya tada motar suka bar haraban hospital din. Sai da suka yi nisa tace "Yaya kai kuma ina ka samo mahaukaciya?" Kallonta yayi, yayi murmushi yace "Tsarin da ya maki kenan?" Ta d'an bude ido tace "Ehh ca yayi min taimakon ta kake, a hanya ka tsince ta" dariya El-ameen yayi yace "Gaskiya ne, amma ae shi ya ban kwarin gwiwan taimaka mata" khadija tace "Toh Allah ya baku lada duka" yace "Ameen," tace "Toh amma Yaya bata ma mutum komai, ni tsoro nake ji" yace "Bata komai yanxu, ta d'an saba da mutane, iyaka yanxu kawai xuwa xa kiyi ki xauna da ita, duk barnar da kika ga xata yi ki hanata, kar kuma ki bari ta fita, sai d'an potatoe da xa ki soya mata ki cika mata ketchup a ciki," a hankali khadija tace "Toh, amma ni dai ina jin tsoro" dariya yayi yace "Ke bata komai, you will like her" suna isa gidan yayi parking a waje ya fita ta bi bayansa, da ganinta kasan a tsorace take, dariya kawai yake har suka shigo parlon, bbu kowa parlon sai ita kadai ga 'yar jakar mama jummai da ta hada kaya duk ta watsar da kayan a parlon, da alamar mama jumman na kitchen, khadija ta labe jikin kofa sai faduwa gabanta yake tana leko parlon, karasowa kusa da ita El-ameen yayi ya fixge jakar yace "Ke idan baki yi barna ba baki ji dadi ba ko" daukar kayan tayi ta mika masa, ya fixge ya ajiye ya xauna ya jawo ta gabansa yace "look. I've brought a new frnd for you, hope xa ku saba da wuri, she's khadija by name" kallonsa kawai take ko kiftawa bata yi, yayi murmushi ganin yanda yayi mata maganar kamar wata me hankali, a hankali ya d'agota ya xaunar da ita gefensa ya juyar da kanta yana nuna mata khadija da taki karasowa murya can kasa yace "A frnd jewel, ur mate" kauda kanta tayi ta xamo kasa xata ci gaba da birkita kayan da take, yayi mata tsawa, da sauri ta dawo jikin kujera tana shisshigewa jiki a tsorace, sosai hakan ya ba khadija da ta kasa daina kallonta dariya, wani tausayinta ya rufeta ganin irin kyanta amma wai ba hankali, mama jummai ta fito tace "A'ah Sannu da xuwa Ahmad, har na fidda ran tafiya yanxu da naga baka xo ba" yace "Warce xata xauna da ita na je daukowa mama, kin ganta can, kanwar Junaid ce" Mama ta kalli khadija tace "Allah sarki, sannu yarinya karaso mana" yayi dariya yace "Wai tsoronta take fa" mama tace "Yo ae ita bata komai wllh" da kyar khadija ta yrda ta shigo tana kallon yarinyar da ita ma ta bi ta da ido, Mama jummai tace "Amma nan xata dinga kwana da ita koh?" El-ameen yace "A'a gaskiya xuwa bayan magrib xata koma gida" "Toh wa xai dinga kwana nan da ita" cewar mama jummai cike da mamaki, ya d'an yi shiru sannan yace "Xan dinga kwana nan ko kuma junaid" mama jummai ta girgixa kai tace "A'a wannan ba mai yiwuwa bane, ko kuma kawae in tafi da ita in dai xa ku yrda wannan ba wani abu bane a gu na" Shiru El-ameen yayi yana kallonta sai kuma yace "Saboda me baxai yiwu ba mama?" Ta xauna tace "A ina addini ya yarje mana da haka d'an nan" xaro ido yayi sai kuma yayi dariya ganin inda xancen nata ya dosa yace "kar ki manta mama ba fa lafiya gareta ba kuma shi ake kokarin ganin an nema mata, karkashin treatment take yanxu, don haka...." ta girgixa kai tace "A'a gaskiya ba wai ina maku shisshigi bane amma bai dace ba, sai dai kawae in hada kayanta mu je kuma na maku alkawarin kwana biyu xamu yi in juyo, kayi mata duk allurorin da xaka mata yanxu" El-ameen ya jinginar da kansa jikin kujera yana murmushi yace "Komai na hannun junaid mama sai yanda yace" tace "Toh kirasa" yana ciro wayarsa kiran Junaid ya shigo ya d'aga, Junaid yace "have you seen khadija?" El-ameen ya hade rai yace "Y weren't you picking my call daxu?" Bbu yabo bbu fallasa Junaid yace "Was very busy, ya ake ciki yanxu?" El-ameen yace "Zaka san you were busy ne, mama dai tace xata tafi da ita don bbu wanda xai dinga kwana da ita a nan," da sauri Junaid yace "What? No, no how can dat be, idan ta kara gaba fa, No she shud leave her xa mu san yanda xa muyi" El-ameen yace "Zaka san yanda xaka yi dai" daga haka ya katse wayar ya kalli mama jummai yace "Kin ji mama wai xai kai ta gun yayarsa ne har ki dawo" mama tace "Atoh hakan ma yayi bari inje to in hada mata kayanta" El-ameen ya bi ta da kallo har ta haura sama, ya juya yana kallon khadija dake ta kallonta ko kiftawar kirki bata yi, yace "Wannan kallon fa" ta kallesa ta sauke ajiyar xuciya a hankali tace "She's so beautiful brother" murmushi yayi bai ce komai ba ya fara danna waya, tace "wace yayar ya Ahmad yake fadi" El-ameen yayi dariya yace "Oho" Mama jummai ta sauko rike da jaka dauke da kaya tace "Ga kayan na hada" El-ameen yace "Sannu mama" kitchen ta shiga ta fito da plate dauke da potatoe da ketchup a gefe ta ajiye gabanta, El-ameen yace "Shikenan mama xa ki iya tafiya kar dare ya maki a hanya" Mama tace "Toh," ta maida dubanta ga khadija tace "Da kin ga ta nufi sama toh kilan bayi take son shiga, ko kuma tana son xuwa ta xuba ruwa jikinta, tana son tea sosai don Allah a dinga mata, sai wannan abun da na soya mata da kunu" Khadija tace "Toh" El-ameen ya ciro dubu talatin ya mika mata yace "Ga kudin mota mama sauran sai kiyi ma mai jego siyayya" dukawa tayi ta karba tana ta sa masa albarka, ta karasa ta shafa kanta tace "Sai na dawo diyata, Allah ubangiji ya yaye maki" kamar taji me tace ta mike da sauri, mama tayi murmushi ta dau jakarta bayan ta gyara kayan da ta xubar mata, tayi wa El-ameen sallama ta nufi kofa, ai da sauri ta bi bayanta El-ameen ya mike yyi dariya yace "ta fa gane tafiya xa Kiyi" shigewa jikin mama tayi, mama tayi dariya tace "Ikon Allah, baxan dade ba 'ya ta jibi xan dawo kin ji" El-ameen ya karasa ya janye ta daga jikin mama ta fasa wani kara xata kwace kanta yayi mata tsawa, tsit tayi tana kallonsa, mama ta juya ta fita cike da tausayinta, yana rike da ita suka koma parlon ya xaunar da ita gefensa hawaye ya gani idonta, khadija ta xamo kasa ganin hakan a hankali tace "She's crying" kallonta yayi yace "Tafi kitchen ki debo min ruwa" mikewa tayi ta nufi kitchen din, tana shiga ya dafata ya lumshe ido a hankali yace "Am sorry jewel, mama xata dawo soon kin ji" dogon hancinsa ya ji ta ja kamar yanda yake mata ya bude ido da sauri, sai kuma yayi murmushi ya lakaci nata hancin a hankali yace "Pretty~Jewel"

✍🏻 *Haske Writers Association* ⚓ *Captain Ahmad Junaid*⚓

_By Khaleesat Haiydar_✍🏻

23......

A hankali ya dago kanta yana kallonta, ya ciro handkerchief aljihunsa ya share mata idonta murya can kasa yace "Am sorry jewel" yana jin fitowar khadija daga kitchen yayi saurin dauke hannunsa a shoulder dinta ya koma baya, ta karaso parlon ta mika masa cup din ruwan, ya amsa ya ajiye sannan ya saukar da ita kasa shi ma ya sauko, dankalin da mama ta ajiye parlon ya jawo ya dauka ya hada da tomatoe ketchup ya kai bakinta, ta sa hannu ta karba ya sake mata, ta lashe tomatoe din, khadija tayi murmushi ta dawo kasa d'an nesa da su ta xauna tana kallonta, haka ta dinga shan tomatoe din kanta a kasa, ya tsura mata ido yana kallo, ta d'ago manyan idonta ta sauke kan nasa, dauke nasa yayi ya mike ya koma kan kujera yace "tafi kitchen ki hado mata tea khadija" khadija ta kama hanyar kitchen yana ganin haka ya kuma saukowa ya dawo ya xauna gabanta ya dau potatoe ya kai mata baki xata kauda kai ya rike kan ya hade rai ya tura mata dankalin yace "Eat!" taunawa ta shiga yi tana kallonsa tana yamutse fuska, ya kalli kofar kitchen sannan ya kalli ragowar ketchup din dake gefen bakinta, ya matso a hankali ya sa yatsa ya kwashe ketchup din ya lumshe idonsa ya kai baki, dai dai nan aka bude kofar parlon, ya koma baya da sauri yana goge bakinsa, Junaid ya shigo parlon, kallo daya yayi masu ya sunkuya ya shiga cire takalmi da safar kafarsa, El-ameen ya mike ya koma kujera yana shafa kai, karasowa cikin parlon Junaid yayi, yana sanye da trouser din uniform dinsa sai farin polo, El-ameen na kallonsa yace "Gud you came, so ya xaka yi da ita da nyt?" Xaunawa Junaid yayi bai ce komai ba, ta dauki plate din gabanta ta mike ta dawo kusa da shi ta daura kan kafarsa, murmushi ya d'an yi ya rike plate din yace "No! Thank you" El-ameen ya dauke kai hade da tabe baki, khadija ta fito rike da cup din tea ta ajiye tana kallon Junaid tace "Welcm bro" yace "Thank you, how about you telling Hajiya you will be spending the nyt at ur frnd's place?" Shiru tayi sannan ta langwabar da kai ta xauna tace "Kasan Abba yana nan" shafa kansa yayi bai ce komai ba ya dauke plate din da ta daura masa a kafa ya ajiye kasa, El-ameen ya d'aga kafada ya mike ya haura sama, kallon khadija Junaid yayi, tayi murmushi tace "Wai yaya ka ban labarin inda Ku ka ganta mana, dama kun santa ne?" Junaid yace "I donno for El-ameen" tablets dinta El-ameen ya dauko a sama ya dawo parlon, sai da ya fara shiga kitchen yayi diluting dinsu sannan ya fito, ba musu ta bude baki ya juye mata tana yatsina fuska, Khadija tayi murmushi ta daura kanta jikin Junaid a hankali tace "I like her Ya A.jay" murmushi yayi bai ce komai ba, El-ameen yace "I will be going back to clinic yanxu, nan da thirty mins xata yi bacci, duk inda ta kwanta ki kyaleta kawai" a hankali khadija tace "Ni fa ina jin tsoro, tafiya duk xa ku yi ku bar mu" El-ameen ya harareta yace "An ce maki bata komai da'alla" Junaid ya tashi shima yace "Baxata maki komai ba sister, am also leaving" shiru tayi bata ce komai ba, El-ameen yayi hanyar kofar, Junaid ya bi bayansa, da sauri ta mike ta nufe su khadija ta bi ta da kallo gabanta na faduwa, gun Junaid ta nufa, El-ameen ya juya yana kallonsu, shima Junaid kallonta ya tsaya yi, tsaki El-ameen yayi ya xaro mata ido yace "C'mon koma kar in baki knock" kara ta saki kamar ta ji abinda yace, El-ameen ya fice daga parlon, Junaid yayi murmushi ya kama hannunta suka koma parlon ya xaunar da ita yana kallonta yace "Look Jasmine xa mu dawo anjima kin ji, khadija will be staying with you har mu dawo" Khadija tace "Waow yaya sunanta Jasmine?" Da sauri ya kalleta don ya manta gaba daya tana gun, yace "Ohh! Did I call her dat" khadija tayi dariya tace "Ehh mana" ya mike yace "No I didn't" ihu ta fasa ta mike da sauri ganin ya tashi, Khadija ta langwabar da kai tace "Yaya ba ka baro gun aiki ba, stay with her plss, bata son ka tafi" yace "Am hungry, gida nake son tafiya in ci abinci" khadija tace "Ae Akwae food stuffs a nan ba sai in girka maka ba" shiru yayi sannan yace "Alryt ki min indomie kawai" tace "Toh" ta mike ta shiga kitchen, xaunawa yayi ya xaunar da ita gefensa yayi murmushi ya ja dogon hancinta yace "I will stay with you Jasmine" suna nan xaune har khadija ta dawo parlon rike da tray me dauke da indomie da fried egg a gefe sai roban ruwa da cup ta ajiye kasa tace "Gashi yaya" saukowa kasa yayi ita ma ya sauko da ita suka xauna sai kallon indomien take kamar idonta xai fito, murmushi yyi ya kalli Khadija yace "Ke baxa ki ci ba" ta girgixa masa kai tace "Na koshi" daukar fork din yayi ya debi indomie kadan ya kai mata baki bayan ya d'an huce, wani kara da yasa shi sakin fork din tayi khadija ta mike da sauri ta bar wajen, ta dinga ihu tana komawa baya tana kallon indomien duk ta ruda shi, ya riketa yana cewa "What happen jasmine, bakya so ne" ihu kawae take tana komawa baya, ya kalli khadija yace "Take it away" dauka tayi ta nufi kitchen da sauri, tsit tayi ta bi khadija da kallo, ta dawo kusa da shi ta xauna, shi kam kallon mamaki kawai yake mata, hannu ta sa ta taba long lashes dinsa, yayi murmushi ya cire hannunta yace "Indomie kike tsoro Jasmine" khadija ta fito tace "Yaya kila tsoron shi take ji, kaje kitchen ka ci" ya girgixa kai yace "no idan naje gida xan ci abincin" kallonta Junaid yayi jin ta jingina jikinsa ya ga bacci ya fara daukarta, ya mike ya kwantar da ita kan kujeran, khadija tace "Baxa ta fadi ba yaya?" Yace "Ehh, bari in tafi gida in dawo yanxu tun da tayi bacci" a hankali khadija tace "Toh amma ka dawo kafin ta tashi plss Allah tsoronta nake ji" Junaid yace "Ohk" yana fita ta dawo kusa da ita a hankali ta xauna tana kare mata kallo, doguwa ce yar siririya da ita, ta tsura ma kyakkyawan fuskarta ido da d'an karamin jan bakinta dake sheki, Khadija ta kama long fingers dinta a hankali tace "I like you sister, Allah ya baki lafiya" kallon hular kanta tayi ta dawo wajen ta d'an cire hular tana lekan kanta ta ga bakin gashinta sai sheki yake, fito da gashin ta shiga yi ta bude ido ganin tsayin gashin, ta lumshe ido tace "Waoww!" Haka tayi ta xama kusa da ita tana kallonta, komai na jikinta me kyau ne, mamaki ta dinga yi inda suka samota har suke son warkar da ita, to yan uwanta fa?? Mikewa tayi jin ana kiran la'asar taje tayi alwala tayi sallah, sannan ta d'an gyara gidan ta dawo ta xauna ta ci gaba da kallonta daga inda ta tsaya, bude kofa taji anyi ta juya da sauri, taga El-ameen ne, ya karaso parlon yace "Capt ya tafi ne" ta gyada masa kai, ya iso kusa da su yana kallonta yace "She's still sleeping koh?" Ta gyada masa kai, ajiye ledan hannunsa yayi ya tada ta ya tafi sama da ita, khadija ta hade rai ta bi sa da kallo, haka kawae taji haushin abinda yayi, ta ja tsaki ta dauke kanta hade da tabe baki ta mike ta koma kujera ta xauna, ba a dau lokaci ba ya sauko, kallonta ya tsaya yi ganin yanda ta hade rai yace "Ke in kin gaji ne tashi ki tafi gidan ku" mikewa tayi ta dau Jakarta ta fice fuu, yayi tsaki ya dau wayarsa da ke ring. Tana fita ta kira Junaid yana d'agawa yace "Ta tashi ne?" tace "Wani tashi? Bayan ya wani ce wai in tafi" Junaid yace "Wa?" Tace "Ya El-ameen mana, wai wani in tafi gida" shiru ya d'an yi kafin yace "Saboda me?" Tace "Oho masa, ya wani dauketa ya kai ta daki bayan bacci take" mikewa Junaid yayi daga zaunen da yake parlon Mumy yace "daki kuma, ke kina ina?" Khadija tace "Ehh mana, ni na riga na fito ma tafiyata xan yi" katse wayar yayi kawai ya ajiye, Mumy dake ta kallonsa tace "Wani dakin? Kuma da wa kake waya" Kallonta yayi da sauri don ya mance tana wajen yace "Ohh dama, dama na aiketa ne, shine... no wai ce min tayi yayarta ta kulle ta a daki, khadija ce" Mumy na masa wani irin kallo tace "Karya kake" ya xaro ido yace "Mumy karya kuma" ta girgixa kai tace "Ahmad am beginning to suspect you this days, behaviours dinka sun fara canxawa, i notice kana boye min wani abu, but be careful" daga haka ta shiga bedroom, Humainah dake xaune parlon ita ma tana gyada kai tace "ta tashi ne? uhnn ko waye ya tashi oho, daki kuma? Uhnn ko wani dakin yake nufi oho, ke kina ina? Uhn ko wacece haka oho, hmm we are beginning to suspect you this days Captain be careful" wani harara ya watsa mata ta mike tayi masa gwalo tace "In tayi tsami ma ji dai" da sauri ta shige dakin Mumy ita ma. Ya shafa kansa a hankali don yasan ko hauka yake baxae bari Mumy taji xancen mahaukaciyar nan ba, tabdi! mikewa yayi da sauri ya dau makullin motarsa ya fita, waje ya fita don bai shigo da motarsa compound ba ya hau motar ya nufi gidan El-ameen, cikin few mins ya isa, yana Parkin ya fito ya shiga gidan, xaune ya tarda El-ameen balcony yana waya, ya tsaya yana kallonsa har ya gama ya hade rai yace "Y did you send khadija away?" El-ameen yace "Haka tace maka, to let me get hold of her" Juyawa Junaid yayi jin an bude gate, wata mace da baxata wuce 27 ba ta shigo, ta karaso balcony ta gaida Junaid, ya gyada mata kai kawai, mikewa El-ameen yayi yace "Welcm, ki shiga daga ciki" ba musu ta shiga parlon, El-ameen yace "we are hiring her for 2 dayz kafin Mama ta dawo, sai ka biyata 10k, old nurse din clinic din mu ce" Junaid ya daga shoulder yace "Anyhow" juyawa yayi yace "sai gobe, na tafi" El-ameen yace "Wato xuwa Kayi ka ga what I was up to da nace khadija ta tafi koh?" Junaid yayi murmushi bai ce komai ba yayi gaba abunsa, El-ameen yayi kwafa ya shiga parlon. Karfe shidda da wani abu Junaid ya shigo gida, ya ga khadija tsaye nesa da balconynsu, Hajiya da Umma na xaune sai Sadiya da Suhaima, Sadiya sai cewa take "Kawai ki bar min komai a hannuna Hajiya idan na lallasa ta xata fadi inda taje wllh" Umma tace " Ni tun da ta fara mu'amala da shegiyar 'yar da aka kawo gidan nan Humainah take kowa, dabi'un ta suka canxa, ke har kin kai matsayin da xa Kiyi karyan xuwa gidan kawa ki fita tun safe sai yanxu kike shigo mana gida don Kazan ki" junaid ya karasa wajen ya gaida su yace "Hajiya tare muka fita, ta rakani ne" Umma ta watsa masa wani kallo tace "Da yake ba Aysha bace ko Fatima dole ka kareta mu bar ta ta lalace" Juyawa khadija tayi fuu ta nufi part din Mumy, Hajiya ta shiga kwala mata kira tana cewa "Kika kuskura kika shiga wajen nan mai raba ni da ke sai Allah, kuma wllh kin ji na rantse sai kin fadi daga inda kike"

✍🏻 *Haske writers Association*💡 ⚓ *Captain Ahmad Junaid*⚓

_By Khaleesat Haiydar_✍🏻

24.....

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull