Ganin ido complete Novel - Chapter 2
Ganin ido complete Novel Chapter 2: Ganin ido complete Novel Chapter 2. "Kamar yanda na faɗa miki a baya Beenafah, magani baya so a riƙa shansa yanda aka…
3,356 words
"Kamar yanda na faɗa miki a baya Beenafah, magani baya so a riƙa shansa yanda aka ga dama,ƙetare lokaci da akeyi idan tasha wata ɗaya ko biyu sai bayan wata ɗaya kuma a sake siye wannan matsala ce musamman ga irin matsalar mahaifiyarki. Magana ta gaskiya ga yanda aka ɗauko hanyar magance ciwonta da ace an ɗore da wannan hanyar da yanzu ta warke baki ɗaya, domin kamar yanda na faɗa miki tun farko cewa ciwon ta ana warke shi baki ɗaya idan har an kula yanda yakamata tun daga kan maganinta da kuma kulawa ta musamman. Ƙetare lokaci da ake yana sa cutar ta dawo wanda muke kira (relapse) wanda halin da ta tsinci kanta a ciki tun karon farko zai iya dawowa har ma yafi na baya muni da hatsari. Sannan tsallake lokaci da ake yana ƙara tsananta cutar, sannan shi karan kanshi jiki janyewa daga magunguna da ake yana sa a samu withdrawal symptoms wanda yake sa yawan zazzaɓi, ciwon kai, mummunar firgici, ko rikicewar barci..."
Cikin hawayenda suka kasa tsaya mini na girgiza kaina cike da baƙin ciki na ce.
" Wallahi likita! Da ace ina da iko ko wani zarafi da mahaifiyata bata kasance a cikin halin da take ciki ba a yanzu. Da akwai yanda zanyi ciwon ta ya dawo gareni da na yi domin ta samu sauƙi, azabar da take ciki ta yi mata yawa..."
Cike da mamaki Dr. Basheer ya kalleni ya ce.
"To amma nasan cewa kuna da zarafi da hanyoyin kulawa da ita kamar yanda aka faro, miyasa kike cewa haka a yanzu?"
Cike da jin wani sabon abu da ya taso ya tokare mini zuciyata na ce.
"Duniya ta shayar da ni mamakin da har yau ban gama farfaɗowa ba Likita..."
"Ina Daddynku Alhaji Mudassir Wazeer?"
Wani guntun murmushin ƙarfin hali na saki wanda yafi kuka ciwo na ce.
"Shine mutumin da yafi kowanne ban mamaki ma likita. Ba zan ɓoye maka ba domin abokin kuka shi ake faɗawa mutuwa. Jiya gaba ɗai abin da ya bamu Eighty thausand ne wai har kuɗin motar tahowarmu nan da kuma kuɗin maganin wata ɗaya duk a ciki...."
Ƙasa na zamo ina mai harɗe hannayena wuri ɗaya murya cike da kuka na ce.
" A yanzu muna cikin tsananin halin neman taimako, bamu da kowa bamu da komai, bamu da wani gata mu ukun nan da ka gani sai Allah. Ba zan iya jure ganin halinda Mahaifiyata take ciki ba,ina tsananin ƙaunarta da kuma wannan ƙanin nawa, don Allah don girman Allah ka taimakamana kamar yanda Allah ya taimakeka, koda taimako ne ka nema mana don Allah ka ce ci Mahaifiyata daga wannan ƙanginda take ciki."
Jiki sanyaye ya jinjina kai sannan ya ce.
" Ina dangin mahaifiyar ta ku to?"
Nan ma girgiza kaina na yi cike da jin wani sabon ƙuncin na ce.
" Likita ka yi haƙuri, amma ba zan iya sanar da kai komai ba dangane da dangin Mahaifiyata."
Sai da ya ɗauki tsawon lokaci tamkar ba zai furta komai ba sannan daga ƙarshe ya sauke ajiyar zuciya ya kallemu ɗaya bayan ɗaya cike da tausayi ya ce.
"Shikenan! In sha Allah zan yi iya abin da zan iya Beenafah. Allah ubangiji ya bata lafiya yasa a da ce."
Cikin farin ciki na shiga yi masa godiya wanda har can ƙasan raina na ji daɗi sosai, kuma hakan sai ya ƙara fahimtar dani cewa har abada mutanen kirki ba su ƙarewa a duniya amma kuma marasa kirkin sun fi su ya wa.
Nurses ya kira guda biyu suka zo da case folder ɗinta ya yi duk wasu rubuce-rubucenda zai yi sannan daga baya ya yi musu umarnin tafiya da ita kamar yanda aka saba tare da shi zuwa can ainahin ɗakin jinya da gwaje-gwaje.
Hannunta ya kalla wanda na ɗaure mata shi tun jiya sannan kuma ya dawo da kallon sa a kaina yace.
"Amma miye abin da ya same ta a hannu haka? Ina ce sai da aka yi miki kashedi akan ajiye duk wani abin da zai sa ta cutar da kanta ko ba haka ba? Kuma duk kin san da waɗannan ƙa'idojin miyasa kike wasa haka? Kin san fa abu ne mafi sauƙi ta illata kanta."
Ajiyar zuciya na sauke cikin rashin jin daɗin abun da ya faru na ce.
"Wallahi babu komai a cikin ɗakinmu likita, daga katifa sai litattafai da kuma kayan sakawarmu. Fita na yi na je shago koda na dawo ta ɗauki dutsen da muke tare ƙofa da shi ta fasa window."
"Ki ƙara kiyaye wa."
"In Sha Allah."
***
Dr. Basheer ya yi mana taimakonda har na mutu ba zan manta da shi ba, domin ya tsaya mana a lokacinda duniyar ta yi mana ƙunci. Ya taimaka mana daga aljihunsa sannan ya nemo mana taimako daga ƙungiyoyi masu bada tallafi wanda Alhamdulillah! A yanzu ta yi jinya mai kyau sannan mun samu tallafin kusan kuɗin maganin wata shida da kuma ɗaukar nauyinmu na zuwa follow-up ko wane wata kamar yanda aka saba. Sannan dangane da Bahrain ma hankalina kwance domin gidansa ya kaimu ni da Bahrain wanda matarsa ta kula da mu tamkar wacce tayi shekaru da saninmu har muka gama zaman asibiti wanda ya ɗaukemu tsawon sati shida duk da cewa ni bacci kawai ke dawowa da ni gidan har muka kambala.
Muna zaune a Office ɗinsa bayan ya kambala duk rubuce-rubucensa na sallamarmu ya kalli Ammie wacce ke riƙe da hannun Bahrain ya ce.
"Hajiya Mulaifa akwai wata damuwa? Ciwo? Ko wani abu dai koma miye"
Girgiza kanta ta yi cikin sanyin halinta ta ce.
"Ba wata damuwa likita, sai dai kuma...Sometimes I used to hear people talking..and I...."
Hannunta na jimƙe sosai a nawa, cikin sigar lallashi na ce.
"Kada ki damu Ammie, in sha Allah shima wannan a hankali zai daina."
Bayan mun kambala a motar sa ya kai mu tashar Mota yana mai ƙara yi min jan kunne akan kulawa da ita sannan ya juya ya koma.
Bayan mun shiga motar mun zauna na shiga yi mata kalamai ma su kwantar da hankali, sai dai kuma koda na leƙa fuskar ta, ta juya kanta tana kallon Window tamkar idanuwanta za su zazzago wanda ko kaɗan hankalinta baya tare dani. Cikin tsantsar mamaki nima na miƙa kaina sosai domin ganewa idona abin da take kallo a waje da har yasa ta bubbuɗe ido haka, ƙirjina ne ya doka sosai ganin mutuminda take kallo a tsakiyar tashar motar wanda kallo ɗaya zaka yi masa ya tabbatar maka da cewa mahaukaci ne. Na shiga ukuna! Kar dai ace wannan.....
✍️ *OUM-AMEER* ✍️ *GANIN IDO* 🥀🥀
*ADABI WRITER'S ASSOCIATION*
*AMEENA IBRAHIM* *OUM-AMEER*
*Wattpad:@Ummu-Ameer* *Arewabooks:@Aminatuibrahimbawa*
*Free-book*
*PAGE 3*
"Amma Ammie wannan da kike ta kallo haka kin san shine?"
Girgiza kanta ta yi a hankali ta maido kallonta zuwa gareni ta ce.
"Ban san shi ba Beenafah, kawai dai ya bani tausayi ne."
Cike da mamaki na ce.
"To amma kuma miye na kuka?"
"Ke yarinya ce Beenafah. Duk wani mahaluƙin da yake cikin irin wannan halin ina matuƙar matuƙar tausaya masa da yi masa addu'ar samun waraka daga wurin Ubangiji mai Rahma. Nasan cewa mikinda yake zuciyata har na kwanta damata ba zai warke ba Beenafah..."
Yatsun hannuna na saƙala a cikin nata ina mai bata kalaman ƙwarara gwiwa na ce.
" Babu wani abin sarari dana ɓoye wanda ya gagari Ubangiji Ammie. In Sha Allah watarana wannan mikin zai warke ya zamto kamar ba'a yi ba."
Daga haka na dawo da ita inda nake zaune na koma jikin window ɗin na zauna, daman can ni ce yakamata ace na zauna wurin tun farko ban san miye abin da ya ɗauke min hankali ba har ta fara wuce ni ta zauna.
Tun da muka kamo hanya babu abin da nake tunani da mafarki a cikin Ƙwaƙwalwata sai hasaso warkewar Ammie, shi ka ɗai ne abin da ya tsaya a tunanina, domin magana ta gaskiya muna cikin wani halin ƙangin maraici da wahala wanda ko ba Uban a tare damu atleast mahaifiyarmu ta zamto inuwa kuma mafaka a garemu. Ina nan a haka muna ta tafiya sai da muka iso Bunguɗu lokaci ɗaya na ji hankalina ya yi tashin gwauron Zabo tuna cewa ko ƙwarar hatsi na kaiwa a bakin salati bamu da shi a gidanmu.
Kuɗinda Dr. Basheer ya damƙawa Bahrain bayan ya biya mana kuɗin mota ya ce wai ya siya chocolate Idan mun koma gida na ciro daga cikin ledar maganinda take hannuna. Ko da na ƙirga su naira dubu talatin ne cif. Wata irin sassanyar Ajiyar zuciya na sauke tare da yin hamdala na sake ninke kuɗin na mayar bayan na cire dubu biyu na riƙe a hannuna wanda bayan mun sauka da su muka hau abun hawa zuwa gida.
Da mu da babu mu a gidan duk uwarsu ɗaya ubansu ɗaya, shiyasa duk yunƙurinda Ammie ta yi na son shiga ɓangaren su Mummy Zaliha na hanata, domin babu wata gudummawar da suke bayarwa wurin kulawa da lafiyarta fa ce ma ƙarin damuwa da sa ciwon nata ya ƙara tsananta sakamakon baƙaƙen maganganu da habaice-habaicen da Mummy Zaliha ke jifar ta dasu a kai-kai ce.
Bayan mun yi salla na ɗauko mana sauran abincinda aka bamu daga gidan Dr. Basheer muka cinye sannan na kalli Ammie na ce mata zan fita kasuwa.
"Yanzu Beenafah duk shagunanda suke a kusa da mu basu isa ba har sai kin je kasuwa?"
Zaunawa na yi tare da nuna mata takardar hannuna na ce.
"Wannan shi ne sabon jadawalin tsarin abincin da zaki riƙa ci shiyasa nake so in je kasuwa domin a can ne zan samu duk abin da nake buƙata."
Lumshe idanunta kawai tayi ta ɗan kishingiɗa jikin katifarta wanda na tabbatar akwai maganganu da yawa a zuciyarta yawan magana ne bata so a yanzu.
"Aunty Beenafah ki sawomin kayan school kin ji dan Allah, kin san dai kin yi alƙawari ko?"
Jinjina kai na yi ina murmushi na ce.
"Na ji Bahrain, amma sai idan zaka tashi yanzu ka shirya kamar yanda na ce ka wuce islamiyya..."
"Kai Aunty Beenafah dan Allah ki bar shi gobe mana, wallahi duk na bi na gaji dan Allah."
"To ni kuma ba zan siyo ba.."
Miƙewa ya yi yana cuna baki ya ɗauko uniform ɗinsa ya saka ya ɗauki jakarsa ya rataya ya yi wa Ammie sallama ya fi ce.
A bakin gate ya haɗu da Biba wacce tana ganin shi ta tarbeshi da dariya ta ce.
"Bahrain! Bahrain ɗan Ammie. Yaushe kuka dawo? Ya jikin Ammien ka?"
Shi ma murmushin ya mayar mata ya ce.
"Sannu Aunty Biba. Ɗa zu ne muka dawo, kuma shine Yayata ta dage wai dole sai naje makaranta yau."
Murmushi ta yi tare da dafa kansa ta ce.
"Haba Bahrain! Auntynka so take ka yi karatu sosai ka sauke alƙur'ani ka zamto babban malami wanda duniyar musulunci zata yi alfahari da kai. Kuma kaga idan kana so ka cim ma buri irin wannan to dole sai ka jajirce sosai ka yi karatu..."
Jin kamar alamar buɗe ƙofa daga ɓangaren Mummy Zaliha ya sanyata yin gaba cikin sauri tana gudun kada wani ya ganta tana magana da Bahrain tunda Mummy Zaliha already ta yi mata zazzafan jan kunne cewa kada ta sake shiga ɓangaren Ammie ko magana wannan ta fatar baki kada ta sake yinta da su, domin idan tana shiga wurinsu yau da gobe sai an wayi gari Ammie ta ji mata mummunar rauni kuma wallahi babu ruwanta ko sisinta ba zata kashe wurin yi mata magani ba tunda ba ita ta aike ta ba.
To amma abin da yake ƙara daurewa Biba kai shi ne, har yau ta kasa gane miyasa hatta wannan magana ta fatar baki ta hanata yi da su sai ka ce ba mutane ba.
***
Bayan na dawo daga kasuwa tare da Ammie muka yi girki inda na ajiye mata kujera a farfajiyar harabarmu ɗan nesa kaɗan daga in da nake yin girki, magi ta ƙanƙare mini da dai sauran abin da bai taka kara ya karya ba, domin har yanzu dole in yi taka tsan-tsan da wuƙa da kuma wuta ko rijiya da sauran su. Muna nan ina yi mata fira har muka kambala wanda sai da mukayi sallar Isha sannan na sanyo mana abincin muka ci mu uku. Bayan mun kambala na ɗauko mata maganinta na bata na gyara mata shimfiɗa da wuri ta kwanta sannan na kalli Bahrain da ke bitar litattafansa na ce ya ci gaba zan je na dawo idan kuma ya kambala yana iya kwanciya.
Yau kam a bakin motar sa na taradda shi da alama yau bai dawo da wuri ba.
Hmm! ɗan Adam kenan mai abin mamaki! Wai yau Daddy ne muka dawo banza wofi a wurinsa. Daddy wanda yake rasa ina zai aza damu a faɗin duniyar nan wai shine shugaba wurin ci mana fuska da wulaƙanta mu. Yanzu gashi mun share tsawon sati shida bama nan amma ko dai ya nuna ya damu da al'amarinmu.....Kai ko waya ce ya ci ace ya kira tunda yana da numbern doctor Basheer amma bai yi hakan ba, tamkar ma ya ga wata sabuwar fuska haka ya tarbeni a yau.
Haƙiƙa ina da zafin rai, ina da matuƙar ɗaukar zafi da rashin jure wulaƙanci a ko ina na tsinci kaina, hatta Mummy Zaliha da ta ƙware wurin iya kai ni maƙura wacce tasan cewa bana iya mayar mata da magana idan ta yi min abu ji nake tamkar na haɗiye zuciyata na mutu. Na tsane ta, na tsani duk wani wanda ya fito daga gefenta, cewa da ta yi babu ruwanta da al'amarinmu ko kallo bamu isheta ba a yanzu, hakan ba ƙaramin gode mata na yi ba, domin tun da ta yi wannan furucin shikenan muka samu sauƙin ta wanda taurin rai da na nuna mata ne har yasa tayi mummunan fushi ta yanke wannan hukuncin. Daddy ma haka, a yanzu bana jin komai a zuciyata na kasancewar sa Uba a garemu fa ce zallar tsana da mummunar ƙiyayya ta har abada.
"Ni fa so nake in shiga ciki Beenafah, kuma kin zo kin tsaya ƙiƙam ke baki ce komai ba."
Cike da fargaba na rusuna na ce.
"Ka yi haƙuri. Daman zuwa na yi na faɗa maka cewar mun dawo.."
"To.. To..Masha Allah! Ya jikin ita Mulaifar?"
"Jiki Alhamdulillah! Ta samu sauƙi sosai. Daman cewa na yi zancen kuɗin maganin watan nan da muke ciki a yanzu, to daga can asibitinma an biyomu kuɗi wanda idan zamu koma zamu bayar..."
"Ke Beenafah bana son Ƙaryar banza da wofi! Uban waye zai bi ku bashi a asibitin tunda ba ku ne kuka kafa musu ita ba...wait! Kina nufin duk tsawon lokacin nan da kuka ɗauka a asibiti duk a bashi kuke zaune?"
Gyaɗa kaina na yi kamar da gaske na ce.
"Eh Daddy. Zaka ma iya bincika wa da kanka ka ji."
Wayarshi ya ciro daga cikin babbar rigar sa ya kira Dr. Basheer wanda a raina ba abin da nake sai addu'a da fatan Allah yasa Dr. Basheer ɗin ya ɗauki haske ya fahimci manufata. Ba komai yasa naƙi faɗa masa cewa mun samu tallafi ba sai domin idan ya bamu kuɗin mu riƙa siyen abinci da kuma korewa kanmu sauran buƙatun rayuwa na yau da kullum.
Ban fahimci komai ba domin wayar ba a handsfree take ba, sai da ya kambala sannan ya kalle ni ya ce.
"Na ji, amma ki sani Wata ya riga ya yi nisa bani da kuɗinda zan baku a yanzu sai dai kuma ki jira ƙarshen wata."
Daga haka ya rufe motar sa ya shige gida ya barni nan ina ta famar share hawaye. Tun a nan na fara lissafin yanda zamu rayu tsawon sati biyu ko fiye ma da hakan kafin wasu kuɗi su sake shigomu domin yau da gobe ta wuce wasa.
Na jima tsawon lokaci a inda nake tsugunne ina karanta wasiƙar Jaki wacce idan kwana zan yi nasan ba za ta tsinana mini komai ba fa ce ƙarin tarin damuwoyi da baƙin ciki.
Bayan tsawon lokaci na lallaɓa na koma sashenmu wanda na shafe tsawon lokaci ban samu bacci ya ɗaukeni ba sai cikin talatainin dare. A yanzu na ƙara tabbatarwa cewa ikon Allah ne kawai da ƙarfin addu'a yasa nake tsaye da lafiyata ba tare da wani ciwon ya kamani ba,domin matsalolin da na fuskanta ko nake fuskanta a yanzu sun fi ƙarfina.
****
Haka dai muka yi ta gurgura rayuwa. Katsar-watsar muka ga sati biyun nan sun zo sun wuce cike da fatan Daddy ya tura mana kuɗin domin ba ƙaramin jigata muka yi ba. A raina ina ta hamdala da tunanin cewa wahalar wannan watan ta riga ta ƙare sai dai kuma idan wata ta zo. Ashe ban san cewa akwai wata babbar jarabawa da ke tunkararmu ba wacce tafi ta baya muni da tsananin tashin hankali.......
✍️ *OUM-AMEER* ✍️ *GANIN IDO* 🥀🥀
*AMEENA IBRAHIM* *OUM-AMEER*
*Wattpad:@Ummu-Ameer* *Arewabooks:@Aminatuibrahimbawa*
*FREE-BOOK*
*PAGE 4*
Yau tun da muka wayi gari na ɗauko wanki ina yi bayan Bahrain ya tafi islamiyya kasancewar yau Asabar ce. Ina cikin yi Ammie ta fito ta zauna tana tayani har kusan ƙarfe sha biyu saura na rana, bayan mun kambala na zuba mata ruwan wanka sannan na gyara wuta na sake ɗora ruwan zafi a tukunya daga nan na zari hijabina sai wurin Baba mai Shago.
Bayan na gaishe da shi ya amsa na ciro takardar da ke ɗauke da lambar wayar Dr. Basheer na bashi na ce dan Allah ya kirasa ya ce masa Beenafah ce ɗiyar Patient ɗinsa Mulaifa Zayd Hudaif.
Yana gama faɗa masa haka ya yanke wayar ko minti ɗaya ba'a ƙara cikakke ba sai gashi ya kira.
Cike da ladabi na gaishe da shi sannan na ce.
"Daman naga mun shigo Sati uku cikin na huɗu, shine na ce bari na tuna maka kada kuma a zo a samu matsala."
Daga can ɓangaren ya ce.
"Haka ne gaskiya, to amma ai date ɗinda za ku dawo yana nan rubuce a jikin takardar da na baki kamar yanda a ka saba. Na san tabbas satin da zamu shiga ne amma ban riƙe date ɗin ba, sai ki duba ki gani."
Gyaɗa kaina na yi na ce.
"OK to, In Sha Allah!"
"Sannan magana ta gaba kuma a ina ne za'a tura muku da kuɗin?"
"Ina ga ka manta ne Likita, amma Numbern Account ɗin tana nan jikin form ɗinda aka bamu muka cike domin sharaɗinma shine, dole account ɗin sai yana da alaƙa da Ammie to kuma na ta ɗinne wanda Daddy ya buɗe mata na saka."
"Ok to. In Sha Allah, zan sanar da su cewa lokaci ya yi, zuwa gobe ko jibi za'a tura da su."
Ɗan rusunawa na yi kaɗan tamkar ina a gabansa na ce.
"Mun gode sosai Likita, Allah ya saka maka da mafificin alheri ya biya maka dukkan buƙatunka."
Ina gama wayar na miƙawa Baba mai Shago na ce.
"Na gode sosai Allah ya saka da alheri Baba. Don Allah kada ka gaji dani, ga ATM card ɗinmu ka riƙe ta a wajenka, ina so ka taimaka ka bamu Shinkafa da Wake da Mai da Magi, wallahi yau kwana na biyu kenan bamu ɗora tukunyar abinci ba, dan Allah ka taimaka mana."
"Kayan kamar na nawa za'a bayar?"
Ɗan Jim! Na yi ina nazari sannan daga ƙarshe na ce.
"Ka kashe mana dubu biyar har da gawayi ma."
"To ɗan jirani yanzu ina zuwa."
Ina nan a tsaye ya auna komai ya bani daga nan na yi masa godiya sosai na koma gida. Ina zuwa na ɗibi Waken na gyara na zuba a tukunyar da na ɗora kafin na fita, daga nan na je na yi sallar Zuhr sannan na dawo na ci gaba da gyara shinkafa ina faɗawa Ammie yanda mukayi da Dr. Basheer.
****
Wasa-wasa tun kafin lokacin tafiyarmu ya cika nake zuwa neman Daddy bana samun sa wanda da alama ya yi tafiya ne. Har lokacin kuma ya cika muka shirye muka je Sokoto muka yi kwana ɗaya muka dawo still bai dawo ba. Munyi kwana ɗaya ne kacal kasancewar gwaje-gwajen da duk aka yi wa Ammie sun nuna komai lafiya, babu wata matsala mai yawa a wannan karon.