Kenza eBookz

Duba min baya fakon biri - Chapter 23

Duba min baya fakon biri - Chapter 23

Duba min baya fakon biri Chapter 23: Duba min baya fakon biri Chapter 23. Ina daki ina sallah naji shigowanshi har kofan mu ya tsaya daidai kofan…

2,993 words

Ina daki ina sallah naji shigowanshi har kofan mu ya tsaya daidai kofan mahaifiyarshi yana sallama hakan yasa nagane ya dawo gidan kamar yadda yace. Baifi minti biyu ba daidai ina idar da sallah naji muryan mum tana kirana daga dakinta shafawa nayi na mike ina amsawa zuwa dakin nata gani mum nace daga inda take zaune take fadin. Jeki falo kiba yayanku abinci don Allah na amsa dato ai naji muryanshi ina sallahne dama na juya zuwa falon kitchen na fara zuwa na dauko abincin nafito mai dashi dama a shirye yake a kitchen din. Zaune yake saman kujera yayi shiru ya kurawa kasa ido kamar mai tunane jikinshi yana saye da tufafi baki na dinki irin na maza sai yar hulan maza irin na pakistan mai gashi daya kafa a kai abinka da farin mutum sai kalan kayan ya amshi jikinshi sosai. Sallamana falon yasashi dago kai yana amsawa cikin yar siririyar murya nagaidashi tare da fadin akawo nan ne ko in aje a dinning ? No kawo min nan ya fada dama nasani yaranta basu damu da zama saman dinning suci abinci ba dan table na jawo na dora masa a gaban sa zan juya yace . Don Allah dauko min ruwa mara sanyi na amsa da to na kawo mai goran faro da cup har da ruwan wanke hannu na aje thanks ya furta tareda cire hannun daya tokare fuskanshi dashi ya motsawa zuwa gaban abincin. Hannu ya daure kafin ya bude abincin ina jin sautin bissimilanshi a daidai lokacin da zaikai loman farko a bakinshi don ina falon ban fita ba saboda na tsaya tattara kayan da mum ta bari nata watse a falon da muka shiga sallah. Ina shiga mum din tana fitowa tace dani harkin bashi na amsa da ehh nashige na dan dade ban fito ba don na tsaya dan gyara a dakin kodana fito falo na fito don indan samu abinda naci alokacin. Yana zaune tare da mahaifiyar nasa da alama wani zance sukeyi hakan yasa ban tsaya ba na shige kitchen acan tsaye na tsaya naci abinci na kusa karasawane naji muryan mum tana kirana na amsa. Koda nafito ban sameshi ba a falon ashe suna wanan ita kuma Aisha matarsa nata kwala masa kira akan yazo ya dauketa mana baiga dare yayi bane da farko ya fada mata yana wajen mum ne ai. Bata daddaraba ta dameshi da kira karshe ma fada da masifa ta kamayi masa duk mum najinsu tace ta tashi yaje itama bata da lokacinsa dole ya tashi yaje ya sameta a inda take shine mum ta kirani na kwashe kayan dayaci abincin a falo. Sai washegari da yamma mum din ke fadin kinga yaronga ko don kada in masa zance akan matarshi son nace ya tabbatar daya daukota sunzo sun gaida Alh da hjy cewa Dada. Shine shima ya tafi ba tare dayazo yai muna sallama ba yaje ko bace ba gashi gata suje suyi tayi dama abinda kowa ke masa gudu ke nan da auren wa yan nan marasa tarbiyan da boko ya ratsa gidansu ke nan. Yanzu haka itace ta hanasa zuwa ko aikema kin sani tunda bai taba tafiya baizo munyi sallama ba ko yayako yake sauri sai yazo gidan nan watara zuwa zuwa ma saisu shigo garin bamu sani ba harsu gama abinda sukeyi basu zo gidan nan ba ke nan. Kai haba mum bari mashi wanan fatan aishi ba zai yarda haka ya faru ba akansa tunda yasan hakkin iyayye yaushe kuma tunda har nace ga abinda zasuyi taki zuwa kuma ta hanashi shima. Wai dako ta zama sakarai wallahi tunda wata rana itama uwace don haihuwa zatayi ai haka dan zai mata kuwa na fada a hasale raina yana baci da zancen ina maijin haushim yaya din. Ta yaya mai hankalibda hangen nesa kamarshi zai tsaya mace ta juyashi kamar sakarai wanan tunanen nakeyi a raina sunana da mum ta ambata yasa na kallota. Tace jinyan da suwaye a wurin hjy suke zancensu nace matan daddy Enugune tace ai sai kowa yaji wanan zancen da hjy ce zance zata kyale sai ranan da suka hadu zatacisu taran hakan amma wa yan nan sushiga mitan hakan ke nan sai kowa yaji agidan nan. Allah sarki komin fushin uwa da danta bata son yau ace ga laifin danta a waje tausayi hjy mum taban don nasan tana iya kokarinta akan tarbiya. Amma yau sai gashi mace tana son shiga tsakaninta da danta ta hadasu fada a tsakaninsu saboda son kai banta ganin uwar data shaku kwarai da diyanta ba har suka zamo abokan shawaranta irin mum ba. A take naji tsanar wanan macen ya fita raina dako ina son ta dongayunta ina ji da ita har ina son koyi da irin halinta ashe kyau dan macijine da ita. Duk macen dake kokarin raba tsakanin da mahaifiyar shi da sunan aure wanan mace ba karamar shedaniya bace son kanta yana da yawa bata kuma kaunar mijin da take aure din. Kabari a cutama yafi kayi cuta irin wanan mai girma a duniya basu ganewa matan saboda son kai ya rufewa wasu ido har suke jin hakan aiba zunubi suke aikatawa ba. Ranan dai gajeren hira mukayi da mum da safen son ko bayan mun gama karyawa ta shige daki bata sake fitowa ba ni kadai nayi ta zirga zirgana har na hada muna abinci nagama. Mum bata kyale ya Addil din ba donko ta kirasa a waya tayi masa kaca kaca ashe matar na kusa a lokacin nan ta fara yan surutai tana fadin dama aiba sonta akeyi dashi ba. Idan hakane ita gara kowa ya kama gabansa zaifi a tsakaninsu shigo yaji surukulen mata nan ya shiga bata hakkuri yana ban baki kan tabari zai zauna da mum din suyi magana ai bata fahinceta bane. Ni dai a yanzu nikan ga mum ta aikeni wani gida da bamu da nisa a layin mu gidan marayune maigidan ya rasu ance yakai shekara kusan ashirin ga gidan babba amma iyalansa ke ciki zaune. To wanan gidan dama nakan dan kai masu sako saidai na yanzu din yayi yawa don yakai harda abinci dafafe idan zamu dafa mukan kara yawa sai tasa i kwashe daban in dauka inkai masu don irin gidajen su Dad manyan gidaje a layin almajirai basu shiga haka kasafai don suna tsoron yankan kai. Yauma su zan kaiwa sako data ban shake a ledan vaco har da tufafi dasu sabulu omo man shafi da makaroni da taliya niki niki na dauko kayan zan fito daga cikin gida da katon hijabi na don sai ka kula zaka gane ai duka hannuna biyu dauke suke da kaya. Anty Nafisace tsaye da wani namiji shi ya bada baya don haka ban gane fuskan ko waye ba a lokacin kai sister me kika dauko haka kike haki kamar zaki fadi ? Mum ce ta aikeni wancan gidan na fada sai lokacin ya juyo nagane ya Hafiz dinsune a wajen ashe nina zatama tayi bazawarine yazo mata hira yadda suke dashi don zaune take cikin motanta shi kuma yana tsaye ya riko kofan motan suna magana. Wai amma kayan nan sun maki yawa ta kara fada na danyi dariyan yake sai naji yace da ita maganinta ke nan ai jakace dama abinda ya dace da ita ke nan daukan kaya. Innalillahi na furta ina runtse ido kamar na dawo in bashi amsa sai kuma na wuce kawai kai tsaye a zuciyana nace na barka ga Allah shi zai aiko mai rama min dan giyan banza kawai . Haka na fita ina fada cikin zuciyana har Allah ya taimakeni nakai gidan ga gidan da shegen girma kafin ka kai cikima aikine a yadda naji wai bayan rasuwan mijinta anso a cinye masu komai daya bar masu. Sai matar bata yarda ba mafarin da batayi aure ba ke nan tana ciki zaune da yayanta su kuma yan uwan mijin sunce basu yarda tayi aure wani miji yashigo gidan dan uwansu ba yaciwa yayansu gado. Rikici dai akace anyi sosai shine ta zabi zama da yaranta a gidan akan taje tayi aure kuma taki yarda da tayinsu na son su aureta da sukayi shine suke cikin wanan bakar wahalan ita da yaran kuma sun hana tasa ko dan haya a gidan ta samu inda abinci zai fito mata mugunta zalla a wajen sukai mata. Tayi murna kwarai tace tana nan zuwa tayiwa mum din godiya da yamma in yara sun dawo daga school kodana dawo ban samu su anty Nafisa din ba motar tama bainan nasan ta fitane lokacin. A part din mu na samu Amir tare da mum zaune kin dawo mama mum ta fada na zaune ina wash amir yazo ya haye min jiki na daukeshi ina masa wasa tare da fadin waya kawoka nan ? Nima gannisa nayi ya fado min yanzu yasan hanya tunda ya samu kafa basai an kawoshi ba ai lokacin nace mum ni bansan abinda nayiwa ya hafiz ba ya tsanani ? Hafiz kuma yazone yana gari ta tambaya a cikin mamaki nace yana nan tare na gansu da Anty Nafisa a kofan gida zan fita son anty Nafisa tace min kayan dana dauko sun min yawa shine yace dani aini jakace dama shine daidai dani. Hummm ki kyaleshi baida hankali inbashi ba ka kira dan uwanka musulmi da jaki kaji dadi akan me don Allah ki barshi karkima kulashi don Allah. Shima mashayi dangiya ai gara da jaki haka Allah ya haliceshi da daukan kaya kar in karaji babu ruwanki inma da gaskiya yana sha tsakaninsa da Allahne wanan babu ruwanki mum ta hanani cigaba da magana alokacin. Shiru tayi tana tunane kafin nace mum matar nan taji dadi sosai wallahi tace ke mai kyautan yan aljanna ce dan kyautanki nazuwa a lokacin da mutum yake cikin matsanacin hali sai mum di n tayi murmushi tana fadin Allah yasa mu dace ga baki dayan mu na amsa da Amin. Bayan kona biyu muna zaune abin mamaki wai saiga ya Hafiz ya shigo part din mu da takardu a hannunshi yake gaida mum kafin ya juyo guna yace ke karbi takardun ki yace in fada maki ranan Monday zakije screening. Yana fadin hakan na mika hannu na karba da sauri ina murna kafin nace nagode na mikawa mum tace takardan kine ai na karatu tun jiya yayaki ya bugo min cewa zai aiko dashi. Sai kibi Nafisa taje dake tai maki komai a can yafada yana karasa mike zai tafi nan mum ke fadin ashe kuma fita zaka sakeyi yace eh wallahi mum can din yafine don su aiki baida wahala acan din. To Allah ya kyauta yasa aje cikin nasara ya amsa da amin yafita hankalina yana kan takardun dake hannuna ina karantawa banko kula da fitansa ba. Na daiji mum na fadin hjy malka bata da tunane yaron nan zata kara turawa kasan waje kuma shi kadai ya zaunacan suna tare da yan uwama bai natsu ba balle yaje shi kadai da sunan aiki. Sam ban tsaya kula mum din ba a lokacin don bayanan dake cikin takardan ya dauke min hankalina Allah ya gani ina son karatu sosai a rayuwata. Na dago ina fadin mum sai nayi wani photo kuma barima in duba ko nawa suka rage min a daki na mike na barta a wajen zaune. Har naje na dauko ban tsaya kallon mum dun ba da gaba daya yanayinta ya sauya lokaci guda ta shiga yanayin tunane mai zurfi dagowan da nayi ina fadin ashe ina da guda biyarma aje. Nan na fahinci sauyin fuskan mum din saidai ban fahinci kona meye ba wanda ba komai take tunane ba a lokacin sai yadda abubuwa zasuzo su kashe tasan dole a samu sabani don rayuka da dama zasu baci a tsakani. Saidai yanzu bata da iko ko power magana koda ko ace itace ta haifeni bata da hurumin ketara zancen mijinta ta tsaya musu dashi duk da ko yanzu din banda bambanci da diyar data haifa. Hakan da za,aimin tauyewane a gareni mai yawa take hangowa don kamar fin karfi da son kai za,a nuna min da iyayyena take gani duk da tasa suma a bangarensu sunfi tsanar hadin fiye dasu. Ita mace ce bata da karfi ko power da zata tsaya min tace kada ayi hadin nan haka kuma iyayyena suma basu data cewa don Alh shine babba ga mahaifina. Mum lafiya kalman dana jefo mata ke nan na katse mata tunanen ta a lokacin ta nisa da karfi tana sauke ajiyan zuciya tace bari kd dai mama duniya nake tunane wallahi. Jikinane ya danyi sanyi a zatona kan zancen tafiyan ya hafiz din ne data dauko min na shareta abin yake damunta sai mm aji tace akwai Allah ya Allah ka shige muna gaban lamarin nan yazowa kowa da sauki. Na amsa da Amin take fadin sai ki shirya don Nafisa zakibi takaiki ranan Monday din abin ai yazo da sauki tunda ana saka wayewan kai aciki ba irin namu bane da kowa jahilci lokacin bamu ba ba iyayyen namu ba. Part dinsu ya nufa kai tsaye don ya karya yana shiga Dada na zaune suna hira da Anty nafisa ya samu gefe daya ya zauna yana bata rai. Dada sai zolayanshi takeyi yace dama ina son ganin ki muyi magana sai gaki Allah ya hadamu a nan yanzu rage fara,an fuskanta tayi don ganin yadda shima yake cikin damuwa tana kallonshi tace ai gani kamar Allah ya turoni meka samo min fadi muji. Dan furzo da iska yayi daga bakinsa kafin yace Dada akan wanan auren hadin da daddy ke son yai min ne gaakiya Dada kwata kwata banson auren nan kuma yarinyar batayi min ba don ba kalan zabina bace ita. Ita mace har tana da wani bambamcine a wajen namiji ina dai mace macece ya tsuke fuska cikin damuwa don ya kula zaisha wuya koda zai samo kan tsohuwar. Dada nasan ke kadaice zaki fahinci me nake nufi ni sam bani kaunar wanan yariyar koda yan uwantaka balle da sunan aure kinga yin aure tsakanin mu hakan kuntatawane ga gaba dayan mu sai hakan ya kara haifar da matsala har yashafi wanda ba,a zata ba.. Tunda ya fara maganan Dada ta bude baki take masa wani kallon na mamaki wanda shi bai iya tantance ko nameye alokacin. Haka mummy ma data fito daki da manzafi data daukowa Dada daga daki dama shi Dada din tazo nema a wajensu ta zauna itama kallon mamaki tabi dan nata dashi lokacin don sun riga dasun aje magana dashi don mafita akan zancen. Kai ashe rashin hankalin naka yakai haka ban sani ba yar uwar haihuwan naka kake fadi a gabana baka kauna koda zumunci balle da aure ? To ka fara zuwa wurin ubanka daya hada zancen a tsakanin ku kafin kazo wurina watau ni gani tsohuwar banza mai yukan yanke zumunci bari kazo wajena ka laba ayi yankar kauna ko ? Ke Dada wai bakya ganewane shifa so wani abune kada ku tauye min rayuwata mana don Allah zaku hada baki ku cinna min wanan mahaukaciyar yarinyar in kaita ina don Allah ? Inda ubanka yakai uwarka nace inda ubanka yakai uwarka Dada tafada a hasale cikin mikewa tana haki kamar zata dokeshi daga inda hjy malka take tsaye ta kwala masa kira tace hafiz bakaji ko zan saba maka idan baka fita part din nan ba yanzu. Kallon mummy din yayi kafin ya juya a kasalance wurin Dada din yace na dauka zaki taimaka min ki rabani da wanan auren alkakan da daddy keson yi min she duk bakin ku daya ban sani anywhere kuyi karku fasa din ai . M ummy ce ta karaso acikin masifa agareshi tana rantsuwa idan bai fice daga part din ba zata saba mashi rai fiye da tsanmaninsa. Lokacin Anty Nafisa ta dago kai ta kalleshi tace Hafiz wai bada kai mummy ke magana ba ka bari a lalaba zancen nan mana tunda ku duka bakwason junan ku. Wani kallo yayiwa yar uwartasa tace yes kamar yadda baka son hadin nan ko ita sister na tabbatar da bata so don ko bashiri a tsakanin ku . Shine daidai idan anyi auren sai suje can su shirya a tsakanin su tunda sunfi kusa Dada ta fada cikin daga murya har ya juya ya fara tafiya jin hakan yasashi ya dan dakata yana mai juyowa ya nuna Dada din da hannunsa. To indai har hakane babu wanda ya isa kaf ya fasa wanan auren acikin uban nan ku muddin ina da raina ya nunata yace aisai ki zauna da ita ki jika kisha tunda kince hakan. Shege ka fasa tunda kace haka in maka na mahaukata wallahi hafizu idan kaga an fasa wanan auren tsakaninka da Abu tabbatar bana raye a doron kasa ta karasa zancen a cikin bacin rai. Anty Nafisa ta mike tana fadin saika fita tunda ka bata komai dama haka kakeso ai Dada ce zaka sama ko daddy dayayi ma wanan hadin meye na Dada a cikin zancen nan. Kai ya girgiza a cikin yakaici yana fita daga falon yakai iya kololowan tashin hankali don yanzu ya tabbatar da wanan auren da daddy ke ikirarin ya zaba mashu mata yar mutunci yar albarka ba fashi sai anyisa. Idan gaskiyane meyasa ba aiwa ya Addil auren dole bashi saishi da aka raina za a kakaba masa wanan kucakar yarinya da sunan aure wai fa zeey a matsayin matarsa.

ZAINAB IDRIS MAKAWA

[2/21, 14:52] Maman K: DUBA MIN BAYA FOKON,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA

2️⃣3️⃣

GA MAISON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI DUBU DAYA KACAL A WANAN LAMBAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , ,

YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DOMIN AMANACE HAKKI,WANI A WAJENKA , , , , , ,

HAKKIN MALLAKAN JUYAWA AUDIOVISUAL S ZARIA TV KEDA WANAN HAKKIN KADA WANI KO WATA YAYI GANGANCIN JUYASHI ZUWA AUDIO.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull