Kenza eBookz

Cutarwa complete by ayshercool - Chapter 50

Cutarwa complete by ayshercool - Chapter 50

Cutarwa complete by ayshercool Chapter 50: Cutarwa complete by ayshercool Chapter 50. Raihan ya yi murmushi ya ce "Dubu ɗarin da ya ce zai baki kuɗin aure,…

3,366 words

Raihan ya yi murmushi ya ce "Dubu ɗarin da ya ce zai baki kuɗin aure, na bashi uku, na ce aje a mayar da wadda aka saka a kula da iyali na gida, ya bar mini ke, jikinsa na rawa ya bar mini ke, dama na gaya miki na fi kowa sonki" yayi maganar yana haɗa fuskar sa da ta ta yana murmushi.

"Cin hanci ka bashi dan ya bar maka ni, cin hanci ba kyau"

"A nan ya halarta" yayi maganar yana dariya.

Raihan na ƙoƙarin ɗaukar su zuwa wata duniyar, wayarsa ta fara vibrating, sunan mami ne a kan screen ɗin wayar, ya ɗaga tare da yin sallama.

"Raihan har ka fi ƙarfin ka zo in da nake ka gaishe ni ko?"

Ya san a rina, ya kwantar da ummi a jikinsa sannan ya ce "A'a ba haka bane mami, zan zo ne"

"Zaka zo sai yaushe? Har an yi ƙulle-ƙullen da zaka kasa zuwa ka gaisheni?"

"Mami, wallahi a gajiye nake ne sosai da sosai, na kira ki ma da safe baki ɗaga ba, but an ce mini gida haryanzu da mutane, na ce bari na ƙyale ki, sai da daddare, amma in sha Allah a satin nan dole na na zo gaishe ki, na gaji ne sosai....

"Dalla rufe mini baki, nusari shashasha. Yaushe aka yi daren da gari zai waye? Lallai lallai ka zo gida ina son ganinka, yarinyar nan safiyya ma na kwance babu lafiya duk saboda kai, kar ka bari ka fusata ni"

Raihan bai yi mamaki ba, ya san a rina, amma shi bai ga haɗin rashin lafiyar safiyya da shi ba, asibiti zai kai ta ko me zai yi mata? Kodayake ba abun mamaki bane ba idan mami na jin rigima.

"Shikenan mami, zan zo in sha Allah" sai dai tun da aka ambaci Safiyya, yana jin yadda bugun zuciyar ummi ya ƙaru a ƙirjinsa.

Ya saka hannu ya ɗagota, amma taƙi kallonsa.

"Sweetheart, an fara kiran sallar magariba, bari na yi alwala na tafi masallaci" ba ta kula shi ba, ta tashi ta nufi ɗaki, ya bi bayanta da kallo, zubin manyan mata sosai.

A hankali ya ce 'Haba mami, is too early for that'.

Bai je kiran mami a ranar ba, dan ya san idan ya je da mutane a gidan, kuma sai ta yi wani abun da zata ci mutuncin ummi, a gaban mutane dan haka ya ƙi zuwa.

Kwanan ummi uku a gidan raihan, ta fara girkin abinci, sai dai rigimar raihan har mamaki take bata, baya zuwa ko ina sai salla, yana maƙale da ita kamar cingam, ga wani irin mugun kunyarsa da take ji, ta kasa sakewa da shi, kusan kullum cikin ƙorafin saka hijjabin nan yake, ta kasa daina yawo da hijjabi.

Kwana na ukun da daddare, Raihan ya je gida, sai da ya je wurin Hajiya yayi mata bangajiya, Alhaji dama baya nan, washegarin ɗaurin aure ya tafi umara.

Sai dai cikin fargaba ya isa sashin mamin.

Ya tarar da ita ta hakimce, gefe ga Nihal a zaune, sai Safiyya da ke kwance a kan doguwar kujera.

Yana shiga suka gaishe shi, ya amsa musu, sannan ya je gaban mami ya risuna yana gaisheta.

"Sai yau Allah ya nufe ka da zuwa? Har ka sallami kanka na yi maka waya ka zo raihan amma ka ƙi"

"Ba ƙi na yi ba mami, wallahi bana iya zuwa ko ina, zirga-zirgar bikin nan na gaji ne wallahi"

"Uwar zirga-zirgar bikin, ka fito fili ka faɗi uban abun da ya hanaka fitar, na yi dana sanin cewa zan yi maka aure ina ganin mafita ce, ashe ruwan dafa kaina ne, ka kwaso bazawara da ta tafi ƙarfin ka, wallaahi ka shiga hankalinka, ka san abun da yake yi maka ciwo"

Ta din ga yi masa faɗa na babu gaira babu dalili, ƙarshe ta rufe da cewar, watanni uku ta bashi, yazo ya nemi auren Safiyya.

Ya ji ta da kunne kawai, ta gama ya ce zai tafi, ta ce ba zai tafi a lokacin ba.

Ummi kuwa na gida na ta duba agogo, dan be gaya mata zai je wani wuri ba.

Har ƙarfe goma saura shiru bai dawo ba, ta kasa jurewa ta kira wayarsa.

Bai ji nauyin mami da ke zaune tana kaɗa ƙafa cikin isa ba, ya ɗaga wayar ya ce "Hello dear".

"Ina ka tafi tsoro nake ji"

Yayi murmushi ya ce "Gani nan, babu dodo a gidan fa"

"Dan Allah ka yi sauri, tsoro nake ji sosai ko falo na kasa fita".

Mantawa yayi da mami a wurin, yayi dariya ya ce "To yi ta addu'a kan na dawo? Kin ci abinci ne?"

"A'a"

Ya ce "But you are not hungry ko?"

Ummi ta ce "Eh"

"Ok ki jirani, in sha Allah yanzu zan taho"

Muryar mami ta jiyo tana cewa "Zaka ajiye wayar nan ko sai na ci ubanka mara kunya" a rikice gaban ummi ya faɗi, ta kashe wayar ba ta san gidan ya je ba da ba zata kira shi ba.

Mami ta tashi ta shiga ɗaki, raihan ya ɗau mukullin motarsa ya fice da sauri.

Abun da raihan yayi, ba ƙaramin mamaki ya bawa mami ba, dan mugunta ta shirya yi, ta zaunar da shi har sha biyun dare, daga nan ta ce dare yayi ba zai fita ba sai da safe, bisa ga miyagun shawarwarin da Anty rakiya ta bata, sai dai abun da raihan ɗin yayi ya bata mamaki.

Ta din ga kiran wayarsa amma a kashe.

A bedroom ya tarar da ummi, kai da ganin ummi ka san a tsorace take, ya ajiye kayan hannunsa ya ce "Sorry dear, yi haƙuri"

"Ban haƙura ba" ta yi maganar cikin shagwaɓa.

"Yi haƙuri, ayi mini afuwa" ba ta nuna masa ta san in da ya je ba.

Ya cika cikinsa da abinci, yana ta yabonta tare da santin abincin.

Ya koma ya hana ummi sukuni, ya gama tara mata gajiya, suna kwance babu tsammani ta ji ya ce "Salma, me ki ka yi wa mijinki na farko ku ka rabu?"

Gyara kwanciyar ta tayi, ta ce "Meyasa ka tambayeni?"

Ya kalli fuskarta ya ce "Am just curious about it"

Tayi ajiyar zuciya ta ce "Labarin babu daɗi, auren huce takaici aka yi masa da ni, saura kwana uku aurensa, ba ya so na, ranar da ango ya tare a tsakar gida na kwana cikin ruwan sama, ba ya so na, tuntuni ni mummuna ce kuma ya rasa wadda yake so yayi niyyar aure. Auren watanni biyu ne dai bai kai uku ba ma, watanni mafi tashin hankali, marasa daɗin tunawa, na tozarta sosai a aurena na fari ko tunawa bana son yi" tayi maganar tana zubar da hawaye.

Ya rungumota jikinsa yana share mata hawayen, ya ce "Is ok, you are much more than special, ke ta daban ce, kuma ya yi wa kansa, ni kuma ya taimakeni irin sosai ɗin nan fa" yayi maganar yana ƙoƙarin zolayarta.

Da safe da ya kunna wayarsa, da kiran mami ya fara cin karo, ya ɗaga ta ƙare masa zagi tsaf, amma ko a jikinsa, shi kasancewar sa da ummi, mantar da shi komai yake yi. Duk da kunyarta har ta yi yawa.

Abu kamar wasa, raihan ya shafe sati biyu cirr a gida, ummi ba ta da aiki sai ɗorawa da saukewa, abokan aikinsa su ka zo ummi ta yi musu girki, har da ƴan china.

Raihan ba ya jin duk wanda zai zo gidansa, saboda matarsa ta iya girki.

Haka zalika ga rigimarsa da ba ta ƙarewa.

Gidan farida kuwa, tun da Allah ya sa ummi ta bar gidan, komai ya taɓarɓare, kausar mugun sok jiki, ba ta iya aikata komai, noor ce ma mai ƙoƙartawa, ita ma idan ta gaji, sai ta watsar da aikin ta ce ta gaji, idan aka tursasata kuma, tayi abun da ba a so.

Uban wankin da ummi ke yi musu, babu wanda zai yi yanzu, mopping gyaran ɗaki, da kuma girki duk abubuwan sai a hankali, girkin ma ba daɗi yake yi ba.

Farida ta ce sai an samo ƴar aiki, dr. Ya ce babu mai kawo masa ƴar aiki, idan aka kawo ta kuwa sai dai ta din ga biyanta, babu yadda za ayi ga kausar a gida, ba aure ba karatu, ace an ɗaukko ƴar aiki.

Dr. Ya kira ummi ya tambaye ta me take so ayi mata da kuɗin sadakinta, ta yi tunanin wata sana'ar, ya bata jari sauran ya cika ya saya mata kadara.

Ummi ta tuntuɓi raihan, amma ya ce a wannan lokacin, ba ta buƙatar sana'a a saya mata kadara kawai.

Duk yadda mami ta so yin abun da za ta ƙure raihan, ta shiga hakkin ummi, raihan sai ya zille, ta yi masa faɗa ta zage shi, ko a jikinsa.

Babban abun da ya ba ta takaici, bai wuce tana tsaka da duba saƙonni, ta ga raihan yayi status da special whats app ɗin sa, da ba kowa ne ya san shi da shi ba, galibi family ne kawai ke da lambar.

Hoton Ummi ya saka, tana zaune a kan dining, ta naɗe kanta da mayafin doguwar rigar jikinta "My perfect woman, khairun nisa'i, Allah ya ƙara miki lafiya"

Ya sake rubuta "Goodnight ƴar aljannata"

A fili ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, bazawarar wannan mummunar"

Hankalin Safiyya ne ya koma kan mami, dan kuwa mami ta sanya safiyyan dawowa gidan da zama.

"Mami menene?"

Ta miƙa mata wayar, bayan ta nemo status ɗin raihan.

Gaban Safiyya ya faɗi, duk yadda ake koɗa munin ummi bai kai nan ba.

Mami ta din ga zage-zage, tana cewa an asirce mata ɗa.

Sai da ta jera kwana biyu tana kiransa ya je tana nemansa, amma ya ce mata ai aiki yayi yawa a office, baya samun isasshen lokaci, alhalin rabonsa da office ɗin tun saura sati biyu bikinsa.

Asabar ce suna baccin safe, kiran Alhaji ya tashe su, raihan ya ɗauka cikin jin nauyinsa.

"Ango ka sha ƙamshi"

"Alhaji ka dawo kenan?"

"Eh na dawo, baka nema na ko?"

Raihan ya ce "Haba dai wane ni"

"To yaya ƴar tawa?"

"Gata nan tana jin ka, ta ce a gaisheka kan mu zo"

"To dan Allah ace mata ina roƙon arziki, a taimaka a bar mini kai ka koma office, ana ta kirana a waya ana nemanka"

Raihan ya ce "To za a gaya mata, amma na zata saura sati biyu sannan na koma"

Alhaji ya ce "A'a babban mutum, a duba mini lamarin nan"

Raihan ya ce "Zan shigo in anjima in sha Allah, sannu da zuwa"

Alhaji ya sauke wayar yana murmushi ya ce "Lallai babban mutum, ka ci gidanku da sati biyun"

Mami da ke kusa da shi ta ce "Kana nufin ba ya zuwa aiki dama?"

"Da sabon auren zai fita aiki? Lallai wato ni ya mayar shashasha, idan na ce ya zo sai ya ce mini wai aiki ya yi yawa".

Alhaji ya kalleta ya ce "Ya zo yayi miki me? Ango ne fa"

A fusace ta ce 'Angon banza, bazawarar?"

"Ba mace ba ce? Ke ina ruwanki ne, Bilkisu ki kiyayi shiga shirgin yaran nan kin ƙi ko? Zaki yi ta fama da takaici kuwa"

Haushi ne ya ishi mami, tare da yi wa kanta alwashin, dole ta san abun yi a kan raihan da ummi, tun da tun ba aje ko ina ba, kansa yana rawa.

Ummi sai magiya take yi wa raihan, ya tafi da ita ta gaida Alhaji, ya ce mata sai an kwana biyu.

Ta ja gefe ta kashingiɗa a kan kujerar da suke ta ce "To ka tashi ka je ka yi masa sannu da zuwa"

"Sai anjima" yayi maganar yana ɗora ƙafafuwan ta a kan cinyarsa yana matsa mata.

Ta buɗe datar ta, taga messages da yawa sun shigo, ta din ga mamaki dan ita wanda take chatting da su ba su da yawa.

Group ta ganta a ciki, na ƴan makarantar islamiyyar su ne, kuma ta ga ana ta tagging ɗin ta, banda messages da ta gani ta private.

Voice messages ta fara buɗewa, ta din ga jin saƙonnin zagi da ashar, wai saboda ta auri ƙanin maryam, ana ta cewa ta yi asara.

Kashewa take ƙoƙarin yi, ta ajiye wayar, ya karɓe wayar, ya cigaba da saurarar abun da suka ce, tare da duba messages ɗin duk da suka yi.

Tun tana jure jin, har ta karaya ta fara kuka, saboda cin zarafin yayi muni.

Wayarsa ya ɗaukko, ya danna ya kara a kunnensa.

"Zan turo maka wasu lambobi, ayi tracking ɗin su duk in da suke dan Allah, zan biya ko nawa, zan turo maka wani abu"

Ya ajiye wayar ya kalleta ya ce "You don't need to cry anymore, zan yi dealing da duk wanda ya ce zai saka ki kuka ko waye shi" daga haka ya tashi ya fita.

Gaba ɗaya jikin Ummi yayi sanyi matuƙa, zagin da suka yi mata yayi mata zafi, tun da suka bar islamiyyar suka yi aure babu wadda ta sake neman ta, sai yanzu da suka sakata a group na makarantar suka ci mata mutunci, da dawo da abubuwan da suka faru a baya, wai tana yawo duk da dauɗa ga muni, dan son zuciya ta auri ƙanin ƙawarsu.

Hankali kwance raihan ya je gida, ya shige wurin Alhaji, Alhaji ya din ga ce masa yayi ƙiba ya ƙara kyau.

Nan suka tare a sashen Alhaji, har da Hajiya da Salim.

Mami ce ta kira shi hankali a tashe ta na tambayar sa yana ina. Ya bata amsar yana sashin Alhaji.

Ko mintuna uku ba ayi ba sai gata, ba ta damu da su hajiya da suke zaune ba, ta nufi raihan tana neman ta kai masa duka.

Alhaji ya miƙe ya ce "Bilki meye haka?"

"Aure hauka ne? A kan me zai sanya ƴan sanda su kama matan mutane? Maryam ta kira ni tana kuka, an kama su an kira shi a waya yaƙi ɗagawa, uban me suka yi maka?"

"Matata suka zaga babu dalili, tsakani nake so ayi musu, kar su zagar mini mata, ba tayi abun kunya ba dan ta aureni"

"Ni ka ke gaya wa haka raihan?"

"Mami ba da ke nake ba, ba kuma da wata manufa na faɗa miki ba, ni na saka ummi ta aureni, idan na zuba ido ana cin zarafin ta, ban yi mata adalci ba".

Hajiya ta yi murmushi ta ce "Allah mai ƙudura, ɗan so ya faɗa hannun matar so, ko dai ki bi a hankali ko ki rasa shi gaba ɗaya"

Ayshercool 08081012143

PAID ADVERT!.

Ina uwargida, amare, har ma da ƴan mata masu burin zama gaba gaba, wurin yin amfani da turarruka na kece raini, masu daɗi da ƙamshi. Mafaka gidan ƙamshi da ke, Ring Rord western bypass kanawa park sun kawo muku

Oll types of Turaran wuta Sandal Halut Irik Difur Gab Gab Kajiji Habil Nabak Humra Kulakcha Dilke da kalta Kayan Garan jiki Muna turara Kaya Kujerar garan jiki Kannada Madarorin turare masu kamshi Man garan gashi Indai kamshine kuzo MAFAKA GIDAN KHAMSHI karshene Sai Sai kin zamo abin kwatanche Ku nememu a wan nan no 08065728702 08025453921

*TALLA!TALLA!TALLA!* *INA MANYAN MATA, UWARGIDA DA AMARE KAI HAR DA ƳAN MATA MASU SON KECE RAINI, DA SHIGA TA ALFARMA, MUN SHIRYA TSAF DOMIN KUWA MUN TANADAR MUKU LAGOS LACE MANYA DA ƘANANA, DAIDAI ALJIHUNNKU BA TARE DA TSAUWALAWA BA* *HAKAZALIKA INA MASU SON ƘAWATA GIDAJENSU DA HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN, UNIQUE DA SAI AN KALLA AN SAKE KALLO, MUN TANADAR MUKU HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN NA ALFARMA NA GIDA DA NA WAJE*. *BAMU TSAYA IYA NAN BA, DOMIN KUWA MUNA SAYAR HAƊAƊƊUN SUPPLEMENT NA GYARAN JIKI, MAYAR DA TSOHUWA YARINYA, GYARAN JIKI DOMIN DAUWWAMAR DA HASKEN TAURARUWARKU A WURIN MAZAJEN KU, TARE DA KECE RAINI A CIKIN SA'ANINKU* *MUN SHIRYA TSAF DOMIN SHARE MUKU HAWAYNKU, DOMIN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU A KAN LAMBAR WAYARMU 08166117985, SAYEN NA GARI MAYAR DA KUƊI GIDA*

BRIGHT PENS A SHIRYE MUKE, WURIN KARƁAR TALLACE TALLACENKU CIKIN FARASHI MAI SAUƘI.

*CUTARWA*

*BRIGHT PENS* (FREE BATCH)

*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*

39

MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.

Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g

Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.

FOLLOW AND SHARE AYSHERCOOL 08081012143

MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.

Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g

Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.

*Alhamdilillah ala kulli halin, ina amfani da wannan damar, wurin isar da ɗimbin godiyata ga ƴan uwana marubuta, tarin masoya makaranta, da sauran al'ummar da suka yi mini ta'aziyyar rashin kakata, ina fatan Ubangiji Allah ya jiƙan magabatanmu baki ɗaya, ya kuma bar zumunci, yayi mana jagora a rayuwa baki daya, Allah ya sanya kaburburan magabatanmu ya zama dausayi daga aljanna, idan tamu ta zo ya sanya mu cika da imani*

39

Alhaji ya ce "Jidda ya haka ne? Wace irin magana ki ke yi kuma?"

Hajiya ta ce "Kaga ƙyale ni na faɗa, ai a baya ban taɓa yi ba, sai mu gani idan dabarar mutum za ta ƙwace shi, me aka yi da maza ko sati uku ba a rufa ba fa? Baki ga komai ba"

Mami kuwa kumfar baki ta din ga yi tana cika baki, Salim ya tashi tsam ya fice, dan baya son hayaniya, hajiya ma ficewa tayi ta bar ɗakin.

"Ka gani ko ka ga abun da ka janyo mini ko?"

Kamar raihan zai fashe da kuka ya ce "Mami me kuma na yi?"

Alhaji ya ce "Raihan bai yi miki laifin komai ba, ke ki ke ƙoƙarin koya masa rashin gaskiya, da kuma raina ki, wuce ka jirani a mota, mu je a kashe wancan case ɗin da ka ɗaukko" Raihan ya fita yana satar kallon mami.

Alhaji ya sake mayar da idonsa kan mami ya ce "Gaskiya hajiya ta gaya miki, na sha gaya miki mu maza idan muna kan wannan gigin da rawar kan, ba a cewa za a tanƙwaramu ta ƙarfin tsiya, ko da kuwa iyayen da suka haifemu ne, ke meye ban yi ba a kanki? Ko kin manta yadda na ɗauke ki, na bar ƙasar sama da wata uku na bar hajiya, na toshe kunnena, na ƙi saurara kowa sai yanzu dan abun ya zo kan ɗanki ki ce ba ki san zancen ba? Shiyasa a kowane ƙadami ake so ka zama mai adalci, ko dan gaba, baki nuna mini illar abun da na din ga yi ba, sai daga baya da na gane kuskurena dan kaina, ka kwanta da mace kawai ba shi ne aure ba, wannan abu ne na lokaci, managarciyar mace mai tsoron Allah, da kuma biyayya ita ake fata. Amma idonki ya rufe dan ɗanki ya auri bazawara, sai me qualities ake dubawa ga mutum mai hankali, ba wai abun da ku ke tunani kawai quality na mace ba" da farko faɗa yake yi mata, daga bisani kuma ya koma nasiha, ya gama ya fice daga ɗakin ya bi raihan.

Ko kaɗan mami ba ta ji nasihar Alhajin ta shige ta ba ma, babban burinta a yanzu kawai, shi ne raba ummi da raihan tun kan ta kanainaye shi gaba ɗaya.

Ba dan tare da Alhaji raihan suka je station ba, da sai raihan ya ja case ɗin, dan kuwa babbar headquarter hukumar ƴan sanda yasa aka kai su, kuma ya tafi da wayar ummi a matsayin shaida.

Alhaji ya ce wa raihan, ya kai shi gidansa, yana son yin magana da shi da ummi gaba ɗaya.

Suna tafe yana yi wa raihan nasiha.

"Babban mutum, na son kana son matarka, amma ka yi ƙoƙari ka din ga ɓoyewa saboda mahaifiyarka da bakin sauran mutane, ka san kishin mata ba lallai sai tsakanin kishiyoyi ba, su ba sa raina abun yi wa kishi, sannan ka yi ta haƙuri kana cigaba da addu'a komai zai wuce, amma matarka ka riƙe ta sosai ka kula da ita"

Readers Also Read