Kenza eBookz

Farrah Book 1 na m shakur complete - Chapter 18

Farrah Book 1 na m shakur complete - Chapter 18

Farrah Book 1 na m shakur complete Chapter 18: Farrah Book 1 na m shakur complete Chapter 18. Zama yayi ahankali a dinning Mami tace "when was the last…

4,166 words

Zama yayi ahankali a dinning Mami tace "when was the last time kaci tuwon shinkafa"? Dan kallon fuskan Mami yayi yace "I can't remember" zubamai Mami tayi da lafiyayen miyan busashen kubewa yaji kifi tasamai spoon dan tasan bazaici da hannu ba, sanan tawuce takoma wajen Dad tacigaba da yankemai kumban, saukowa Farrah tayi bayan ta chanza kayan makaranta tasa wani Riga da skirt na kanta black and white dasuka mata kyau ko dankwali bata daura ba ko kadan batasan Zayn na dinning ba falo ta sauko kaman zatai kuka tace "Mami yunwa" Mami dake yankema Dad kumba tace "jeki zuba yana dinning" juyawa tayi zatai dinning Zayn tagani zaune yana cin abinci, daure fuska tayi tawuce dinning din ko kallonshi batayiba shima haka ta dauki plate ta saka tuwo tazuba miya da namomi daban daban sanan ta zauna adayan side of the dinning tafara ci Zayn yadan saci kallonta namomin dayagani tazuba saida yasa yakusan tuntsirewa da dariya, ijiye spoon din yayi bayan yaci just little dan shi he's not a of su tuwo sanan yamike yana rike da glass cup na juice kaman zai zaga ya ijiye wani abu yana zuwa ta bayan Farrah bata ankaraba kawai hannunshi tagani cikin plate na abincin ta ya kwashi namomi iya naman da hannunshi suka iya kwasa dabaisan guda nawa bane, zabura tayi ta mike tareda kwala kara, tace "Mami, Mami kinga Ya Zayn ya debe mini namomi na ko"? Dasauri Zayn yatura namomin abakinshi daidai Mami da Dad najuyowa suka kallosu wani kalan kwarewa Zayn yayi dayasa yafara tari ya watso namomin waje Farrah tahau dariya sosai, Dad yataho wajen harda gudu yakama Zayn din yana bubbugamai baya yace "sorry son, bani ruwa Farrah" ruwan ta tadauka tabama Dad, Dad yakarbi ruwan zaikai bakin Zayn dasauri Zayn yature ruwan yace "bazan sha ruwanta ba Dad" dariya sosai Farrah tayi harda tsalle tamai gwalo tace "eh nima banso kashamin ruwa kasha naka" tsayawa daga Mami har Dad sukayi suna kallonsu juice dinshi Zayn ya kwankwade tass sanan tarin ya tsaya, yakalli Dad yace "Dad kar akara bari tana kwasan nama haka, all she knows how to do is cin abinci babu abinda ta iya" murgudamai baki Farrah tayi yajuya yafice daga dakin fuuuu.

Dad yakalli Farrah dake tsaye har lokacin tana murmushi yace "cinye abincin to azo agyara wajen" gyadama Dad kai tayi dasauri tazauna tace "Dad ni zan gyara dazaran nagama ci, na iya ai ko Mami" Gyadamata kai Mami tayi, Dad yadawo ya zauna, mota Zayn yashiga yafice harzai wuce masallacin su nawaje sai kawai yatuna baiyi salla ba, dan yatsine fuska yayi zagin Farrah na fadomai arai takirashi stupid irresponsible boy&, zai nuna mata he's responsible kuma yasan abinda yakeyi. [12/21, 1:36 PM] +2347066933957🥰: 4️⃣6️⃣

12 suka sauka a airport din garin, wasu manyan government cars ne sukazo daukansu da governor Adamawa da kanshi yazo ya tarbi Dad duk gaisawa sukai sosai sanan aka shishiga mota aka kama hanyan akauyen su Farrah da already tuni security personnel sun cika kauyen dan yau sanadin Dad Gwamna zai taka kafanshi a wannan kauyen. Kusan tafiyan 2hrs yakaisu har kauyen.

Mai gari dawasu manyan mutanen gari ne suka tarbesu sanan aka hadu aka wuce falon mai gari, duk aka zauna kafin kace me mutanen kauye sun taru agaban gidan mai gari ana yada cewa gwamna yazo, saida sukadan natsu sannan Dad yafadi wanda suke nema tukunna da sauri Mai gari ya aika aje akira Malam yazo fada yanzun nan kada yabata lokaci.

Malam na zaune kan tabarma yanacin dafadukan shinkafa da wake dan yanzu rayuwa tai kyau tun kudin da Alhaji yabashi yanzu agarin sune yangayu bayan gidan mai gari, dagashi sai Rakiya ne agidan Inna as usual tanachan gidan nai gari sallama dayaji anata bugawa a kofar gidansu yasa yahakura da abincin yamike yana zura silipas yace "waye, ganinan zuwa" butanshi yadauka yakafa abaki yasha ruwan sanan ya ijiye yay zaure yabude kofa, ganin yaran mai gari Madibbo da babban aminin mai gari yasa yace "ah'ah Tanimu da Modibbo ne, Meya kawoku nan" Tanimu dake kallonshi yace "munyi manya manyan baki a rugar nan, mai gari na neman ka yanzun nan" dan zaro idanu Malam yayi yace "incedai Lafiya" dasauri sukace "lafiya lau muje ance kada mubata lokaci" gyara riganshi Malam yayi yace "to shikenan muje" yana biyedasu abaya har zuwa gidan maigari dayaga kusan duka mutanen karkaransu agaban gidan ga yan sanda nataresu kada su shiga, suna zuwa yaga anbarsu sun wuce faduwa gabanshi yayi yana tunanin mesukayi, suna shiga falon yaga Alhaji (Dad) da wanan kannin nashi (Uncle) dayama ganinsu yaganesu wani bakin yawu yahadiye yana addu'a Allah yasa badai sun gaji da Farrah sun dawomai da ita bane tunda tabar gidan nan gidan yanzu kaman anjanna more kudinsu suke sunaxin dadi hankalinsu kwance yana zaman lafiya da Inna abinshi idan sun dawomai da Farrah ai yashiga uku, waje yasamu ahankali yazauna duk jikinshi yau wani kalan sanyi yace "barkanku da war haka Alhaji dafatan kun iso lafiya, ince bawani abu Farrah tayi kuka dawo da ita ba"? Yay maganan yana karabin falon da kallo yana neman Farrah, murmushi kowa na falon yayi Maigari yace "ba abinda yakawosu ba kennan, abinda yakawosu yafi karfin wannan" wani kalan yankewa gaban malam yayi yafadi yakara kwalalo idanu yace "tooooh" gyaran murya Dad yayi yace "to Alhamdulillah da Allah yasadamu anan wajen gabaki daya" yadanyi shiru yanadan girgiza kai kafin anatse yadubi gwamna yace "gwamna wato kaga Allah yanada yanda yakeyin abubuwan shine sai yanzu nakara gasgata hakan rabo ne yakawo Zayn wanan gari" murmushi gwamna yayi yace "rabone kam yaron dako hanyan dazaibi yazo adamawa bai saniba balle kauyen kudiri" dan murmushi Dad yayi sanan yakalli Malam yace "Malam kasan nai adopting diyarka abisa ka'ida na shari'a dudda hakan bai dauke cewa amusulunce kaine mahaifinta mai asalin iko akanta ba tunda kaine yayan mahaifiyarta uwa daya uba daya saisa yau natako nazo garin nan domin ka" gyadamai kai Malam yayi yana kallonshi shi kawai kalman dayace yake bala'in tsoronji shine suce sun dawo da Farrah kokuma sun gaji da ita zasu maidota, Allah ka dawwamar da ita achan Malam yay addu'an azuciyanshi.

Anatse Dad yace "Malam namo nemawa yarona daka sani Zayn, wanda diyarka Farrah ta taimakamawa awanan gari, nazo nemama d'ana Auren yarka Farrah idan ka yarda" "waiiii!" Malam yafadi yana goge gumin dake ketomai yashiga murmushi yace "Alhamdulillah Alhamdulillah, yooo Alhaji idan ban baku Auren yarnan ba wayema zan bamawa" yasake washe baki yace "kuda kuka mata sutura sannan ni kawunta ma kukamin suruta ai nafadiwa mai gari shatara na arziki dakukamin dan haka Alhaji amatsayina na jinin Farrah, amatsayina na Kawu kuma Uba awajenta nabaku Farrah, ni so samune ma adaura Auren yanzu kubani sadakinta tunda ga mutane daman makil awaje ko mai gari" Malam yay maganan yana washe baki, mai gari ya gyadamusu kai yana murmushi yakalli Modibbo dake gefenshi yace "jekira Alaramma" dasauri Modibbo yatashi, Gwamna yabada ordwr anshigo da goro biscuit da alawa da abubuwa da yawa wanda yasa aka siyo aka loda a booth din mota tun da safe yau dama, nan aka shiga shigo da abubuwa Dad sai washe baki yake yakalli Uncle dake zaune dunkum kaman dusa yace "ciro wayanka kai video komi" gyadamai kai Uncle yayi yaciro wayanshi, Gwamna yace "abar mutane su shigo" kafin kacema fadan yacika makil wasu awaje wasu ta window, liman yatashi atake aka daura aure tsakanin ZAYN GANUWA && FARRAH MUHAMMAD akan sadaki miliyan goma!. [12/21, 1:36 PM] +2347066933957🥰: 4️⃣5️⃣

Wuraren 10 aka budema Uncle gate yashigo gidan yana kallon ko'ina he can't wait for lokacin da all this money will be his, saiya gina gidan dayafi wannan kyau yay alkawari, bari Yaya yayama zaman gidan da akasa yayi a asibiti yahuta yadawo office zaisa yakira lawyer shi, anyway mema yasa yacemai yazo da sassafen nan haka. Wuraren 10 Uncle yashigo falon Mami, tana zaune ita kadai tana duba wani medical book hakanan ga farin glasses a idanunta, gaisawa sukai da Uncle dake sanye da manyan kaya yace "Mami ina Yaya"? Sama Mami ta nunamai tace "yana dakinshi asama" daidai lokacin Dad yahau saukowa daga stairs yaci manyan kaya farare yana kamshi, kallonshi Mami tayi tace "I thought you are still on bed rest ina kuma zaka"? Wani kalan murmushi yayi yazauna kusada ita yace "I will tell you about it idan nadawo yanzu baga Uncle din danki ba he will take care of me don't worry" kallonshi Mami tayi kaman zatai magana saikuma tai shiru, tashi Dad yayi hakan yasa Uncle shima yatashi yadubi Mami yace "tom saimun dawo" "adawo lafiya" dukowa Dad yayi ya manna mata peck a goshi yace "smile for me Matata" dan murmushi tamai hakan yasa yace "tom natafi, idan Zayn yadawo daga wajen aiki kice nace kada yafita yajirani" gyadamaikai tayi tana kallonshi yafice daga dakin.

Saida suka shige jeep din Dad bodyguards suka rufo kofan sanan Uncle yadubi fuskan Dad yace "Yaya wai ina zaka ka kirani karfe biyun dare kaga yanda naji tsoro nazaci wani abu yama sameka ne, ance kadinga bacci maisawai baka iya bacci, me kake tunani haka"? Dan ijiyan zuciya yasauke ahankali yace "tunanin Zayn kehanani bacci" yadaga kanshi yana kallon bodyguards dinshi dake tuki ahankali yace "when we get on board we will talk about it" gyadamai kai Uncle yayi haka dukansu suka zauna sukai jugum har airport, wannan karan private jet suka shiga saida suka tashi sanan Uncle yakalli Dad dayay nisa atunani yace "Yaya wai ina zamune? Yaya tell me what is going on, wani abu yakuma faruwa ne ko Zayn yamaka wani abune Dan Zayn ne kadai kesa kashiga irin wannan damuwan aduniya" dan ijiyan zuciya Dad yasauke ahankali ya kalli Uncle yace "nayi magana da governor Adamawa yanzu haka motoci na jiranmu a airport dashi gwamnann inaso naje kauyen nan na nemama Zayn auren Farrah, inaso adaura Auren!" Wani kalan kallonshi Uncle yayi gabanshi na bugawa ahankali yace "did Zayn know about this?!" Girgixamai kai Dad yayi yace "hatta mahaifiyar shi batasani ba dan banson any abu dazai batamin hukuncin dana yanke bayan angama komi nakoma gida zan gayamusu" daga Uncle har Dad din shiru sukayi suna kallon juna, murya chan kasa Uncle yace "Yaya kasan aure baya gaban Zayn, banda haka ayanda Zayn yake tayaya zai iya rike Farrah amatsayin mata, bama wannan ba kanaganin Zayn zaiso Farrah she is just 18, Yaya anya wanan decision din naka is right kuwa?" Shiru Dad yayi kafin ya sauke ijiyan zuciya yakalli Uncle yace "bayan abinda yasameni dan zaman gidan nan danayi na hutu I was seriously praying har istikhara nayi kan Zayn bawai hakanan natashi zan hada aurensu ba naga abubuwa da dama na sign da alamomi da Allah ya nuna mini dayasa na natsu da hukuncin dana yanke kan shi da Farrah, da ko maganan kirki basayi but kwanakin nan suna magana suna wasa suna tsokanan juna and nasan is a sign Allah ke nunamin I know what I am doing" yay shiru, sanan ahankali yace "bayan abinda yafaru fushin da ni da mahaifiyarshi mukayi dashi yasa yadan natsu at least bai kara zuwa club ba, akwai mutane danasa ana binshi duk inda yashiga sabida yanzu dakanshi yake driving kar wani abu yakara samunshi yasa bai hiring security personnel sudinga binshi dan har yanzu ban manta cewa akwai people out there dasuke son hurting mini yaro ba, yabar zuwa club ko gidan banza, daga office sai school nasu Farrah kawai yake zuwa haka suka gayamin, yadan fara salla yanzu, yadawo da gemunshi baki, sanan tabama yarage sha sosai though yanasha bawai yadaina bane but yaragu, bansan ko nine ke suspecting nashi ba but I've seen him making advances on Farrah!" Yay dan shiru, ahankali Dad yace "da Zayn yama Farrah wani abu gwara na aurar mishi da ita, she's very young tarayyansu I believe shine sanadin shiryuwanshi dan na nemi zabin Allah kafin nai abin nan, naki fadama Mami dan nasanta bazata taba yarda ba, I know my wife sosai, saisa kaga I am doing this all on my own, kaima I need you to support me" gyadamai kai Uncle yayi yace "to Yaya are you planning on suyi moving zuwa gidansu ko mene" girgizamai kai Dad yayi yace "for now suna gabanmu, we will be monitoring them, Zayn is still 26, inaso nagane menene so, inaso yay developing strong affection for Farrah, yarona baitaba soyayya ba, baitaba son wata ba tunda yake saisa nakeso yaso Farrah matuka ta yanda sonda yakemata zaisa ya chanza, Zayn is a good person idanmu iyayenshi bamu iya mun fito da that good side of him outside ba I believe Farrah can, just trust me" gyadamai kai Uncle yayi ahankali &yace "shikenan Yaya Allah yabada sa'a. [12/21, 1:36 PM] +2347066933957🥰: 4️⃣7️⃣

Zaune yake a office din Dad yana sanye cikin wani black suit dayamai kyau bana wasaba idan kaganshi da farko baraka yarda Zayn bane dan he's so concentrating, tunda Dad yabashi aikin nan sai yaune ranan dayasan yazauna ma aikin dan murmushi yayi yadago kanshi dan yagama cikin just how many minutes, hakanan kawai wani kalan faduwa gabanshi yayi dayasa ahankali yakai hannunshi kan kirjinshi yashafa daidai atishawa yazomai dan mikewa yayi tsaye yanabin duka office din da kallo kafin yakalli ogogon bangon office din yaga 1:30 na rana, dan ijiyan zuciya ya sauke sanan yafara tafiya yay hanyar kofa gently yasa hannu yabude kofan sanan yafita, Layla yagani zaune kusada secretary dinsu kallo daya yamata yadauke kai shi baison mace tafiya naci da maita offing nashi abin yake, maida kofan yayi yawuce dasauri Layla tabiyoshi daidai ya shiga lift kafin kofan yarufe ta shige tana kallonshi tace "wai mekake nufi ne batare akace muyi aikin nan ba kullum Saika dinga koroni kana hanani shiga office din" wani matsiyacin kallo yamata sanan ya yatsine fuska kaman badashi takeba wani kalan kulewa tayi hakan yasa tace "wai maisa kacika rainama mutane wayau Zayn eh inamaka magana kamaidani mahaukaciya" wani kalan juyoda idanunshi yayi ya kalleta sannan yadauke idanun abin bakaramin zafi yamata ba hakan yasa tace "wai sabida kazamiyan yarinyar nan Farrah kakemin haka?" Kaman ta tabo wani abu ajikinshi dasauri ya kalleta fuskanshi babu alamun wasa ganin haka yasa tace "yes Zayn, tell me meke faruwa dan bangane maka ba, kai mutum ne dabaka damu da kowa aduniyan nan ba sai kalla, why are you so caring towards that girl, kana fifitani akanta meta fini dashi? Nafita wayewa nafita ilimi nafita kyau nafita karatu, look at me kalli jikina babu abinda zaka nema da bazan iya baka ba, kana marina kanta tell me sonta kakeyi ne are you in love with Farrah Zayn!" Wani kalan bugawa kirjinshi yayi jin kalman so datafadi daidai lokacin sukakai ground floor hakan yasa yabi ta gefenta zai fita hannunshi takama dasauri tafashe da kukan datake rikewa sosai ahankali tace "Zayn please wlh kome kakeso zan baka, I want to be your girlfriend mudinga komi tare har shaye shaye please Zayn" wani kalan juyowa yayi yakalleta sannan yakai hannunshi kan hannunta data daura kan nashi yacire tareda murde hannun idanunshi suna kadawa yace "listen and listen attentively! Karki sake bari wannan bakin naki ya ambato sunan Farrah, and as for this place you can find anybody to work with but forget working with me and lastly" yay maganan yana huci yana matso da fuskanshi dab da nata yana kallon kwayan idanunta yace "I don't f*ck beggars masu rokon maza su cisu naaaa! Zayn yafi karfinki" yakarashe maganan yana jefarda hannunta sanan yajuya fuuuu yawuce mosque abinshi.

Tsugunnawa awurin Layla tayi tana kuka, inhar bazata sami abinda takeso ba to wlh kome Momy keson mishi zata tayata, tanason Zayn yana bala'in burgeta saisa daman taso suyi soyayya suci juna dan Allah ya kera yaron da kyau wlh bata tabayin saurayi kwatankwacin Zayn ba balle nai kama da Zayn.

Salla yayi dan anriga anyi jam'i tun dazu yana idar da sallan ya jingina da bango yay shiru maganan Layla namai yawo azuciya are you in love with Farrah, son Farrah yake? Ya tambayi kanshi he's trying to compare the thing yanzun nan Layla take kuka wiwi sosai agabanshi babu abinda yaji azuciyanshi saima dada murdamata hannu dayayi yamata warning kan karta sake kiran sunan Farrah, da Farrah ne ke kuka haka daba karamin damuwa zaiyiba, he can't stand seeing her angry, nor sad, wani zubin idan yaganta he just want to tease her dan kawai tamai tsiwa tana zaromai manyan white eyes dinnan nata kaman idan ance ta dakeshi zata iya, he loves seeing her happy and smiling tunda yake baitabajin hakan game da any mace ba koda yay sex dake yaji dadi ba sai Farrah da babu abinda ya tabayi da ita beside ma she's too small, is that what love is? Is he falling in love with Farrah yaya ake gane soyayya? Wayanshi yaciro dasauri yashiga browsing how to know you are in love with someone yadage yana karatun sosai.

"Assalam Zayn!" Yaji anmai magana ana shafa kafadanshi dasauri yadago kanshi wani Indian imam dinsu ne na masallacin nan, yanama Dad aiki ustaz ne sosai, dan murmushi Zayn yamai batare daya amsashi ba, zama Imam din yayi agabanshi tareda lankwashe kafa yasha ganin Zayn company nan ma waye baisan labarin Zayn only yaron Ganuwa ba saidai idan baka company nan, anatse yace "what's the matter Zayn"? Shiru Zayn yayi yana kallon mutumin he's elderly dan akalla yayi sa'an Uncle kuma malami ne nagidi, at least baitabama kowa magana ba outside parents nashi baida aboki yamai magana ne, yay shiru dan murmushi Imam din yayi yace "you can always talk to Me Zayn dudda nasan I am nobody zan iya taimaka maka da shawarwari" yay maganan anatse hakan yasa Zayn yaji kawai ya yarda dashi ahankali yadan cije lips sanan yasaki lips din murya kasa kasa ta yanda kowani yashigo masallacin bazai jisuba yace "Imam I am a bad boy I know you know that cus you work here" yadanyi shiru sanan yace "my parents are not happy with me, I am trying to change but kasan menene matsala na I don't think I can leave without women" yadan yatsine fuska dan iyakan gaskiyanshi yake fadi yace "ni baran iya 2-3days without a woman ba before banama iya one day saida nadawo Nigeria ne nazo nafara koya da kyar murya chan kasa yace what do I do"? Anatse Imam yace "kodai ka dunga azumi kokuma kai aure sabida kadinga samin natsuwa daga wajen iyalinka" dan shiru Zayn yayi yana kallonshi batare dayace wani abuba hakan yasa Imam yace "kanada wacce kakeso"? Shiru Zayn yayi saikuma ahankali yadan fuzarda iska Farrah na fadomai arai yace "I don't know, ni banmasan ko inada wanda nakeso ba all I know is kamin tambayan nan is one person yafado raina Farrah and she hates me cus ta taba ganina da wata" yasake maganan yana yatsine fuska, dan murmushi Imam yayi yasaka hannayenshi biyu yakamo hannayen Zayn anatse yace "yaune rana na farko dana taba zama na magana dakai and all I see was myself lokacin danake da shekarun ka, I was once in your position Zayn duk wani rashinji daka sani nayishi aduniyan nan but rana daya shiriya tazomini sabida question din is menene amfanin been a bad boy can you answer this question Zayn"? Ahankali Zayn ya girgizamai kai, murmushi Imam yayi yace "is not easy kabar komi da komi tashi daya but idan kai niyya kazo kafara bautama Allah da kyau he will help you, and yama baka the greatest reward by giving you the best woman" yasake murmushi yace "ingaya maka ta yanda zaka gane you are in love with someone Zayn"? Dasauri Zayn ya gyadamai kai, dan murmushi Imam yayi yace "when you care for them genuinely, baka iya jure tsana daga wajensu, u can't stand hurting them kokuma kaga ana hurting nasu, you love seeing them happy, kuma kawai kaji kanamusu wani kulawa na musamman is love, and if this things are abubuwan dakakeji game da yarinyar daka fadimini tom you are in love with her Zayn" sosai Zayn yake kallonshi yama kasa magana, gyadamai kai Imam yayi yace "tashi ka koma aiki" gyadamai kai Zayn yayi yamike tsaye ahankali har lokacin jikinshi yay sanyi yawuce yakoma office koda yashiga kwanciya yayi kujera yay shiru tunanin Farrah kawai yake yana koran tunanin amman yakasa daina ahaka baiyi komiba yaji ankira la'asar hada tarkacenshi yayi yafito saida yafara ijiye jakan laptop din a motanshi sannan yawuce yatafi masallaci &ana idarwa yafito yashiga mota yawuce. [12/21, 1:36 PM] +2347066933957🥰: 4️⃣8️⃣

Dagudu yake tuki as usual wani boutique yagani agefen titi da mannequin ansa musu kayan mata masu kyau sosai yaga sunmai kyau hakanan Farrah ne tafadomai arai, he's trying to stop kanshi but gani kawai yayi yay kwana yay parking gaban shagon yashiga ciki, lafiyayyen english wears yashiga kwasan ma Farrah shirts da wanduna da gowns, yabiya kudi almost 300k masu shagon sai godiya sukemai yashiga motanshi yajawo motan zuwa gida.

Yauma kaman kullum exam din yau yamata dadi, zaune take a falo rikeda iPad din Mami wanda yanzu kusan koda yaushe yana tareda ita tana karatu dashi, Mami na kitchen dudda Farrah taso ta tayata girki kadota tayi tajetai karatun exam, hakan yasa tadawo falo tana zaune ta sanya wata Yar rigan kanti mai dogon hannu baka tanada zanen flowers farare ya tsayamata kasan gwuwanta kanta babu dan kwali sai kalaban data tufke da ribbon baki mai kyau, kaganta zaka dauka wata balarabiya ce zaune akatafaren falon, tana zaune ita kadai akan kujera da iPad din Mami a hannunta tana zane tana kallon zanen Amoeba 🦠 a iPad din tana zanawa da pencil a book din tana koyan lebelling dan gobe biology garesu gabaki daya hankalinta yay nisa a zanen, ahankali aka bude kofan falo aka shigo, Zayn ne yana rikeda katuwan ledan a hannunshi idanunshi akanta saikace tsafi ganinta kawai dayayi dudda ma bata ganshi ba jiyayi zuciyanshi tamai wani kalan sanyi tamai wani wasai now all he needs is tadan kalleshi and get all those her expression akan fuskanta.

Kamshin dataji yadaki hancinta wanda tasan kanshin Zayn kadaine yasa kaman wata Yar bera tadaina zanen datakeyi, duwawun pencil din hannunta takai bakinta sanan ahankali tadago kanta tareda juyowa hada idanu tayida Zayn daya tsaya yana kallonta kaman baitaba ganintaba ga katon jaka a hannunshi ga jakan laptop a dayan hannunshi yana kallonta, hakanan jitayi gabanta yadan fadi hakan yasa tadauke kanta daga kallonshi dasauri tana zare pencil din daga bakinta cikin kunkuni tace "mutum ko sallama bai iyabama" karasowa gabanta yayi ya tsaya dab da ita dan yanda ya tsaya akanta kafafunta nataba Yadin wandon jikinshi wani iri taji tanaji gabanta nafaduwa hakan yasa taki kallonshi drawing datake yabida kallo yace "look at abinda take zanawa kaman fuskanta" dawani sauri takalleshi zatai magana ya watsa mata mugun kallo yace "kawomin abinci I am hungry" hararanshi tayi ahankali tace "bara'a kawob……." Daidai Mami nafitowa daga kitchen hakan yasa dasauri tabi ta gefenshi tai hanyar kitchen din tana kara budema Mami kofa da kyau tace "Mami sannu da aiki kawo nakai miki" kafin Mami tahanata ta karbe kulan takai dinning Mami takalli Zayn dayake shirin zama inda Farrah ta tashi tabari tace "kadawo" zama yayi ahankali yana daukan iPad din yace "yes Mami" "kaci abinci" dan yatsine fuska yayi yace "no" tasan dama baicika cin abinci ba hakan yasa takalli Farrah tace "kawomin serving spoon da tray a kitchen" dasauri Farrah tai kitchen ta dauko, seafood pasta da Mami tadafa lafiyayye tazubamai tahada a tray tasama Farrah a hannu tace "gashi kaimai kizo kidauki juice kikaimai " karba Farrah tayi tawuce tazo ganin yawani kwanta kan kujeran data bari daga iPad dinta harda book dinta yajefar akasa yasa taji ranta yabaci ko kadan Zayn baida manners. Ijiye tray abincin tayi akasa saida tray yay kara hakan yasa Zayn yadan bude idanu kadan yakalleta yanda tai da manyan idanunta kaman zata cije shi yasa yanuna mata small coffee stool nasu da yatsa in a very lazy voice yace "put the tray on that stool" hararanshi tayi tamike tsaye tana kwashe iPad din da book dinta daya Yar akasa sanan takalleshi cikedajin haushi tace "ina pencil dina"? Lumshe idanunshi yayi ahankali muryanta namai wani sanyi azuciya yana neman sakashi jin bacci, zatai magana daga kitchen Mami tace "idan kin bashi juice din kizo nan Farrah" dawani kalan sauri ta tashi ta ijiye iPad da littafin akan kujera tai dinning fresh juice din da Mami tahada ta dauko da cup suma a tray takawomai har lokacin yana kwance kan kujeran idanunshi a lumshe shima ijiyewa tayi akasa saida tray yay kara tamike tsaye jin baimata magana ba yasa tadan saci kallonshi idanunshi a lumshe kaman ma yay bacci wani irin bacci ne cikin 1min haka. "Did u put the food on the stool ko u are still looking at a fine boy" wani kalan ballamai harara tayi tana nadaman tsayawa ma kallonshi datayi sabida kawai Mami na kitchen yasa tajawo stool din tadauki tray tadaura mai abincin akai sanan tawuce batare data kalleshi ba zuwa kitchen.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull