Kenza eBookz

Farhatul qalbi complete - Chapter 11

Farhatul qalbi complete - Chapter 11

Farhatul qalbi complete Chapter 11: Farhatul qalbi complete Chapter 11. "Kina emmata baki da waya. Wait a wane school kike?"

4,499 words

"Kina emmata baki da waya. Wait a wane school kike?"

"Ina ss2..."

"Ah dai dai kenan. .. Ashe mun kusa kammala school dinma ko?"

Ta gyada masa kai da sauri tana murmushi . Zai sake magana kenan. Nadra ta kwalawa Waheedah kira

"Zo nan sis zamu shiga ciki."

Waheedah ta amsa da sauri. Don dama tsaiwar dole take agaban su. Ta ketare ta gefen Zayn zata wuce. Awawwaton hannunta ya riko zaren aikin hannun rigar sa .

Ta juya da sauri. Yayinda shima juyowar yayi. Karen hancin su saura kadan ya hadu. Yayin da numfashin junan su ya shiga haduwa a tare.

Kamshin turaren jikin ta dana Zayn suka hadu suka bada wani ni'imattaccen kamshi mai wuyar fassarawa .

"Sorry...... " Ya fada kasan maqoshi. Yayinda ya daga hannun sa ahankali yana zare zaren daga jikin awawwaron nata .

Waheedah tayi tsit. Tana sauraron bugun zuciyar sa da ke bugawa da sauri sauri. Irin bugun nan da zuciya keyi idan tana cikin farin ciki ..

#FARHATAL QALB (FARIN CIKIN ZUCIYA)

❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯

*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*

*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*

*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*

πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„

*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*

*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*

INAYA(riba biyu)___mamughee

SANADIN LABARINA___Rano

BABU SO___Billynabdul

FARHATUL K'ALB___Miss xoxo

GURBIN IDO____Huguma

*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*

*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*

Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300

*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*

HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank

*Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902

*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107

*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°_*FARHATAL-QALB*_ _(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_ πŸ’ž _NA_

_NANA HAFSATU_ _(MX)_

_AREWABOOKS:MISSXOXO_ _WATTPAD: MISSXOXO00_

_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_

_PG:32_

===

Gaba daya ji Zayn yake yi tamkar babu laka ajikin sa. Saboda yanayin yadda jikin nasa yayi laushi ya kasa zare zaren. Jikin sam ba karfi.

"Sorry...." Ya sake maimaitawa yanata kiciniya.

Nadra dake jiran Waheedah ta karasa . Hannu daya ta saka ta yage awawwaron zaren ya fita daga ciki.

"Ya Zayn . Ahlam na jira fa..."

"Gani nan... " Ya amsa ta yana sauke kai.

Wasu masu serving abinci zasu shige ciki ya dauki ruwan roba daya daga cikin ledar sa. Nan da nan ya shiga kwankwada. Sakamakon wani zafi dayaji yana taso masa.

Abokan suka karasar da shi wajen Ahlam. Ta kama hannuwan sa acikin nata. Yayinda kafadun su ke gugar na juna. Ya juya ya kalleta. Ta dan daga tsayinta zuwa kunnen sa ta rada masa,

"I've the right hubby ...... An daura ai ko?" Ta karasa ce masa tana murmushi.

A haka suka shiga cikin marque din ango Zaid da amaryar sa Jannat sune a farko. Sunyi matukar kyawu ta saka wata riga baka gown me flowing da wasu stones masu glittering farare tas.

Sai shi ango Zaid da yayi shigar alfarma shima cikin wagambari fara data sha aikin baki. Yayi bala'in kyau ba kadan ba. Shi da amaryar tasa sun bada color .

Sai couple na biyu. Ango Zayn dayayi shigar wagambari baka data sha aikin kala fara. Sai amaryar sa Ahlam data sha kyau itama cikin farar gown mai glittering (kyalkyali) na stones baki.

Ba kadan ba sunyi kyau. Kyawu irin wanda alkalami yayi kadan wajen fassara shi. . ..

Gaba daya kowa sai da ya miqe a cikin marque dinnan in honor of the couples. Har sai da suka zazzauna awajen zaman su. Tukun sannan kawayen amare da abokan angwaye suma aka sakar musu speaker rawa suka dan tattaka. Kafin su koma wajen zaman da akayi musu na musanman suka zazzauna.

Daga nan aka kira wata babbar malama. Ta bude taro da addua. Sannan gayshe gayshen yan uwa da abokan arziki. Sanarwar zuwan manyan baki na musanman. Bada tarihin amare da angwaye daga abokanai da kawaye. Sai kuma refreshments.

Abinci ne kala kala babu irin wanda babu. Menu aka bawa kowanne yayi ticking abincin da yake so. Dik wanda ka zaba shi din ake kawo maka. Nadra da kanta ta zabarwa Umma Hadiza. Aka kai mata. Yayinda Waheedah ta zabi wanda take so.

Karar kwanuka da cokula kawai kakeji sai slow music da ke tashi. Amare da angwaye ma an saka su dole su ci. Bisaga jagorancin Ummimi da tace jikokinta ba zasuyi jidalin yunwa ba. Bayan kowa ya take ciki yana cika cikin sa.

Aka saka dariya baki daya. Ahlam ta juya ta dubi Zayn da ke danna wayar sa.

"Hubby .. abincin fa?"

"Na koshi..." Ya amsa yana kallonta

"Ya zaka ce ba zaka ci ba...? Bayan Ummimi tace duk mu ci. "

"Banacin abincin wadanda bansani ba gaskia. Wanda na sani dinma rarely nake ci."Ya karasa yana cigaba da danna wayar sa.

Ahlam ta juya ta kalli su Zaid da Jannat. Suna feeding junan su suna hirar su kasa kasa. Wani tuququn bakin ciki ya tsaya mata a makoshi. Ganin ita natan yayi biris da ita waya ce ma agaban sa. Ko irin lallashin nan nata baya yi.

"Zayn...."

"Naam .. Ahlam"

"Ba zaka ce naci abincin ba?"

"Tohm Waheedah ki ci abincin ."

"Waheedah Kuma?" Ta tambaye shi cikin tsantsar kulawa.

Sai a sannan Zayn ya gano baranbaramar da yayi. Yayi saurin fuskewa hadi da mayar da wayar sa aljihu. Kasan zuciyar sa tunanin Waheedah yake tabbas. Amman harshen sa daya ambata sam baisan dalili ba .

"Look Ahlam...."

Ta katse shi.

"Babu zancen look ... Zayn I'm i that unimportant? "

"Noo . .. Kinaji Dawud ne ba kinga dazu na je wajen sa ba...!"

"Eh...."

"Toh maganar Waheedah din yake mun . Yana son ta "

Ahlam ta sauke gauruwar ajiyar zuciya. Amman duk da haka ta sake tambayar shi da,

"To meyasa zaka kira ni da Waheedah? Tun da ai ba awajen bane. Yanzu ni da kai ne a zaune "

Ya sosa keyar sa yana murmushi.

"Yes I'm all ears Zayn .. saboda me zaka kira sunana da Waheedah?? Sunana bashida matsayi a zuciar ka ne ko kuwa?"

"Da shi muke magana ta WhatsApp ... Kingan shi da can wayar sa a hannu."

Ya nuna mata Dawud da yatsa. Nan taga Dawud din wayar sa a hannu yana dannawa. Hankalinta sai ya kwanta. Ta danyi murmushi lallausa

"Na yadda .."

"Yauwa.... " Ya amsata yana murmushi

"Abincin fa?"

"Ki ci...."

"Ka bani.... Feed me pls"

Ba yadda ya iya. Ya debo fried rice da patoosh salad a spoon ya saka mata a baki. Ya zuba ruwa a cup ya bata.

Kawayen amarya na ta awwwwn.. Waheedah ta dube su cikin kulawa. Suna birgeta kwarai matuka da ka gansu kasan su din suna kaunar junan su .

Ya dakko tissue ya goge mata baki.

"Thank you hubby...."

"Anytime...."

Yana daga kai suka hada idanu da Waheedah . Ya janye idanun sa da sauri yana saisai ta kan sa.

Haka aka cigaba da gudanar da shagalin bakin ranar. Yan uwan juna gaba da baya. Kamar ko da yaushe. Babu wasu bare sai yan gayyata da wasu tsirarru na daga kawaye ko abokai dama makota da sauran su

Anyi 'barin kudi ranar tamkar bishiyun kudi ne da su suke zazzaga su.

Dukkanin iyalan Ummimi matan su 3 anko sukayi gwanin shaawa. Cikin wani dandatsetsen lace mai dan karen kyau da kyalkyali. Yayin da mazan suma sun zuba wata gezna shadda mai madaukakin tsada da kyau

Lamarin sai wanda ya gani ya kuma halarci taron kawai. Anci an sha anyi hani'an.

Zayn yayi excusing kan sa ya fita daga cikin marque din. Ya tsaya a tsaye yana mai furzar da iskar bakin sa. Kansa sai wani sara masa yake yi .

Yanayin jikin sa baki daya ba dadi. Ya kuma tabbatar da hakan nada nasaba da wannan bikin. Gaba daya ya rasa wane tunani ma zai kama da zai fitar masa da mafita.

"Zayn... Ka dawo ciki zaa dauki pictures." Cewar Awais abokin sa.

Gyada kai kawai yayi alamun toh. Ya koma ciki. Aka shiga daukar hotuna ta ko'ina photographers nata haskakawa da aiyukan su.

Sannu ahankali wadanda aka gayyato suka fara tafiya inda suka fito. Ciki har da Waheedah da Umma Hadiza. Daga karshe kuma bayan yan uwan sun gama warkajami. Aka tashi daga taron sai kuma na washegari idan Allah yayi da rabon ga ni....

❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯

*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*

*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*

*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*

πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„

*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*

*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*

INAYA(riba biyu)___mamughee

SANADIN LABARINA___Rano

BABU SO___Billynabdul

FARHATUL K'ALB___Miss xoxo

GURBIN IDO____Huguma

*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*

*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*

Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300

*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*

HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank

*Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902

*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107

*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°_*FARHATAL-QALB*_ _(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_ πŸ’ž _NA_

_NANA HAFSATU_ _(MX)_

_AREWABOOKS:MISSXOXO_ _WATTPAD: MISSXOXO00_

_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_

_PG:33_

=====

*GIDAN MALAM NALADO*

*DA* sallama a bakunan su, Suka shiga cikin gidan na su. Marka na kwance akan shimfidar tabarmar ta. Saitin gefenta daga dama kuwa fitila ce ta wuta mai lagwani.

Bata amsa sallamar ba. Sai ma dago fitilar da tayi don ganewa idanun ta.

"Wohoho. Fito nan mai sunan malam. Ai na gayan ka."

Nan da nan Malam Nalado ya fito daga cikin daki. Ya tsugunna agaban mahaifiyar ta sa.

"Kaga ni ko .....? Wane tsinannen biki ne za'a tafi tun rana tsaka sai dare zaa dawo?"

Umma Hadiza ta fara girgiza kai zata yi bayani. Marka ta hanata. Ta hanyar mikewa jikinta har kakkarwa yake saboda bala'i.

"Dube su ... Dubi kayan jikin Wahidin fisabilillahi... Wannan shiga ta dace? Dubi fatar jikin ta da fuskar ta. Tayi kwailin.. kalli yadda ta kode tsabar bilicin."

"Wallahi Allah bana bleaching Marka .. Mai ne da sabulu Nadra ta bani. Wadda Umma ke yiwa mahaifiyar ta ai..."

"Zaki rufe mun baki ko sai na zo na gabje ki anan?"

"Allah yabaki hakuri ...." Ta fada hawaye sirara na zuba a kyakkyawar fuskar ta...

"Na gaji..... Mai sunan Malam. Yau dai kagani da idanun ka. Ire iren rashin tarbiyyar da suke gudanarwa acikin gidan nan.."

"Wallahi Malam... Ko tashi ba'ayi ba awajen taron muka taho."

"Bikin gidan na uban ku ne dama da zaku zauna?. Ai malam na dauka abun na mutunci ne da arziki da mu ma za'a gayyace mu. Muje mu kashe kwarkatar idanun mu. Amman saboda tsabar akwai kaucewar hanya ai kaga su kadai suka tafi. Sai cikin dare. Kowane gidah sun kulle gidajen su banda mu. Su sun tafi regargadin biki gidan mu a yashare. "

Umma Hadiza ta tsugunna tana jujjuya kai. Idanunta sun kawo ruwa sosai. Cikin muryar ban hakuri da sanyin jiki tace,

"Dan Allah Marka kiyi hakuri .... Wallahi wallahi babu inda mukaje sai wajen taron bikin nan. Kuma acikin gidan yake daga wani bangaren. Kayi hakuri Malam. Dan Allah ku yafe ni."

"Hakuri ... Wohoho ko ba hakuri ba? "

"Eh dan Allah Marka "

"Mai sunan Malam.."

"Na'am Marka ."

"Kace Hadiza ta bar maka gidan ka. "

"Kiyi hakuri Marka .." ya fada a hankali yana kallon Hadiza ta gefen idanu

"Nayi hakuri ?" Ta tambaye shi. Tana binsa da kallo sheqeqe.

"Ehh ."

"Matsa can. Sahoro mijin sahorama. Gidah na waye?"

"Na ki ne Marka."

"Toh wabillahil lazi zaman Hadiza ya kare a gidan nan."

"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun!!!" Kamal ya shiga furtawa. Yana takawa dakyar hannun sa dafe da bango

"Matsa can. Gawa taki rami kawai "

"Haba Marka .. Haba Marka." Umma Hadiza ta fada . Hawaye na kwarara a fuskarta sosai jin yadda Markan ke aibata Kamal jikan ta.

"Karya nayi? Ba ragowa bane shi? Kullum akan magani. Nakasasshe, Bushassshe. Kanjamamme. Ai kuwa gawa ce shi din da taki rami "

Kamal yayi murmushi. Ya dafa bango ya zauna yana sauke numfarfashi

"Marka... Ki dena cewa haka ... Tamu kaddarar kenan. Lapiyayyun ma basu da tsimi bare dabara. Kowanne rai Allah ya halicce da dukkanin dik wasu abubuwan da zasu faru agare shi. Don haka wannan cuta da muke fama da ita kankarar zunubai ake mana...Marka mu fa jikokin k .."

"Karka karasa... Kar ka soma karasawa. Bani da tabbacin kudin jikoki na ne ko akasin haka. Mai sunan malam babu yadda banyi ba kar ya auro Hadiza. Amman ya toshe kunnen sa. Yayi kunnen uwar shegu. Hadi da badawa idanun sa kasa. Ya kafe ya nace ya cije kan dole sai ya aurota. Gashi nan ai baki dayan tattalin arzikin sa ya kare akan ku da uwar ku. Dukkanin ku ku ukun ba mai lapia ingatacciya. Ita wannan baki daya ma makanta ce da ita. Sai da temakon gilashi take gani. ..." Ta karasa tana mai sakarwa Waheedah rankwashi .

Waheedah bata ce komai ba. Yayinda kanta ke a kΓ sa kawai.

"Kai maganganun menene haka ne..? Cikin bacci na ke jiyowa." Cewar Inna Sa'adatu . Ta gantsare tana miqa hade da yin hamma.

"Su wa kika sani? Hadiza da iyalanta ne. Ina magana suna mayar mun. Munata musayar yawu da ni da uwar tasu. ."

"Au wai sai yanzu kuka dawo...? " Inna saadatu ta tambaya tana mai sauke kallon ta bisa fuskar Umma Hadiza .

"Eh yanzu muka dawo Sa'adatu " Umma Hadiza ta amsa ta.

Inna Sa'adatu cikin makirci ta sake cewa,

"Yanzu ku kuna mata ku ka kai wannan tsakar daren awaje? Fisabilillahi biki bana dangin iya ba bana baba ba ? Meyakwan ke Hadiza ki taso keyar ta ku dawo tun tuni."

"Wacce hadizan ce zata ce wa yarta su dawo da wuri? Bayan watsewar ita ke koya mata .."

"Allah ya baku hakuri Marka.."

"Ni fa idan kina gayamun Kalmar hakurin nan ji nake tamkar wuqa kika dabamun a zuciya. Hakurin ubanme zanyi? Kama ki zan na saka a garke na daure ko kuwa? Ai babu abunda ke tsakani na da ke Hadiza. Ba auren 'da na kike ba .... Shekaru masu dadewa."

Umma Hadiza ta tamke idanunta tana dartse bakinta. Baki daya kanta ya mata nauyi. Duk tarin shekarun nan da aka dauka. Bata taba buda baki tacewa yaranta basa tare da mahaifin su ba. So take akwai lokaci da ta ware zata sanar musu idan Allah ya so. Amman baki daya Marka ta tarwatsa mata lissafi. Kusan kullum seta goranta mata. Tayi ta shelan ba aure tsakanin ta da dan ta. Tamkar wani lefi tayi babba da yasa ya saketa. Bayan Markan ce ta saka dole ya saketa babu wata kwakkwarar hujja.

Hawaye sirara suka shiga zuba a idanun Umma Hadiza. Marka ta kalleta tana yamutsa baki.

"Ni fa kukan munafurci ne banaso. Uban me na miki iyye?"

Umma hadiza ta girgiza kai kawai. Hade da saka hannu ta share hawayen ta.

"Babu komai .."

"Toh mai sunan Malam... Yau magana ta kare. Idan Allah ya kai mu wayewar gari. Inason Hadiza ta tattare nata ya nata ta bar mun cikin gida. Kar kuma ta sake tako kafarta kofar gidan nan idan ba da wani dalili ba kwakkwara. Wannan shine zancen da na yanke. "

"Tohm Marka.. Allah ya tashe mu lapia " Umma Hadiza ta fada hade da miqewa tsaye. Ta kamo Kamal ta temaka masa ya shiga daki.

Dan sauran kayan kwalam da suka samu awajen bikin ta juye musu akan faranti ta raba musu shi da Najib.

Sannan ta kunna musu maganin sauro tasa daga bakin kofar daki. Tayi sai da safe ta koma daki.

Waheedah ta cire kayanta ta mayar da na gidah. Wata riga da ta mayar da ita ta bacci. Sai hula da ke kanta

"Baki kwanta ba....? Tara da kwata fa "

"Zan kwanta Ummaa. Yanzun dai bana jin bacci "

Umma Hadiza ta sauke nannauyar ajiyar zuciya. Hawayen da ta ke kokarin zubowa ya shiga tsiyaya . Tayi sauri ta goge . Nan ta fara jiyo sautin na waheedah har da shessheka. Tayi saurin janyo ta jikinta tana lallashinta.

"Bar kuka Waheedah ... Kowane dan adam da tasa kaddarar., Mu ta mu .....

❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯

*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*

*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*

*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*

πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„

*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*

*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*

INAYA(riba biyu)___mamughee

SANADIN LABARINA___Rano

BABU SO___Billynabdul

FARHATUL K'ALB___Miss xoxo

GURBIN IDO____Huguma

*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*

*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*

Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300

*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*

HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank

*Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902

*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107

*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°*_RANO SCRUMPTIOUS MEAL_*

_(Where every flavour tells a story .....)_

*_By HAFSAT RANO_* _(Mother/wife/writer)_

_08030811300_ _IG:Rano_scrumptious_meal_

_INA MA'ABOTA ABINCI? WATO *TRADITIONAL FOOD IN KANO*? GANGARIYAR ABINCI NA AL'ADUN HAUSA DA NAHIYAR KETARE? BA ANAN KADAI MUKA TSAYA BA. MUNA DA LEMUKA WATO *LOCAL DRINKS*. ZAKU IYA KAWO NA HIDIMOMIN LIYAAFA MUYI MUKU_

_MU NA YIN:_

*_FUNKASO_* *_ALKUBUS_* *_SINASIR_* *_WAINA_*

*_ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI)_* *_COW TAIL/COW LEG (DAB'URI)_* *_CHICKEN AND FISH PEPPER SOUP_*

*_LOCAL DRINKS:_*

_HIBISCUS (ZOBO)_ _GINGER_ _AMAANI FRUITY SHAKE_

_MUN TANADAR MUKU MOUTHWATERING ABINCI KALA KALA WADANDA KE GINA JIKI DA KARA LAPIA. ABINCIN MU A TSAFTACE YAKE. KUMA MUNA YIN SU NE AKAN YADDA KOWANNE MUTUM ZAI IYA CI . AKWAI SPECIAL SOUPS NA MASU ULCER WADANDA BABU YAJI. AKWAI KUMA NA PEPPER DEM GANG GA MASU SON HOT AND SPICY...._

_KADA KU MANTA MUNA YIN NA TAKEAWAY/ORDER . MUNA KUMA YIN NA BIKI (WE CARTER TO SMALL/LARGE EVENT...._

_FUNKASO TO PAIR WITH COW TAIL:2K_ _WITHOUT COW TAIL:1K_

_ALKUBUS TO PAIR WITH ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI) 2K. WITHOUT ASSORTED MEAT :1K_

_PLS NB: PAYMENT VALIDATES INTEREST..... DELIVERY WITHIN KANO:500 NAIRA_

________ *_FARHATAL-QALB_* _(FARIN CIKIN ZUCIYA)_

_NA_

_NANA HAFSATU_

__PG: 36_

*Dakyar* Waheedah ke iya bude idanunta. Saboda tsananin yadda kanta ke sarawa. Kanta na mata madaukakin ciwo. Ya yinda gangar jikinta ta dauki zafi rau tamkar garwashin wuta.

A haka Kamal ya shiga dakin a daddafe don shima ba dadin yake ji ba. Ya nemi waje ya zauna akan wata kujera ta tsugunno.

"Sannu Waheedah..."

Bude idanun tayi da suke rufewa da kansu. Sunyi jawur da su. Sun kara furfutowa waje tubarkaAllah.

"Yaya Kamal.... Kai zan wa sannu. Ya jikin?"

"Da sauki ... Alhamdulillah. Ya jikin?"

"Da sauki..." Ta fada tana mai cije labbanta. Ta miqe ta zauna dakyar daga kwanciyar da ta ke.

"Yanzu Najib ze kawo miki ruwan gishiri ki sha. Saboda karfin jikin naki .. Kin sha panadol din ko?"

"Ban sha ba... Zan sha yanzu."

"Yana ina?"

"Gashi nan..." Ta nuna masa kan murfin samira. Ya dakko ya tashi ya tafi dakin su ya dawo da pure water guda 3.

"Ungo sha maganin... Wannan sai a hada miki ruwan gishirin ko . (ORS). ?"

"To Yaya ... Ka koma ka huta." Ta fada a wahalce

Ya danyi murmushi kawai. Yana dada kallonta sosai. Lalle Waheedah batata lapia sosai. Don bata kwanciya akwai kazar kazar. Bata taba cewa ta gaji akan aikace aikace.

"Mu idan muna kwance ba lapia Waheedah ba ki taba kosawa. Komai da komai yi mana kike yi ba gajiwa. Ubangiji Allah ya baki lapia ya sa kaffarane. "

"Aamin Yaya..."

"Kibar kukannan haka kinji?

"Tohm ...Yaya" Ta fada muryar ta na rawa.

Ba jimawa kuwa Najib ya shigo hannun sa dauke da leda baka. Ruwan gishirin ne sachet 3 aciki da kuma pure water rabin leda a dayan hannun sa.

"Dakko jug dincan ka hada mata. Ka ga ka fara dauraye shi tukun ka ji?"

"Tom Yaya."

Najib ya debi ruwa a kwalla ya wanke jug din ya hada mata ruwan gishirin ya miqa mata.

"Ka da ki sha ruwa sai kin gama shan sa.."

"Tohm Yaya...." Ta amsa shi.

Kasan zuciyar ta ta tuno yayan nasu da tuni yanzu yana aiki a asibiti ko wata ma'aikata data shafi harkar lapia ko kamfani. Domin chew (community health extension worker) ne shi kafin ciwo ya kankame shi baki daya..

Har ya mike yar wayar sa mai torch light ta shiga kara a aljihun sa, Ganin number Najan Isubu ce. Hakan ya sa ya dauka da sauri. Ya kuma koma ya zauna

"Wa'alaykm Salam... Ina wuni? Ah Alhamdulillah wallahi. Waheedah? Da sauki gata ta dan zauna... Eh shima yana nan. To bara na turo shi. Mungode, Allah ya saka da alkhairi. Amin. Okay tohm "

"Ka karasa hada mata...?"

"Eh. Gashi nan tana sha ma "

"Yauwa. Kaje gidan Najan Isubu ka karbo abinci. Umma ce ta bata ta kawo mana.."

"Allah sarki Umma. Muna ran ta. Uwa mai dadi. Allah ubangiji ya saka mata da mafificin alkhairi. "

"Aamin Yaa Rabbi ."

"Aamin."

"Bara na dan watsa ruwa "

"Tohm Yaya..."

Kamal ya fice zuwa bandaki. Yayin da Najib ya fice zuwa gidan Najan Isubu. Daki ya zama sai Waheedah ita kadai tana zaune. Kanta a sama.

Marka ta leka ta windown tana tabe baki. Kafin ta shiga ciki ba ko sallama ba re sannu

" A koke."

"Naam Marka ."

"Ungo debo mun ruwa acikin nan..." Ta miqa mata wani bokitin karfe kato.

Waheedah ta cika da madaukakin karshen mamakin halin ko in kula irin na Marka. Yanzu yanayin da take ciki na rashin lapia haka zata fita ta ebo ruwa bayan ga su Zainab can tana jiyo karakainan surutan su.

"Ko ba zaki ebo bane? Yo naga ma fuskar ki a murtuke kaman zararriyar zakan ya. Zaki hau kai na da bugu ne?..."

Waheedah ta girgiza kanta da a'a. Ta miqe dakyar. Jiri na neman kayar da ita. Amman a haka dai ta daure ta karbi bokitin tana dafa bango. Har ta fice daga dakin.

"Mene nan? Gayyar munafurci." Marka ta shiga bude kwanuka. Harda daga jug din ruwan gishirin da kalar sa tayi kaman lemo. Ta kwankwada zata sha banza ta dauka lemo ne. Da sauri ta fuce ta isa ga rariya ta amayar da shi tana tabe baki

Wani jiri ya kwashi Waheedah. Tayi sama dabas tayi zaman yan bori a kΓ sa. Nan da nan ta sa kuka. Ba wai kukan faduwar da tayi bane. A'ah kuka ne akan zallar kiyayyar da Marka ke nuna musu a cikin dukkanin jikokin ta... Sun zama saniyar ware acikin jikoki. Tsana ce ta ke musu mai yiwuwar fassarawa.

Kamal ya fito daga bandaki da sauri. Ya ajiye kwandon sosan wankan su a gefen daki. Ya nufi wajen Waheedah da ke sheme ta na kuka babu mai tanka mata. Ya dagata da sauri yana dudduba kafafunta da hannuwan ta.

"Ba inda kika ji rauni ko? Eh Waheedah."

"Babu Yaya..."

"Me zakiyi da bokitin nan.?"

"Ruwa.. Zan debowa Marka."

Ya dauki bokitin ya fice waje ya ebo ruwan ya kai dede kofar dakin Marka ya ajiye .

"Ba kai daya nake so ba .... Kai biyar nake bukata." Ta karasa fada tana yatsina.

"Yaya zan ebo."

"Keda baki da lapia. Barshi "

"Uhm se an ebo dai. " Marka ta sake fada hade da sakin guda.

"Wai ni Marka karfe nawa zamu tafi ne. Naga garin ya fara hadewa " cewar Inna Sa'adatu.

Marka ta sheke da dariya tana murna . Farin ciki ya wanzu a fuskar ta sosai tace,

"Mai jegon ma ta kira wayar mai sunan Malam. Tace ko mai dare da yardar Allah zasu zo nan. Anan zatayi wankan ina tunani "

'ahto Alhamdulillah.. Allah ya kawota."

"Aamin."

Kamal ya cigaba da zubawa Marka ruwa. Har sai da yayi kai biyar tukun sannan ya ajiye bokitin. Ya koma ya temakawa Waheedah ta koma daki. Sannan ya shige dakin su. Saboda jikin sa har ya fara ciwo.

Marka ta debi ruwa tayi bandaki tana yan wake wakenta.

Ba jimawa Najib ya shiga gidan dauke da babbar kular abinci ya kai daki wajen Waheedah.

"Gashi ..."

Waheedah ta daga kai ta kalle shi.

"Ku zuba ku ci..."

"Bari na kira yayan...."

Ya je dakin su ya kira Yayan na su. Dan har ya kwanta ma shi Kamal din yanata juye juye.

"Gani nan......" Ya fada a wahalce.

Ko da suka koma dakin suka bude kular, Waina ce da funkaso da sinasir da alalan cikin ganye. Sai miya dauke da nama fal a kulle a leda baka babba

"Samo wuri ka zuba shi ..."

"To Yaya."

Najib ya samu mazubi ya zuba komai. Suka debi nasu suka bar na waheedah. Sauran kuma zasu dumama suci.

Fitowar Marka daga bandaki kenan. Zahara'u yar autar Marka. Wadda ta haihu tace zata biyo gidah komai dare. Ce ta shigo gidan

Tana gaba yaran ta 3 wani na bin wani suka biyo ta a baya. Ita kuma da jaririn a bayanta. Yayinda mijin na ta Adamushe yana bayan su yana muzurai.

"Oyoyo oyoyo..." Yara sukayi kan zahara'u da yaranta anata murna.

Marka ta karbi jaririn tanata masa wasa.

Adamushe ya harde kafafu yaci magani. Fuskar sa ta cika tayi fam tankar zata fashe cikin kolokuwar bacin rai . Ya saita hannun sa setin kan fuskar Zahara'u tamkar zai waska mata mari yace,

"Na sake ta saki 3 ....... Babu komeee. Sannan wannan bakin jaririn da hanci hura hura da girman Allah ba 'da na bane. Ba jini na bane. Na karkare miki zance. Wadancan ukun ma ban amince na waje na bane. " Yana karasa fada ya yi hanyar zaure zai fuce ...

_INA MASOYA KUMA MA'ABOTA KAMSHI MA SU KAUNAR KAMSASAWA A KODA YAUSHE? DOMIN KAMSHI RAHAMA NE.._

_TO KU MATSO, DOMIN WANNAN KARON MA ZAFAFA BIYAR SUN ZO MU KU DA TALLAN MASARAUTAR KAMSHI NA KAMFANIN TURAREN *YERWA INCENSE AND MORE*_

_A *YERWA INCENSE AND MORE* ZA KU SAMU TURARUKAN WUTA NA *GIDAH, NA KAYA, NA TSUGUNNO* BA A NAN KADAI SUKA TSAYA BA. AKWAI *KHUMRAHS* MASU KAMSHIN LARABAWA DANA FRUITS KAI DAMA KAMSHIN TURAWA. AKWAI KHUMRAHS TA MATAN AURE DA TA YAMMATA_

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull