Kenza eBookz

Daudar gora book 1 & 2 by billyn abdul - Chapter 29

Daudar gora book 1 & 2 by billyn abdul - Chapter 29

Daudar gora book 1 & 2 by billyn abdul Chapter 29: Daudar gora book 1 & 2 by billyn abdul Chapter 29. A safiyar basu sami damar barin masarautar ba zuwa ga…

4,337 words

A safiyar basu sami damar barin masarautar ba zuwa ga Barbushi kamar yanda sukaso saboda zuwan baƙi. Sarakunan ƙasar ruman gaba ɗaya ne suka sake zuwa domin ƙara duba jikin Tajwar Eshaan. Inda wannan dubiya ta bama al'ummar ƙasar ruman damar sanin yanayin jikin Shahan-shan ɗin. Dan Alhamdullah har fitowa yay falon da akai musu masauki. Yayi zaman kusan mintuna talatin da su, lokacin da yake miƙewa domin komawa kunnensa ya riski matsananciyar hayaniyar da ke ɗan tashi sama-sama kamar daga wajen masarautar. Da farko baiyi mamaki ba, dan tunanisa har yanzu waccan zanga-zangar ba'a dainata ba. Sai dai ya ɗan dakata daga yunƙurin barin falon ya kai dubansa Sayeed Fayzul-haq daya jagorancin shigowar sarakunan garesa. Cikin sauri ya matso garesa kansa a risine cike da girmamawa. “Amincin da kariyar UBANGIJI su cigaba da gadinka ya adalin shugabanmu ko ana bukatar wani abu ne?”. Shiru kamar bazai ce komai ba, sai kuma ya nisa a hankali tare da ɗan lumshe idanunsa ya sake buɗewa a kansa. A kan lips ɗinsa ya furta, “Akwai abinda ke faruwa ne bayan wanda na sani?”. “A sani na dai babu wani sabon abu, sai dai idan akan waccan hayaniyar ne ƴan jarida ne ke cike da nacin son sanin yanayin jikinka kamar yanda al'ummar ƙasar ruman ke ƙulafuci suma. Duk da kullum cikin jeren zuwa suke ƙofar masarauta dama, amma yau ganin baƙi suke tunanin zasu sami abinda suke so shine suka taru fiye da kullum. Shine jami'ai ke ƙoƙarin hana dukkan hanƙoramsu ta hanyar sake tsaurara tsaro”. “A tara taron manema labarai zanyi magana da su zuwa gobe Insha ALLAH”. A firgice, a razane, a kuma ɗimauce Sayeed Fayzul-haq ya ɗago batare da ya farga da abinda yay ɗin ba. Dan wata irin saukar tarnatsa kalaman Tajwar Eshaan ɗin da suka fita a bazata sukai a cikin kunensa. Tabbas bashi kaɗai ba ga duk wanda zaiji dolene al'amarin ya firgitar da shi, dan abune da bai taɓa faruwa ba kai tsaye kamar haka a ƙasar ruman. Koda Shahan-shan nada buƙatar ganawa da manema labarai sai dai ya wakilta waninsa bisa umarninsa ya tattauna da su da yawunsa. Amma duk da Tajwar Eshaan ɗin bai fito yace shine zai tattauna da su ɗin ba a yanzu Sayeed Fayzul-haq ya girgiza ƙwarai matuƙa. A cikin abinda bai wuce awa guda ba wannan saƙo na Tajwar Eshaan ya shiga karaɗe lungu da saƙo na ƙasar ruman da kewaye. Ko'ina ka leƙa zancen da ake kenan Tajwar Eshaan zai zauna da manema labarai a safiyar gobe insha ALLAHU. Kowa burinsa gari ya waye kawai, ba ƴan jaridar ba ba talakawan ba, hatta da manyan ƙasar ma masu manufofi daban-daban sun shiga jerin masu jiran.

A daren shugabannin ƴan jarida na ƙasar ruman suka buƙaci zama na gaggawa, dan dolene su tattauna abinda ya dace kasancewar akwai tambayoyi fal zukatan al'ummar ƙasar ruman da ke son a amsa musu, kuma daga bakin Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed suke buƙatar ji duk da basu da tabbacin samu saboda abune mai matuƙar wahalar gaske kowa ya sani......

★•••• ★•••••

Hankali a tashe suka iso ga Barbushi. Duk da tsalawar dare da na duhuwar jejin babu alamar tsoron abin cutarwar tattare da su saboda bushewar zukata. Hasalima su ba abinda zai basu tsoro anan bane damuwarsu. Wanda ya wuni basu tsoro da zama cikin wasi-wasi na rashin makamar riƙewa ne matsalarsu. Boka Barbushi da ƙazanta da dattin kafirci yay ma fuskarsa da gangar jikinsa ƙawanya ya tuntsire da wata irin mahaukaciyar dariya da sai da ta ƙular da Miran Arshaan da Miran Jasim. Sai dai basu nuna ba balle damar cewa wani abu. Sai da yay mai isarsa kafin ya tsagaita da maida hankalinsa garesu. Basu da matsala akan faɗin abinda ya kawosu, dan sunyi imanin ya san komai hatta gaibu (wa'iyazubillah 😭🙏), sakamakon idan sun zo wajensa tun kan su faɗi abinda ya kawosun shike zayyane musu. A yanzun ma dai yana rufe bakinsa daga dariyar tasa ya fara zayyano musu.... “Sarƙa-sarƙar sarƙaƙiya ce mai cike da mugun ƙullin dake ɗaure da kowa. Babu mai iya gane tushen farawarta balle kamo bakin zaren ƙarshenta kasanwar anyi komai a cikin duhun da idanun kowa bazai gani ba ko wanene shi a hatsabibanci. Ina mai tabbatar muku shi ɗin hatsabibi ne ƙwarai da gaske. Kuma tabbas a yanzu ne aka fara wasan hhhhhhhh!!!! Hahahahahahaha!!!!...” Yanda mummunar daiyarsa ke amsa kuwwa a jejin haka sautin bugun zukatan Miran Jasim da Miran Arshaan ke bada nasu sautin a ƙirazansu. Hatta yawun dake gudana da kai kawo a bakunansu zuwa maƙoshi ya ƙame ƙaf. Hargitsatstsun idanunsu kawai suka iya zubawa boka Barbushi da ke kwasar dariya har yanzu. Cikin ƙarfin hali da tsawa-tsawa na fitar hayyaci Miran Jasim yay ƙoƙarin dakatar da shi a kausashe.. “Koma mi ya taka ko yake taƙama da shi mu bai damemu ba. Muna son a ƙarasa mana rayuwarsa a wannan dare, haka itama yarinyar ta hanyar uwarsa Malikat Bushirat, asirinta ya tonu duniya duk ta shaida itace ta kashe yarinyar kaga sai ya gana da ƴan jaridar da hujja. A haddasa babban rikici tsakaninsu da talakawan ƙasar nan harma da tsohuwar can da rayuwarta ta zame mana ƙadagaren bakin tulu. Mu kuma zamuyi amfani da wannan rikicin wajen kawar da Eshaan ɗin ta hanyar aikin da likitoci zasu masa, sai kawai ace bugun zuciya ne dalilin abinda ke faruwa..” “Hhahahaha!!! Hhhhh!!!” Barbushi ya shiga kwasar dariyar wulaƙanci sa mai tsananin bada amsa kuwa. “Ina son mugunta da mugu hhhhh!!. Ina son naga ana mugunta HHhH!!. Koba komai ƴan wuta sun sami ƙaruwa hhhhh!! (Wa'iyazubillah. Ya rabbi badan halinmu ba ka karemu daga nema a wajen waninka, ka tsaremu daga shirka da mushirikai🙏😭). Duk da kalamansa na ƙarshe basu ji ko gezau ba akan ƙudirinsu, duk da kuwa sunyi imanin UBANGIJI ya halicci (WUTA DA ALJANNA) babu kokwanton zai cikasu kuma kamar yanda ya alƙarwanta, sai dai son cikar burin duniya na ƙanƙanin lokaci ya rufe zukatansu da idanunsu, sun jima matuƙa tare da shi sai gabanin asubahi suka koma masarauta ta ɓarauniyar hanyar kamar yanda suka fita....

*_WASHE GARI_*

Ƙarfe goma na safe ƴan jarida da taron al'ummar ƙasar ruman sun cika ƙofar masarautar Ruman cika mai ban mamaki kai kace Tajwar Eshaan ɗin zai fito ne ƙuru-ƙuru su gansa kamar yanda suka jima suna bege a rayuwarsu. Dole aka baza jami'an tsaro saboda gudun abinda zaije ya dawo.........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (05)

........Tun a jiyan Doctor Afif yaso fahimtar da Tajwar Eshaan haƙuri da wannan zama saboda jikinsa har yanzu bawai ya kasance yanda ake bukata bane ba. Hasalima ana shirye-shiryen masa aikin da ya rage ne daga nan zuwa kwana biyu. Kallonsa kawai Tajwar Eshaan yay har ya kammala masa bayanin cike da girmamawa kai a rissine. Bai ce da shi komai ba tsahon lokaci, sai daga baya ya ɗan girgiza kansa kawai iya amsar kenan. Dole doctor Afif ɗin ya haƙura gudun shiga hurumin daba nasa ba.

Kamar yanda ya saba komansa kafin faruwar al'amarin haka ya gudanar a yau ma duk da rashin ƙarfin jiki dana ciwon dake sukarsa kaɗan-kaɗan. Sai dai kasancewar jarumin jarumai gwanin juriya da shanye kowane irin al'amari cike da ƙarfin hali ya shirya cikin ƙasaitaccen shirinsa mai firgitar da duk wanda ya ɗaura idanunsa a kansa shi ɗin wanene. Shirine da ya bayyanar da tsantsar ƙyawun da ALLAH ya bashi da cikar kamalar mulki mai tafiya da kwarjinin kasancewar sa cikakken mutum mai matuƙar zama barazana ga kowa. Ƙamshinsa matuƙar narka da zuciyar mai shaƙa yake a kowane motsinsa. Ya cika ɗawusun da al'ummar ƙasar sa ke kiransa wajen iya ado da zauna masa a jiki koma ya zarce. Dan tabbas ko'a cikin dubu baya boyuwa da lalube ma cankosa ake kasancewarsa ɗaya ƙwallin ƙwal Shahan-shan Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed da babu wani mai irin matsayinsa a ƙasar ruman da kewaye kaf. A lokaci ɗaya gaba ɗayan masarautar ta ɗauki tsitt kasancewar fitowarsa a zahirinsa cikin takun dake tabbatar ma ga duk wanda bai san wannan fuska a zahiri ba shi ɗinne dai da suke cike da ƙishirwar son gani. Cikin karkarwar jiki data zukata hadimai ke faman zubewa bisa kafafunsu zukatansu na neman wantsalowa ta bakunansu duk da a kallo ɗaya da suke masa basa sake iya daga kai yin gigin kallo na biyu. Baga hadiman kawai ba hatta da masu faɗa ajin masarautar ma wutar kawunansu gaba ɗaya ta gama ɗaukewa dan al'ajabi. Domin kuwa tun fitowarsa hadimansu ƴan leƙen asiri har ci da goshi suke wajen isar da tsegumi ga iyayen gidan nasu kan fitowar Shahan-shan Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed yau a zahirinsa ga kowa babu shamaki.....

★A yanda dokin ya cika bargar da haniniya da fisge-fisge ya matuƙar tada hankalin masu kula da su. Iya kokari yi suke na ganin sun dakatar da shi daga ballewa saboda saninsa amma hakan ya gagara. Da yay wata irin mahaukaciyar girgiza sai ga zaratan mazan su biyar a ƙasa wanwar. Darewa a ka dingayi duk inda ya keta a cikin masarautar, yayinda hankalin mafi yawan hadimai ya tashi sanin babu mai iya dakatar da shi sai mai shi......

Cak ya tsaya daga yunƙurin shiga motar da aka tanada domin zuwansa falon da zaiyi zaman tattaunawa da yan jaridar duk da kuwa a cikin masarautar ne. Ko'a cikin barci yaji takun waɗan nan kofatan bazai iya manta mai su ba. A zabure jami'ai Da Gazi dake zagaye da shi suka zabura domin dakatar da ingarman farin doki da ko ga mai kallo ya san ya wuce tara irin ta gaba-da-gaba. Amma domin kare shugabansu a gare su tunkararsa dole ne koda tasu lafiyar bazata samu kariya ba. Ai girgiza ɗaya yay ya zubar da kusan uku da suka tunkaresa, wasu na ƙoƙarin sake tunkararsa yay wata irin turjiya, ya kwafuci ƙasa ya sake ƙwafuta yay girgiza mai haɗe da haniniya sai gashi gaban Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed. Dole kowa ya dakata wajen ya ɗauki shiru na wucin gadi duk suna kallon ikon ALLAH. A hankali ya kai tattausan hannunsa a fuskar dokin ya shafa, haniniya ya sakeyi da ƙwafutar ƙasa ya girgiza jikinsa. Wannan al'amari ya matuƙar ƙayatar ga duk wanda ke wajen, duk da kuwa ba'a yau suka saba ganin irin haka ga dokin ba a duk lokacin da ya kasance tare da Tajwar Eshaan ɗin.. Cikin muryarsa mai tausasawa da tarin nutsuwa ya kema dokin magana yana shafasa a hankali fuskarsa da ƴar sakewa kaɗan sai dai ba murmushi ya ke ba. Hasalima sai mai lurane zai fahimci sassaucin fuskar tasa a zahiri. Ya kwashe tsahon mintuna huɗu da dokin, hakan ya bama duk wanda ke a wajen damar cigaba da satar kallonsa, wanda kuma aka kaima gulma na ƙoƙarin tururuwar fitowa da leƙe a maƙe. Cike da ƙasaitarsa ya damƙa dokin a hannun Sayeed Fayzul-haq, shi kuma ya shige motar da ke buɗe har yanzu. Da sauri hadimin ya maida ya rufe murfin kansa a rissine. Da ga haka motocin suka nufi inda za'ai zaman.

★Isar da saƙon shigowarsa katafaren falon ya saka duk wani mahaluki mai numfashi yin ƙasa da kansa. Daddaɗan ƙamshinsa shine abu mafi ɗaukar hankali a garesu da saka nutsuwar zuciya. Yayinda takun sawayensa masu tabbatar da ƙasaitarsa ke ɗauka da sauka da bugun zukatansu. A zahiri da baɗininsu cike suke da ɗokin kasancewa a tare da shi koda bazasuga fuskar tasa ba. Duk da kasancewar sa Shahan-shan mafi ƙarancin shekaru a cikin duk Shahan-shan da suka gabata a daular ruman kwarjininsa na razanar da su, dan ko makaho ya laluba zai bada amsar Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed cikin jerin jaruman maza zaratan gaske koda basu ganin ainahin zahirinsa kuwa. A hankali ya kai zaune saman kujerar da aka tanada dominsa cikin nutsuwarsa da sanyin da rashin ƙarfin jiki ya haddasa masa. Kallo ya dinga binsu da shi cike da nazarinsu kafin ya lumshe idanu da buɗewa yana jan ƙaramar iska ya fesar. Su Miran Jasim da ke biye da shi bayan an kai musu labarin fitowarsa babu shamakin da ke ɓoye zahirinsa suma duk zaman sukayi ransu yana ƙuna matuƙa, wasu kam ransu fari ƙal da abinda Tajwar Eshaan ɗin yayi. Kasancewar sun tsara abin a yanda sukazo bisa jagorancin wakilai ɗai-ɗai daga kowace jiha sai zaman ya kasance a tsare. Ko sau ɗaya a cikinsu babu wanda ya gwada iya ɗaga kansa ɗan kwarjininsa ya gama mamayesu tun kan su gansa, sai dai tabbatar da kammalawar zamansa ya sakasu sake gurfana gaishesa. An amsa musu da yawun Shahan-shan batare da shi yako motsa ba daga zaman ƙasaitar da yayi har sai da falon yay shiru. Umarnin da aka basu na shiryawa ya saka su miƙewa musamman masu gyara camaras da tabbatar da abin ɗaukar maganarsu ya zauna yanda ya kamata a inda aka jerasu reras gabansa kaɗan. Kaɗan ya rage zukatan wasu su wantsalo da gasken gaske. Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed a zahirinsa, wannan fuskar da suka jima da mafarki da kulafucin son gani a bayyane ce a zahiri babu shamaki yau. Duk da kowa yay masa kallo ɗaya baya sake maimaitawa a ransu ayyanawa suke dole ya dinga kasancewa a ɓoye kam duk da cewa hakan al'adarsu ce, dan zasu iya cewa shine na farko a tarihi cikin duk Shahan-shan da suka gabata daya bayyana fuskarsa a zahiri. Abune da bai taɓa faruwa ba. Mafi yawancin al'ummar ƙasar ruman ƙyawawane duniya ma ta shaida hakan, sai dai fa a yau kam sunga inda ƙyawu yake na zahiri, ƙyawu irin wanda ko'a ƙasar ruman ɗin zasu ambacesa da ƙyawu ɗan gaske da ba'a iya ɗauke ido a kallo ɗaya ga mai shi... Wannan firgici ba'a iya falon kawai ya kasance ba. A duk lungu da saƙo na ƙasar ruman ne dan tunda aka ɗora Camara ga Tajwar Eshaan komai ya koma live ga masu kallo da saurare kamar yanda ya bada umarni.. A karan farko ya motsa pink lips ɗinsa da kyar ya fara magana a hankali. “Inama duk wanda ya kasance anan fatan alkairi da godiyar amsa wannan gayyatar. Tare da duk al'ummar ƙasata baki ɗaya. Kakannina, Iyayena yau ga ɗanku. Yayuna ga ƙaninku, ƙannena ga Yayanku, ƴaƴana ga Abbun ku ba'a matsayin shugaban ku kawai ba. Zaune nake anan da suna Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ba Shahan-shan ka ɗai ba. Zaune nake domin baku haƙuri, zaune nake anan domin roƙonku alfarmar zama lafiya, zaune nake anan domin baku damar bin hanyar data dace kubi dan ganin kun miƙani a duk inda kuka aminta da a tuhumeni bisa duk laifukan da kuke kallon nayisu gareku. Na yarda kuma na amince zan zama mai amsawa in har na aikata koda zai kasance ƙarshen numfashina kenan. Bakuma zan zargeku ba. Kuje, kuje daga yau na baku damar yanke hukunci, zan kasance mai jiranku. Zan kuma kasance mai biyayya ga shari'a, zan kuma damƙa wannan mulkin ga duk wanda kuke buƙata na biku da fatan alherin ya kasance alkairi ga ƙasar ruman baki ɗaya a bayana. Fatan alheri a gareku baki ɗaya, da roƙon afuwar gazawata akan ku. Nagode nagode da fatan alherin da kuka min a baya da ma wanda wasunku ke min har a yau👏”.

Tabbas da akwai camara da zata iya ɗaukar ƙasar ruman baki ɗayanta a wannan lokaci da ansha kallon mamaki, da ansha kallon yanda komai ya tsaya cak tamkar ana juya ƙasar da na'urar remote. Kalmomi ne da gaba ɗaya bazasu gaza ɗari da hamsin ba, amma sun shiga al'umma fiye da zamansu guda dubu. Sunzo a wata siga da babu wanda ya taɓa zato ko tsammanin fitarsu daga bakin da suka fita. Abu na gaba mamakin ganin fuskar wanda ya ambatasu ga wasu mutane da ruɗani ya riska. Dole su kira al'amarin da ruɗani kasancewar sanin wannan fuskar a fuskar da basu taɓa zato ko tsammani ba. Motsin gaɓɓai basu fara bayyana ba a zahiri sai da ƙyaƙyƙyawar fuskarsa ta gushe daga allunan talabijin ɗinsu. A take amon sautika ya fara tashi a sigar furuci daban-daban wanda ya hargitse ƙasar baki ɗaya tako ina, har zuwa dare kuma babu alamar lafawarsa, dan tako ina sharhine ke kai kawo ga masu fashin baƙi akan kalaman Tajwar Eshaan ɗin, ata wani gefen kuwa wasu videos masu ban mamaki suke faman kaikawo a yanar gizo daga talakawan ƙasar game da fuskar da suka gani yau matsayin Shahan-shan ɗinsu. Sai dai abin farin cikin kowane furuci kan fitane da alkairansa batare da sun san shi ɗin wanene ba. Yayinda wasu kuma ke nuna irin shock da suka tsinci kansu na ganin fuskar a matsayin Shahan-shan ɗinsu.........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (06)

........Sir Fawzan na ɗaya da ga cikin waɗanda suka tsinta kansu a wannan razanin. Hakama Azaan da Fhakir da suka kasance yaransa da duk inda ya saka ƙafa a ɓoyayyen yanayinsa suna biye batare da sun san ainahin wanene shi ɗin ba. Ire-irensu nada yawa da Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ya mu'amulanta ta fuskoki daban-daban na alkairinsa da bibiyar al'amarin al'ummar ƙasar tasa batare da sun sani ba sai a yau da ya bayyana kansa a zahirinsa garesu.....

★★.....

A cikin masarauta wannan al'amari daya jagoranci motsin ƙasar a yau ya matuƙar sakasu a rudani da firgici, dan da gasken gaske Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ya musu duka irin na bayan ƙeya na cikin duhuwar da ko zaka tsinke wuyanka dan waige bazaka iya hango wanda zai maka ba sai bayan yayi idan yaso. Hankula da damar gaske sun tashi, irin tashin da sukejin ko wuta aka nuna musu zasu iya jagorantar jefa Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ɗin a yau. Shi mai mulki ne, mulkin kuma shine abin baƙin cikin mafi yawansu. Su da shi duk suna gwagwarmaya ne akan waɗanda yake mulka ne. Sai dai su ƙoƙarin wargaza kansu suke yi masa bore domin cikar burikansu, shi kuma son dunkulesu yake domin sauke nauyinsu da ALLAH ya daura masa duk da kasancewarsa mai shekarun da har yanzu basu cimma arba'in ba a duniya...

Abinda zai sake birgeka ga wannan bawan ALLAH tun da ya gama fuskantar al'ummar sa babu wanda ya sake jin wani motsinsa a wannan dare sai likitocin da ke zagaye da shi, wanda a yau zasu masa aikin da ya rage insha ALLAHU kamar yanda ya buƙata......

★★..... ★......

Duk jarumtarta da juriya a wannan gaɓar sai da nakasun ƙaddara ya kaita ƙasa. Ƙarancin cin abincinta da tsantsar damuwar da suka zame mata abokan rayuwa sun mata illa matuƙa. Ta fita a hayyacinta sosai tamkar ba Iffahr nan ba ƴar gayu mai bakin da kadata sai wanda ya gawurta. Duk da ƙarfinta ya ƙare, rashin yaƙinin cigaba da rayuwa bai sa ta sallama ba akan burin maida fansar ta ga su Miran Jasim. Babban burin da take fata a yanzu koda bayan ranta shine al'ummar ƙasar ruman su kasance masu tsananta bincike wajen sanin ainahin Tajwar Eshaan bin Haysam Abdul-majeed a zahirinsa da baɗininsa. Duhuwar ƙaddara da bin makauniyar hanya sun haska mata wasu muhimman abubuwa a wannan tafiyar, sai dai kash ita tata tazo ƙarshe, labarinta ya zama tarihi a gaɓar daya kamata ace itace mai rubuta tarihin abinda ya kasance burinta da sadakarwata. Ta saki wani murmushi mai wahalar fassara ga wanda ya santa sakamakon ƙamshin turaren data ɗauka tsahon mintuna tana shaƙa a dinɗaɗɗen ɗakin kurkukun da take da yaƙinin yafi na kowa matsi da tsauri, sannan ita kaɗai ce mutum mai numfashi a wajen sai ko dakarun da ke zagaye da ita da sunan tsaro....

(Kowanene Iffahn ta shin shino haka kuma? Ta hanyar turarensa, da alama dai wanda ta sani ne ko take hasashe🚶).

Batai yunƙurin buɗe idanunta ba kamar yanda bata motsa ba. Ɗakin ya cigaba da zama shiru babu alamar wanda ke tare da itan zai tanka har tsahon wasu mintuna data fara jin gundira da kasancewar koma waye a tare da itan. Sai dai kuma da alama akwai wani farin ciki, dake kokawa da gargaɗin ba haka bane a tattare da yaƙininta. Kunya da tunanin idon da zata iya kallonsa in har ma shi ɗinne yasa taji bazata iya ɗagawa ta tabbatar ba. Duk da duhun ɗakin hasken dake leƙowa ta mitsitsin windown da wutar lantarkin waje ta hasko ya taimaka wajen ganin wanda ke zaunen. Sanye yake da kaya baƙaƙe hatta da yatsun hanunsa a cikin safar hannu suke. Fuskarsa kam na sakaye da norse mask daya sakaya ainahinsa, sai baƙin gilashi daya ɓoye idanunsa. Ga mutum mai hangen nesa da ilimin saurin ɗaukar haske kan abu zai kira kowanene da mace, dan ƙira da dirin jiki sam basuyi kama dana namiji ba duk da akwai maza masu ƙarancin girma ta ɗa namiji. Babu alamar damuwa da rashin ɗagowar Iffahr da ta tasa gaba ta na kallo, haka suke sake shanye adadin wasu mintunan babu alamar nuna gundira duk da kuwa tsakkiyar dare ne da shiru ɗin masarautar zai iya tabbatar maka da haka kai tsaye. Da alamar jiran cikar lokaci aka kai duba ga agogon dake a tsintsiyar hannu, batare da cewa komai ba akai saurin ɗaga yatsu biyu ga wanda ke baya tsaye da babu tantama shikam namiji ne. Cikin gyaɗa kawai ya zaro syringe dake jikinsa mai ɗauke da ruwan allura ya nufi Iffah da har yanzu bata ɗago ba, babu ma alamar zata ɗago ɗin. Zabura tayi da ƙoƙarin son sakin ƙara sakamakon jin saukar ƙarfen allura ta kusa da gefen wuyanta da ke tsakani da kafaɗa. Abinda aka manne bakinta da shi ya hana fitar ƙarar, cikin abinda kuma bai wuce mintuna uku ba sun fice dai-dai da shaƙar wani ɓoyayyen ƙamshi daya bambanta dana farkon data fara shaƙa data gama hasashen mai shi. Sai dai na yanzu ya sake tabbatar mata da an yaudareta da ƙamshin ne kawai ba Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ɗin bane......

Kammala theatre ɗin Tajwar Eshaan dai-dai da fiddo Iffah da mintuna kaɗan baya aka farga da halin da take a ciki ta dalilin jami'an dake zagayata a kowane dare domin tabbatar da lafiyarta bisa umarnin Malikat Haseenat. Da farko su sunma zata ta mutu ne, ruɗewarsu da kururuwarsu taja hankalin jami'an dake zagaye da sauran ɗakunan masu laifin dan waɗanda ke zagaye da Iffar har su huɗe duk suna zube alamar akwai abinda aka shaƙa musu suma. Sunyi gaggawar sanar da halin da take a ciki, cikin ƙankanin lokaci ƙwararren likitan dake a clinic ɗin masarautar ya isa gareta, sai dai a take ya fahimci abin babban al'amari ne, dan haka shima ya tabbatar da dubata bazai yiwu ba anan. Kai tsaye Malikat Haseenat ta bada umarni ɗaukarta zuwa clinic ɗin. An isa da Iffah clinic hankali tashe, yayinda likitoci suka rufu a kanta, sai dai abin mamaki iya bincike har na kusan awanni biyar basu gano komai ba, gata kuma a sanƙare babu inda ke motsi a jikinta sai bugun zuciyarta da na fitar numfashi kawai. Hatta abincin da aka kai mata a daren ranar dana safiyar duk anyi bincike kansa babu komai da aka zuba wanda zargin kowa ya karkata akai. Tofa wannan al'amari yazo da wani sabon hargitsi da yafi na lokacin Tajwar Eshaan, dan fa a wannan karon zukatan jama'ar masarautar ma kansu da bakunansu sun fara karkata da wani abu daban mai nuni da (anya kuwa babu wata a ƙasa?). Wannan kalma tayi wata irin amsa kuwa ga mafi rinjayen al'ummar cikin masarautar da zuwa yanzu komai yaje ga kowa. Dama gasu a cikin wata ɗimuwar da aketa faman ka-ce-na-ce da babu alamar zai ƙare anan kusa...

(🤔nifa gaskiya🥱, tom🤫 bara dai nayi shiru🤭).

★★.....

Readers Also Read