Cutarwa complete by ayshercool - Chapter 38
Cutarwa complete by ayshercool Chapter 38: Cutarwa complete by ayshercool Chapter 38. Dr. Ya sha mamakin jin waye raihan, tare da yi wa ummi fatan, Allah…
3,374 words
Dr. Ya sha mamakin jin waye raihan, tare da yi wa ummi fatan, Allah ya sa ƙarshen wahalarta ne ya zo.
Nan Alhaji Tahir yake gaya wa dr. Tuni ya saka an gama yi masa bincike a kan ummi, kuma ya ji daɗin sakamakon binciken, dan haka ko yanzu aka ce su bayar da kuɗin aure dr. Ya yanka za su biya, idan kuma shima zai yi bincike a kan su tukuna shikenan.
Dr. Ya ce "Eh to, ina son a bani damar binciken tukuna, sannan kamar nan da sati biyu zan yi magana, saboda in kira wasu daga ƴan uwana a karɓi kuɗin auren"
Alhaji Tahir ya ce "Babu laifi, Allah ya kaimu"
Ba tare da wata alkunya ba, suka ci abin da dr. Ya gabatar musu, suka yi masa godiya suka tafi.
Farida ta din ga bin sa tana tambayarsa suwaye wannan baƙin, amma yaƙi gaya mata ko suwaye.
Ummi ta sha mamaki, ba ta zaci da gaske ba, sai da ta ga su Alhaji Tahir sun zo.
Alhaji Tahir ya koma gida, ya kira mami sashinsa, Hajiya na tare da shi, sai dai bai gaya mata ba ita ma, sai da Mami ta zo, ta tarar da su ta wani haɗe rai tana harare-harare.
Alhaji Tahir ya ce "To ke fa abun arzki ya same mu, ban sani ba ko mun yi laifi"
Mami ta ce "Meyafaru?"
"Babban mutum ya zo mini da magana, ya je zance an ritsa shi an ce in je in gabatar da kaina idan da gaske yake, dan yau ma daga can nake da ni da su Alhaji Hamza, nan da sati biyu zamu koma mu kai kuɗin aure"
"Ikon Allah, kuma shi ne ba a saka ni a maganar ba sai yanzu?"
Hajiya ta ce "Masha Allah lallai babban mutum an girma, Ubangiji Allah ya sa abokiyar arziki ce, Alhaji a ina take zan yi shishshigi"
Alhaji Tahir ya ce "Au kema babbar aminiyar ta sa bai gaya miki ba? Wai wata yarinya amm.. ammi ne sunan nata ne ko ummi ne, wai ƙawar maryam ce dai".
Hajiya ta ce "Laaa ko dai Ummi, Ummi dai da suka yi islamiyya tare?"
Ya ce "Yes of course haka ya ce mini"
Cikin tsananin mamaki da takaici mami ta ce "What! Wannan kwazgwamar yarinyar baƙa ƙirin?"
Ayshercool 08081012143
FOLLOW ME ON WATPAD VIA THIS LINK.
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends
Masu neman free books ɗina, da free pages duk akwai a kan watpad account ɗina. Irinsu Abduljalal Wata kissar sai mata Wuta a masaƙa Cutarwa Ƙanwar maza Gaba da gabanta Aƙidata Ruɗin ƙuruciya
Zaku iya samun paid pages ɗin a Arewabooks @ayshercool7724. Ko ku tuntuɓe ni kai tsaye ta lambar wayata. 08081012143.
And also don't forget to subscribe my YouTube channel via this link. https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ayshercool.
PAID ADVERT!.
Ina uwargida, amare, har ma da ƴan mata masu burin zama gaba gaba, wurin yin amfani da turarruka na kece raini, masu daɗi da ƙamshi. Mafaka gidan ƙamshi da ke, Ring Rord western bypass kanawa park sun kawo muku
Oll types of Turaran wuta Sandal Halut Irik Difur Gab Gab Kajiji Habil Nabak Humra Kulakcha Dilke da kalta Kayan Garan jiki Muna turara Kaya Kujerar garan jiki Kannada Madarorin turare masu kamshi Man garan gashi Indai kamshine kuzo MAFAKA GIDAN KHAMSHI karshene Sai Sai kin zamo abin kwatanche Ku nememu a wan nan no 08065728702 08025453921
*TALLA!TALLA!TALLA!* *INA MANYAN MATA, UWARGIDA DA AMARE KAI HAR DA ƳAN MATA MASU SON KECE RAINI, DA SHIGA TA ALFARMA, MUN SHIRYA TSAF DOMIN KUWA MUN TANADAR MUKU LAGOS LACE MANYA DA ƘANANA, DAIDAI ALJIHUNNKU BA TARE DA TSAUWALAWA BA* *HAKAZALIKA INA MASU SON ƘAWATA GIDAJENSU DA HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN, UNIQUE DA SAI AN KALLA AN SAKE KALLO, MUN TANADAR MUKU HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN NA ALFARMA NA GIDA DA NA WAJE*. *BAMU TSAYA IYA NAN BA, DOMIN KUWA MUNA SAYAR HAƊAƊƊUN SUPPLEMENT NA GYARAN JIKI, MAYAR DA TSOHUWA YARINYA, GYARAN JIKI DOMIN DAUWWAMAR DA HASKEN TAURARUWARKU A WURIN MAZAJEN KU, TARE DA KECE RAINI A CIKIN SA'ANINKU* *MUN SHIRYA TSAF DOMIN SHARE MUKU HAWAYNKU, DOMIN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU A KAN LAMBAR WAYARMU 08166117985, SAYEN NA GARI MAYAR DA KUƊI GIDA*
BRIGHT PENS A SHIRYE MUKE, WURIN KARƁAR TALLACE TALLACENKU CIKIN FARASHI MAI SAUƘI. *CUTARWA*
*BRIGHT PENS* (FREE BATCH)
MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.
Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.
FOLLOW AND SHARE AYSHERCOOL 08081012143
MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.
Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.
31
Har raihan ya bar harabar gidan bayansa ummi take kallo, ko sau ɗaya bai waiwayo ba, ita kuma ba ta daina zubar da hawaye ba, gani take kamar kallon ƙarshe take yi masa, ba zai sake dawowa rayuwarta da sunan yana son ta ba.
Ta tashi jiki babu ƙwari, ta tafi ɗakinta, ta rufe ɗakin ta saka sakata, saboda kar noor ta zo ta isheta da surutu.
Ta zauna ta din ga kuka, ta ma rasa kukan me take yi.
Ta yi shiru tana tuno irin rayuwar auren da ta yi a gidan idiris, ta kasa manta irin wulaƙantar da ta yi a gidan idiris, irin tozarcin da ya yi mata, tamkar ya auri mushen dabba ba ɗan Adam ba, kuma ɗan Adam ɗin ma ƴar uwarsa.
Ta tuna yadda abokansa suke zunɗensa da angon ɗoɗɗoya, ba zata manta tonon asiri da wulaƙantarwar da Idiris yayi mata ba.
'To idan kuma haryanzu ban warke ba fa'?" Ta tambayi kanta.
Ta dafe ƙirjinta tana zancen zuci, ita dai tun da Allah ya sa kawu yahaya ɗaukkota, yayi ta ƙoƙarin saya mata magunguna, cikin ikon Allah ba ta sake jin wannan matsalar ba, ko maƙiyinta ba ta fatan Allah ya haɗa shi da bala'in da yake cikin larurar sanyi.
Tun da farida ta dawo daga gidan inteesar, tamkar ita za ayi wa kishiya, kamar za ta yi hauka, domin kuwa da ita da wasu daga ƙannenta suka dawo gidan, suna ta bata haƙuri, a kan sai ta daure ita ma, idan ba haka ba inteesar ba zata kwantar hankalinta ba.
Sun cika falo suna mayar da yadda aka yi, noor kuma na ta kokowa da remote tana ƙara volume ɗin tv.
"Wai ke noor baki da hankali ne? Ba ni san meya samu yayarki Inteesar ba ne?"
Noor ta juyo ta kalli mai maganar ta ce "Mutuwa ta yi ne?"
"Wane irin mutuwa, ke ko gidan nata ma baki je ba, balle a haɗu a rarrasheta da ke, kina kallon mahaifiyarku hankalinta a tashe, ita ma can muka baro ta tana kuka, amma ke kina nan kina ƙure wa mutane kunne da ƙarar tv"
Noor ta taɓe baki ta ce "To tun da dai ba mutuwa tayi ba ai barkanta, wanda ba shi da kunya ai dole ayi masa kishiya, haka wata malama ta ce rannan a tv, na ce ashe saura maama"
"Ke uwar taki ki ke cewa ayi wa kishiya?"
Kausar ta ce "Mama hadiza, ki ƙyale yarinyar nan kar ta saka hawan jininki ya tashi, ba isasshen kai ne da ita ba, yanzu sai ta yi miki rashin kunya, kuma ba kowa ne ke zigata yana koya mata wannan iskancin ba, ban da ummi, idan ba haka ba ta yaya ɗa zai yi fatan a yi wa uwarsa kishiya, banda shashasha mara hankali"
"Ni dai ban saka da daƙiƙi a maganata ba, mutum ya bari ya fara gane karatu" kausar ta ja bakinta tayi shiru, idan ta cigaba da tankawa noor, sai noor ta kunyata ta a gaban mutane.
Nan kuma akalar hirar ta koma kan ci wa ummi mutunci, da ziga farida a kan lallai yakamata ummi ta bar mata gida, tun da ta tsofe a gidan babu aure.
Suka gama soko burutsunsu, suka bar gidan.
Ummi kusan kwanan zaune tayi, tayi ta salloli tana kaiwa Allah kukanta, wayarta kuwa ta dubata babu adadi, amma babu saƙon raihan ɗaya da ya sake shigowa cikin wayarta.
Ƙasan zuciyarta ya shiga tabattar mata da sun rabu da raihan kenan.
Bayan ta idar da sallar asuba, message ya shigo wayarta, wani website da raihan ya saka ta shiga, ta yi submitting cv ɗin ta, an kira su screening ciki har da ita, wani sabon gidan talabijin da ba a daɗe da fara shirye-shirye a cikin sa ba.
Yau da safe aka ce su je wurin, ba ta ga saƙon ba sai yanzu, cikin sauri ta tashi ta haɗa credentials ɗin ta, agogo ta kalla, muddin ta ce za ta jira ta yi musu girki, to fa zata makara, dan haka ta dudduba jakunkunanta, ta samu kuɗi ta fito, ta turawa Abdul message na in da ta tafi.
Ko da ta je wurin ta tarar da mutane da yawa, haka nan ta fara bin layi ita ma, ta din ga duba wayarta tana tunanin raihan, shi ne mutum na farko da yakamata ta kira, ta sanar masa da an kirata screening, sai dai ba ta da wannan damar a yanzu.
"Dama na sani, babu lallai ka dawo gareni raihan, amma duk da haka ba zan ga laifinka ba, ina yi maka fatan alkhairi a duk in da ka ke".
Farida tamkar ita aka yi wa kishiyar, ko bacci gagararta yayi, ta taso da nufin ta tarar da abincin safe, Abdul ya shigo ya sanar da ita saƙon ummi, tana fara zage-zagenta, ya fice ya bar mata falon.
Raihan yana zaune yana ta juyi a kan kujera a office ɗin sa, ya kasa taɓuka komai, ya juya kai nan ya juya kai can, in aka jima sai ya ciro wayarsa ya duba ya mayar ya ajiye.
Ya kifa kansa a kan teburin gabansa, yana jin yadda kansa yake masa wani irin zafi.
Jin motsin an buɗe ƙofa ya sanya shi ɗaga kai ya ga me shigowar, babu tsammani ya ga safiyya, tana sanye da doguwar riga straight gown, sai mayafinta a kafaɗa da jakarta, ta shigo bakinta ɗauke da sallama.
Ya amsa mata tare da mayar da kansa ya kifa.
"Yaya raihan, barka da rana?"
"Yauwwa sannu"
Ta nemi wuri ta zauna ta ce "Gidan su wata ƙawata na je, a nan tsukin ne, na ce bari na biyo mu gaisa"
Yayi shiru bai ce mata komai ba.
"Are you ok?" Tayi maganar tana kai hannu goshinsa, ganin yana gumi duk da akwai sanyi a office ɗin.
Rau ta ji goshin nasa ya ɗau zafi, ta ce "Subhanallah, yaya raihan baka da lafiya ne? Jikinka zafi"
Ya ɗago a hankali ya ce "Safiya, ki tafi gida Please, ki ƙyale ni"
"Amma ya zan tafi na barka a wannan halin?"
Kallonta yake yi, yana tunanin dama ummi ce a zaune a gabansa take yi masa magana yanzu.
"Ki tafi na ce" yayi maganar a ɗan hasale, tare da jin haushin yadda ya ta tsare shi da ido, saɓanin ummi da ba ta iya ƙura masa ido haka, sai tana yi tana kawar da kai.
Safiyya ba ta fi shekaru goma sha tara ba, ummi ta girmeta sosai, sai dai shegen iyayi da rawar kai, duk in da ta zauna ba ta da aiki sai hira da samari a waya, ga shegiyar kwalliya kamar ƴar tsana.
Ta razana da tsawar da yayi mata, ta tashi da sauri, har ta kusa fita ya ce "Kar ki sake biyo ni office, office wurin aikina ne ba shirme ba" tayi sauri ta fice tana waiwayensa.
Ummi kuwa ta galabaita a ranar, dan bayan screening, aka ce su jira aka tura musu waɗanda suka yi nasara a waya, ciki har da ita, aka ce su jira ayi musu interview.
Kuɗin hannun ummi ba zasu kai ta ci abinci ba, ga yunwa ta isheta, haka nan suka cigaba da jira.
Ba a zo kan ummi ba, sai kusan biyar na yamma, da farko bayan shigarta studion aka fara yi mata interview, a ɗan tsorace take, ga yunwa tana ji, ɗaya daga cikin masu interview yana cewa masha Allah muryarta mai daɗi.
Ɗayan ya ce "Jin ta ya fi ganinta, wannan da radio ce irin su ne masu sauraro ke ɗokin gani"
Shugaban wurin ne ya shigo, ma'aikatan suka din ga gaishe shi, yana hura hanci, ya dubi ummi ya ce "Wannan fa?"
"Sir tana cikin wanda suka tsallake screening, interview ake yi mata"
"Wannan ɗin?"
"Eh sir"
"Dan Allah ku zaɓo wanda za su yi attracting ɗin mutane, ba wanda sai mun yi ta faman sanya filter muna fafutuka kan mu haska su ba, wannan shirin talabijin ne, ba na gidan rediyo ba!"
Tsit mutanen wurin suka yi, ba wannan ne karo na farko ba, amma a duk lokacin da aka yi mata, jin abun take kamar sabo, sum-sum, ta tattara kayanta, tayi waje, duk suka tsaya suna kallon ummi, shi kuma ko a jikinsa ya cigaba da maganar sa.
Ita ba ta san ma yadda aka yi ta isa gida ba, abubuwa daban-daban cunkus a ranta, ta ɗaukko gajiya da baƙin ciki, tana zuwa gida farida ta dira mata nata tashin hankalin.
"Raihan ka gani ko?, ka kori wanda zai aureni, kaima ka tafi ka bar ni, komai yayi mini zafi"
Tayi kuka-kuka iya yin ta, har ta gaji tayi shiru.
Ta wuni da yunwa, haka ta kwana da wata.
Kwanaki huɗu rabon raihan da ummi, yayi ƙoƙarin sanya abun da ta gaya masa a matsayin hujjar da za ta rabu da shi, amma shi sam bai ji hakan a matsayin hujja ba, dan damuwa yake ƙara shiga na rashin ta, ya zuba mata ido ya ga iya gudun ruwan ta, ko za ta neme shi, amma ya ji shiru.
Hakan ya sanya ya fara zargin anya ba da gaske take ba ta son sa ba, tun da ta iya gaya masa cewar su rabu, kwanaki huɗu amma ba ta sake nemansa ba, dan haka tsoro ya sake shiga zuciyar sa, ummi ba ta son sa.
Ƙasan zuciyarsa yana mamakin yadda ta ce masa ta taɓa aure, shi ba auren ta ne ya dame shi ba, meya kashe auren? A yadda ummi take har ace namiji ya sake ta?.
Daurewa yayi, ya sake bawa ummi kwana ɗaya, ya zamana kwanaki biyar, amma shiru ba ta neme shi ba.
Kwana na biyar, da yamma ya koma gidansu ummi, sai dai ya kira wayarta amma ba ta shiga.
Yana tsaye sai ga motar dr. Raihan ya risuna ya gaishe shi, dr. Ya amsa masa, yayi parking a waje, ya shiga cikin gida.
Raihan ya dudduba, mai gadin gidan ma baya nan, yayi ta kiran lambarta amma shiru ba ta shiga.
Ya samu wuri ya zauna a ƙofar gidan, yana cigaba da dannan wayarsa.
Dr. Ya sake fitowa, ya ga raihan, ya kalli raihan ya ce "Yarona wa ka ke nema ne? Ko wurin Abdul ka zo?"
Raihan ya ce "A'a Abba, wurin Ummi na zo"
Dr. Ya ce "Too, ummi kuma lafiya dai ko?"
"Eh lafiya ƙalau, wurinta dai na zo, na kira wayarta ba ta shiga ne"
"Amma wani abun tayi maka ne?"
Ya girgiza kai ya ce "A'a, ba ta yi mini komai ba"
Dr. Ya jinjina kai ya ce "Yaron kirki, ai babu lallai ummi ta tsaya ta saurareka, a yanzu mijin aure ne ya dace ya zo wurinta, ba wanda za a yi soyayya ba kawai, wannan idan ba ku yi sa'anni ba, ba zaka girmeta da yawa ba. Ka yi haƙuri ka ji ɗana.
Cikin girmamawa raihan ya ce "Abba ummi ta sanni, akwai alaƙa tsakani na da ita, wallahi abba ba ɓata mata lokaci zan yi ba, aurenta zai yi, ina son ta wallahi".
Dr. Yayi shiru yana kallonsa, sannan ya yi murmushi ya ce "Meye matakin karatunka?"
"Na yi degree a ɓangaren Business administration, a ATBU"
"Idan da gaske ka ke zaka aureta, ranar lahadi ka turo mini mahaifinka mu yi magana da shi"
Raihan ya washe baki ya ce "To Abba, in sha Allah zan gaya masa, na gode sosai da sosai"
Dr. Yayi murmushi yayi gaba, a tunaninsa yayi maganin raihan, dan ya zata irin yaran nan ne marasa ji, amma duk da haka nutsuwa da kamalar raihan ɗin.
Raihan tafiya yayi yana murmushi, yana ganin abun kamar a mafarki, yau ya tsinci dami a kala, abun kamar a shirin film, wai ya tura Alhajinsa a nema masa aure? Kai tsaye gida ya tafi.
Sai dai ƙasan zuciyarsa yana tunanin, ummi za ta amince ko kuwa za ta cigaba da gardama ne? Dan ya ga kamar ta raina shi ne a matsayin mijin aure, yayi mata ƙanƙanta.
Yana zuwa ya tafi sashin Alhaji, dan kwanakin nan kusan kullum Alhajin yana gida, ya daki sa'a shikaɗai ya tarar a sashin nasa.
Alhaji Tahir ya gyara zaman tabaran sa, ya ce "Ya aka yi ne? Yanayin farinciki haɗe da damuwa a fuskar babban mutum"
Raihan ya je ya zauna a kusa da shi, ya ce "Kowanne akwai Alhaji"
"Bani labari"
Ya ciro wayarsa, ya nemo hoton ummi da yayi mata, lokacin da suka sayo dogwayen riguna, ya ce "Alhaji ka ga wannan"
Alhaji ya karɓi wayar, ya ƙare wa hoton kallo ya ce "Na gani, meyafaru?"
"Alhaji tana da kyau?"
Ya ce "Masha Allah, very beautiful kuwa, da gani kuma tana da kunya"
"Ita nake son aura Alhaji, zaka nema mini aurenta?"
Alhaji Tahir ya kalli raihan yayi murmushi ya ce "Babban mutum wannan ai matar manyan ce, anya ba ka yi tsaurin ido ba kuwa?"
"A'a Alhaji, ai nima babban mutum ne, dan Allah tayi? Wallahi mutuniyar kirki ce"
Alhaji ya yi shiru ya ce "Ai ni kallon sani nake yi mata ma"
Raihan ya ce "Eh, ƙawar maryam ce, amma ita ba ta girme ni ba, shekrunmu ɗaya da ita, kuma mutuniyar kirki ce ka tambayi Hajiya ma ka ji"
Alhaji Tahir ya dafa kafaɗar raihan ya ce "Easy my dear, in dai kana son ta tayi mini, za a nemi aurenta in dai za a bamu"
Raihan ya washe baki ya ce "Babanta ya ce ranar Sunday wai ka je ku yi magana, gani yake yi kamar ba aurenta zan yi ba, Alhaji tana bani shawarari masu kyau, tana da kirki sosai"
"Allah ya kaimu lahadin, zan je in sha Allah, ko a lokacin suka ce sai a ɗaura, Ubangiji Allah ya sa abokiyar zama ta gari ce"
Raihan ya sosa kai ya ce "Alhaji saura abu ɗaya"
"Ok to ina jinka"
Raihan ya ce "Dan Allah kar ka gaya wa mami sai maganar ta faɗa, ban san yadda za ta karɓi maganar ba. I really have to marry her, Alhaji rayuwar ummi akwai ƙalubale da ban tausayi, dan Allah ka tsaya mini"
Alhaji Tahir ya jinjina kai ya ce "In dai ni ne ka san baka da matsala da ni, ko tsohuwa ka ce kana so, zan wuce maka gaba in dai tana da tarbiyya, kuma ko a hoto, ni yarinyar ban ga aibunta ba, ko ta girmeka in dai kana son ta shikenan, ai soyayya ba ƙarya ba ce raihan, mune muke barin al'ada na rage mana jin daɗin abun da addini ya halatta mana. Allah ya sanya alkhairi ango"
Raihan ya sunkuyar da kai yana murmushi, wani irin farinciki na ratsa zuciyarsa.
Dr. Ya manta da batun haɗuwarsa da raihan, dan ko ummi ma bai nema da maganar ba, sai dai ya rage ganin gilmawarta ko a gidan, ya bar hakan a wataƙila takurar farida ce ta saka ta ƙara takura kanta.
Washegari raihan ya tafi wurin aikin Ummi, amma manager ya ce "Ai ummi yau kusan kwana uku ba ta zo ba, ni ban sani ba, ba ta da lafiya ne ko ya aka yi ban sani ba, kawai ta ce mini za ta je screening, tun ranar ba ta sake zuwa ba, na zata ma ko ba ta gama ba ne ba".
Raihan ya yi shiru ya ce "kira ta a waya ka ce ko ta dawo aiki, ko zaka koreta".