Kenza eBookz

Garkuwa book 2 - Chapter 6

Garkuwa book 2 - Chapter 6

Garkuwa book 2 Chapter 6: Garkuwa book 2 Chapter 6. Aunty Rahma dake shigowane tayi saurin ƙarasowa tare da cewa. "Kai Aunty Hafsat haba dama ni na lura…

4,450 words

Aunty Rahma dake shigowane tayi saurin ƙarasowa tare da cewa. "Kai Aunty Hafsat haba dama ni na lura kamar ciki take dashi naga tana yawan bacci". Juyowa sukayi suna kallon Safiyyah daketa dariya ƙasa-ƙasa cikin dariyar tace. "Au ku dama kallon mai ciki kukeyi mata ashe. To wannan kam yanzuma bata salla, kuma dama wasu in suna al'ada suna yawan bacci inaga ita hakane".

"Kai Safiyyah wannan tsarabe-tsaraben naku na Nurses baya gaya muku gaskiya wasu lokutan". Mamma ta faɗa da iya kar gskyar ta. Ita dai Safiyyah dariya tayi kana ta fara kiran Aysha.

Ita kuwa Aysha tun mgnar Mamma na forko ta farka daga baccin ta dai ci gaba da rufe idonta ne kawai sabida karta katse musu hirarsu.

A hankali ta buɗe idonta tare da yin salati kana ta miƙe zaune. Cikin kula Mamma tace. "Sannu ko tashi kiyi salla ki shirya dan har an fara kai mutane wurin walimar". Cikin sanyin bacci tace. "To Mamma". Daga nan ta miƙa ta nufi Bathroom. Ita kuwa Mamma miƙawa Safiyyah ledar kayan Jannart tayi kana ta ajiyewa Aysha nata a bakin gado tare da cewa. "In kin fito ga kayan da zakisa a cikin jakar nan a bakin gado". "To ngd Mamma". Tace tana rufe ƙofar Aunty Rahma kuwa hannu tasa ta ɗauki Ishma dan zataje ta kimtsata.

Safiyyah kuwa da sauri ta kaiwa Jannart nata kayan ta dawo.

Tuni ƙawayen Umaymah manyan mata da matan abokan Abbansu Haroon matan sarakuna Da ƴaƴan sarakuna duk anata kaisu wurin da aka tanada dan yin walimar.

Manyan mutane dattawa maza masu karamci da mutunci yan kasuwa da yan siyasa da sarakuna duk sun cika maƙil a babban hall ɗin.

Katon hall ne wanda a ƙalla zai iya ɗaukar mutune dari takwas zuwa ɗari dubu ɗaya.

An gyara wurin an ƙawatashi. Ansa wani labule mai zaman kanshi an raba wurin biyu, kasan cewar dama ƙofofin shigowan biyune, haka yasa aka tsara wurin yadda mata zasu zauna a gefe ɗaya maza a gefe ɗaya bazama su ga junaba.

Sai can sama akayi wani ɗan dandamali wanda sai ka taka steps huɗu ana biyar zaka hau. Shine wuri na musamman wurin zaman malami.

Ƙasa kaɗan dashi kuma wani ƙawataccen table ne mai kujeru shida, inda nanne wurin zaman angwaye da amare.

Can gefen inda malamin zai zaunama akwai ƙofar da ta nan zai shigo.

Tako ina ka cilla idonta haskene ras tamkar rana, wurin yayi kyau gwanin ban sha'awa. Gaba ɗaya wurin mata da mazan ya cika maƙil duk manya-manyan baƙin sun samu isowa. Hatta Sarki Ahmadu da tawagarsa da Abbansu Haroon da tawagar abokanshi duk sun iso. Hakama Umaymah da da mutanenta hakama Mamma ta iso da Hajia Mama da Ummi da Aunty Juwairiyya da Hibba da Azeema.

Isowar Sheykh Jabeer da Ango da amaren kawai ake dako. Madadin zama shurun sai akasa, sautin karatun al'ƙur'ani mai girma.

A can gida kuwa, Ibrahim, Haroon Sheykh da ne tsaye a harabar farfajiyar Side Umaymah, suna cikin wata iriyar fitinenneyar shiga mai masifar kyau da ban sha'awa. Shigar fararen jallabiyar ƙirar Pakistan irin mai riga da wonɗonan ne kalar Sky blue mai azabar kyau da taushi da sheƙi. Sai wasu tattausan al'kyabbar farare ƙal tamkar madara, al'kyabbar sun irin mai shara-sharan nanne haka ya bawa kolliyar tasu damar zama kamar adon sararin samaniya.

Sai hiramin dake kansu ne ya banbanta na kan Haroon da Ibrahim farine tas.

Sheykh kuwa nashi farine sai ɗigo-ɗigon Sky blue, hakama takalminshi hafl cover suma fararene sai ɗigon Sky blue. Sai kekyawan zoben Daimond mai ɗigon Royal blue mai masifar kyau sai wal-wal yakeyi.

Sai ƙamshi sukeyi da sheƙi. Ibrahim ne ya kira Safiyyah a waya tare da cewa suyi maza su fito mana.

To tace kana ta kalli Aysha dake cikin shigar doguwar riga mai masifar kyau da tsada, rigar iri ɗaya ce da Tata data Jannart. sai dai tafi kama jikin Aysha sabida ta fisu faɗin ƙasa da sama. Sunyi kyau sosai sunyi rolling kawunansu da gyalullukan suka fito tamkar yammatan larabawa.

Cikin sauri ta fesa turare kana ta kalli Safiyyah tare da cewa. "To na gama mu tafi ko". Murmushi Safiyyah tayi tare da cewa. "Masha Allah kinyi kyau. Mu tafi". Da haka suka fito.

A falo suka samu hadiman Umaymah nata gyara gidan.

Suna fitowa Aunty Rahma da Jannart suma suka iso.

Da sauri Ibrahim ya buɗe motarsa ya shiga, Safiyyah ta shiga gefenshi. Aunty Rahma da Ishma suka shiga baya. Haroon kuwa kama hannun Jannart yayi suka shiga bayan motarsa direbanshi na gaba. Sheykh kuwa a hankali ya buɗe motarshi dasu Sulaiman da Ya Hashim suka zo da ita, kuma su tuni an kaisu can wurin walimar. Kasan cewar babu mai janshi ne yasa ya shiga ya zauna a mazaunin gireban.

A hankali tabi bayanshi ganin tuni Ibrahim yaja motarshi hakama motar Haroon.

Cikin takun nitsuwa ta iso gab da motar, hannu tasa zata buɗe baya ta shiga. Jin marfin a rufe yake yasa ta ɗan matso kusa da inda yake tare da cewa. "A rufe yake". Ƙwayar idanunshi ya juya mata tare da mata alamun ta zagaya ta shigo can gefenshi. Kasan cewar yana latsa wayarshi haskenta ya haska fuskarshi yasa ta gane manufarshi. Zagayawa tayi ta buɗe ta shiga kana ta maida marfin.

A hankali ta juyo ta ɗan kalleshi jin yace. "Bismillah". Kana ya tada motar yaja suka bar harabar wurin.

Kasan cewar wurin babu nisa sosai da masarautar. Tuni su Haroon sun isa har sun shiga sun zauna yanzu isowar Sheykh kawai ake jira.

Suna isa harabar wurin. Bayan yayi parking, suka fito. Suna isa suka samu tarin fadawa a bakin ƙofar. gaba yayi ya nufi ƙofar da zai shiga ta wurin. Ita ma binshi a baya tayi.

Suna shiga, tayi maza ta kange fuskantar da bayanshi sabida. Tarin mutanen da ta gani sun firgitata, sam batayi zaton yawan mutanen ya kai haka ba. Fahimtar hakane, yasashi yin gaba ita kuma tana biye dashi. Har inda su Haroon suke. Kujerar dake gefen Jannart ya nuna mata. Ai da sauri ta zauna. Shi kuwa sunkuyowa ya ɗanyi kan Haroon kana yace. "Ka nitsu da kyau ka saurari abinda Allah da Manzonsa suka ce a tsakanin ma'aurata". Cikin murmushin dake bayyana zallar jin daɗi da zumuɗin amarci Haroon yace. "To Sheykh". Daga nan ya juya ya koma inda aka tanada domin shi.

Yana zama wani ɗan agaji ya dawo bayanshi ya tsaya. kana ya miƙo mishi abin mgn. Amsa yayi kana ya saƙalashi a bakin al'kyabbar jikinshi.

Gyara zamanshi yayi da kyau kana ya fuskanci taron al'ummar baki ɗaya. Ɗaya daga cikin ƴan agajin ne yasa hannunshi ya katse sautin karatun Alqur'ani dake tashin.

Cikin nitsuwa kamala haiba da ilimi ya ɗanyi gyaran murya tare da fara bude taro da bimilla da addu'a da sallama. "Bismillah rahmanirrahim. Assalamu alaikum warahmatullahi wa barka tuhu. Innal hamdalillah nahmaduhu wanasta inuhu wanastagfiru wana uzubillahi min shururi am fusina wa sai'yi ati amalina. Manyahadillahu fala mudillalah, famanyuddul fala hadiyala wa asshahu'alla'ila'ha'illalahu wahdahu lasheri kallah, wa asshahadu annamuhammadan abduhuwarasulu. Ya ayu allazina amanuttaƙullaha haƙƙa tuƙatil wala ta mutunna illah wa antum muslimun ya ayu hannasu taƙu rabbakum. Kalakum min nafsin wahida, wa kalaƙa minha zaujaha wa bassa minhuma rijalan khasiran wa nisa'ah wattaƙullah lazitasa'aluna bihi, wal'arhama innallaha kana alaikum raƙiba, ya aiyu allazina amanutaƙullah wa ƙulu ƙaulan sadidah yuslahlakum amalakum wayagfirlakum zunuba kum, waman yuɗillah wara sulahu, faƙadfaza fauzan azeema ambaduhu fa inna'asdaƙal hadisi kitabullah wa'ahsanal hadi hadiyu Muhammadin (S.A.W) wa sharal umuri muhdasatuha fa innakulla mudasatin bidi'a wa kulla bidi'atin balala wa kulla balaltun finnar." Dogon nufamshi ya sauƙe mai ɗan nauyi sabida jan dogon numfashin da yayi, kana ya kalli Side ɗin dasu Abbansu Haroon suke yace. "Alhamdulillah kamar yadda muka sani, walimace ta farin cikin auren ƴan uwanmu, kana kamar yadda kowa ya sani walima shine aci asha kana a watse. To a madadin muyi zaman da ci da sha kawai ya dace mu haɗa da ambaton sunan Allah, dayiwa ango da amrya taƙaitacciyar nasiha akan tsarin aure a musulunce da haƙƙoƙin ma'aurata ga junansu da addu'an zaman lafiya." A hankali yayi gyaran murya. Kana ya muskuta ya gyara zamanshi da kyau ya fuskanci taro al'ummar Annabi dake gabashin. Manya da yara maza da mata. Especially matasa, yatsarshi manuniya yasa gyara zaman siririn farin gilashin dake manne a fuskarshi.

Ɗan sunkuyar da kanshi yayi. Dai-dai inda abin sautin mgnar ke saƙale a wuyan al'kyabbar jikinshi.

Gaba ɗaya hall ɗin yayi tsit bakajin motsin kowa sai sautin numfashin mutane dana A/C.

Cikin tattausan lafazi muryarshi ta ratsa kunnuwan duk wanda yake wurin inda yace.

*AURE* Ma'anar aure a musulunce shine. Sunnan Allah a wojen halittar Allah daya halitta ya haliccemu ne a jinsi guda biyu macce da namiji. Kamar yadda Allah (S.W.A) ya ce, a Suratul Zariyya aya ta 49:-

(WA MIN KULLI SHA'I'IN KHALAƘNA ZAUJAINI LA ALLAKUM TAZAKKARUM) "Kan ko wa wane abu Allah ya halice shi namiji da mace don ku yi tunani a kansa.

Sannan Allah maɗaukakin sarki a wata ayar ya sake cewa a Suratul yashin aya ta 36:- (SUBHANALLAZII KHALAƘAL AZWAJA KULLAHA MIMMA TUMBITUL ARDU WA MIN AMFUSIHIM WA MIMMA LA YA ALAMUN) "Tsarki ya tabbata ga Allah wanda ya halicci ma'aurata namiji da mace, dukkansu daga abinda ƙasa ke sirarwa, kuma daga ko wannensu kuma da ma abin da basu sani ba!."

Kanshi ya ɗan ɗago ya kalli gefen maza, idonshi ya ɗan lumshe sabida gamsuwa da nitsuwarsu data tabbatar mishi, zantukanshi na ratsasu. Idonshi ya ɗan tsaida kan fuskar Haroon ango mai jiran gado. Sai kuma ya janye idonshi yaci gaba da cewa. "Tabbas da wannan tsarin na auratayya ne. Allah ya zaɓa mana ya zama hanyar da zamuyi ta haife-haife muyi ta karuwa a bayan ƙasa.

Domin shi aure wata muhimmiyar igiyace wadda idan aka ƙullashi zai bawa ma'aurata daman saduwa tsakaninsu ba tare da wata ƙyama ba, kuma ta hakane ma'aurata zasu zama sutura ga junansu kamar yadda Allah maɗaukakin sarki ya faɗa a Suratul Baƙara aya ta 187:- "Su mata suturane gareku maza, sannan kuma maza sutura ne garesu-su matan. Saboda haka zamu tabbatar lallai akwai al'ƙawari da amana mai ƙarfi a tsakanin ma'aurata, kuma Allah ya al'barkaci aure kuma yana son tabbatarsa , yana kuma ƙin ɓacinsa ba tare kwakkwaran larura ba.

Shi aure sunnace daga cikin sunnonin da ɗan Adam ya sami kansa a ciki, sannan kuma larurace daga cikin larurorin rayuwar ɗan Adam domin da aurene mutun zai kiyaye dangantakarsa, kuma ya ƙididdige ƴaƴansa wanda ya haifa kuma da shine zai kiyaye mutuncinsa, martabarsa dama dukkan dangantakarsa ga sauran ƴan uwansa da jama'a baki ɗaya kamar yadda Allah (S.W.A) ya faɗa a Suratul Furƙan aya ta 54:- ( WA HUWALLAZII KHALAƘA MINAL MAA'I BASHARAN FAJA ALUHU NASABAN WA SIRRAN WA KANA RABBUKA ƘADIIRA) "Kusani Allah shine wanda ya halicci mutun daga ruwa kuma mai dangantaka surukuta kuma ka sani Allah mai iko ne akan haka".

Sassanyan numfashi ya fesar a hankali, kana yaci gaba da cewa. "Shi Aure sunna ne mai samar da nitsuwa tsakanin ma'aurata. Ɗan Adam bazai samu cikekkiyar nitsuwa ba a gidansa ba, sai in har yanada mata wacce ya aura. Domin zata ɗebe masa kewa ta sashi ya samu nitsuwar hankalinsa. Saboda zamansu tare a inuwar aure zatayi masa maganin kaɗaici kamar yadda Allah (S.W.A) ya faɗi a Suratul Rum aya ta 21:- (WA MIN AYATIHI AN KHALAKA LAKUM MIN AMFUSIKUM AZWAJAN LITASKUNUW ILAIHA WA JA'ALA BAINAKUM MA'WADDATAN WA RAHMA INNA FII ZALIKA LA AAYAATIN LIKAUMIN YATAFAKKARUN) ma'ana. Yana daga cikin ayoyin Allah mai girma da ya halitta mana mataye daga kawunan mu, mataye da muke aure da su. Domin su samu nitsuwa da junansu, sannan kuma ya sama musu soyayya a tsakanin su, tare rahama da tausayawa juna lallai a cikin wannan al'amari akwai ayoyi abin lura ga jama'an da suke masu tunani. Saboda haka idan muka dubi wannan ayar ga ma'aurata zamu gane girman kudirar Allah da hikimarsa mai girma da ya halicci maza da mata kuma ya sanya ko wanne sashi mai karkata ga junansu kuma ya sanya igiya ya ɗaure tsakaninsu, wannan igiyar kuwa itace soyayya da tausayin juna da jinƙai. Kuma Annabi (S.A.W) ya ce, cikin hadisin da Ibnu Majah ya ruwaito cewa. (Babu wata fa'ida da mutun zai samu bayan ya. Takawar da Allah (tsoron Allah) wanda yafi masa al'khairi fiye da ya samu salihar mata ta kwarai wanda idan ya umarceta da tayi masa abu zata yi masa biyayya idan ya dubeta ta faranta masa ransa idan yayi rantsuwa game ita akan zatayi abu kaza ko bazata aikata abu kaza ba, zata kuɓutar dashi akan wannan rantsuwar da yayi, idan baya gida baya tare da ita, zata kiyaye mutuncinsa (Bazata yi fasiƙanci ba) kuma zata kula da dukiyarsa. Ku duba cikin Fikihul Wadi littafin Dr Muhammad B Isma'il shafi na 9 zaku sami wannan hadisin.

A hankali Haroon ya ɗan juyo ya kalli fuskar amaryarshi Jannart, hannunshi yasa ta ƙasa table ɗin dake gabansu, tafin hannunta ya haɗe da nashi, tare da ɗan ronƙofowa kaɗan kana yace. "Kina ji da kyau dai ko?". Cikin lumshe ido tace. "Sosai ma kuwa". Aysha dake gefensu Haroon ya kalla tare da cewa. "Al Sheƙiya matar Sheykh, ko zakije ki ja mishi baƙine?". Ido ta ɗan sunkuyar tare da fidda nannauyan numfashi kana a hankali tace. "Ba dan gefen can da tarin maza manya iyaye da kakanni da sarakuna ba, tabbas da naje na zauna gefenshi na ja mishi baƙi". Safiyyah da Ibrahim dake bisa kujerun dake gefensu ne suka kalli juna tare da yin murmushi.

Abokan Haroon kuwa gaba ɗaya sun nitsu. Abbansu Haroon da tawagarsa kuwa sai jinjina kai suke alamun gamsu ɗari bisa ɗari.

Ita kuwa Aysha a hankali ta ɗago kanta ta kalli inda yake, aikuwa karab idonsu ya haɗe cikin na juna, taɓe laɓɓansa yayi tare dasa hannunshi ya shafi tattausan sajenshi kana a nitse yaci gaba da cewa. "Aure kariya ce, kuma GARKUWA ce ga Musulmi saboda duk wanda yakeda mata, to ba zaka ganshi ya bar gida yana yawace-yawace ba ko ka ganshi yana leƙe-leƙe a woje ba, don yana da irinsa a gidansa, saboda haka mata ta zama GARKUWA a rayuwar ɗan Adam. Saboda haka ne ma Annabi (S.A.W). Ya kwaɗaitar da matasa samari da yin aure a cikin wani hadisin da muka samu a cikin Fiƙhul waɗi littafi na 2 na Dr Muhammad B Isma'il shafi na tara, Annabi (S.A.W) ya ce:- Yaku samari wanda ya samu iko daga cikin ku to yayi aure. Domin shi aure yana kare mutuncin farji da aukuwa cikin haram, (Yin zina) wanda bai sami iko ba to lallai ne ya juri yin azumi. Domin assaumu junnatu, shi azumi GARKUWA ne. Kuma shi aure cikon addini ne, saboda idan muka dubi aure sosai. Zamu fahimci aure yana taimakawa musulmi wajen tsare-tsaren addininsa kuma da wannan ne addininsa yake cika kamar yadda. Dabarani da Hakim suka ruwaito daga Buhari da Muslim inda Manzon Allah (S.A.W) yake bamu labari a kan cewa aure tsari ne wanda yake taimakawa ga mutum ya cika addininsa a in da yake cewa: Yana daga cikin arzikin Allah. Allah ya azurtaka da mace salihan ko salihan mata, haƙiƙa zata taimaka ko wannan auren zai taimaka akan wani yanki na addini ka sai kuma kaji tsoron Allah akan sauran yankin. Aure sunnace ta Annabawa da manzanni, saboda haka idan kayi aure ko yi ne da Annabawa da manzannin Allah. Allah maɗaukakin sarki ya faɗi:- (WA LAKAD ARSALNA RUSULAN MIN ƘABLIKA WAJA'ALNA LAHUM AZWAJAN WA ZURRIYYAH) Haƙiƙa mun aiko manzanni kafin kai, (Muhammad, S.A.W) kuma mun sanya matayen aure da zuriya a garesu. Idan muka duba zamuga cewa yin aure koyi ne da aikin Annabinmu Muhammad (S.A.W) ne in da yace:- (Kuyi aure ku yawaita domin ni zanyi alfahari da yawanku ranar lahira".

Juyowa yayi ya fuskanci gefen taron maza, kana yaci gaba da cewa. "Kamar yadda muka sani cewa. Mace abokiyar zama ce kuma shimfiɗa ce ga mijinta kuma mai rainon gidansa ce kuma abokiyar rayuwarsa ce, sannan kuma uwar ƴaƴansa ce sannan mai kula da dukiyarsa ce da mutuncinsa cikin amana saboda haka idan mata-ta zamo salihan ta gari to sai ta zamo kyakkyawan abu na duniya kuma ni'ima daga cikin manya-manyan ni'imomin da Allah ya azurtaka da ita".

Gyaran murya yayi tare da gyara zamanshi, kana ya fuskanci Haroon da Jannart da kyau, sannan ya ɗan kalli Aysha da wutsiyar idonshi. Tura bakinta ta ɗanyi fahimtar ita yake kallo, kanshi ya jinjina kana ya buɗe muryarshi da ɗan ƙarfi dai-dai misali yadda amon mgnarsa zata ratsa kunnen kowa yace.

HAƘƘOƘIN MA'AURATA GA JUNANSU.

bari mu fara da haƙƙin macce akan mijinta.

HAƘƘIN MATA A KAN MIJINTA.

Haƙƙoƙin mata a kan mijinta suna da tarin yawa. Kuma ya zamo wajibi a kan mai gida ya tsareshi dai-dai gwargwadon hali, kuma wannan haƙƙoƙin Allah da Manzonsa sun tabbatar dashi, ga faɗin Allah madaukakin sarki akan haka inda yayi mgna cikin Suratul Baƙara aya ta 228:- (WALAHUNNA MISLULAZII ALAIHINNA BIL MA'ARUF WA LIRRIJALI ALAIHINNA DARAJAT) Mata sunada haƙki a kan mazansu kamar yadda aka sani. Sannan maza suna da wata daraja akan mata. Haƙƙokin mace a kan mijin ta, suna da yawa amman ga wasu daga cikinsu.

(1) Wurin zama ga matar aure wajibi ne a kan mijinta. Miji zai tanadi wurin zaman matarsa gwargwadon ikonsa da samunsa kamar yadda Allah maɗaukakin sarki ya faɗa a cikin Suratul Ɗalak aya ta 6:- (ASKINU HUNNA MIN HAISU SAKANTUM MIN WUJIDIKIM WALA. TUDAARUHUNNA LITUDHAYYIKUM ALAIHIN) Ku zaunar da matanku inda kuke zaune wato gidajenku. Ba mummunan wurin zamaba kada ku cutar dasu don ƙuntata musu.

(2) CIYARWA. Ciyarwa yana daga cikin abubuwan dake wajabta kan miji wato wajibi ne miji ya ciyar da matarsa, kuma ciyarwar zai yishi ne gwargwadon ikonsa kamar yadda Allah maɗaukakin sarki yace a cikin Suratul ɗalak aya ta (7). (LIYUN FIƘ ZUU SA'ATIH MIN SA'ATIH, WA MAN ƘUDIRA ALAIKU RIZKUHU FALYUNFIƘ MIMMA AATAHULLAH LAA YU KALLIFULLAHU NAFSAN ILLA MAA AATAHAA SAYAJA ALULLUHU BA'ADA USRIY YUSRAA). Ma'ana. Mawadaci sai ya ciyar da abinda Allah ya bashi na wadata, shi kuma wanda Allah ya ƙaranta masa arziƙinsa to sai ya ciyar daga abinda Allah ya bashi. Domin Allah baya ɗorawa bawa abinda bazai iyaba kuma ka sani Allah zai baka wadata bayan ƙuncin da ka shiga. Dangane da hadisin Annabi (A.S.W) yace a hadisin da a ka ruwaito daga mu'awiyya Bin Haidatu Allah ya ƙara masa yarda yace: Sai muka tambayi Manzon Allah (S.A.W) shin menene haƙƙin mata akan ɗaya daga cikinmu?. Annabi (S.A.W) ya ce. "Idan kaci abinci to ka ciyar da ita, idan ka ɗinka sutura to itama ka ɗin ka mata, sannan kuma in tayi maka laifi zaka bugeta, to kada ka bugeta a fuskarta kada ka munanata, idan zaka ƙaurace mata to kada ka ƙaurace mata a woje sai dai a ɗaki." (3) Kyakkyawan mu'amala. Shi mu'amala mai kyau babban abune ga ma'aurata. Especially shi miji, yana daga cikin haƙƙin mace akan mijinta, yayi mu'amala mai kyau da sakin fuska a tsakaninsu, raha da barkwanci ta yadda zasu shaƙu da junansu. Lallai waɗannan muhimman abubuwane da miji zai kiyaye su, kuma wajibi ne miji ya yawaita nasihi da wa'azi ga matarsa a kan harkar addini da sauran al'amuran yau da kullum sai dai a kula wurin nasihar da wa'azin kada ka tsananta kuma kada ka sake kwarai sabida sani yadda mata suke murɗaɗɗune sai anyi da lura. Duba da wani hadisin da Annabi (S.A.W) yana cewa a cikin hadisin da aka samo daga Abu Huraira inda yake cewa. Manzon Allah (S.A.W) yace: "Mafi cikar mumini a wajen imani shine wanda ya fiku kekkyawan ɗabi'a kuma zaɓaɓɓe a cikinsu shine wanda yafi Kyakkyawar mu'amala da iyalinsa. A wani hadisin kuma yace. Lallai ku sani cewa an halicci ƴa mace da ƙashin haƙarƙari ne bazata taɓa miƙewa gareka ba, wato ka sameta sak ba matsala, wannan kam bazai taɓa samuwaba in ka samu jin daɗinta to zaka samu jin daɗin ta ne a ƙarƙashin yadda take, (kuma ka sani in ka nemi miƙar da ita to tabbas zata karye. Karyewarta kuwa shine SAKINTA saboda haka sai kuyi taka tsan-tsan acikin lamuran."

Gyara zamanshi yayi da kyau, kana yasa hannunshi ya gyara gilashin fuskarshi da kyau, Sannan ya sa hannunshi zai ɗauki goran ruwan dake gabanshi. Da sauri ɗan agajin dake bayanshi ya ɗauki gorar kana ya buɗe ya tsiyaya mishi sassayan ruwan cikin kofi, kana ya miƙa mishi sannan ya koma inda yake ya tsaya.

Amsa yayi yasha ruwan sosai kana ya ajiye cup ɗin. Sunkuyar da kanshi yayi sosai sannan yasa hannunshi ya gyara hiraminshi ya rufe gefe da gefen fuskarshi.

Al'ummar jama'ar dake wurin kuwa kan sun nitsu sunyi shiru maza da mata manya da yara. Kab an zuba mishi idanu alamun ana dakonshi yaci gaba. Domin sosai walimar tayi armishi sabida dace da tayi da fasihin malami. Shiru kakeji sai sauti A\C dana numfarfashi. Aysha kuwa haka nan take jin wani irin mashahurin daɗi. Gaba ɗaya tsikar jikinta tashi takeyi, tana jin Allah yayi mata babban rahama da ni'imar duniya da bata Sheykh Jabeer a matsayin Garkuwan ta mijinta.

Da sauri ta ɗago kanta ta kalleshi lokacin da yaji yace.

(4) SADUWA DA ITA.

Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k Normal group 300. 0005388578 Jaiz Bank Aisha Aliyu Garkuwa. Ta nan zaki turo kuɗin, sai screenshort na shaidar biyanki ki turo min ta whatsapp 09097853276.

By *GARKUWAR FULANI* 3/23/21, 5:06 PM - ": Littafin nan na kuɗine, akwai Normal group 300 a wata biyu za'a kare Part 1 and 2, kiyi transfer'n dari uku ta asusuna na Jaiz bank. 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai kiyi screenshort na shaidar biyanki ki turo min ta whatsapp 09097853276. In Kuma special Group kikeso wanda a wata ɗaya za'a gama Part one, two. 1k zaki turo ta ac no ɗin nan 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number da nake whatsapp dashi 09097853276.

Akwai kayan gyaɗa na amareni uwar gidaye sitin hawa-hawa ne, akwai na dedai talaka akwai na masu hannu da shuni, in kina buƙatar saya kimin mgn ta whatsapp 09097853276.

Idonshi ya ɗan lumshe kana ya ɗanyi ƙasa da kanshi cikin nitsuwa yaci gaba da cewa. "Anan ana son miji ya dinga yin jima'i (Saduwa) da matarsa ko da sau ɗaya ne a cikin ko wanne tsarki ta, na Al'ada amman ƙaranci kada ya wuce wata huɗu ba tare da ya sadu da itaba kamar yadda wasu malamai suka faɗa, in bazai iya biya mata buƙatarta ba, kuma wannan za'a kauwacewa al'amarin jima'i kamar yadda al'ƙur'ani mai girma yace. (Allah yayi mgna game da mazajen da suke barin matansu basu kula su har tsawon wata huɗu kai harma suna ƙarawa da rantsuwa bazasu tara (Sadu) da suba, to idan daga baya sun dawo ga iyalan nan to shike nan Allah mai gafara ne mai jinƙai. Saboda haka idan muka dubi wannan ayar zamu fahimci cewa, idan miji ya bar matarsa tsawon wata huɗu bai sadu da itaba haka nan kawai ba tare da wani kyakkyawan dalili ba, to ya cuceta, kuma ana iya raba auren, Allah ya kiyaye.

Sai na (5) kiyaye mutuncinta kishi a kanta yana daga cikin mu'amala mai kyau tsakanin miji da mata ya zama miji ya kiyaye mutuncin matarsa da yin kishi a kanta, saboda haka wajibi ne ga miji yayi kishin matarsa ya kareta daga dukkan abinda zai taɓa mutuncinta da martabarta da dukkan abinda yayi kama da hakan domin mumini mai kishin gidansa ne, kamar yadda. Dabarani ya ruwaito daga Ammar Ɗan Yasir Allah ya ƙara musu yarda, cewa Manzon Allah (S.A.W) yace. Mutane uku bazasu shiga aljanna ba, 1 wanda baya kishin iyalansa 2 macen da take shigar maza, 3 wanda bai damuwa akan kowa da kowa ya shiga wajen iyalinsa. Sai Sahabbai suka tambayi Annabi (S.A.W) suka ce,. Ya manzon Allah shin dai bugegge sun san shi, to amman (Addayyus) wato mara kishi iyalinsa shine bamu sanshi ba. Sai Manzon Allah (S.A.W) yace musu. Shine wanda bai damuwa kowa da kowa kare da doki su shiga gidansa wato mutumin banza da wofi idan sun shiga gidansa baya damuwa. Shi wannan hadisin ya nuna mana cewa dole mu tsare mutuncin matanmu. Wannan kenan sune kaɗan daga haƙin mata akan mijinta.

Sai kuma haƙƙoƙin miji akan matarsa. (1) yin ɗa'a ga mijinta domin Allah ya faɗi a Suratul Baƙara aya ta 228. ( WA LIRRIJALI ALAIHINNA DARAJAH) Su maza sunada wata daraja a kan matansu. (2) Kula da dukiyarsa wajibi ne a kanki haƙƙine wanda ya zama dole mata su kiyayeshi Dole mace ta kula da dukiyar mijinta fiye da yadda shi zai kula dashi. Kamar yadda Allah Mai girma da ɗaukaka ya faɗa a Suratul Nisa'i aya ta 34. (FASSALIHATU ƘAANITAATUN HAAFIZAATUN LILGAIBI BIMA HAFIZALLAH) Allah ya ambaci salihai mata masu ɗa'a ga mazajensu masu tsoron Allah masu kiyaye abinda ke ɓoye na al'amuran mazan aurensu sobada Allah yace su kiyayeshi, kiyayewar kuma ta haɗa da tsare mutuncin kansu dana mijinsu ko yana nan ko baya nan. (3) Yiwa miji hidimar cikin gida kamarsu girki shara kula da yara da dai sauransu duk aikin macene. Kamar yadda Allah maɗaukakin sarki yace. (WALAHUNNA MISLULLAZZI ALAYHINNA BIL MA'ARUF) Mata suna da haƙƙi a kan mazansu kamar yadda suma maza sukeda haƙƙin a kan matansu. (4) ikon canza mata wurin zama daga wannan garin zuwa wancan gari. Kamar yana aiki a jihar Ɓadamaya sai aka canza masa wurin aiki zuwa Tsinako to yana ikon ɗaukarta daga can zuwa nan. Domin musulunci ya bashi dama kamar yadda Allah maɗaukakin sarki yace. (ASKINU HUNNA MIN HAISU SAKANTUM MIN WUJDIKUM WALA TU DARRUWHUNNA LITUDAYYIƘUN ALAIYHIN) ku zauna dasu inda kuke kada ku cucesu ku ƙuntata musu wajen zama. Idan muka dubi wannan ayar tana gargaɗin mazaje ne akan cewa kada ka sauya mata garin zuwa wani garin ya zama cutarwa a gareta. In taga cutarwa ne nan zata iya ƙin zuwa in ya matsa ta gayawa waliyansu. (5) kada mace ta shigo da wani mutun gidansu sai da izinin mijinta, domin wannan haƙƙine kuma damarsa ce. Numfashi ya sauƙe tare da kallon taron mazan kana yaci gaba da cewa. "A gurguje. (6) Neman izinin miji dan yin azumi. Baya halasta ga mace tayi azumi in dai na nafila ne sai tare da izinin mijinta matukar mijinnan yana gida tare da ita. Duba haɗisin daya gabata na haƙƙin maigida saboda haka ya zama dole mace ta nemi izinin mijinta kafin tayi azumi nafila amman banda na farillah". Haroon ne yayi wani irin murmushin jin daɗi kana ya kalli Jannart cikin raɗa yace. "Kinaji kina ɗauka kina fahimta ko?". Longoɓar da kai tayi.

Umaymah kuwa sai murmushi takeyi tana ƙara godewa Allah da samun Sheykh a ahlinsu. Mamma ma sai murmushi takeyi.

Jamil Jalal Azeez da Sadiq da Imran ne suka ɗan haɗe kansu suna ƴar hira ƙasa-ƙasa.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull