Kenza eBookz

Farhatul qalbi complete - Chapter 25

Farhatul qalbi complete - Chapter 25

Farhatul qalbi complete Chapter 25: Farhatul qalbi complete Chapter 25. "ALLAH (SWT) da ya sanya wannan danga ta tsakanin mace da namiji bai barsu haka nan…

4,500 words

"ALLAH (SWT) da ya sanya wannan danga ta tsakanin mace da namiji bai barsu haka nan kara zubeba , suyi ta saduwa barkatai ba tare da wani tsari ba.saboda idan abin ya zama haka tsarin rayuwar yan adam zai wargaje. Domin kuwa za ai ta samun“yaya barkatai batare da masu daukar nauyinsu ba. Don kuwa basu da wani uba guda daya tsayayye wanda zai dauki dawainiyarsu. Wannan zai sa rasa tausayi tsakanin alumma, domin kuwa babu wani wanda zai nuna cewa akwai wata alaka ta jinnu tsakaninsa da wani wanda har zaisa ya rinka jin tausayinsa yana raga masa. Saboda haka ALLLAH ya hallata aure tsakanin mace da namiji, ya zama kuma cewa aure sunnace guda ta annabi ce da take wajibi a wajen duk mai iko yayi shi. Kuma yazama dole kafin ayishi sai anyi sadaki da waliyai da kuma shaidu. Sadaki yana nufin ladan da zaa baiwa mace saboda halarta farjinta, kasancewar kuma mace bata aurar da kanta , ya zama dole asamu waliyi (mahaifinta ko danginta maza ko alkali ko sarki) da zai aurar da ita. Wannan zai iya zama garkuwa gareta daga wulakanici da zai iya yiwuwa mijinta yayi mata. Shaidu kuwa, domin su shaida kulla dangantaka aure tsakanin maauratan domin kiyaye da yin shaida kan dukan wani hakkoki da suka rataya da aure, zuriya da sauransu.Musulunci addini ne da ya kunshi komai da komai don inganta rayuwar dan Adam a duniya da Lahira.

"Bai bar dan Adam ya yi amfani da hankali da tunaninsa kawai don tsara wa kansa makoma ba, saboda shi dan Adam mai rauni ne, mai son zuciya ne, mai hadama ne, mai rowa ne, kai karewa ma mai butulci ne ga wanda Ya halicce shi... Astagfirullah, To in har zai yi butulci ga Mahaliccinsa, ta yaya zai tsara rayuwar da sauran abokan zamansa za su ji dadi?

"Aure daya ne daga cikin ginshikan rayuwar al’umma, wannan ya sa Musulunci bai bar shi sasakai ba ka’idoji da dokoki ba. Kuma baya ga ka’idojin zamantakewa a tsakanin ma’auratan, duk da ba a fata, amma ya tsara yadda za a rabu idan aka kasa samun jituwa ko maslaha a tsakanin miji da matar. A cikin Alkur’ani Mai girma a Suratul Bakara Aya ta 221. Allah Madaukaki Yana cewa: “Kuma kada ku auri mushrikai mata (arna), har sai sun ba da gaskiya. Hakika baiwa mumina ta fi mushrika koda ta kayatar da ku. Kuma kada ku aurar wa mushrikai maza wadanda kuke yi wa walicci, har sai sun ba da gaskiya. 'Hakika bawa mumini ya fi kafiri, koda (kafirin) ya kayatar da ku.

"Wadancan suna kira ne zuwa ga wuta, Allah kuma Yana kira ne zuwa ga Aljanna da gafara da izininSa. ' tsarki, amma duk sauran abubuwa sun halatta su yi da su. 223. “Matanku gonakinku ne, sai ku zo wa gona kinku ta inda kuka so, kuma ku gabatar da (basmala da hamdala da addu’o’i na alheri) don kanku, ku ji tsoron Allah, ku sani hakika ku masu gamuwa da Shi ne. "Kuma ka yi wa muminai albishir “dakyakkyawan sakamako).” Hadisin Annabi (SAW) da Buhari ya ruwaito ya ce, “Dukkan abin haihuwa an haife shi ne a kan tafarkin Musulunci, sai dai iyayensa su mayar da shi Bayahude ko Banasare ko Bamaguje. ki sani, allah Mai ji ne, Masanin abin da kuka fada ko kuka aikata... Kina saurara na?"

Ahlam ta dan juyar da kan ta. Ummimi ta zura hannu ta kwace wayar da Ahlam din ke kokarin boyewa bayan ta gama chatting. Ta cigaba da cewa,

"Bana jin kinsan hakkokin miji akan matar sa, An karbo daga Abu Hurairah (RTA) yace: Manzon ALLAH (SAW) Yace: dan mutum ya kira matarsa zuwa ga shimfidarsa amma bata je masa ba, sai ya kwana (a wannan daren) yana fushi da ita, Mala'iku za suyi ta la'antarta har (zuwa) wayewar gari». Bukhariy da Muslimne suka rawaito shi.

"A wata ruwayar ta su kuma:; «Idan mace ta kwana tana mai kauracewa shimfid'ar mijinta, Mala'iku za suyi ta la'antarta har (zuwa) wayewar gari»A cikin wata ruwayar kuma: Manzon ALLAH (SAW) Yace: «Na rantse da wanda rai Na yake hannunsa, babu wani mutum da zai kira matarsa zuwa ga shimfidarsa kuma sai taki zuwa gareshi, face wanda Ke cikin sama Ya yi fushi da ita har sai (mijinta) ya yarda da ita» A cikin wannan Hadisi: "akwai dalili mai karfi akan haramcin bijirewar mace dan mijinta ya bukace ta zuwa ga mu'amalar aure, domin cewa lallai fushin ALLAH zai tabbata a gareta, a tare da haka kuma akwai la'antar Mala'iku".Wajibi ne mace ta zamo mai kokari wajen sauke hakkokin mijin ta akanta daidai gwargwado ba tare da jinkirtawa ba, ko a sanya sharuda ko sharadin sai ya mata wani abu ko ya bata wani abu wannan haramun ne, matukar dai tana halin lafiya, wajibi ne akanta ta sauke hakkin mijin ta musamman hakkin mu'amalar aure duba da in taki amincewa hakan zai cutar da shi ya iya jefa shi cikin hali na damuwa ko sabon ALLAH.Manzon ALLAH (S.A.W) Yace; Idan namiji ya kira matar shi ga bukatar sa to taje masa ko da tana kan tanda ne [Tirmidhi] Wannan hadisin; Dalili ne akan wajibcin da'a ga miji musamman da'a mu'amalar aure, kuma yana nuni mace ta gabatar da da'an akan shagalgalun ta. Shima kuma miji wajibi ne gare shi, matukar yana ha'lin lafiya ya amsa kiran ta in ta bukace sa, domin dukkan su masu hakki ne akan junan su, rashin bata hakkin ta itama zai cutar da ita ya iya Kaita ga sabon ALLAH, ALLAH ya tsare...

"Haka zalika ki sani aljannar ki tana karkashin kafar mijin ki. Duk kaurace masa da kike a shimfida da kuma kin ladabci agare shi da kula da shi. Lalle kina tattare da fushin mahaliccin ki. Tunda baliga ce ke. Kinsan gaskia kinsan akasin ta Ahlam . Ki sani shirka babbar abace . Domin kuwa hada Allah da wanin sa ne. Bayan Allah buwayi ne gagara misali. Bai haifa ba. Kuma baa haife shi ba. Ba shida kishiya ba kuma ya son a màsa kishiya. Kin dau sirrikan ki komai da komai kina gayawa kawar ki saboda ke din bakida hankali Shashasha ce kuma sakarai lamba daya. To ki sani daga yau wallahi babu hannuna a auren ki da Zayn. ..."

Da sauri Ahlam ta kalli Ummimi.

"Saboda me Ummimi?"

"Saboda bakida hankali. Auren ku ya zo karshe ni dai awaje na. Don ba zaki cutar da su ba. Wallahi kinji na gaya miki. Dan uban ki baa kara auren aka auro mahaifiyar ki? Ko ita kadai kika tashi kika gani agidan ku. ? Wacce bakar mummuna kuma muguwar rayuwa kika daukawa kan ki? Duk akan ya karo aure? Ke dai bakida mutunci."

Kawai Ahlam ta fashe da kuka.

"Ummimi amana ta yaci fa. Ya rasa wadda zai auro sai Waheedah dana rika a matsayin yar uwarta kanwa ta ta jini Ummimi? Taya zanyi zaman kishi da Waheedah Ummimi? Taya? Meyasa Zayn zai munafurce ni ya auro Waheedah Ummimi? "

Ummimi taja tsaki. Kafin tayi kwafa tana kada kai. Cikin hasala tace,

"Halayen ki .. Su suka fara nesanta ki daga zuciyar Zayn. Bakida kirki Ahlam . Summimi kasau ce ke. Mai bin Shawarar kaawaye . Gashi kawar ta kai ki ta baro ki. Kafata kafarki kinji na gaya miki. Dukkanin hirararakin naku da kawar taki duk mun saurara. Zakuje wajen boka ko da zai lalata rayuwar Waheedah. Ta fita daga gidan Zayn. Ku kuma raba Zayn din da mahaifiyar sa data kawo shi duniya. Sannan ku mayar shi saniyar tatse da rakumi da akala sai yadda kikayi da shi ko? Yar banzar yarinya yaushe har kikasan wadannan mugayen alkaba'en.? Ki auri mutum da hakoran sa 32. Da mahaifiyar sa da ta dauke shi wata 9 ta haife ta shayar da shi har girman sa ki ce zaki raba su? Haka zalika Allah ya hada auren sa da Waheedah. Yarinyar da biyayya tayi ba zabin ranta ba aka aura masa ita kice ta ci amanar ki zaki salwanta rayuwar ta? Karya kike wallahi. Ba boka da ke aiki kamar yankan wuka ba. Kinsan Allah kinga wayar nan daga yau tabar hannun ki. Ke da ki sake saka yarinyar nan kawar ki a idonki ko kuyi magana a waya sai ranar da Allah yayi da rabo. Amintar ku ta kare wallahi. Ba bu ke babu ita. Auren ku kuma bazai bata zumunci ba wallahi. Dole a hakura da shi. Idan kinyi hankali inda rabo kya dawo. Amman dai yanzu ya kare. Tunda ba kaunar sa kike ba..."

"Wallahi Ina kaunar sa."

"Kina kaunar tasa kike Shan magungunan hana daukar ciki? Matar da bata son karuwa da mijinta ai ba mata bace. Ko kuwa?"

Ta juya tana kallon yan parlorn. Suka amsa baki daya. Dukkanin su ransu ba dadi. Mahaifin Ahlam ya tashi a zuciye. Gamin yadda take bin Ummimi da wani kallo. Ya wanke kuncinanta da mari har hudu. Tamkar ruwan taurari me hatsihatsi haka Ahlam ta shiga gani tsabar gigicewa da zafin marukan. 🤣

"Marar mutunci. Shashasha. Sokuwa kuma sakarai marar kwakwalwa. Ki sunkuya ki bawa Ummimi hakuri kuma ki bawa Haj Hameedah hakuri dan uban ki.... Wannan da haihuwar ki gwara a ..."

"Dan Allah kar ka karasa. Ka dubi girman Allah .." Ummimi ta hana shi.

Haka dai suka tasata agaba. Kowanne yana tofa albarkacin bakin sa. Me fada nayi me zagi nayi. Kowanne dai sai da ya tsawatar wa Ahlam

Wunin ranar baki daya akan Ahlam ya kasance. Har dare bayan anyi sallah. Jan kunnen suka cigaba da yi. Daga karshe aka karkare akan tafiya da Ahlam .

Ummimi ta tasata agaba suka tafi. Kan idan ta kintsu zaa dawo da ita. Idan kuma akwai sauran daga to auren su da Zayn ya kare. Don basa san zumuncin ya rabu shi ya saka suke bin zarcewar umarmin sannu ahankali.....

#DeStInEd LoVe...💕 _INA MASOYA KUMA MA'ABOTA KAMSHI MA SU KAUNAR KAMSASAWA A KODA YAUSHE? DOMIN KAMSHI RAHAMA NE.._

_TO KU MATSO, DOMIN WANNAN KARON MA ZAFAFA BIYAR SUN ZO MU KU DA TALLAN MASARAUTAR KAMSHI NA KAMFANIN TURAREN *YERWA INCENSE AND MORE*_

_A *YERWA INCENSE AND MORE* ZA KU SAMU TURARUKAN WUTA NA *GIDAH, NA KAYA, NA TSUGUNNO* BA A NAN KADAI SUKA TSAYA BA. AKWAI *KHUMRAHS* MASU KAMSHIN LARABAWA DANA FRUITS KAI DAMA KAMSHIN TURAWA. AKWAI KHUMRAHS TA MATAN AURE DA TA YAMMATA_

_SANNAN SU NA DA *TURAREN WANKA DANA SHAFAWA BAYAN AN KAMMALA WANKA.* BA ANAN TURARUKAN NA SU SUKA TSAYA BA. AKWAI *KULACCAM* MAI MATUKAR KAMSHI DA SANYAYA ZUCIYA, SANNAN SU NA DA *MADARORIN TURARUKA NA JIKI DA NA KAYA*_

_AKWAI TURAREN *AL'AJABU NA TSUGUNNO DA KHUMRAH* DIN SA_

_SANNAN SU NA DA *TURAREN GASHI NA CREAM DA KUMA SPRAY DIN SA NA FESAWA*_

_BA ANAN SUKA TSAYA BA. SU NA DA *TURAREN MOPPING, DA NA BANDAKI AKWAI NA RUWAN WANKI DA NA FESAWA A DRAWER KO AKWATI*_

_AKWAI KAYAN GYARARRAKI NA FATA. KUJERAR TSUGUNNO, KASAKE NA WUTA, COAL IGNITER TA KUNNA GARWASHI, ELECTRIC BURNERS DA ENGLISH COAL_

_AKWAI LAFFAYAS DA SAURAN TURARUKA NA KAMSHI KALA KALA_

_SU NA BADA KAYAYYAKIN SU AKAN FARASHIN SARI KO SAYA AKAN DAYA DAYA. SANNAN SUNA TURA KAYAYYAKIN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE. KAYAN SU YAN CHADI NE DA SUDAN DA KUMA YERWA WATO MAIDUGURI._

_KYAU, INGANCI DA RAHUSA SAI KAYAYYAKIN KAMFAMIN YERWA INCENSE AND MORE. SAI KUN GWADA ZAKU BAMU LABARI_

_NAMBAR TARHON SU DA ZAA KIRA KO MUSU MAGANA TA WHATSAPP ITACE: 08095215215_

_INSTAGRAM HANDLE DIN SU: @yerwaincense_and_more_

_YERWA INCENSE AND MORE: A NUMBER ONE STOP SHOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS AND MORE_

❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥

*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*

*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*

*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*

😄😄😄😄😄😄😄

*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*

*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*

INAYA(riba biyu)___mamughee

SANADIN LABARINA___Rano

BABU SO___Billynabdul

FARHATUL K'ALB___Miss xoxo

GURBIN IDO____Huguma

*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*

*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*

Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300

*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*

HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank

*Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902

*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107

*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 [11/23, 9:02 PM] Mummyn Yara: _*FARHATAL-QALB*_ _(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_ 💞 _NA_

_NANA HAFSATU_ _(MX)_

_AREWABOOKS:MISSXOXO_ _WATTPAD: MISSXOXO00_

_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_

_PG:64_

_WANNAN LITTAFI DA MA SAURAN NA *ZAFAFA* NA *KUDI* NE. DAN ALLAH KI/KA BIYA KUDI KI/KA MALLAKI NA KI. DON GUDUN SHIGA HAKKOKIN MASU RUBUTAWAR DA MA WADANDA SUKA CIRE KUDI SUKA SAYA..._

______

*Garin* yayi matukar sanyi mai ratsa jiki. Sakamakon ruwan da akai tamkar da bakin kwarya da asubar ranar.

Zaune yake akan sofar da ke dakin sa na cikin gidan su. Room heater na ta dumama dakin.

Ya daga kansa saman pop. Da alamun ya zurfafa a tunani. Wayar sa dake gefe ya janyo.

Gallery ya shiga cikin wani folder da yayi saving da

#ItWasAlwaysYouW💕 Hotunanin Waheedah ne aciki birjik. Wasu daga ciki wanda ya daddauketa ne batada masaniya. Wasu kuma a statuses dinta ya dauka. Ya yinda wasu daga ciki wanda ta tuttara masa ne alokacin da ya tunkare ta da abunda ke cikin zuciyar ta da sunan Dawood.

Zooming fuskar ta ya shiga. Murmushin ta me kayatarwa ya bayyana da hakoran ta a jajjere farare tas da su. Ya shiga zooming wadanda tayi a tsaye.

Kwantaccen gashin kanta dana gira. Ya sai ta zoom din zusa labbanta da suka sha maroon din jambaki. Yaja kasan leben sa. Yana mai saka hannu yana kara karewa labban nata kallo. Ya yinda ya shiga zagaye nasa labban da yatsan sa. ..

Ji yake inama tana tare da shi a halin yanzu. Yana matukar bukatar ta a kusa da shi. Ya sauke nannauyar ajiyar zuciya mai tattare da labarin zuciyar sa.

Kasa hakuri yayi. Ya shiga bandaki ya kuskure bakin sa da mouth wash vanilla flavor. Kai tsaye ya fice daga dakin sa yayi sashen Haj Hameedah mahaifiyar sa.

Yana tafiya yayinda gaban sa ke dukan uku uku. Fatan sa Allah yasa kar su hadu da Maa ta hana shi shiga. Don haka yayita maza ya danna kai sashen.

Yaci sa'a wata mai aikin su ta fito da shara a disposable bag zata zubar. Yayi saurin shigewa ciki bakinsa dauke da sallama a kasan makoshi.

Saman ya haye yanata dube duben lungu da sako . Babu kowa. Hakan yasa ya kutsa kai cikin dakin Waheedah.

Tana kudundune a cikin bargo. Tana bacci hankalin ta kwance. Ya tura kofar ahankali ya datse ta bayan ya murza mata mukulli.

Bargon ya yaye ahankali ya shiga ciki. Tamkar zaa ruga shi ko a hane shi. Saboda yadda jikin sa yake rawa tamkar mazari.

Cikin bacci Waheedah ke jiyo tafiyar tsutsar da ake mata a jiki. Ta karkade jikinta da hannu ta sake mayarda idanun ta ta lumshe saboda yadda bacci ke fuzgarta.

Hakan ba karamun dadi ya yiwa Zayn ba. Ya sake rungume ta a jikin sa. Kanta akan kirjin sa. Yanayin yadda numfashin ta ke fita a hankali yana dukan kirjin sa ya sashi lumshe idanu. Ya yinda dayan hannun sa ke yawo a ilahirin jikin ta...

Ya dan zame kanta ya mayar kan pillow. Ya yinda ya kishingida ya ajiye kansa akan hannun sa. Idanuwan sa na bin Waheedah. Kallon ta yake tamkar zai hadiyeta don kauna.

Dan karamun bakin ta mai dauke da farin man lebe sai sheki sukeyi. Ya kasa hakuri. Ya dora labban sa akan nata. Ya shiga sumbatar ta ahankali a kuma nutse. Daga bakinta ya koma kan hancinta da goshin ta. Bayan kunnenta da kuma kan cibiyar ta..

Lamarin yafi karfin tah. Ta bude idanu da sauri saboda bakon yanayin da ya fara tasiri a jikin ta. Bakinta dauke da addua . Ganin mutum a kusa da ita yasa ta sake bude baki zatayi magana ya hanata.

Ta hanyar saurin hade bakin su waje daya. Ya yinda hannun sa daya ke shafa kwantaccen gashin kanta. Da ke tashin scented hair cream and spray na kamfanin turaren yerwa incense and more.

"Your hair smells heavenly my love.... Shhhhhh! mijin ki ne ... Matsoraciya." Ya karasa fada a saitin kofar kunnenta . Hadi da busa mata iskar bakin sa a kunnen tah... "

Ta shiga mutsumutsun ture shi daga jikin ta. Ya hanata ta hanyar rungume ta tsam a jikin sa tamkar za'a kwace masa ita...

"Baki ji garin da sanyi ba?.... Ki tambayi Maa inada lalura idan sanyi yazo.. "

Kallon sa tayi . Ta kauda kai gefe. Yayi murmushi yana danne dariyar data taho masa.

"Taba jikina kiji zafin da yayi. Amma shikenan idan baki yadda ba .. Bari naje wajen Ma..."

Wajen Maa ya gaya mata bata yarda da ciwon daya fada ba? Tayi saurin riko hannun rigar sa. Daman hakan yake bukata. Gashi ya mata wayo

Ya sake tukwikwiye ta yana mai kara shigewa cikin jikin ta.

"Sanyi .... "

Ya kwantar da su. Tana kallon sa, Amman ta runtse idanu. Shi kuwa sai shagalin sa yake da wasu rassa na jikin ta.

"Kiyi hakuri Love...Haduwarmu ta kasance ne bisa kaddara, Zamowar mu masoya ya faru ne bisa zabin Allah, na bawa son ki gurbi a cikin zuciyata, ya zama dole ne a gare ni, saboda kin zamo wani bangare na rayuwata, haka kuma tunanin ki ya zama masarrafin sarrafa akalar rayuwa da tunani na ..Ina kaunar ki irin kaunar da gangar jiki take wa ruhi. Waheedah, You are my answered prayer, My fulfilled wish, My realized dream..." Ya karasa fada yayinda hannun sa ke kan girarta yana shafawa ahankali.

Gaba daya dan mutan the Adams family ya sake kuncewa Waheedah notin da ke saisaita tunanin ta.

Yadda yake mata ne yasa ta kasa hakuri. Sassan jikinta na aminta da sakon da Zayn ke aika musu. Kasan zuciyar ta na begen bashi hadin kai. Dauriya kawai take yi bataso tabada kai bori ya hau.

Zayn ya lura da hakan. Don haka ya sake zage damtse ya shiga yin yadda yaga dama. Ita har mamaki yake bata. Yanzu yadda yake da shiru shiru da dan daga kai shine me wannan danyen aikin yana sumbatu.?

Ya birgino da ita. Ta dawo kan inda yake bukata. Waheedah ta runtse idanun ta da sauri tana sake matse su. Hade da sunkuyar da kanta kasa...

"Waheedah....." Ya ja sunan cikin salon kauna...

"Um..."

"I want you..... All of you... This instant.. please."

Wani dadi ne ya mamaye ta. Tunawa da tayi da tana period fa. Dariya ta taho mata ta danne. Dan bata kaunar ayi abun kunya agidan Maa.

"Kinyi shiru .. should I...go on...?"

"Ina al'ada..."

Ya danne kasan leben sa da karfi. Takaici ya taso ya kudundune masa a makogaro amman ya danne kawai. Dan yaso ya gano dazun sai kuma bai tabbatar ba .

Gyara mata kwanciya yayi yana murmushi, Itama murmushin nan tayi masa irin na kwalelan ka. Ya girgiza kai kafin yace da ita,

"Farkon sallama ckin salamar samun sa'a da murnar kasantuwa a cikin dausayin ni'imar sanyin murmushin labban bakinki. 😜Kin zarce shiga kinkai bangon kurewa acikin jerin matan da ke takama da kyau, Shiyasa idona baya gajiya da kallonki ayayinda murmushina yake bayyanuwa alokacinda nake kallonki Waheedah... A koda yaushe tun farkon haduwar mu da ke. Kika zama mamallakiyar ZUCIYA ta. Tun ban tabbatar ba Waheedah.. Ko kinsan yawan zuwan da nake sashen nan duk akan ki ne? Wani lokacin zakiga idan kin gayshe ni ina basarwa ko naki amsawa wallahi Waheedah kaunar ki ce ta mun illa acikin zuciyata. Ta mun wani irin kamun da idan banyi tozali da ke ba ranar ZUCIYA tah ba ta samun FARIN CIKI....My permanent relationship status – taken forever by the most gorgeous woman in this universe. Love ya soo much wifey.. Waheedah.."

"Uhmm"

"Wait.. Ni fa nagaji da sauraron uhm da um dinki tun dazu. Ki bude baki ki mun magana. Dan Allah ki dena azabtar da ni da rashin jin muryar ki... Waheedah "

"Na'am..." Ta amsa shi a hankali...

"Ki ce wa Maa zaki bini mu kuma gidan mu .. Kinji?"

Tayi shiru bata amsa shi ba. Don ba zata taba aikata wannan magana ta rashin kunya ba.

"Kinji?" Ya sake fada mata yana zagaye labbanta da hannun sa.

"I can't... I won't"

"Haka kikace?"

"Eh..."

"Okay fine...."

Tayi shiru bata sake cewa komai ba. Ya sake gyara mata kwanciya yana shafa gadon bayan ta . Gaba daya ya hanata komawa bacci. Ta rasa yadda zatayi.

"Kinyi shiru ..."

"Bacci nake ji dan Allah..."

"Ni mamaki kike ban. Har kina iya bacci a gidan sirikan ki. Ga gidan mu can ki zo mu koma kin ki. Itama Maa ta bani matata taki. Gaskia an kusa kai ni karshe. Hakuri na ya kusa karewa. Allah zan zo na sace ki mu gudu. Ba zasu kara ganin ki ba sai kinzo haihuwa gidah . Ko kuma mu zo mu su da jaririn ko jaririyar..."

Ita dariya ma zancen na sa yaso bata. Ta dan murmusa kawai. Wannan murmushin da tayi ya sake tabo kaunar ta dake zuciyar Zayn. Hakika Waheedah na da wani murmushi da ke kara mata kyau. Haka kawai idan tayi sai kaji ka samu nutsuwa.

Zayn ya samu kansa da dago da habarta. Ya sumbaci saman bakin ta da karan hancin ta. Ita dai ta kulle idanunta gam. Tana kambama kokarin sa da baya gajiyawa da showering dinta da kisses..

"Waheedah... So tamkar hasken rana yake da yake haske fuskar da take d'auke a jikin gangar jiki, ma'abociyar ZUCIYAr da take 'kunshe da so. Kasantuwar so a cikin zuciya kan motsa ruhi ya kuma busar da idanuwa daga barin yin bacci a mafi yawancin dare, So kan samar da wasu rassa a cikin ZUCIYA bayan bayyanar sa, wato bakin-ciki da kuma FARIN CIKI. Zan ci gaba da son ki a cikin kowane irin yanayi. Ina kaunar ki sosai...You fill all the emptiness in my heart. I’m so thankful to have you in my life. I love you very much...."

Daman bacci ne yake fizgar su duka. Murmushi kawai tayi jin karshen kalaman sa. Ya kundune ta tamkar itace bargon su. Dakyar ya kyaleta taja bargo ta lullaba.

Yanata neman maganar sa bata kula shi ba. Saboda baccin da ke cin ta. Nan da nan kuwa ya dauketa ba jimawa kuwa shima baccin ya sace shi.

Dukan su numfashin su na fita ahankali. Suna baccin su gwanin ban sha'awa. Zaka rantse irin masoyan nanne da sukai shekaru suna dakon kauna...

×××××

°°°°

×××××

*WAYEWAR GARI*

Waheedah ta riga Zayn tashi bayan da gari ya waye. Ta dubi yadda ya cukwikwiyeta tamkar kayan wanki. Ta shiga kokarin zame hannun ta da jikinta daga nasa. Amman ta kasa, Saboda tsananin yadda yayi mata rikon da ba na wasa ba

A dole haka ta hakura ta koma ta kwanta. Sai bayan wajen minti talatin tukun sannan Zayn ya farka. Ya kishingida yana kallon Waheedah da wani baccin ya sake dauke ta.

Kallon ta yake tamkar zai hadiyeta dajya. Kallon ta yake cikin so da kauna. Kallon ta yake cikin silar FARIN CIKIN sa. Kallon ta yake kallo na mamallakiyar ZUCIYAr sa da gangar jikin sa baki daya. Shi kansa bai san adadin kaunar da yake yi wa Waheedah ba.

A hankali ta shiga bude idanun ta har ta sauke kallon ta baki daya akan sa. Ya kai saitin bakin sa labbanta kenan aka shiga bugo kofar dakin.

Da sauri waheedan ta mike tana inda inda. Yatsanta a baki. Zayn sai murmushi yake.

"Waheedah... Kin tashi?" Muryar Maa ta doki kofofin kunnuwan su.

Zayn ya saka murmushi. Waheedah ta juya ta dankara masa harara. Ta matsa kusa da shi kasa kàsa tace,

"Kace na tafi makaranta.."

"Weekend din?" Ya bata amsa yana daga girar sa.

Sankarewa tayi a tsaye. Kafin da sauri ta shige bandaki. Shi kuma Zayn ya mike dama. Daama yake nema kuma ya samu a kusa. Ya bade idanun sa da kasa. Ya bude kofar da mukulli. Yana murmushi.

"Ah.... Maaa.! Barka da safiya" 😂ya durkusa har kasa yana gayshe ta.

Ita kanta Maa din sai kunya ta kama ta. Gefe daya kuma tasan da biyu yayi hakan. Don ya nace a bashi Waheedah taki. Shine ya biyo mata tanan. Don da daddare ita ta rufe kofar sashen don haka da asubah ya shigo .

"Alhamdulillah..... Kana lapia? Kace kanka yana ciwo jiya da safe."

"I've never been this better .... 🤭Jazaki Allah bil jannah Maa.. oh Waheedah tana wanka" Ya karasa fada yana sosa keya.

Bata sake cewa da shi komai ba. Ta sauka kasa. Shi kuma ya danne leben sa yana murmushi.

Ya koma cikin dakin ya zauna a bakin gado. Sai murmushi yake shi kadai. ZUCIYAr sa dankare ta ke da FARIN CIKI....

_____________________

Sosai Umma Hadiza kasuwancin da take ya karbe ta. Allah ya sanya mata albarka aciki. Tana ciniki sosai.

Don ta dawo da Najib ma gaban ta. Shagon da ke wajen gidan gwaggo haule anan Najib din ke kwana.

Haj Hameedah ce ta bawa Umma Hadizan jari me tsoka ta kuma kara mata da wanda farfesa Adams yake bawa maaikatan sa na zakkah.

Ranar Umma Hadiza har kukan FARIN CIKI tayi. cikin ZUCIYAr ta babu wata sauran damuwa sosai

Ta samu albarka na suturu da kayan abinci sosai alkhairi kala kala. Hajia Hameedah da danginta sukai mata.

Bataso rabuwa da ita ba. Sai dai babu yadda za'ayi tacigaba da aiki a karkashin su duba da uwnzun ta zama sirika awajen su. 'yar ta na auren 'dan su. Yanzun Najan Isubu ke mata aikin.

Duk sauran bakin cikin da ke ZUCIYAr Umma Hadiza da ahalinta ya kare. Sai FARIN CIKI da ya maye gurbin sa.

Hakika hakurin su yayi riba. Allah kuma ya karbi adduoin su. Ya dubi wankakkun zuciyoyin su ya musu zabi da mafificin alkhairin sa.

Tarin manema nata zuwa mata. Neman auren ta, Amman Umma Hadizan ta dakatar da dukkanin su. Musanman yanzun da bata fita ko'ina. Tana dai zaune tana mai kula da lapiar Najib....

*GIDAN MALAM NA LADO*

_INA MASOYA KUMA MA'ABOTA KAMSHI MA SU KAUNAR KAMSASAWA A KODA YAUSHE? DOMIN KAMSHI RAHAMA NE.._

_TO KU MATSO, DOMIN WANNAN KARON MA ZAFAFA BIYAR SUN ZO MU KU DA TALLAN MASARAUTAR KAMSHI NA KAMFANIN TURAREN *YERWA INCENSE AND MORE*_

_A *YERWA INCENSE AND MORE* ZA KU SAMU TURARUKAN WUTA NA *GIDAH, NA KAYA, NA TSUGUNNO* BA A NAN KADAI SUKA TSAYA BA. AKWAI *KHUMRAHS* MASU KAMSHIN LARABAWA DANA FRUITS KAI DAMA KAMSHIN TURAWA. AKWAI KHUMRAHS TA MATAN AURE DA TA YAMMATA_

_SANNAN SU NA DA *TURAREN WANKA DANA SHAFAWA BAYAN AN KAMMALA WANKA.* BA ANAN TURARUKAN NA SU SUKA TSAYA BA. AKWAI *KULACCAM* MAI MATUKAR KAMSHI DA SANYAYA ZUCIYA, SANNAN SU NA DA *MADARORIN TURARUKA NA JIKI DA NA KAYA*_

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull