Kenza eBookz

Captain ahmad junaid complete - Chapter 6

Captain ahmad junaid complete - Chapter 6

Captain ahmad junaid complete Chapter 6: Captain ahmad junaid complete Chapter 6. Sulalewa kasa tayi ta xauna ta takure waje daya tana rufe fuskarta da…

3,967 words

Sulalewa kasa tayi ta xauna ta takure waje daya tana rufe fuskarta da dogon gashinta, dakewa yayi ya karaso cikin dakin kamar bai son taka kasa yana kallonta ya isa gabanta sae dae banda faduwa bbu abinda gabansa yake, bata dago har lkcn ta kallesa ba sae d'ada takurewa waje daya take, cire tsoro yayi ya durkusa gabanta a hankali, dago kanta tayi tana kallonsa a tsorace, murmushi yayi murya can kasa yace "Hello!" Kuri ta kura masa da ido, shi ma hakan yayi ma manyan fararen idonta, can ya lumshe ido ya bude cikin sanyin murya yace "Allah ya baki lafiya don son ma'aiki S a w." A hankali ya kai hannunsa kanta ta kuma shigewa jikin bango, murmushi yayi ya matsa gabanta ya tattare mata gashinta ya mayar baya yace "Ki daina kunce gashin ki idan an daure maki Kinji" yana magana ne yana kallon fuskarta, ita kuwa wani gun daban take kallo, ji yayi ana haurowa sama, ya juya yana kallon kofa sae ga El-Ameen, dauke kai yayi El-Ameen ya shigo yana murmushi yace "Uhnn! Ka daina tsoron nata kenan yanxu?" Mikewa Junaid yayi bae ce komai ba, El-Ameen yayi dariya yace "In gaya maka meyasa kaga ta kyale ka?" Junaid ya juya yana kallonsa, sai da ya dau kusan minti daya sannan yace "akwae alluran da na mata daxu shi yasa ta nutsu, but ina me tabbatar maka da xaran ya saketa xaka gane kuran ka idan ka tsaya gabanta" yana murmushi ya kare maganar, Junaid ya tabe baki ya juya ya fice daga dakin ba tare da ya tanka sa ba, El-Ameen ya bisa da kallo yana dariya sannan ya juyo yana kallonta, karasawa gabanta yayi ya durkusa ya dago kanta, hade rai yayi yace "Sae da kika kuma cire ribbon din koh?" Kallonsa kawae take ko kiftawa bata yi, ya hade rai yace "I will knock yhu idan baki bar kallona haka ba" kamar taji me yace ta dauke idonta daga nashi, mikewa yayi ya dauko ribbon ya dawo gabanta ya durkusa ya kama gashinta waje daya ya daure da ribbon din sannan ya dagota suka mike a tare ya kama hannunta, kin binsa tayi tana tutturjewa yace "Keehh" daga haka ya ja ta suka fita daga dakin tana bin sal, Palo ya sauko da ita ya xaunar da ita kasan rug, ya dauko ledan da ya shigo da ya durkusa gabanta ya bude, fried Irish ne da kwae, sae tomatoe ketchup, ya dauki potatoe daya ya dibi kwae ya kai mata baki, dauke kai tayi da sauri tana komawa baya, ya tsaya kallonta, kai wa bakinsa yyi ya ci, Junaid dae sai kallonsu yake yana yi yana danna waya, kara daukar wani chip din El-Ameen yayi ya dangwali ketchup ya kai bakinta, tsura ma dankalin ido tayi sae kuma ta matso a hankali ta lashe ketchup din, El-Ameen ya wara ido yana kallonta, sai kuma ya saka dariya, murmushi junaid yyi yana ci gaba da danna wayarsa, sae tsotsan ketchup din take a baki, El-Ameen ya kuma dangwala ya kai bakinta ta kuma lashewa, rike kanta yayi ya tura mata dankalin a baki ta fito dashi ya fadi kasa, ya hade rai yace "I will slap yhu fah" kallonsa kawae take ko kiftawa babu, ya dauki wani dankalin ya dangwali ketchup ya kuma kai mata baki, lashewa ta kuma yi ta bar masa dankalin tana tsotsan bakinta, yayi murmushi yana kallon Junaid yace "this shows tana son ketchup lkcn da take da hankali" shi dae junaid bae ce komae ba, El-Ameen ya dinga dangwalan tomatoe din yana kai mata baki tana lasa, exotic drink ya bude ya juya yana kallon Junaid yace "Get me cup plss a kitchen Captain, kaga dai patient dinka nake feeding" Junaid bai ce komai ba ya mike ya nufi kitchen ya dauko cup din ya kawo masa, ya karba ya tsiyaya drink din ya dauka ya kai mata baki, dauke kai tayi da sauri, ya juyo da ita ya rike kanta ya kai cup din lip dinta, kadan ta kurba ta cire bakinta tana yamutse fuska, xae kara bata ta sa hannu xata karbi cup din ya sake mata, ta dade tana kallon cikin cup din kafin ta kifar da lemon nan tsakiyarsa, El-Ameen ya mike da sauri ya bar wajen cikin tsawa yace "Kehh!" Tsorata tayi sosae ta dinga shisshigewa jikin kujera, ya karasa kusa da ita ya duka ya mata knock a kai yace "kika sake min irin haka sae na tsula maki bulala" Murmushi Junaid yayi yana shafa kansa, El-Ameen ya dago ta ganin drink din duk ya bata kayan jikinta, tsaye ya bar ta nan wajen ya fita xuwa ya kira Mama, ta juya tana kallon Junaid dake kallonta, ya sakar mata murmushi ta dauke kai ta durkusa wajen ta jawo ledan take away din da Irish din ke ciki ta dauki wanda yake bata ta ajiye gefe, ta bude wanda bae taba ba ta tsura ma dankalin ido, kifarwa tayi a kasa, Junaid ya mike da sauri yace "Noo! Me yasa kika xubar" kallonsa tayi kafin ta maida hankalinta kan abinda take, ta dauki take away din da ya fara bata ta juye cikin na wanda ta xubar a kasa sannan ta mike tsaye, tattare gown din jikinta tayi ta juye dankalin a rigarta ta jefar da take away din, Junaid ya langwabar da kai yana kallonta ya ma rasa me xae ce mata, El-Ameen ne ya shigo Mama na biye da shi a baya yana mata magana, tsayawa yayi daga bakin kofa ya bude baki ganin barnar da tayi, tana ganinsa tayi kusa da Junaid ta tsaya rike da rigarta da ta juye dankali ciki tana kallonsa, El-Ameen ya karaso palon da sauri cikin fada yace "Whatt! junaid kana kallonta ta xubar min da abincin da xan ci?" Bai jira cewar Junaid ba ya nufeta, sake rigarta tayi dankalin ya xube gaba daya kasa tayi bayan junaid da sauri, har wani bari jikinta yake, Junaid ya dakatar da shi da sauri yace "Hey, Look Dr, naga in tana da hankali ae baxata yi haka ba, have you forgotten mahaukaciya ce kamar yanda kake kiranta, wannan ae xalunci kawae kake ma patient din taka, ba dae yunwar Irish kake ba, kar ka damu I will get yhu enough idan muka fita" El-Ameen yyi masa wani irin kallo yace "Da'alla my frnd ba kana kallonta ba ka kyaleta, Better tunda dai xaka siya min wani, but wnn ae iskanci ne ba rashin hankali ba, don bata da hankali sae ta dinga sa mu aiki?" Junaid yace "naji xan gyara wajen is that all" Mama dake tsaye palon tana kallonsu tayi murmushi tace "xan gyara wajen bokon turai, kasan sae a hankali, kuma ma wllh hauka me tsafta take yi bata da kaxanta ko kadan" El-Ameen yayi kwafa yana kallonta ganin yanda take lekosa daga bayan Junaid yace "Ni nasan maganin ki ae, kina wani leko ni da Idanuwan nan naki" Junaid ya d'an tabe baki ya koma ya xauna, Mama ta nufi kitchen don dauko abinda xata gyara wajen. karasawa gabanta El-Ameen yyi ya kama hannunta ta fasa ihu, kunnenta ya ja ta nufi sama da ita, Junaid ya bi su da kallo sannan ya girgixa kai a hankali ya jinginar da kansa jikin kujera. Bayi El-Ameen ya shiga da ita ya wanke mata hannayenta sannan ya fito da ita ya xaunar gefen gado sai kallonsa take, wani kayan ya ciro mata ya ajiye gefen gadon, yana kallonta yace "ki daina kallona haka keh, kuma kika kuskura kika tashi a nan sae na xane ki, clear?" ita dae kallonsa kawae take, sae ta basa dariya ganin irin kallon, ya rungume hannu yace "Uhhn! Halan dai kin san ni ne?" murmushi yyi ya juya ya fita daga dakin. Mama jummai yace ta tafi ta canxa mata kaya bayan ta gama gyara gun da ta bata, mama tayi shiru sae kuma tace "Naga idonta biyu fa" El-Ameen yayi dariya ya xauna yace "ae bata komae mama, shi yasa nace ki tafi ki canxa mata, kar ki samu damuwa bbu abinda xata maki, tana da nutsuwa sosai" mama jummai bata musa ba ta nufi sama cikin rashin kuxari. Tana nan xaune inda El-Ameen ya bar ta a dakin ta sameta, kin rufe kofar Mama jummai tayi in case, ta karasa kusa da ita tana d'ari d'ari ta dauki blue gown din da ya fiddo mata, a hankali mama jummai tace "Baiwar Allah kaya xan canxa maki kin ji" ko kallonta bata yi ba, hakan ya kuma tsorata mama jummai, juyawa tayi a sanyaye ta koma Palo tana kallon El-Ameen tace "D'an nan wallahi tsoro nake ji ni kam, kaga sae tana bacci nake shiryata" dariya yayi ya mike ya nufi stairs din suka koma sama a tare, junaid ya bi su da kallo. Xaune suka tar da ta har lkcn sae dai wannan karan windon dakin ta tsura ma ido, El-Ameen ya karasa kusa da ita, ta juya da sauri tana kallonsa, kayan ya dauka ya mika ma mama jummai yace "Gashi mama" karasawa tayi ta karba, ya dago ta yana kallonta ya hade rai yace "Mama xata canxa maki kaya yanxu, stay still kin ji" ita dae kallonsa kawae take, ya juya ya kalli Mama jummai yace "Toh karaso Mama" a hankali ta karaso kusa da su, hannunta na rawa ta kai kan maballin rigar xata cire mata, ta fasa wani ihu tayi bayan El-Ameen da sauri, cikin sakwannin da basu wuce uku ba sae ga mama jummai can bakin kofa a mugun tsorace bayan ta sake kayan hannunta nan gabansu, dariya sosai El-Ameen yake yana kallonta yace "Mama baxa fa ta maki komae ba wllh" tace "A'a d'an nan nafi gane tana bacci wllh" a tsorace take maganan daga haka ta juya ta koma kasa, murmushi yayi ya juya yana kallon ta bayansa, dawo da ita yayi gabansa, ya kusa minti biyu tsaye kamar me naxari sai kuma ya leka rigar jikinta don ganin ko akwai kaya a ciki yaga akwai vest, rufe idanuwansa yyi a hankali ya balle dogon rigan jikinta snn ya fara cirewa idonsa kulle, ajiyewa yayi bayan ya cire har lkcn idonsa na rufe ya duka a hankali ya shiga laluban kayan da Mama jummai ta yar a kasa, yana tabawa ya dauka sannan ya mike, lalubawa yayi yaji bata wajen kuma, ae ba shiri ya bude ido da sauri yana waige waigen inda xae ganta, tsaye ya ga perfect fair figure dinta can jikin window, daga ita sai white vest da ya kusa cinyarta, vest din ya kamata sosai kasancewarsa very elastic, gaba daya shape dinta ya fito ga long fresh legs dinta da bbu tabo ko daya, kamar xaka latsa ta jini ya fito tsabar haske, juyawa yayi da sauri kamar wanda ya ga abun tsoro ya nufi kofa da hanxari, ko me ya tuna kuma sae yyi still bakin kofar ya kusa 3 mins kafin ya juyo a hankali ya dawo dakin ya nufeta ba tare da ya kuma kallon jikinta ba, hannunta ya kama yana kallon fuskarta ya shiga sa mata rigar hannunsa, yana gamawa ya xaunar da ita gefen gado ya hade rai ya dunguri kanta yace "Don't try dat again" cup ya dauka ya dauraye yayi mata diluting drugs dinta da ruwa sannan ya dawo kusa da ita ya rike kanta ya kai cup din bakinta, kauda kai tayi da sauri, yayi mata tsawa ita ma ta fasa masa ihu, rike kanta yyi ya tura cup din bakinta har sai da ta bude ya xuba mata, sae da ya tabbatar ta hadiye sannan ya kyaleta tana yatsinan baki tana komawa baya, jinin da ya gani bakinta yasa ya tsura ma lips din ido, handkerchief ya ciro aljihunsa ya goge mata bakin yace "Sorry!" Mayar da handki din yayi ya kwantar da ita ya mike ya fita daga dakin ya ja kofar. Palo ya sauko ya ga ba Junaid, ya kalli mama dake xaune yace "Mama Junaid fa?" Tace "Ya tafi wai" shiru yayi bae ce komae ba, can yace "Ohk xan tafi yanxu, da daddare xan dawo, bacci xata yi yanxu" tace "Toh Allah ya kai mu, Allah kuma ya bata lafiya" yayi murmushi yace "Ameen" sannan ya fita.

✍🏻

*Haske Writers Association*💡 ⚓ *Captain_Ahmad Junaid*⚓

_By Khaleesat Haiydar_✍🏻

12.....

Gidansu faisal Junaid ya nufa, yana gama parkin ya nufi babban palon gidan, babu kowa palon sae TV dake aiki ya shiga dakin faisal, kwance ya samu faisal yana waya, Junaid ya tabe baki ganin yanda yake wani kwantar da murya ko ba a fadi ba yasan da mace yake wayar, can karshen gadon Junaid ya xauna, faisal ya mike xaune yace "Babe xan kira ki ltr," daga haka ya ajiye wayar yana kallon Junaid yace "Uhn! B'atan hanya kayi captain?" Junaid yace "No!" Faisal yayi dariya yace "A'a kae dai fadi gskya, ko wajen El-Ameen xaka yi ka mance ka yo nan" Junaid yace "What ever, Mama fa?" Faisal yace "Tana kano jiya ta tafi" Junaid yace "Allah dawo da ita lfya, kana ta shagalin ka da 'yan mata abin ka" faisal yayi dariya ya dawo kusa da shi yace "Kai aure ma ni xanyi fa yanxu" junaid ya kallesa yace "da gaske?" Faisal yyi kwafa yace "Stay there kai da El-Ameen kuna hauka sae kun ji ma an sa min rana soon" murda kofar dakin aka yi duk suka juya suna kallon kofar El-Ameen ya shigo, faisal ya d'an bude ido yace "Show! Ko dai tare ku ke?" El-Ameen dake ta kallon Junaid yayi murmushi ya karaso cikin dakin yace "Ashe nan ka yo captain, toh what's the meaning of going without saying a gud bye, dama daga nan gidan ku xan tafi ban mance Irish dina ba wllh tunda yunwarsa nake" Junaid bae ce masa komae ba ya fiddo wayarsa yana dannawa, El-Ameen ya xauna gefen faisal ya dafa kafadarsa daya yace "Ya aka yi guy, ya aiki?" Faisal yace "Alhmdllh mun gode Allah, muna week end yau, ya su Ummi?" El-Ameen yace "Duk lfya, plss in tambaye ka mana" Faisal yace "Ina jin ka" El-ameen na shafa kai yace "wannan abokin naka psychiatrist, I can't recall his name yanxu, yana nan katsina har yanxu kuwa?" Faisal yace "Wai Dr isah?" El-Ameen yace "Exactly, yana nan?" Faisal yyi dariya yace yace "Yana nan, Ashe baka mance shi ba, ko jiya muna tare da shi" El-Ameen yace "Yauwa plss wani taimako nake son ka min, Gamma knife or Cyber knife xaka tambayar min a gurinsa nasan baxae rasa ba" faisal ya gyara xama yana kallonsa yace "Me xaka yi da gamma knife kuma, naga baka concentrating a field dinka na neurology yanxu" El-Ameen ya sauke ajiyar xuciya yace "ina yi mana, sosai ma, yanxun ma wani frnd dina ne ke da wata patient with mental disorder, so am putting her under medication ne yanxu, after some month idan naga ba a dace ba, I will advise him to take her to a psychiatry for psychiatrist to take over, kila a dace a can din" El-Ameen na magana ne yana kallon Junaid fuskarsa dauke da murmushin rainin hankali, junaid dae ko kallonsa bae yi ba sai danna wayarsa yake, Faisal yace "Allah sarki, xa ma a dace idan Allah ya yarda, sae dai idan ba Neurologist El-Ameen din da na sani bane," dariya El-Ameen yayi yace "Noo, Dr El-Ameen dai, yanxu dai plss xuwa gobe ka lallaba sa ko na clinic ne ya aro min, coz nasan frnd din nawa will not afford it idan nace yaje can kasashen turai ya siya, its more than expensive" ya kare maganar yana ma Junaid wani irin kallo yana murmushi, Murmushi junaid yayi ba tare da ya kallesa ba, faisal yace "Alryt xan kirasa anjima, amma a ina xaka sa ta under medication din, clinic din ku?" El-ameen ya xaro ido yace "Sai in ce ma Abba a ina na samota?" Da mamaki Faisal yace "Kamar ya, 'yan uwanta fa?" El-Ameen yayi dariya yace "Ohh ai d'an uwanta a dai yanxu daya ne kacal a duniyar nan" kallonsa kawai Faisal ke yi da confusion shi ko sai dariya yake, Junaid ya tabe baki ya mike ya nufi bathroom ya dauro alwala ya fito don lkcn sllh yayi, bae jira su ba ya fice daga dakin don xuwa masallaci, Faisal ya bi sa da kallo yayi dariya yace "Kai halin Junaid sae shi, toh meye ma'anar hakan da yake yi, namiji dan uwansa ma sai ya ma miskilanci ina ga mace" El-Ameen yayi dariya yace "Let him, I think yana d'an da brain disorder'n shi ma, of recent na lura da hakan, kaga sae in hada shi da patient din tawa in sa su under medication" dariya sosai faisal yayi, El-Ameen yace "Amma fa rufa min asiri kar ka gaya masa sae ya Iya daukar gaba da ni daga yanxu har bayan watanni" bayi ya nufa yana dariya, faisal na taya sa. A tare duk suka fito daga mosque din bayan an idar da sllh, Junaid ya nufi motarsa ba tare da ya kallesu ba yace "Am going home" Faisal yace "Haba so early dama ba hira ka xo mu yi ba" Junaid ya kallesa yace "Ga Dr nan sae kuyi hiran, am going home kafin Mumy ta fara kirana" faisal ya rungume hannu yana dariya yace "Ehh gskya ne kuma wannan, madarar ka na can a feeder kar ya huce koh" murmushi junaid yayi yace "Yea! Sure." Daga haka ya nufi motarsa, El-Ameen yayi dariya yace "Allah ka nuna mana ranan da Junaid xae girma kamar mu" makullin motarsa ya mika ma Faisal yace "kaga shigar min da motata ciki, tare xa mu tafi, ltr xan dawo inji yanda ku ka yi da Dr isah" faisal yace "Ohk sai ka dawo" motar Junaid El-Ameen ya nufa da sauri ya bude ya shiga, Junaid dake kokarin tada motar ya kallesa yace "Ya aka yi?" El-Ameen ya hararesa yace "Mu je ka siya min potatoe dina mana, ko ka xaci na manta ne" murmushi junaid yayi ya tada motar ya ja suka bar wajen. Wani eatery ya tsaya ya fito ya shiga ciki, El-Ameen ya bi sa da kallo, ba a dau lkci ba ya fito rike da take away din fried Irish har hudu, ya bude bangaren da El-Ameen ya ke ya dungure masa ledojin a kan kafarsa snn ya rufe motarsa ya xaga ya shiga, dariya El-Ameen yayi yace "Toh me kenan, ni ae wannan ya min kadan" Junaid bae tanka sa ba ya tada motarsa suka bar wajen. Sae da suka hau kan titi ba tare da ya kallesa ba yace "Ina ka nufa don ni am going home" El-Ameen yace "drop me at home," junaid ya kama hanyar gidan nasu yana isa yayi parking ya juya yana kallon sa, bude motar El-Ameen yayi yace "Gobe xa ayi diagnose dinta!" Junaid ya gyada kai yace "Allah ya kai mu" El-Ameen ya fita daga motar yace "Ka gaida Mumy" kai junaid ya kuma gyada masa sannan ya ja motar ya bar kofar gidan.

yana isa gida ya dde xaune cikin motarsa a parking lot yana danna waya, fatima ce ta leko jin bae kashe motar ba har lkcn, yana ganinta ya kashe motar ya fito ya rufe, kallo daya yayi ma Umma da fitowarta daga side din Abba knn ya dauke kai yayi side din Mumy, Umma ta bi sa da kallo ta gefen ido tayi kwafa ta nufi bangarenta. Kwanciya Junaid yayi bayan ya gaida Mumy, Mumy ta xauna tana kallonsa tace "Ga lunch dinka a dinning" yace "Toh Mumy," Humainah ce ta fito daga kitchen ta shigo palon tace "Na gama Mumy" Mumy tace "Sannu Humainah, dauko ma yayanki abincinsa a dinning" ta juya ta tafi dinning din ta dauko warmer biyu, daya me dauke da jollof rice daya kuma farfesun naman rago, ta dauki plate da spoon ta dawo palon ta dire gaban Junaid dake kwance har lkcn idonsa lumshe, ta mike ta koma ta dauko drink da ruwa sae cup ta dawo ta ajiye, Mumy tace "Toh tashi ka ci abincin mana" mikewa xaune yayi yana kallon Humainah dake durkushe wajen har lkcn ya hade rai, ita ma haka, harara ya galla mata yace "ke wa yace ki shiga dakina ki dauki turare" ta tabe baki tace "Toh meye? kuma naga turaren kala kala ne shi yasa" Mumy tayi dariya tace "Atoh!" Ya wani hade rai sosai yace "God help yhu ki sake shiga daki na ki ga" mikewa tayi tace "Mumy xan je gun Hajja" Mumy tace "Toh kiyi mata sannu da xama" daga haka ta galla masa harara ta fice daga palon, sakkowa Junaid yayi ya xauna kan carpet yace "Yarinyar nan ta raina ni fa Mumy" Mumy tayi dariya tace "Ko dai kana ciki ne Captain" kallon Mumy yayi da sauri sai kuma ya marairaice mata yace "Ina ciki kuma Mumy, A'a ni matata na nan xuwa in'sha Allah, beside bana sha'awar auren xumunci ni" Mumy tayi dariya tace "Toh ka dinga sake mata don tunanin da Hajja da 'yan gidan ma xa su yi kenan, idan suka ga kuna haka da ita, kasan yanxu samarin nowadays idan suna son mace sae suyi ta wani basarwa, kaga suna yawan fadace fadace da ita barin ma idan yar uwar sa ce, wae su nan kar ta gane suna sonta ta raina su, wasu har da duka wae kuma duk cikin so ne fa" dariya sosai Junaid yayi yace "Ae kauyanci knn Mumy" Mumy tayi murmushi tace "Atoh, sae ka ga daga karshe idan suka ga yarinyar na neman kubuce masu su haukace su fito fili suce su fa sai ita" dariya junaid yake yace "Kai Mumy, wannan ae sae film ba dai reality ba" Mumy tayi murmushi tace "Toh shknn, it seems you've neva come across dat before" yace "Uhnn toh Allah kyauta, but it kinda funny mum" abincin gabansa ya bude ya dibi shinkafar dai dai wanda xae ci da plantains da nama sannan ya rufe, yayi bismillah ya fara cin abinci, yana gamawa Mumy ta kira mai aikinta ta fito ta kwashi plates din da warmer ta kai kitchen, kiran sllhn Asr yasa shi mikewa ya shiga bayin dake Palon ya dauro alwala ya fito, fatima da fitowarta palon kenan ita ma da shirin islamiyya tace "Ya A.jay xaka yi dropping dina in jira" yace "No" kofa ya nufa ya fita daga palon. Yana dawowa daga masallaci part din Hajja ya shiga, ya sameta xaune ta sa TV a gaba, Khadija kuma na kwance tana danna waya, xaunawa yayi yana kallon Hajja dake bin sa da kallo yace "wannan kallon fa Hajja" Hajja ta tabe baki tace "Ba sai ka tsole min idon ba" Khadija ya kalla ya hade rai yace "Ranan da xan xane ki na nan tahowa a gidan nan, baki da aiki sai danne danne kin yaye islamiyya yanxu koh" Hajja ta gyara xama tace "Ai mu sai Allah yayi mana shari'a da shegen wahalallen da ya kirkiri waya a duniyar nan ya bata mana 'ya 'ya, yanxu ace kamar Khadija daga safe har talatainin dare wancan shegen abun na hannunta tana latsawa tana murmushi, ta fa ji tsoron Allah taji tsoron gamuwarta da shi, Allah kadai yasan tsiyar da take tsulawa a shegen abun, shi kuma Muhammadu ba mai sa ido ba, ta inda bala ya fi sa kenan don har yau bai bari Humainah ta rike waya ba, wannan bala'i da me yayi kama? kana mata magana ma bata san kana yi ba ido kyar a kan waya, amma mu je xuwa ranan da Allah xai tashi kamata sai dai yar iskan wayar tayi bindiga a hannun ki wllh" kallon Hajja kawai Junaid yake kafin ya tabe baki ya kalli wayarsa dake ringing a hannunsa ya ga El-ameen ne.

✍🏻 *Haske Writers Association*💡 ⚓ *Captain Ahmad Junaid*⚓

_By Khaleesat Haiydar_✍

13....

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull