Kenza eBookz

Farhatul qalbi complete - Chapter 6

Farhatul qalbi complete - Chapter 6

Farhatul qalbi complete Chapter 6: Farhatul qalbi complete Chapter 6. *_Muna godiya da zaΙ“in zafafa biyar πŸ˜˜πŸ˜˜πŸ˜˜πŸ™πŸ»_* [11/23, 9:01 PM] Mummyn Yara:…

4,497 words

*_Muna godiya da zaΙ“in zafafa biyar πŸ˜˜πŸ˜˜πŸ˜˜πŸ™πŸ»_* [11/23, 9:01 PM] Mummyn Yara: _*FARHATAL-QALB*_ _(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_ πŸ’ž _NA_

_NANA HAFSATU_ _(MX)_

_AREWABOOKS:MISSXOXO_ _WATTPAD: MISSXOXO00_

_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_

_PG:16_

"A tsallaken unguwar nan ta gaba. Inda ake kira da Mahe janshan."

"Oh okay nagane inda take fada Maa. Wajen gidan su Ibro me gadi. Mahe junction."

"Oh okay nagane..... "

"Eh to.. Ta nan unguwar taku suke bi su karasa makarantar saboda yafu kusa. Tsallaka titi kawai zasuyi. Idan ta unguwar mu ne kuwa sai sunyi shatale tale."

"Eh gaskia kam tanan din zai fi. Allah basu sa'a."

"Aamin Yaa rabbi Hajia."

"Secondary kenan?"

"Eh sakandire. Tana aji na daya na babbar sakandire. Sauran aji biyu ta kammala."

"Allah sarki ... Ashe ma ba wata babba bace. "

"Eh .. Daga yayan su sai ita. Dan akwai tazarar shekaru ma tsakanin su. Sai kaninta Najib. Shekara daya da wata biyar ne a tsakanin su ita da shi"

"Allah sarki. Allah raya su duka "

"Aamin Yaa Rabbi ..."

"Maa! Abincin."

"Idan na gidah kake so yana kitchen. Na Zayn kuma ya .."

"Ah banason na akhi. Maa."

Nadra na daga dinning ta kufce da dariya harda kyakyatawa. Itama Umma Hadiza ta murmusa .

"Ai haka suke . Basuda aiki se tsokanar yayan su "

"Allah sarki... "

Cikin haka sai ga sakkowar dan autan ta Moha daga sama. Sanye cikin kayan bacci yanata murmurza idanu

"Maaa ."

"Habibi.... Zo, Ka tashi?"

"Uhm..."

Da gudu ya rungumeta. Ta dora shi akan cinyarta .

"Baka gaysheta ba."

"Ina wuni ?"

"Lapia kalau dan baby. Ka tashi daga baccin?"

"Uhm..."

"Me zaka ci? Oats da pancake ?"

"Nadra je ki masa reheating tun dazu daman na yi masa "

"Okay Maa."

"Kayi brush?"

"Eh .."

"Ka kuskure da mouthwash dinka?"

"Uhm uhm"

"Muje a kuskure. Monday dai insha Allah zakay resuming school. "

Riko hannun sa tayi suka hau saman tare. Daga kuskura bakin ta hada masa da wanka. Ta sauya masa kaya zuwa English wears. Riga da wando na jeans. Rigar spider man.

Sannan suka sakko tare. Ta zura bakar abaya ta yane kanta da mayafin abayar. Dayan hannunta kuma rike da jaka.

"Nadra ki hada masa komai. Ni zan tafi asibiti "

"Okay Maa "

"Hajia fita zaki yi?" Cewar Umma Hadiza. Ta miqe daga zaunen da take

"Eh nace miki inada tiyata dazu ko? Toh zan tafi yanzu ne. Lokacin ya kusa."

"Allah ya temaka, Amin"

"Aamin Yaa rabbi. Bazan wani jima ba zan dawo insha Allah "

"To Hajia Allah ya bada saa yasa ayi aikin cikin nasara "

"Allahumma Aamin Hadiza."

"Akwai abunda zaayi?"

"Kai babu gaskia. Sai dai.. ko..ko ko dauraye ledar abincin can kawai. Kuma dan Allah ki zauna kici abincin nan kafin a gama na rana kinji ko? Da wanda Zayn ya bari duk ki hade."

"Insha Allah Hajia. "

"Yauwa, Sai na dawo "

"Sai kin dawo. Allah ya tsare hanya Amin."

"Amin Yaa rabbi. "

Nan da nan ta isa ga wajen dinning area ta dauki ledar da aka jera abincin akai ta fita da ita wajen famfon wajen. Ta kada omo tayi masa sabi uku ta dauraye ta shanya. .

Ko data kammala. Abincin ta dakko na wajen Zayn dana kitchen din ta hade su waje daya tana kallo

Kayan dadi ne fal. Don wainar kwai ma fala fala har 3 masu nauyi. Nan da nan ta daddauki komi ta raba kashi 3. Taci kashi daya ta kora da ruwa.

Gyatsa tayi ahankali. Ta dora da hamdala tana kambama kyautatawa irin ta Hajia Hameeda da yaranta.

Yar tabarmar dake gefen sink ta janyo ta shimfida ta kishingida. Dake akwai ac a kitchen din. Sanyi mai dadi ya kama ciki da wajen sa. Nan da nan wani daddadan bacci ya shiga fuzgarta. Har dai yayi nasarar dauke ta. Ta shiga bacci tana sauke numfashi ahankali .

*****

Koda ya fita, Direct mota ya shiga ya tada ta ya tafi construction site dinsu.

Nan dinma bai wani mayar da hankali sosai ba. Illa dai ya dudduba files ya kuma ciccike abubuwan da suka kamata hade da saka hannu a wasu ayyukan.

Ya kwantar da kansa ajikin kujera . Yayin ya kallon sa ya koma saman pop. Hankalin sa da nutsuwar sa suka tafi izuwa yanayin daya samu kansa dazu da Waheedah.

Ya rasa mai yasa gaba daya tunanin yanayin su na dazu ya kasa fita daga kwakwalwar sa. Zuciar sa na masa zillo. Yayinda ransa ke hasaso masa wasu tunanin na daban.

Wayar sa nata agajin dauka. Baki daya hankalin sa baya kai sam bai ji ba. Sai da akayi knocking kofar ofishin sau 3 tukun sannan ya samu kansa da dawowar tunani.

"Yes...."

Sakataren sa ne ya shiga ofishin . Cikin girmamawa yace da shi,

"Ranka ya dade. Me gidah wai yana kira baka dauka, Yace ka kira shi idan ka karasa abunda kake."

"Okay tohm."

Sakataren na fita, Zayn ya dau wayar sa da sauri yana dubawa. Tabbas mahaifin na su ya kira sa har sau uku bai dauka ba.

Cikin sauri ya kira shi ya na mai gyara zaman airpod din kunnen sa.

"Assalam Abiey... Eh! Barka da rana. Afuwan Abiey. Okay Ummimi? Alright zan je yanzu naga abubuwan da suka dace a sayo. Tohm. A huta lapia." Yana gama wayar ya zurata a aljihun gaban rigar sa.

Tashi yayi daga kan kujerar ya fice daga cikin ofishin. Kai tsaye ya wuce wajen motar sa. Ya shige ciki ya nufi hanyar gidah kai tsaye.

Kan titin da zai shigar da kai kan hanyar zuwa gidan su ta baya . Wata mota ta mutu akan titin. Wadda ta haddasa go slow sosai. Gashi irin babbar gingimarinnan ce tafkekiya mai dauke da shanu aciki. Kuma motar zatayi U-turn sai ta tsaya chak ta lalace awajen.

Hakan yasa motocin da zasu shige . Da wanda zasu miqe da masu yin kwana duk sun tsaya chak. Ba dama ka juya ka canza hanya. Traffic din ya riga da yayi jamming .

Takaicin hakan yasa Zayn sakin siririn tsaki. Ya kara ac hade da saukar da kujerar sa tayi baya. Ya dan kwantar da kansa.

Wayar sa ya janyo yana duba mails. Chan ya koma kan Whatsapp . Group dinsu na dangin THE ADAMS FAMILY ya hada tarun sakonni fal.

Shiga yayi da niyar clearing ya ga hotuna rututu sunata turawa. Harda na Ahlam data turo bakin style din the bratz.

Nan danan ya danna button din clearing ba tare dayabi kan tattaunawar sa suke ba. Ya kashe datar ya ajiye wayar a agefe.

Cikin haka sai ga dandazon yan makarantar government senior secondary school shurah an ta so su. Sunata tudadowa.

Dake titin a tsaye yake chak saboda motar data lalace, Hakan ya sanya daliban samun damar wucewa hankulan su a kwance.

Waheedah da ke tafe tare da su Hindu Allah Allah take ta koma gidah. Saboda yadda kanta ke sara mata.

Tamkar ance ya dago. Ya samu kansa da sauke kwayar idanun sa akan.....

❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯

*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*

*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*

*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*

πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„

*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*

*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*

INAYA(riba biyu)___mamughee

SANADIN LABARINA___Rano

BABU SO___Billynabdul

FARHATUL K'ALB___Miss xoxo

GURBIN IDO____Huguma

*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*

*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*

Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300

*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*

HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank

*Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902

*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107

*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°_*FARHATAL-QALB*_ _(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_ πŸ’ž _NA_

_NANA HAFSATU_ _(MX)_

_AREWABOOKS:MISSXOXO_ _WATTPAD: MISSXOXO00_

_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_

_PG:17_

Akan yan makarantar dake wucewa. Wasu na tafe suna ciye ciye. Wasu suna hirarrakin su yayinda wasu ke tafiya kawai.

Ya kifa kansa akan sitiyarin motar yayin da fuskar sa ke kallon waje. Tamkar almara yana sake bude idanun yaga tamkar yarinyar nan ta dazu. Suna tafe su uku. Biyu na hira, Ya yin da ita kuma kawai tafiya take. Amman daka gansu kasan atare suke.

Hannunta daya ta saka ta na gyara zaman gilashin idanunta da suka kara mata kyau. Ya sake bude idanu. Wata zuciyar na ingiza shi. Da shi kansa ya kasa gane menene dalilin?

Ya sake matse idanu ya bude. Wannan karon kuma ba ita yagani ba. Wasu ne daban yan makarantar su ma su uku suna tafe.

Girgiza kai yayi kawai. Kenan yarinyar nan gizo ta fara masa.? Har idanun sa ke nuna masa hotanta bayan ba ita din ba ce.

Ya sauke zucia . Hade da kunna rediyon motan. Labarai akeyi na kasa da yadda ruwa ya yi gyara awasu guraren.

Wayar sa ce ta shiga kara. Mahaifin sa ne ke kiran sa. Nan da nan ya dauka ya dauka.

"Hello Abiey. Na'am, Wallahi Abiey ban karasa ba. Wani hold off ne ya tsare ni. No! Mota ce ta lalace. Amma suna gyarawa. Alright insha Allah."

Dakyar aka iya gyara babbar motar data lalace. Aka samu aka mayar da ita gefe yayin da motoci suka shiga wucewa hanyar su .

Zayn yaja dogon tsaki yana waiwayar motar. Banda rashin bin kaidar tuki na garin kano. Taya babbar gingimari zata biyo hanyar kananun motoci?

Da takaicin hakan ya karasa gidah. Tun daga nesa masu gadi suka wangale masa gate ya shige,

Kai tsaye ya wuce sashen da su Ummimi ke zama idan sun zo. Hannun sa dauke da notepad da pen.

Ya shiga zagaye parlukan sashen da dakunan ciki. Harta bandakuna da duk wasu sockets na gidan sai daya dudduba komai. Ya rubuta abubuwan da suke bukatar a canza da wadanda babu a kawo.

Yana gama rubutawa ya shiga mota ya koma office. Kai tsaye ya wuce babban ofishin mahaifin su dake cikin kamfanin. Dankareren ofishin mai dauke da manyan rubutun: Professor Adams Nasser.

Sai daya fara knocking kafin ya bude kofar ya shiga bakinsa dauke da sallama.

Mahaifin nasa na zaune akan wata kujera mai cin mutane uku. Center table na gabansa yana cike wasu takardu.

Tsugunna wa yayi har kasa ya gayshe da mahaifin na su. Kafin ya miqa masa takardar da yayi rubuce rubuce ajiki.

Mahaifin nasa ya karba yana dubawa. Hade da gyara zaman gilashin da ke jikin fuskar sa.

Take Waheedah ta sake fado masa a zuciar sa. Ya runtse idanun sa da sauri. Kamshin turaren ta na dawainiya a kofofin hancin sa.

Mahaifin nasa ya daga kai ya dube shi.

"Ya akai Zayn?"

Ya bude idanu da saurin sa yana girgiza kai hade da soso kasan keyar sa.

"Bakomai Abiey...."

"To masha Allahu. Kana ji ko?"

"Eh Abiey."

"Zan turawa su Simon list dinnan. Sai su kai komai gidan. Yanzu ka biya wajen Lajawa kace gobe idan Allah ya kai mu yazo gida "

"Tohm Abiey. Insha Allahu "

"Yauwa Allahumma bareek."

"Aamin..."

"Zaka iya tafiya."

"Tou Abiey . A huta lapia "

Ya bude kofa ya fice zuwa inda suke buga snooker shi da abokan sa, A bakin wani pool site

Ko da yaje ma kasa tabuka komai yayi. Ya koma kan kujera ya zauna kawai .

Useey abokin sa dake gefen sa da wayar sa a hannu yace dashi,

"Maza ya ne?"

"Steady oga."

"Nagan ka yau pale. Akwai damuwa ne?"

"Bakomai fa. Kawai nagaji ne."

"Toh Allah yabamu saa. "

"Aamin."

Cikin haka sai ga wasu yan mata su biyu sunje wucewa, sunci ado cikin dogayen riguna fitted. Mayafan su shara shara kamar na tatar koko.

Lameen dake buga snooker da Awais ya riqe bakin sa. Karasawa wajen su Useey dake zaune shi da Zayn

"Wow woah, wawwww"

"Meye hakan sekace ambulance. Haba kaman wasu yan kwana kwana."

"Wasu masu zafi na hango mana. ."

"Suna Ina?"

"Gasu can zasu tsarar da me napep."

Useey ya miqe yana hango su. Tsayawa sukayi su na kallon su banda Awais da Zayn.

"Kallo daya bisa ka'ida dai akace." Cewar Zayn da ke zaune yana duba wayar sa. Don shi ko tashi bai yi ba.

Ussey da Lameen suka tsallaka har inda suke a tsaye sunata tsara su. Kowanen su ya karbo number wadda tayi masa. Useey ya zaro sabuwar dari biyar ya mikawa mai napep din. Yaja suna masu daga musu hannu

Suka tsallaka sunata dariya. Awais yace dasu,

"Ba dai kyau wallahi. Zaku batawa yaran mutane lokaci. Soo not fair. "

"Sai mu zauna mata su bace mana? Ga dama agaban mu?" Lameen ya amsa shi yana daria.

"Rabu dashi. Kasan meyasa yace haka lameen?"

"A'ah."

"Saboda already an hadashi da matar aure."

"Dan an hadani da wadda zan aura sai akace bani da damar kara wasu ukun? "

"Eh dukda hakan kasan dai baka isa ka auro wata nan kusa ba. Sai ka fara aurar sury.."

"Kyale su aboki na. Tunda sunada hankali sukayi fatali da sanin hakan." Cewar Zayn . Fuskar sa a hade.

Ussey ya tuntsire da dariya har yana riqe ciki,

"Banda kai da abun ka abokina. Kai da shi ai du kanwar ja ce. Kai har gwara gwara shi ma, A iya cewa yana da damar karo uku. Kai fa you can't marry any other girl da bata cikin naku family . Dole sai yarinya yar cikin dangin ku. Jinin ku, Kuma tsatson ku daya . Na yan uwan ku The Adams family.."

"Ku inda ake nuna muku a har kullum ba shi kuke hanga ba. "

"Rabu dasu maza, Su je suci gaba da yaudarar yaran mutane. At the very end su zo su auri wadanda basu taba tsammani ba."

"Kai de banza ne Awais. Ji wani mugun fata."

Dariya suka kyalkyale baki daya. Kafin su cigaba da yin snooker din su.

"Ni yunwa ma nake ji."

"To ina zamu je.?"

"Okay I'm out. Later." Zayn yace dasu. Domin shi gaba daya baya cin abokcin eateries ko roadside ko na ordering. Harta na masu aiki bayaci sai wanda Maa ta dafa masa da hannun ta ...

❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯

*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*

*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*

*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*

πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„

*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*

*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*

INAYA(riba biyu)___mamughee

SANADIN LABARINA___Rano

BABU SO___Billynabdul

FARHATUL K'ALB___Miss xoxo

GURBIN IDO____Huguma

*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*

*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*

Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300

*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*

HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank

*Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902

*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107

*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°[11/23, 9:01 PM] Mummyn Yara: _*FARHATAL-QALB*_ _(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_ πŸ’ž _NA_

_NANA HAFSATU_ _(MX)_

_AREWABOOKS:MISSXOXO_ _WATTPAD: MISSXOXO00_

_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_

_PG:18_

Nadra ce ta shiga kitchen din. Hango Umma Hadiza tayi a kwance tanata baccinta hankali kwance, Tausayi ta bata. Ta rufo mata kofar ahankali don kada ta tashe ta.

Tana komawa parlor ba dadewa sai ga mahaifiyar su ta dawo, Dr. Hameedah. Bakinta dauke da sallama,

"Wa'alaykm Salam., Maaa"

"Naam Nadra." Ta karasa fada a gajiye hadi da zubewa a kan kujera . Saboda madaukakiyar gajiyar data kwaso.

"Ban ruwa mara sanyi Nadra "

"Aha MΓ a."

Da sauri ta dakko ruwan a wani mini cooler kaman fridge dake gefen side tables.

"Gashi."

Karba tayi in da sauri tafara sha bayan tayi Bismillah. Sai data shanye tukun sannan ta yi hamdala.

"Ina Hadiza?"

"Tana bacci."

"Allah sarki baiwar Allah."

"Amma kitchen floor fa Maa."

"Haba Nadra ya zaki bar ta ta kwanta a kitchen ? Bayan ga maids restroom nan ."

"Maa bansani ba fa. Kawai na shiga kitchen an ba dadewa naga tana baccin. "

"Ke tun dazu kina Ina?"

"Moha ne ya dame ni sena solving masa puzzle. So Ina sama."

"Mtssss " Dr. Hameedah ta saki tsaki hade da miqewa tsaye tayi kitchen din. Sam bataji dadin kwanciyar da Umma Hadiza tayi a tsakiyar kasan kitchen ba. Bayan ga dakin maaikata nan da suke hutawa da gado da kayan kallo aciki

"Hadiza... Hadiza."

"Naam Hajia. " Umma Hadiza ta tashi da sauri. Da ke batada nauyin bacci. Har damkwalin ta ya zame.Kanannadedden gashin fulani baqi wuluk me sheki ya bayyana.

"Kin dawo.,? Sannu da dawowa Hajia. Bacci ya dauke ni. A gafarce ni. " Ta karasa fada kanta a kΓ sa.

"Haba Hadiza meye haka? Uhm?"

"Nayi lefi Hajia. Banda sharri na bacci ya kwasheni a wajen aiki na? Dan Allah k."

"Ya isa haka mana Hadiza bar bada hakuri Dan Allah. Kaman wadda kikayi wani lefi? Dawowata kenan nima. Nake tambayar Nadra kina Ina tace kina bacci a kitchen. Kinji abunda yaban haushi kenan. Taya ga dakin maaikata nan da gado aciki. Meyakwan ta nuna miki. Tayi shiru."

"Wallahi batada lefi Hajia. Don basusan ma nayi bacci ba Allah. Ni kai na na gama duk abunda zanyi. Sena janyo tabarma dake iska na busawa. Wallahi bansan sanda bacci barawo ya sace ni ba. Don ko a gidah bana wannan baccin. Naurar nan ce masha Allahu take ta busa ni. " Ta karasa tana mai nuna air conditioner din dake buso sanyi

Dr. Hameedah tayi murmushi kawai.

"Muje na nu na miki dakin."

"Da girman Allah Hajia baccin nan na gama shi haka nan. "

"Kinyi sallah?"

"A'ah. Anyi ne? Lalle na jima ina bacci."

"Uku fa ta kusa "

"Kai! Lalle na jima. SubhanAllah; bara nayi alwala. "

"Ga dakin can da bandaki aciki "

"Toh Hajia."

Bakinta dauke da sallama ta shiga cikin dakin. Kwarai matuka ya tafi da ita. Yanayin tsaruwar sa harda kayan kallo. Tamkar dakin amarya amman ace dakin masu aiki ne?

Ta jinjina kai tana sake yabawa da tsaruwar bandakin bayan tayi addua ta shiga ciki.

Ta kama ruwa hade da dauro alwala bayan ta kuskuro bakinta saboda baccin da tayi.

Tuni har an shimfida mata sallaya da hijabin sallah. Nan da nan ta ta zura ta fara sallah. Cikin nutsuwa da bin ka'idojin sallah.

Tana idarwa ta yi adduointa daga bisani ta mayar da komai yadda yake ta koma cikin parlorn.

"Hadiza kinci abincin dazun?"

"Eh Hajia. Bayan naci nema na kwanta."

"Ko dan gaba ki dena kina cin abinci ki kwanta. Ki dinga bari se abincin yayi digesting first. "

"Dajastan.?"

"Afuwan. Ina son nace ki bari abincin ya ., Wannan . Sorry. ..Ah"

"Tanason tace ki dinga bari abincin da kikaci ya tsurga. Kafin ki kwanta " cewar Nassem daya shiga alokacin.

"Oh yes. Tsurga."

Umma Hadiza tayi murmushi

"Kingane ko Hadiza? "

"Nagane Hajia. Allah ya saka da alkhairi."

"Aamin ya rabbi "

"Da akwai abunda zan kama kafin na tafi?"

"A'a babu. Ki tsaya kici abincin rana ko zaki tafi da shi kici a gidah ?"

"To Hajiya."

"Okay great. "

Dr. Hameedah da kanta ta nufi kitchen din. Masu dafa abincin gidan har sun dafa sun kawo. Wata food flask ta dakko me girma ta zuba mata abincin aciki .

"Daga yau ga food flask din abincin ki Hadiza. "

"Hajia du wannan?"

"Eh..."

"Nagode. Allah ya saka da alkhairi. Abincin yayi yawa Hajia. Kinga na dazu ma na rage zan tafi dashi. Da kin rage."

"Ki dena cewa haka Hadiza. Naga yaran naki ba maza bane. Sai mace daya dake zuwa makaranta ? Ko ta iya girki?"

"Eh su uku ne Hajia. Eh ta iya babu lefi."

"To banason musu Hadiza. Kije kuci da yaran dan Allah kinji?"

"Toh Hajia. Allah ya saka muku da alkhairi. Yasa a mizani"

"Amin Hadiza "

Dr. Hameedah ta fice daga kitchen din. Yayinda Umma Hadiza ta sharce hawayen farin ciki. Ta zura hijabinta. Hadi da harhada komai ta zura a hijabi.

"To Hajia zan tafi. Sai zuwa da safen ko?"

"Allah ya kai mu Hadiza. Ki gayda yaran."

"Zasuji insha Allah. "

Ta fuce daga cikin gidan tana mai kambama dattako irin na uwar dakin nata Haj Hameedah.

Har ta karasa gidah. Zuciyar ta bata dena yaba kyawawan halaye na Hajia hameedah ba. Tabbas an nuna mata karamci da tsantsar mutunci .

Ta shige gidan bakinta dauke da sallama. Zainab ta amsa tana kan kujera turmi agabanta tana dakan kuli.

"Umma sannu da zuwa " cewar Waheedah data fito daga cikin daki

"Yauwa Waheedah. "

"Waye ne ... Iyye?" Kande ta shiga kwarara murya fitowarta kenan daga bandaki. Zanin ya dage ana hango jemammun duwaiwukanta a waje. Bayan sarai tasan ummah Hadiza ce.

"Ni ce Marka."

"Ah ni fa in ce naga anyi wuff an shige. Ashe sarki da nadi ce. An dandalo arziki an boye a kurya."

"Kayya Marka kiyi hakuri. Ba haka bane."

Ta yamitsa fuska bayan ta daga hannu ta nana shi a shamilallun cinyoyinta da ba tsoka sai kashi

"Kaji tsoron mutum. Wato Hadiza tunda aka samo miki aikatannan kike wani daga kai kina hura hanci. To bari kiji hurerar bappajo (mahaifiyar Umma Hadiza ) itace tsarar cacar baki na ba ke ba. Dande ta mutu ne da girman Allah da yau har gidan bappajon senaje mun kwashi yan kallo da ita. Mtssss! Aikin kawai." Ta karasa fada hade da kwafa ta koma cikin bandakin

Jikin ummah Hadiza a sanyaye ta shige cikin dakin su. Waheedah nata rarrashinta. Duk yadda taso ta cije sai data kasa. Wasu zafafan hawaye suka shiga reto a fuskar ta. Domin dan aikin nan data samu ya tsolewa Marka idanu har bata iya boye hassadarta .

Dakyar da temakon Waheedah Umma Hadiza ta dena kukan . Ta kasafta abincin. Kuskus ne da jar miya dataji kaji da daffaffen kwai guda 3 . Ta ware musu nasu. Sannan ta dibawa Marka da na MalamNalado da na Inna Sa'adatu.

Ko da aka kaiwa Marka sam tace ba zata karba ba sai an canza mata da kashin hakarkari an saka mata cinya mai tsoka. A Kuma kara mata miyar.

Babu ma. Sai takan abicinta Umma Hadiza ta kalato ta karawa Markan Waheedah ta mayar mata ta karba. Tana danna loma tana aibata su

Inna Sa'adatu ma da Waheedah ta kai catai ba zata karba ba. Karamun dan tah hamisu yasa kukan seyaci. Sai data talle masa keya sau 3. Da karin rankwashi biyu a tsakar kansa. Sannan ta dungurar masa abincin a gaban sa hade da doriyar lailayo ashar ta dura masa

Su kuwa su Waheedah sunaci kunnuwan su na motsawa. Ga karin na safe na Zayn da aka barwa Umman na su dana kitchen da akace ta hade.

Su Najib sai yagar nama suke suna hadawa da abincin. Farin ciki marar misaltuwa ya bayyana a fuskokin su. Ciki harda Kamal da ke kwance a gefe shima yaci ba laifi.

Umma Hadizan nata basu labarin yadda ake mutinta ta agidan na THE ADAMS FAMILY!!!

❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯❀‍πŸ”₯

*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*

*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*

*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*

πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„πŸ˜„

*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*

*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*

INAYA(riba biyu)___mamughee

SANADIN LABARINA___Rano

BABU SO___Billynabdul

FARHATUL K'ALB___Miss xoxo

GURBIN IDO____Huguma

*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*

*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*

Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300

*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*

HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank

*Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902

*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107

*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯° [11/23, 9:01 PM] Mummyn Yara: _*FARHATAL-QALB*_ _(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_ πŸ’ž _NA_

_NANA HAFSATU_ _(MX)_

_AREWABOOKS:MISSXOXO_ _WATTPAD: MISSXOXO00_

_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_

_PG:19_

Γ—Γ—Γ—

Sannu ahankali, Kwanakin mu nata ja, Ya yinda awanni da mintuna suke shudewa. Kwanakin Umma Hadiza da fara aiki bakwai cif. Sati daya kenan

Hakan kuma yayi dai dai da kammalawar karashen aji na daya na babban sakandiren su Waheedah.

Lamarin sai godiyar ubangiji. Don zance na gaskiya Allah ya kara saukakawa Umma Hadiza da ahalinta. Ci da shan su acan acan. Don na safe kawai suke saya su ci. Na rana da wanda zasu ci da daddare Umma Hadizan na tahowa dashi daga gidan aikin na ta.

=========. ===========.

Tunda ta tashi da safe bayan ta gama zuba ruwan, Dauraye kwanuka tayi ta kife hade da kunna turaren wuta na tsinke.

Daki ta koma. Umman su na kwance . Idanunta sun kada sunyi jazir. Ya yinda jikinta ya dau zafi sosai.

Waheedan ta taba jikinta tana rausayar da kai. Cikin rawar murya tace,

"Umma .. Jikin ki zafi."

"Waheedah ya akai?. Bari na tashi ."

"Umma baki da lapia. Muje kyamis"

"Lapia ta lau Waheedah." Ta fada cikin dauriya.

Nan da nan hawaye suka shiga reto a kyakkyawar fuskar waheedan.

"Umma Allah ya baki lapia. Wayyo Allah na Umma."

Umma Hadiza taja siririn tsaki. Cikin kufulewa ta dubi Waheedah

"Allah zan make ki idan kika sake mun kuka. Shikenan ni ba dan adam bace kamar kowa da ba zanyi rashin lapia ba? Haba Waheedah."

"Ummah kiyi hakuri "

"Yauwa, Kin leqa dakin su Yayan na ku?"

"Eh ya koma bacci shi "

"Toh. Ki duba kasan samirar can akwai dari biyu ki sayo kosai ga ragowar biredin jiya nan sai ku hada ku ci. "

"Umma ke fa?"

"Je ki ki sayo ke dai"

"Tah "

Bata sake cewa komai ba, Ta miqe ta dauki kudin bayan ta zura hijabin ta.

Tana tafe tana tunanin halin da ta baro mahaifiyar tasu aciki. Ta sayo kosan ta dawo gidah.

"Umma gashi "

"Toh. Dibi naki ki kai musu"

"Umma ke fa?"

"Wai Waheedah menene haka iyye? Ina magana kina yi. Zaki tashi ko sai na bar miki wajen?"

"Kiyi hakuri Umma." Da sauri ta dibi nata jikinta na bari. Ta gutsiri biredin ta mayar musu nasu

Ta tashi ta kai dakin su Najib. Bayan ta kwankwasa yar kofar kafin ta shiga.

"Umma na kai musu "

"Madalla " cewar Umma Hadiza. Ta miqe dakyar tana gyara zaman hijabin jikinta.

Tun dazu take son tatafi gidan aikinta . Amman data yunkura zata tashi sai jiri ya debeta.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull