Kenza eBookz

Garkuwa complete Novel - Chapter 45

Garkuwa complete Novel - Chapter 45

Garkuwa complete Novel Chapter 45: Garkuwa complete Novel Chapter 45. Umaymah kuwa na ɗakin Ummi suna tattauna wata mahimmiyae mgna, sai ƙarfe sha biyu ta…

4,498 words

Umaymah kuwa na ɗakin Ummi suna tattauna wata mahimmiyae mgna, sai ƙarfe sha biyu ta shigo. Tayi mamakin ganin Aysha konce tana baccin. A hankali tace, uhum tana tashi zan kai maka ita tunda ka iya kora masu maganin ka kora sarkin bakan masarautar Joɗa kana ka kora wanda iyayenta suka zo dashi.

Daga nan taje tayi al'wala tazo ta kwanta.

A can wani yankin kuma. Sarkin baka ne da Ɗalhatu mai sa tayis ne, zaune su, suna musu bayanin duk abinda ya faru. Dariya tayi mai cike da jin daɗi tace. "Uhumm ai zanyi maganin ƴan iska watan cin uwarsune ya kama. Wannan shegen yaro Jabeer Allah ya sani bana ko son ganin fuskarshi. Duk sanda na ganshi sai inji zuciyata ta tsinke hankalina ya tashi. Ɗaya dake gefenta ne, yace. "Aini da inada dama da a daran nan zan kashe shegu gaba ɗayansu." Kai ta juya tare da cewa. "Uhum baka san rashin kunya da tijara da magangun da wannan matar tashi mai kama da aljana tayi minba ne. Shiyasa dole in taka mata birki zanci uwarta zata gane bata da wayo." Daya na gefenta ne yace. "Uhummm ni wlh da zan samu wutan zan bunkawa shegu duk su babbake". Nan dai sukaci gaba da yiwa Ahlin Sheykh tanadin mugunta.

A can cikin dajin kuwa zaune yake gaban bokanshi shi. Cikin hatsala yace. "Kace min abubuwa suna gabda nasara amman akwai tsaiko menene tsaikon gaya min shi in kaudashi". Dariya bokan yayi tare da zazzare idanu kana yace. "To ka dai san babban abunda ya hanamu nasara kan yaron nan, shine addu'o'in da yakeyi da yawan zama da al'wala da karatun al'ƙur'ani. To yanzu kuma na gano wannan matar tashi da aka aura mishi idonta a buɗe suke. "Akwai makaran gado, wanda sukeda ƙarfin iko, ko jiya wata cikinsu tazo tajamin kunnen kada in kuskura in cutar da ita. Sannan kuma akwai saurayi ta da ya raineta ya shirya mata jiki, kana tana iya gane sihiri a wuri duk ƙanƙantarshi. To in dai ba rabashi mukayi da itaba ko a kasheta ba tsira zamuyi ba. Kuma tana iya tona asirin kowa". Cikin tashin hankali yace. "Uhumm zata kuwa bar Masarautar Joɗa nan kusa. In kuwa ta nuna taurin kai tabbas zata bar duniyar nanda bada jimawa ba, bazan bar duk wani abun da zai shiga tsakanina da sarautar masarautar Joɗa ba". Daga nan sukaci gaba da tattaunawarsu.

Barun kuwa ana korashi ya nufi ƙasar Cameroon, Ba'ana bai iya jiranshi ba, tahowa yayi suka haɗu ya gaya mishi duk yadda sukayi da Sheykh. Nan suka sake komawa cikin Rugar tasu can inda ya samu sabon uban gida. Yanaji kamar ya mutu dan baƙin ciki. Nan yaci gaba da shirya yaƙan Sheykh.

A nan kuwa ɗakin Aysha. Ƙarfe ɗaya da rabi Aysha ta farka da salati a bakinta. Cikin sauri ta buɗe idonta. Tare da miƙewa a hankali ta nufi falon. Domin taji zogin na dawowa. Tazo falon kenan ta hango mutun da irin shigar ranan cikin tsoro tace. "Waye ne kai me kakeyi mana a nan?". Juyowa yayi ya kalleta cikin isa ya fara takowa zuwa gabanta. Da sauri ta fara jan baya-baya tana cewa. "Me hakan? Me kake nema damu?". Cikin Tsuke fuskarsa yace. "Me na samu dai. Ai Jahan tun kafin ya nemi abu yake samun abun a hannunshi". Da ƙarfi ta buɗe bakinta zata zurma ihu. Taku biyu yayi ana uku ya isota. Tafin hannunshi yasa ya rufe mata baki tare da cewa. "Kada ki razana wancan mataccen mijin naki". Wani irin zazzaro ido tayi tare da jujjuyasu cikin alamun firgici da tsoro da kiɗima. Kanshi ya jujjuya mata tare da cewa. "Kada kisa zuciyarki ta buga a banza dan nace wancan mataccen mijin naki. Ban kasheshi ba, amman dai ke a wurinki dashi da mace yar uwarki ba sauyi". Hannunta mai lfyar ta fara kiciniyar ɗagawa zata ture hannunshi da ya ɗaura kan bakinta, ya rufe, ya haɗa kanta kuma da jikin gini.

Juyota yayi da ƙarfi ya manna bayanta da ƙirjinshi still hannunshi na kan bakinta. Ɗaya hannun kuma, bisa ƙirjinta ya ɗaura.

Taku ya farayi yana janta ya nufi hanyar fita woje.

Wani irin bugu zuciyarta keyi tamkar zai faso ƙirjinta ya faɗo woje. Zuface ta tsananin firgita da tsoro ta karyo mata tako ina na jikinta. Tuni tsoro yasa numfashin ta ya fara subce mata. Kiciniyar kwace kanta takeyi ta samu damar yin ihun amman ta kasa.

Sabida ba ƙaramin riƙo yayi mataba.

Hannunshi dake kan ƙirjinta ya cusa cikin rigar ta saman wuyan rigar tata.

Wani irin azabebben cizo ta dartsawa tafin hannunshi, amman duk da haka bai janye hannun nashi ba. Sai ma lumshe idonshi yayi tare da jan dogon numfashi mai fitar da ɗimaucewar da yake ciki. Wani irin shafa yayiwa breast ɗinta, wanda yasashi rawan jiki bnnarsa tayi wani irin azabebben zabura da miƙewa gal. wani kiciniya ta fara da iya karfinta dai-dai lokacin kuma suka iso bakin ƙofar fitan

Hannunshi dake cikin rigarta ya zaro bayan ya burza nimple ɗin ta.

Murza key ɗin ƙofar yayi ya kana ya jawo ƙofar ya buɗe. Wani irin karkarwa jikinta ya fara, Garin son kwace kanta da neman taimakon kanta, ta buge hannunta mai ciwon jikin ƙofar.

Dai-dai lokacin kuma ya janye hannuunshi kan bakinta. Wani irin razanenne kuma gigitaccen ihu tasa mai sauti.

Shi kuwa Jahan da gudu ya fice kamar walƙiya.

Ita kuwa cikin karkarwa da tsoro da gigita ta juya ta nufi cikin falon tare da zurma wani ihun mai cike da kiɗima da azaba gaba ɗaya jikinta karkarwa yake.

Cikin bacci Umaymah da Ummi suka jiyo ihunta da rabka musu kiran da takeyi. A guje suka fito cikin ɗakunan suka nufo inda suke jin ihunta.

A bakin ƙofar suka haɗu cikin karkarwa ta faɗa jikin Umaymah tare da Ruggume ta da hannu ɗaya. Cikin kuka da fitan haiyaci take cewa. "Umaymah wani, Ummi yau ma ya sake shigowa, zai saceni ya jani har bakin ƙofa, kunga can ƙofar a buɗe ko. Wayyo Allah na, wayyo hannuna". Da sauri Umaymah ta ruggumeta gab zamewa tayi suka zauna a nan. Ummi kuwa hannunta mai ciwon da taga yana rawa tamkar mazari ne ta rinƙa hurawa iska tana cewa. "Sannu Aysha innalillahi sannu". Sai ta kuma fara kiran Sheykh. "Sheykh! Sheykh!! Sheykh!!!". A gigice ya buɗe ƙofarshi ya fito, ya nufi inda suke yana cewa. "Na'am! Na'am Ummi meya faru ne". Cikin gigita tace kalli fa. Dai-dai lokacin kuma numfashin ta ya tafi cak ta sume tana cewa. "Jahan wai zai saceni". Cikin gigita Umaymah tace. "Jazlaan ta suma, ta sumafa. Waye ne Jahan kagafa can ƙofar a buɗe". Hannunshi yasa ya amsheta jikin Umaymah dan yaga itama jikinta karkarwa yakeyi. Ruwan sanyin da Ummi ta miƙo mishi ya amsa, kana ya kurba a bakinshi ya fesa mata ruwan a fuska. Cikin wani irin jan dogon numfashi ta sa hannunta mai lfyar ta saƙalo wuyanshi, tare da ɓoye fuskarta cikin jikinshi tana cewa. "Zai saceni, ɗan iska ne shi". Ummi ce ta miƙe taje ta rufe ƙofar.

Shi kuwa Sheykh a hankali ya kalli Umaymah dake gigice yace. "Umaymah ki kontar da hankalinki, babu abinda zai samemu da izinin ubangiji. Kije ku kwanta. Ummi kuje, kwana kima tayi haka cikin Ramadan inaga al'janunta ne ke rikitata. Dan ranar da tace ta ganshi ya shiga Side na ba inda bamu dubaba ba kowa". Cikin kiɗima Umaymah tace. "Yau dai kam tabbas akwai abinda ta gani tunda harda suma kuma ga ƙofar a buɗe, Jazlaan na gaji wlh zaku bar Masarautar Joɗa ko zamu samu kwanciyar hankali a rayuwar mu". Cikin son kontar mata da hankali ya ɗan dafe kanshi kana yace. "To Umaymah zamu barta jeki kiyi al'wala kiyi addu'a Allah ya kare mu". Ya ƙareshe mgnar yana miƙewa tsaye da ita a jikinshi. Dan tayi mishi riƙon ɗaurin goro da hannunta mai lafiya.

A hankali Umaymah da Ummi suka juya suka tafi.

Shi kuwa Side ɗinsa ya nufa, kai tsaye. Har cikin Bedroom, maida ƙofar yayi ya rufe. Kana yazo kan gado ya sunkuyo ya kwantar da ita. Jin yadda ta riƙe mishi wuya ƙam-ƙam ne ya sashi cewa. "Zafa ki kasheni da shaƙa". Shiru tayi tana ƙanƙame da wuyanshi, hannunta sai karkarwa yake amman bata kuka alamun zafin yayi zafi tsananin yayi tsanani domin wani zafin ya wuce inda hawaye suke.

Dole a hankali ya zame wuyanshi kana ya zauna gefenta. Idonta suna buɗe amman sunyi masifar ja, goshinta sai zufa yake tsastsafowa. Numfashin ta wani na korar wani.

A hankali ya gyara zamanshi ya fara yi mata tofi yana karanta duk surar da tazo bakinshi.

A hankali hannun ya fara rage karkarwan. Tsawon miti talatin yana mata tofi yana jin tausayinta har cikin ransa ya dade yana mata tofin. Sannan ta iya juyowa ta kalleshi cikin rauni da zubda hawaye tace. "Yah Sheykh ka yanke min hannunan mana ko zan huta da azabar da nakeji in ya tashi". Ido ya ɗan zuba mata tare da cewa. "Kiyi bacci kinji ko?". A hankali tace. "Ina tsoronshi kar ya dawo". Cikin sunkuyowa yana kallon hannun yace. "Bazai shigo ɗakina ba. Ki dena tsoronshi babu abinda ya isa ya miki! Ki dena tsoronshi ko yaushe yana tare dake bai cutar da keba ki yarda dani". Cikin zubda hawaye tace. "Ɗan iska ne mugu ne". Cike da mamaki ya yamutsa fuska tare da cewa. "Ɗan iska kuma to me yayi miki na iskanci?". yunƙura tayi ta konta kan gefenta na hagu ya zama fuskarta na kusa da cinyarshi a hankali tace. "Tattaɓani yayi, yasa hannunshi har cikin". Sai kuma tayi shiru, cikin rumtse idonshi yace. "Cikin me?". A hankali murya na rawa tace. "Cikin rigata yana taɓa min". Fuskarshi a murtuƙe kamar zaiyi ruwan jini yace. "Meyasa kika tsaya har ya taɓa ki, kema iskancin kikeso ayi da keɗin inba iskanciba, ai hannunki ne ke ciwo ba ƙafarki ba, ki gudu mana". Juyowa yayi ya fuskanceta tare da ciwa. "Tukunma wanne iskancin ne ke fito dake da dare, in ba bikinku ba ɗaya ba, zakizo kina mana ihu da suman ƙarya ai so kike ayi ta taɓe-taɓe ko?. In tattaɓakin kikeso anayi ki gaya min mana ba sai in tattaɓakin ba hankalinki ya kwanta in miki abin da kikeso duka har sai kince ya isheki". Cikin zubda hawaye tace. "Ina gudu ya kamoni kuma na fitone zanzo kamin tofi a hannuna na haɗu dashi. Wlh ni dai ba yar iska bace. Inata ihu har na fame hannuna Ina kafin kukaji kuka fito". Wani irin kallo ya watsa mata ƙasa-ƙasa kana.

Ya juya ya kwanta, a haka sukayi bacci.

Washe gari da asuba kuwa. Ta koma ɗakinta tayi baccinta.

Shi kuma yana dawowa masallaci, yayi Azkar ɗinsa. Kana ya ɗauko gorar zam-zam. sannan ya ɗauki ganyen magarya guda bakwai, cikin wanda ya amsa wurin Gimbiya Aminatu tun jiya da yamma. Sa ganyen yayi a cikin gorar bayan ya ɗan sha ruwan ya rageshi.

Kasancewar bakin gorar nada ɗan faɗi.

Haka yasa ya zauna dashi bisa kan sallayarshi. Ayatul shifa ya fara karantawa yana tofawa cikin ruwan zam-zam da ganyen magarya guda bakwan.

Kulhuwa

Falaƙi

Nasi

Ƙuluhiya

Ayatul-kursiy

Amanar-rasuulu

Attaba'u ma tatlush-shayaɗeenu ala mulki Sulayman.

Ita kuwa Aysha a hankali taje tayi wonka bayan Umaymah ta haɗa mata komai na wonka. Koda ta fito kasa saka rigar tayi sai dogon wondon kawai ta saka. Ganin hakane yasa Umaymah ta miƙo mata rigar dama da ɗan madaidacin hijabi a jikinta. Da hannun hagu ta amshi rigar, ta tsaya tana kallon Umaymah. Ita kuwa Umaymah cikin bada umarni tace. "Kije Jazlaan ya saka miki rigar". Cikin sanyi tace. "Umaymah Hibba tazo ta saka min". Fuska ta haɗe tace. "Kije ya saka miki nace ko". Cikin sanyi tace to. Kana ta juya ta funi Side ɗinsa.

Ummi da Hibba da Saratu kuma suna Kitchen.

A hankali ta shiga falon.

Shiru tayi tana tunanin ta yaya zataje tace mishi ya saka mata riga.

Hakan yasa a hankali ta warware karin gugar rigar. Sannan tasa hannunta na hagun ta riƙe wurin zip ɗin, sannan tasa bakinta kuma ta riƙo wuyan rigar. Zut taja zip ɗin ta buɗe shi. Hannunta na hagu ta zura cikin hannun rigar. Sai kuma ta cireshi a hankali tasa hannun damanta mai ciwon a hankali. Ya zama rigar na kan kafaɗar hannun damar Tata. Shi kuwa Sheykh ya gama yin tofin, ya ɗauko goran ruwan ya nufi falon don zai maidashi cikin Fridge. A hankali ya turo ƙofar. Dai-dai lokacin ita kuma tasa hannun hagun nata mai lafiyar ta kamo hijabin jikinta ta ɗagoshi ta gaba zata cireshi. Ya zama daga ita sai dogon wondon, daga ƙugunta zuwa shafeffen cikinta da ƙirjinta dake cike tab-tab da jajayen Caɓɓule duk suna fili.

Wani irin ƙara tayi a hankali jin hijabin ya riƙo ɗan kunnenta yaja da ƙarfi. Da sauri tace. "Wayyo Allah na ya zanyi hannu mai ciwo hijabi ya riƙe ɗan kunne, riga bata shigaba". A hankali ta fara juyi tana kiran Ummi Ummi. sabida duk yadda ta motsa hijabin sai taji ya ƙara jan hujin kunnenta.

Yadda take taku tana juyi ne yasa jikinta keyin wani irin kaɗawa.

Shi kuwa Sheykh, wani irin masifeffen numfashin ya fixga da azaban ƙarfi. Rumtse idonshi yayi da sauri. Tare da juyawa ya fuskanci Dinning area idonshi a rufe. Yana jin tsikar jikinshi yana zubawa yana mummiƙewa. Zuciyarshi na harbawa a dubu. Yana isa ya ajiye goran kan Fridge ɗinsa. Sannan ya juyo da sauri.

Juyowar da zaiyi kenan yaji yayi karo da ita. Ta manna bayanta a ƙ....!

By *GARKUWAR FULANI*Bayanta da ƙirjinshi. Da sauri ta ɗan koma gaba tare da cewa. "Innalillahi". Sai kuma ta tsaya ta juyo ta fuskanceshi da kyau. Idonshi ya rumtse da sauri, Allah yasani bazai iya jurarar ganin waɗannan ababen ba masu masifar tada hankalin da gigita kwakwalwar ɗan adam.

Ido a rufe ya buɗi baki murya can ƙasan maƙoshi yace. "Me hakan?". Da sauri ta fara ja da baya tana cewa. "Ka tafi! Ka tafi!". Buɗe idon yayi a hankali kana yayi taku biyu zuwa uku ya kamota, a hankali yace. "Ke meyasa bakya nitsuwa ne akan komai! Yanzu a hakan ina zakije a tsiraranki". Ya ƙareshe mgnar yana sa hannunshi ya janye rigarta dake cikin hannun ta. A hankali hannunta na hagun ta zaro tare da rufe ƙirjinta da ko rabinsu bai rufuba. Cikin sanyi ya matsota da kyau, a hankali yace. "Me zakiyi ne?".

Murya a kunyace tace. "Zan saka rigatace kuma na kasa shine. Umaymah tace inzo in baka kasamin."

"Uhummmm". Shine abinda ya iya furtawa sabida ji yake kamar bazai iya mgna ba.

Ita kuwa cikin sauri tace. "Wash". Jin ya fara jan hijabin. Da sauri tace. "Kayi min a hankali kunnena".

Ba tare da ya sunkuyo ya kalleta ba yace. "Meya samu kunnen?".

Cike da kunya tace. "Hijabin ya sarƙafe min ɗan kunne".

Bai tanka mata ba, sai hannunshi yasa ya buɗa hijabin. Ya maidashi a hankali yasa yatsunshi biyu, yana cire ɗan kunnen.

Matsota ya kumayi, kana ya samu ya warware garkuwan ɗan kunnen daga jikin yadin hijabin. Sai kuma yasa hannunshi ya cire mata hijabin duka.

Ya zama daga ita sai wondon dake manne a jikinta.

A hankali ya sunkuyo ya ɗauki rigar tata, sannan ya juyo ya zama tanata cikin falon shi yanata baƙin ƙofar shiga, Yayi mata ƙawanya da jikinshi.

Idonta a sunkuye, hannunta na saman caɓɓullenta. Zura mata rigar yayi a wuyanta. Cikin nitsuwa ya buɗe hannun rigar na dama ya sakamata cike da takatsantsan. Sannan a hankali yasa hannunshi ya kamo hannunta na hagun ya saka mata hannun rigar.

Cikin hikima ya sake rigar tayi ƙasa, sannan a hankali ya juyo bayanta, dai-dai ta wuyan rigar yayi kana yaja mata zip ɗin. Ɗan sunkuyowa yayi ta kafaɗanta, ganin gaban rigar bai dai-dai-ta yadda ya kamata bane yasa a hankali yasa hannunshin cikin wuyan rigar. ciki da mamaki da tsoro ta rumtse idanunta. Shi kuwa hannunshi yasa ya dai-dai-ta caɓɓullenta cikin breastcub ɗin. Kana ya dauki ɗan kwalin ya ɗaura mata a kanta kamar mayafi kana ya juya ya nufi. Dinning area yana maijin wani irin yam-yam da tafin hannunshi ke mishi tun sanda ya taɓa caɓɓullenta, hannunshi yasa ya ɗauki goran zam-zam ɗin da ya mata addu'o'in karya sammu. Gabanta ya dawo, ita kuma tana ta son ɗaura ɗan kwalinta. Goran ya miƙa mata tare da cewa. "Gashi wannan shi zakisha duk sanda kikaji ƙishi. In kinsha kuma ki ɗan shafawa hannun ki mai ciwon". Cikin yin ƙasa da idonta ta amshi goran tare da cewa. "Ngd". Bai tanka mata ita kuma ta juya ta tafi.

A falo ta samu Ummi da Umaymah da Hajia Mama, suna zaune. Cikin wani irin yanayi ta kalli Hajia Mama kana tace. "Ina kwana". Fuska cike da fara'a tace. "Lfy lau. Alhamdulillah yau jiki da sauƙi ko?". A taƙaice tace. "E". Daga nan ta wuce. Hajia Mama kuwa Umaymah ta kalla tare da cewa. "Khadijah ya lbrin Auren Haroon ne Kam?". Ajiyan zuciya tayi tare da cewa. "To aure kam yazo ga mai nisan kwana". Bayan sallan layya da kwana goma za'a fara bikin".

"A lallai aure kam yazo ga mai nisan kwana". Hajia Mama ta faɗa.

Ita kuwa Ummi murmushi tayi tare da cewa. "Lallai jihar tsinako zata kwashi baƙi".

Nan dai sukayi ta hira.

Sheykh Jabeer kuwa. A hautsune ya koma bedroom, kan gado ya kwanta tare da yin rubd ciki. Idonshi ya rumtse da ƙarfi wai ko zasu dena harsasho mishi hoton abinda ya gani.

Kiran da akewa wayarshi ne ya sashi jan tsaki Karo na uku yanajin kiran yana shiga. Ya sani babu mai mishi wannan kiran mafarautan sai mutun biyu. Haroon ko Ahmad wani babban abokinshi ɗan kasar Cameroon.

Hannunshi yasa ya amsa kiran tare da danna amsa kuwa. Tsaki yaja jin Haroon na cewa. "Kai kace baka son yawan kira, in an kiraka sau ɗaya kuma baka ɗagawa dan wulaƙanci. Ni kuma gani Sitti ce ta buwayeni da in Kira mata kai taji lbrin jikin amarya." Cikin sanyi yace. "Yaushe kaje lamorde julɓe?".

"Yau kwana biyar".

A hankali yace. "Anya kuwa Haroon in kayi aure bazaka dena aiki ba".

Taɓe fuska yayi tare da cewa. "Babu mamaki in bar aikin ma inji da amaryata".

Ɗan gajeren tsaki yaja tare da cewa. "Bawa Sitti wayar".

Miƙa wa Sitti wayar yayi. Cike da kulawa da so tace. "Muhammad".

"Na'am Sitti ya gida".

Cikin kulawa tace. "Gida lfy lau. Ya jikin iyalin naka?".

A hankali yace. "Alhamdulillah".

Da sauri tace. "Muhammad yaushe zaka kawo min itane?".

"Nima ban sani ba". Ya bata amsa a gyatsine.

Murmushi tayi kana tace. "Shike nan zan zo ai".

Da sauri yace. "A a bance ba, ki bari in ta samu lfy zata zo". To tace tana murmushi tasan yasan in tazo tofa. sa'idonta yafi na akowa. Duk motsinshi zata gayawa Lamiɗo. Nan dai suka ɗan yi hira kana suka ƙatse kiran.

Da daren ranar kuwa koda suka zo konciya Umaymah tace. "Aysha tafi ɗakin mijinki kar hannun ya tashi dare-dare ya zama kina fita." A hankali tace. "Umaymah yau hannun da sauƙi tunda nasha ruwan addu'o'in nan bana jin zogin sosai".

Cikin jin daɗi tace. "To Allah yasa mu kwana lfy ba tashi". Amin Amin tace kana suka kwanta.

Allah cikin ikonsa da buwayarsa da al'farmar Annabi da al'ƙur'ani a daren sau biyu kawai ta ɗan tashi. Shima in Umaymah ta shafa mata ruwan dai sai ta koma bacci a take.

Washe gari da safe kuwa, Cikin mamaki ta kalli Umaymah dake shafa mata ruwan tace. "Umaymah bakiga kamar kumburin ya raguba".

Siyayan ruwan tayi a tafin hannunta tare da cewa. "Sosai ma kuwa Aysha hannufa Alhamdulillah da sauƙi sosai. Ga mgni kusa dake a bakin mijinki muje anyi ta wahala". Uhumm tace tare da sunkuyar da kanta.

Ummi kuwa Murmushi tayi.

Koda aka gama breakfast.

Ranar a haka a kaikacen ta daure taci. Kafin azahar sosai hannun ya lafa.

Yau kuma tunda safe ko inda hanyar Side ɗinsa yake bata kallaba, in taji zogin ta ɗauko ruwan tasha a shafa mata.

Shi kuwa Sheykh ranar tunda safe ya fita bai dawoba sai tara da rabi na dare.

Still yauma an kwana hannun da sauƙin.

Washe gari da safe.

Sheykh ya kuma ɗauko wani zam-zam ɗin da ganyen magarya guda bakwai, Yazo yana mata tofin cikin ruwan. Yana mgnar zuci. "Uhum jiki yayi sauƙi zamu huta da koken masifa da shogoɓar tsiya".

Koda ya gama yaje ya ajiye a Fridge kana yazo. Ya shiga wonka kasan cewar yau Monday ne tushen aiki ko nasara na tsoronta.

Ya fara kimtsawa.

Ita kuwa a falon bayan sunyi breakfast, suka dawo nan cikin falon, juyowa tayi ta ɗan kalli Umaymah dake shigowa falon tace. "Uhum Umaymah ruwan fa ya ƙare".

Shigowa tayi ta zauna gefenta kana ta kalli hannun ya saɓe sosai. "To kije ki gaya mishi mana, ai bai fitaba, tashi kije da sauri kada ya fita baki gaya mishi ba".

To tace kana ta miƙe ta nufi can.

Tana shiga yana fitowa. A hankali ta koma gefe ta tsaya. "Ina kwana". Tace mishi ido a ƙasa

Ta gefen idonshi ya kalleta tare da cewa "Lfy ya jikin?."

"Da sauki". Tace kana ta ɗan kalleshi tare da cewa. "Yah Sheykh!". Ido ya ɗan zuba mata kana yace. "Na'am!".

hannunta ta ɗan sa ta shafi fuskarta kana tace. "Uhum dama maganin nawa ya ƙarene shiyasa nace bari in gaya maka".

Hannunshi ya miƙo tare da cewa. "Inga hannun".

Ɗago hannun tayi ta miƙa mishi. Amsar hannun yayi kana ya juyo ya nufi tsakiyar falon. Tana biye dashi abaya. Bisa kujera ya zauna tare da nuna mata gefenshi. Zama tayi, duk yana riƙe da hannun, ɗan sunkuyowa yayi ya fara karanta Suratul Baqra yana tofa mata, yana sa yatsunshi biyu yana ɗan murza hannun a hankali-hankali, ido ta ɗan rumtse tare da motsoshi jin yana ɗan jan hannun.

Wash tace a hankali. Ɗan ƙara murza hannun yakeyi yana tofa mata. Hannun hagunta tasa ta damƙi damtsen hannunshi na dama. bai kulata ba yaci gaba da jujjuya mata hannun dan ya lura tana barin hannun a ƙage wuri ɗaya ko yaushe tana naɗe dashi. Murza hannun yakeyi da ɗan janshi yana miƙar dashi da ɗan ƙarfi. Wani irin bubbuga sawunta tayi tare motsoshi da kyau. Tsakanin sawunshi tasa cinyarta ta dama. kana tasa hannun hagun nata ta maƙaleshi.

duk ta kanainayeshi tako ina. zuface ta fara keto mata tako ina na jikinta, Ajiyan zuciya ta fara sauƙewa jin ya sake mata hannun.

Kanta ta manna a damtsen hannunshi tana maida numfashi.

Shi kuwa shiru yayi yana jin yadda take maida numfashi. Kusa 6 minute kana a hankali yace. "To ɗan sakeni in kin gama hutawa ko". A kunyace ta ɗan zame jikinta ta janye cinyarta.

Miƙewa tsaye yayi yana gyara al'kyabbar jikinshi. goran ya ɗauko a Fridge ɗinsa kana ya miƙa mata. Amsa tayi kana suka fito a tare.

Affan suka samu da matarsa Mami.

Suna fitowa Affan ya miƙa tare da miƙa wa Hamman nashi hannu bayan sun gaisane yace. "Ya mai jikin dai?".

"Alhamdulillah jiki da sauƙi". ya bashi amsa

Mami kuwa a hankali ta zame ta ɗan rusuna cikin girmamawa tace. "Barka da safiya Hamma ya mai jiki".

Hannunshi ya kai ya ɗan shafi kan ɗansu Karami Aliyu tare da cewa. "Lfy lau Alhamdulillah jiki da sauƙi. ya yaran?".

Suna lfy tace tare da kallon Aysha dake murmushi jin Affan na cewa. "Aunty Aysha ya jikin dai yanzu kam hannun bazai faɗi bako".

Murmushi tayi tare da cewa. "Alhamdulillah da sauƙi".

Sallaman su Umaymah Sheykh yayi ya tafi.

Murmushi Mami tayi cikin son matar Hamman nasu tace. "Ina kwana Aunty Aysha".

"Lfy lau".

"Ya jikin naki". Tace tana kallon hannunta.

"Alhamdulillah jiki da sauƙi sosai ma". Ta bata amsa. Tana zama kusa da ita, tasa hannun hagun ta amshi Aliyu wanda Dr Aliyu sukayiwa mai suna.

Affan ne ya ɗan kalleta tare da cewa. "My Aunty ga iyalin nawa. Ƙanwar Yusuf aboki nane yayar matarshi Zahra ce kuma."

Cikin fara'a da son Mami tace. "Ayyah yayi kyau Allah ya ƙara zaman lfy da zuriya mai Al'barka".

Murmushi yayi tare da cewa. "Amin tare daku, mu yanzu wannan na uku fa, ai munyi ƙoƙari ko Umaymah". Cikin dariya Hibba tace. "Kai Ya Affan abinma ƙoƙari ne kenan". Dariya sukayi duka kana sukaci gaba da hira. Aysha tana jin gamsuwa da gskyar Mami fiye data Aunty Juwairiyya. Ranan dai anan Mami ta wuni.

Haka dai taci gaba da amfanin da ayatul shifa da zam-zam da ganyen magarya.

Cikin ikon Allah da izininshi. Cikin kwanaki goma sha biyar hannun nan ya warke ya koma garau. Har tana shiga kitchen ayi aiki da ita.

Hakane yasa Umaymah ta fara shirye-shiryen komawa tana mai jin sanyi kaɗan a ranta.

Yau kwananta ashirin da zuwa, kuma yaune zata koma. To fa batun ƙomar da zatayi da Hibba ne yasa. Aysha taji babu daɗi.

Allah yasani ta saba da Hibba sosai. Ganin yadda ta koma ne yasa Umaymah ta ɗan zauna kusa da ita cikin lallami tace. "Kiyi haƙuri Aysha kinga badon makarantar Hibba ba dana bar miki ita. Yanzuma duk an gama mata komai na karatun zata tafi SS1 harma yan uwanta sun fara zuwa.

Kuma kema an kusa janye yajin aikin da University's Suka tafi, nayiwa Jazlaan mgna ana komawa kena zaki koma kici gaba da karatunki kewan zai ragun miki. Rafi'anki zata dawo itama". Cikin sanyi tace. "To Umaymah ki bar mana ita mana, sai in gayawa Yah Sheykh ya sama mata wata makarantar a nan". Murmushi Umaymah tayi tare da cewa. "Abbansu bazai yarda ba Aysha". Cikin sanyi tace. "Uhumm Allah sarki to shikenan Umaymah. Amman wlh gidan zai mana babu daɗi ko Ummi". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Gsky kam Aysha zamuji kewar Hibba".

Ita kuwa Hibba tana tsaye gefen Jalal ne. Da alamu wani abun yake nuna mata a wayarshi.

Jamil kuwa murmushi yayi tare da cewa. "Uhum in tayi tsami dai maji". Hararanshi Jalal yayi tare da cewa. "Namu ƙamshi zaiyi ba tsamiba, ko Hibba". Murmushi ta ɗanyi tana share hawayenta, duk da rarrashinta da yakeyi kan kada tayi kuka. Har yake nuna mata text message ɗin daya turawa Hamma Jabeer ɗin su cewa. "Yana son Hibba".

Kowa yasan Hibba na masifar son Ya Jalal ɗin. Duk abinda yakeyi burgeta yakeyi.

Tun yana kaucewa har dai shima ya gane yana sonta ne.

Shi kuma Jamil sarkin latsi yaje can yace, i love You yaje can ya kuma cewa haka har yau bai tsaida matsaya ɗaya ba. Kuma soyayya ta hanashi maida hankali kan aikinshi.

A hankali Aysha ta sunkuyar da kanta ganin hawayen Hibba na zuba.

Shi kuwa Sheykh Jabeer ido ya zuba mata.

Lokacin da taga Umaymah ta miƙe tace. "To Ummin Jabeer Allah ya sadamu da al'khairi".

Amin Amin Ummi tace cikin kewarta tun kafin ta tafi.

Hibba kuma ruggume Aysha tayi tare da cewa. "Aunty Aysha zanyi kewarki sosai". Ta ƙarashe mgnar murya na rawa. Tuni hawaye suka tsinkowa Aysha. Aunty Juwairiyya ma sai ga hawaye. cikin danne zuciya Umaymah tace. "Ha Juwairiyya harda ke a kukan so kuke in tafi nima ina kukan ko".

Kai Juwairiyya ta jujjuya.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull